matsayinta, bani da mutunci ko miskala zarratin kuma ban san hanyar in da mutunci take ba, dubeki wata a koɗe dake futu futu kin yi tsufar kokon giya, wlh na zabga maki mari idan baki mai da hankalinki ba, an gaya maki ruwa sa'ar kwando ce? Ke baki ga kalar ba? Na yi kala da waddan tsofaffin kokon giya zasu kawowa wargi ne? Yanzu zan sa ki gane annabi ya faku". Cewar Hauwa.
Yadda take magana tamkar wadda ake karantowa tana faɗa ko kuma wadda aka sanyawa battery, daga ji kasan wannan dama tun ainahi ƴar tijara ce, bala'i da masifa ya jima da samun matsuguni a wajenta.
Tsit maman Haidar ta nutsu, dama tsoron bala'i ke gareta, kawai dan sun rena maman Zainab ne yasa suke cin mutuncinta dai'dai gwargwado, amma banda haka mugayen matsorata ne, to yau dai sun sami dai'dai da su.
Maman Zainab kam sake baki ta yi tana ganin ikon god, ashe dama akwai abin da zai sanya maman Haidar yin shiru a duniyar nan? Wannan shi ne gaba ma da gabanta wai aljani ya taka wuta, duk iskancinta da balai'nta yau dai ga shi ta nutsu tsit ana kwashe mata albarka ba bakin tankawa. Babbar magana, ana dirama a cikin wannan gida.
Haidar dake a tsaye a bakin kofa ne ya yi kanta cikin fushi da nufin dukanta, a cewarsa bai ga dalilin da zai sanya ya tsaya wata ta tsaya tana gayawa mahaifiyarsa maganganu marasa daɗi son ranta ba.
Wani irin tsawa ta daga mashi wadda ya sanya shi jan birki babu shi, a walaƙance ta ce. "Dakata ƙaramin maras kunya, ai kai taka rashin kunyar nafila ce tun da iya nan gidan kawai ka iya baje ta, wlh idan ka yi kuskuren sanya hannunka a jikina duk danginka babu mai kwatarka, sai kun yi danasani mafi girma a rayuwarku".
Sai a lokacin baban Zainab ya saka baki a in da ya dakawa Haidar ɗin tsawa da ya fita mashi daga cikin parlourn ko kuma yanzun nan ya canza mashi kamanni. Babbar magana, a kan Hauwa fa babu abin da baban Zainab ba zai aikata ba, lallai akwai rikici ba kaɗan ba.
Ba ƙaramin kara tsorata su maman Haidar suka yi ba na ganin yadda baban Zainab ɗin ya hayayyako masu dan kawai Haidar ya yi yunƙurin taɓa Hauwa, yana gani Hauwar ta ci masu mutunci bai saka baki ba, amma daga za'a taɓata ya wani hayayyaƙo masu kamar zai cinyesu ɗanye, lallai akwai matsala babba ma kuwa.
Ita kam maman Zee komawa ta yi saman sofa ta yi zamanta tare da buga uban tagumi tana ganin wannan cakwakiya. Tatas baban Zainab da Hauwa suka yi wa su maman Haidar, daga karshe baban Zee ya koresu ma daga cikin gidansa, basu kuma da zaɓin da ya wuce su tafi, dan kuwa a yadda yake ɗin nan tsab zai iya yi wa mace ɗan banzan duka, Allah ma ya rufa asiri basu zo da hajiyarsu ba, abin ya tsaya a iya kansu kawai, ai da anyi ba daɗi.
Haka suka kwashi jiki cikin ruɗu tare da mamaki haɗe da tunanin baban Zainab kam anya lafiyarsa kuwa, a haka suka bar gidan suka nufi gidan Hajiyarsu, dan su sanar da ita halin da ake ciki.
Ita kuwa Hauwa bata bar wannan gida ba sai da ta tabbatar ta ƙunsawa maman Zainab abin da zai hanata yin barci a yau, sannan ta ce da baban Zainab su tafi. Shi kuwa bawan Allah kamar raƙumi da akala haka ya bita zalau zalau suka bar gidan kamar yadda suka zo.
Suna fita maman Zee ta rushe da wani irin kuka mai tsuma zuciyar mai sauraro, tun daga saman kujera ta zubo kasa saman gwiwowinta tana kuka, Khadija dake zaune komai ya faru a kan idanunta ne ta zo ta rungumeta tana rarrashinta ita ma kuma tana nata hawayen, abin gwanin ban tausayi.
🕊️🌼🕊️🌼🕊️🌼🕊️🌼🕊️🌼🕊️🌼🕊️🌼🕊️
Idan muka waiwaya Dubai kuwai.
GIDAN ABU ABDUSSALAM BIN BADEEN🔥🌼
Lest cut the story, tsawon wata guda Leesharh tana aiki a cikin wannan gida, amma kuma ko kusa ko alama bata samu ganin wanda ta zo aiki a kansa ba, wato Ramish kenan, bayan Ummie and Sharifa ma sai su Radia babu wani bakon fuska da ta sake gani a cikin gidan, abin ya ɗaure mata kai, ji take yi kamar ta tambayi su Radia ina Ramish yake kuma wanenen shi? Amma da yake bata saki jiki da su ba, bata shiga cikinsu, kuma tana tsoron su zargeta a kan wannan tambaya yasa ta ja bakinta ta yi shiru, kawai ta zubawa sarautar Allah idanu, amma kullum da wannan tunani take kwana, da shi kuma take tashi, ga wayar da aka bata kullum a kunne yake, amma babu wanda ya taɓa kiranta ko ya turo mata saƙo, waɗan da suka bata wannan aiki da alama sun san da cewa ganin Ramish da ido ma kawai ba ƙaramin aiki bane, shi ne yasa basu nemetaba tukunnan, da alama suna samun information a kan wani hali take ciki sosai ba tare da saninta ba, amma su waye masu basu information a kanta? Allah masani. ita dai a yanzu bata san a wani matsaya ma take ba baiwar Allah.
A bangaren shi kuwa Ramish yana nan a cikin gidan, sai dai samin damar ganinsa ne ba kowa ba, ko ita kanta Ummie tana fin sati biyu bata sanya shi a idanunta ba, ba wai kuma dan baya nan ba, no a cikin gidan yake kwana yake tashi, sai dai yadda kuka san wani aljani haka yake, tamkar yasan akwai mayunwatan kuraye dake farautar rayuwarsa a cikin gidan, bawan Allah nan baya tashi dawowa sai tsakar dare yake shigowa cikin gidan, duk balainka da nacinka baka isa kasan lokacin da Ramish yake fita ko yake dawowa ba, zaka iya zaman shekara guda a cikin wannan gida baka haɗu da shi ba, shi ɗin ba kamar sauran mutane yake ba, and kuma ba shi kaɗai bane, matasa ne su huɗu wadda dukkansu babu wanda ya kai 30 years a duniya, cikinsu kuma harda Rizwan yayan Yah Jawad, first born ɗin uncle Abbas kenan, amma fa dukkansu kafin ka samu damar ganinsu wlh kana iya fin shekara a cikin wannan gida, su ɗin ba mutane ne kamar kowa ba na gaya maku.
Wai wanenen Ramish? Bari mu ɗan ji wanenen shi kaɗan wata kila zamu iya fahimtar dalilin da yasa ake nemar rayuwarsa ruwa a jallo.
Ramish dai ɗan King Zuhair ne ba ɗan Abu Abdussalam bin Badeen bane, yayan gimbiya Aneesa ƴar mamace uwarsu ɗaya, wato ɗan mama ne shi kenan. Ramish fa Special weapons and tactics. Wato SWAT, kuma shi ne operation lieutenant ɗinsu gabakiɗaya. Special weapons and tactics, ku daga jin sunan special kun san they're special ɗin ne da gasken gaske, su ɗin wasu irin jami'ai ne da ake basu horo na musamman fiye da duk sauran jami'ai da kuka sani, saboda su idan ka gansu a waje ma to fa abu ya lalace, sai special waje ake turasu aiki, ba kamar jami'an air force, jami'an soja, jami'an ƴan'sanda da sauran masu kaki suke ba, no su they're very special, da farko kasar America ce ta fara kaddamar da Special weapons and tactics, daga baya sauran manyan ƙasashe ta duniya suka kwaikwayesu suma suka kaddamar da su, aiki suke yi kamar agogo, ga ɗan banzan fikira dake garesu, ga zafin nama, cikin ƙanƙanin lokaci suke aiwatar da duk abin da zasu yi, ba iya karfin dantse ne kawai suke da shi dan an basu horo na musamman ba, no su ɗin aiki suke yi da kwakwalensu cikin kwarewa tare da tunani mai zurfi, duk fa idan suka yanke hukunci a kan abu to ko gwamnati bata ja da su, domin ansan gaskiya ce, suna da uban tarin makiya ta gabas da yamma kudu da arewa, saboda sun yi aiki tukuru, sun kashe iyayen wasu, sun kuma jefa iyayen wasu gidan prison, su fa har manya manyan ƙusoshin gwamnati basu bari ba, duk wanda ya keto ta cikin aikinsu to ba makawa zai jisa a in da sai ya yi danasanin zuwansa duniya, wannan takaitaccen bayani ne a kan wanene Ramish, sauran bayanai ya biyo daga baya, kada ku manta shi ɗin jinin Modarawa ne, ɗa ne ga King Zuhair. To amma meyasa ake farautar rayuwarsu har haka? Lokaci ne zai nuna mana komai.
Ramish yana da kani mai suna Bilal wanda ya kasance yaya ne ga Gimbiya Chuchu uwarsu ɗaya, wato ɗan mummy kenan, Bilal air force ne shi, ba sai na tsaya yi maku dogon bayanai a kan su waye air force ba, kun san jami'ai ne da suke sadaukar da rayukansu a kan ƙasarsu, sun fi sojoji shiga haɗari nesa ba kusa ba, su ɗin jami'an sama ne, yakin sama ake turasu, jami'ai ne da ba kowa yake iya yin aikin da suke yi ba, jajirtattun ne kuma jarumai na gasken gaske. Bayan Bilal kawai Dr Raj wanda ya kasance shi ma ɗan mama ne, Kanin Ramish kenan uwa ɗaya uba ɗaya, shi kuma hamshaƙin Medical Dr ne, mutun ne shi da ya san aikinsa, baya kuma wasa da aikinsa, bama sai na ɓata bakina wajen gaya maku cewa yaran King Zuhair basu da wasa ba, ku da kanku kun san jininsu a tafashe yake, sun gada wajen mahaifinsu, Akka da take mace ma da yake jinin Modarawa ne ke gudu a jikinta ita ɗin ma, baku ganinta a zafafe take ne? Tana da zafin nama bare kuma su maza, sam basu da wasa ko kaɗan, kuma idan ka kuskura ka kawo masu wasa a cikin lamuransu yanzun nan zasu saɓa maka kamanni.
Rizwan kuma wato yayan Yah Jawad, kamshaƙin ɗan kasuwa ne wadda yake business tsakanin manyan kasashen duniya, yana da kamfanonin a ƙasashe daban daban, baya da ra'ayin siyasa ko sarauta, haka zali baya ra'ayin kaki, duk da cewa kowace irin kaki ya yi ra'ayi zai iya sanyawa ga jikinsa ya yi aiki, domin kada ku manta da muƙamin uncle ɗinsu wato uncle Abu Abdussalam bin Badeen, shiyasa su Ramish ɗin ma suke da manyan muƙamai a wajen aikinsu, kuma ya haɗu da basu da wasa, jajirtattu ne su ɗin. To shi Rizwan ya zaɓi kasuwanci ne abinsa, shi ne ra'ayinsa. Dukkan ƴaƴan King Zuhair idan ka kallesu ba sai an ce maka ƴaƴansa bane, akwai alamar kamanni ta jini a tsakaninsu, musamman Ramish da kaninsa Dr Raj, suna kama sosai, duk kuma kamannin Akka suka ɗauko, shiyasa suke sajewa da su Abu Abdussalam bin Badeen, sun zama dai duk iri ɗaya.
Wannan shi ne takaitaccen labarin waɗan nan zaratan samari na Abu Abdussalam bin Badeen wanda kuma ya renesu kamar wasu zakuna, suka taso a haka, tun suna kanana suke a hannunsa, shi kuma ƴaƴansa maza biyu basu a tare da shi, suna gidan the most powerful King Badeen, wato gidan mahaifinsa kenan, ƴarsa Sharifat ce kawai a gidan, sai Ummie, yana kaunar King Zuhair ne over, hakan yasa yake kaunar ƴaƴansa ma.
To mu koma kan labarinmu tun da kun ji su waye su Ramish, ɗan mama ne dai, mama sarkin masifa, ƴaƴanta maza biyu ne sai Aneesa ta uku, kuma ga duka yayan nata da Ramish da kuma Dr Raj ɗin duk a Dubai, amma a haka kullum take tsayar da bala'i a kan ita King baya yi mata adalci, ya fi son Momman auta, ɗan adam kenan, ba'a iya mashi, ita fa ƴaƴa maza manya har biyu ke gareta saɓanin Mummyn Gimbiya Chuchu da take da iya Bilal kawai, amma Mummy bata wani damu ba, ita kuma mama sarkin haɗama so take ace ita kaɗai ce take da ƴaƴa maza, kuma fa su Ramish ɗin nata sune manya a kan Bilal ɗin Mummyn Gimbiya Chuchu, idan ma mulki take so ai su zasu karɓi mulki, amma ita dai duk bai yi mata ba, sai ka rasa me take so a duniyar nan kuma, mummy ma fa tana da babban ɗanta na fari kafin Gimbiya Aunty MieMie wanda ya rasu, rasuwa ya yi shiyasa yanzu su Ramish sune manya a kan Bilal ɗinta da yake matsayin ɗanta a uku, sai Chuchu auta. Fatan dai kun gane?.
A kullum baza idanu Leesharh take yi tana tunanin ta in da zata kalli Ramish, amma shiru babu shi babu labarinsa.
Yauma dai kamar kullum, ta gama aikin gyaran parlourn ita da su Fadila da suka tayata, tana shirye cikin arab jallabiya ash color, ta yi kyau matuƙa, yanzu ta kara gogewa ta yi wani fresh da ita, ta kuma ɗan yi kumatu, amma kullum tana cikin zulumi tare da fargabar ya zata kalli Ramish? And ya zata kaya da wannan aiki da yau tsawon wata guda kenan bata fara shi ba? Yaushe zata kammala wannan aiki har ta koma ga mahaifinta?. Kullum tana cikin yin wannan tunani.
"Leesharh ki je ki gyara room ɗin guyson and na Aunty Sharifat bari mu kuma mu fara shirya kayan abinci kamar yadda muka saba". Cewar Fadila.
Da okey ta amsa masu tare da nufar room ɗin nasa, shi kansa Omar ɗin yau tsawon wata kenan bata samu damar ganinsa ido da ido ba, sai dai a wannan hoton, kuma kullum ita take gyara mashi room ɗin nasa, amma suna samun saɓani sosai da shi, wani lokaci sai ya fita take shigowa ta gyara ɗakin, wani lokaci kuma tana gama gyara ɗakin ta fita shi kuma zai shigo, Sharifat ta so ta haɗata da shi dan ya ga kyakkyawa, amma ina ba dama, dan kuwa bai zauna ba, yana shirye shiryen komawa KINGDOM OF POWER, so dayawan lokuta yana gidan King Badeen, yanzu bai cika zama a gidan Abu Abdussalam ba, shiyasa basu haɗu ba.
Room ɗin nasa ta nufa, hannunta na rike da mooper da abin share share. Duk da ta san cewa ba lallai ta sami mutun a cikin room ɗin ba hakan bai hanata ta yi sallama cikin sanyin murya ba. Tana yin sallamar kuma ta afka cikin room ɗin. A tsakiyar ɗakin ta ajiye kayan share share da goge gogen nata. Kai tsaye ta nufi saman katafaren bed ɗinsa na alfarma mai matukar girman gaske, room ɗin nasa ya ji komai na more rayuwa, sai tashin kamshi yake yi, ko'ina tsab tsab, amma a haka sai ta sake gyarawa ta goge ko'ina.
Jibgegiyar duv ɗinsa dake a saman bed ɗin nasa ta sanya hannu tana ƙoƙarin janyewa, domin ta cire ta canza mashi wani, kullum sai ta sake wani bedsheet ɗin, bata da tabbacin ana kwanciya a gadon ne ko ba'a kwanciya, amma dai kullum sai ta canza.
Tana ganyo duv ɗin mutun ya bayyana kwance a saman gadon, da yake duv ɗin yana da girman da idan mutun ya kule a ciki ma ba lallai kasan yana a cikin ɗin ba, ba zaka yi zaton akwai shi a ciki ba, shiyasa ta zo ta janye kawai.
Tana janyewa kuma kamar wadda aka yi wa allura ya fara mutsu mutsu haɗe da murkusoso kamar wadda yake shirin mutuwa, tamkar ana zare mashi rai, juyi ya fara yi a saman bed ɗin, jikinsa na a sanye da farar jallabiya tas da shi, farar kyakkyawar fuskarsa ta yi kal kal da ita, ya yi wani fayau, da kallo ɗaya zaka yi mashi kasan yana cikin mawuyacin hali, kyakkyawar arab hairnsa da ya zubo mashi har ta gaban goshinsa yasa ba'a ganin face ɗinsa da kyau, ga shi kwanciyar ruf da ciki ya yi, so ya bawa Leesharh ɗin baya, ko ba'a gaya mata wanene bane tasan shi ne guyson, saboda room ɗinsa ne, kuma tasan hotonsa, kullum idan ta shigo babbar parlourn da face ɗinsa take fara cin karo, yana sakin ƙayatatcen murmushi, so tasan shi ne.
Ganin shi cikin wannan mawuyacin hali ba ƙaramin ɗaga mata hankali ya yi ba, a razane ta zaro dara daran idanun nan nata tana kallon yadda take juyi kamar ba zai rayu ba, idanuwansa a rufe ruf, yama datse idanun nasa ne sosai tamkar zai fasasu, da alama yana jin tsananin azaba, kuma da alama ma baya a cikin hayyacinsa, sai wasu siraran hawaye da suke fita mashi daga idanuwansa suna bin gefe da gefen face ɗinsa, hakan zai kara tabbatar maku da yana cikin mawuyacin hali.
Sam Leesharh bata taɓa kallon irin hakan ba, hakan yasa hankalinta ya yi mummunar tashi, cike da ruɗu ta...........
🤍KADA KU MANTA WANNAN DADDAƊAR LABARIN DAGA ALKALAMIN FATEEMA ZAHRA MUSA A-K-A PRINCESS TEEMA TAKU TA AMANA YAKE🔥💘
Share fisabilillahi 👏
ALLAH KA KARA MANA SON MANZON ALLAH 🔥🤍
🤍🔥𝗥𝗔𝗪𝗔𝗡𝗜𝗡 👑 𝗭𝗔𝗟𝗜𝗡𝗖𝗜🔥🤍
🔥CROWN OF INJUSTICE🔥
𝗠𝗔𝗟𝗟𝗔𝗞𝗜𝗡
❤️🔥FATEEMA ZAHRA MUSA ❤️🔥
(❤️A-K-A 𝑷𝑹𝑰𝑵𝑪𝑬𝑺𝑺 𝑻𝑬𝑬𝑴𝑨🔥)
🔥🤍T🔥🤍T🔥🤍W🔥🤍......💻
❤️𝑫𝑨𝑻𝑬 26/8/2024.....✍️📚🌹
For more information 08161390581 Whatsapp me only!!.
🤍𝑺𝑻𝑬𝑷 1......✍️📚🔥
اللَّهُمَّ صَلِّ عَلَى مُحَمَّدٍ وَعَلَى آلِ مُحَمَّدٍ، كَمَا صَلَّيْتَ عَلَى إِبْرَاهِيمَ وَعَلَى آلِ إِبْرَاهِيمَ، إِنَّكَ حَمِيدٌ مَجِيدٌ، اللَّهُمَّ بَارِكْ عَلَى مُحَمَّدٍ وَعَلَى آلِ مُحَمَّدٍ، كَمَا بَارَكْتَ عَلَى إِبْرَاهِيمَ وَعَلَى آلِ إِبْرَاهِيمَ، إِنَّكَ حَمِيدٌ مَجِيدٌ❤️
E____________38🔥
*Assalamu alaikum everyone ina fatan kowa yana cikin ƙoshin lafiya?! Allah yasa! Ina yi wa kowa da kowa fatan alkhari tare da fatan kasancewa cikin ni'ima da kuma rahmar Ubangiji, a duk in da kuke Allah ya cigaba da dafa maku yana kara tsareku da tsarewarsa, Allah ya jiɓanci al'amuranmu bakiɗaya, ina matuƙar farinciki tare da godiya da irin tarin addu'oinku dana samu daga bakunanku masu albarka, na kuma ga tasirin addu'oinku wlh, Allah ya amsa jikina ya warware Alhdulillah, babu abin da zance maku face in ce Allah ya bar kauna ya kuma cikaku da farincikin da babu bakinciki a bayansa, arxikin da babu talauci a bayansa, daga karshe Allah ya bar kauna ina godiya 💘 taku PRINCESS TEEMA ta amana✍️💘*
E____________38🔥
Sam Leesharh bata taɓa kallon irin hakan ba, hakan yasa hankalinta ya yi mummunar tashi, cike da ruɗu ta kai hannunta ta mayar mashi da duv ɗin da nufin ta gudu ta fice daga room ɗin kada ace ita ta yi mashi wani abin, kunsan maras gaskiya da shegen tsarguwa, sai yaga kamar komai ƙanƙantar motsi idan ya yi asirinsa zai iya tonuwa.
Sannan kuma kunga tana janye mashi duv ɗin ne ya fara wannan murkusoson, so sai tana ganin kamar za'a ce ita ce sila.
Har ta juya zata fita ta tsinkayo zazzaƙar voice ɗinsa ya daki dodan kunnuwarta, idanunsa a datse gam yana ruwan hawaye, voice nasa ɗan siriri kamar na mata, ga shi cool voice gare shi sosai, akwai daɗin saurara, bare da ya haɗu da yana cikin ciwo, sai maganar tasa tana fita wani iri.
Cikin harshen larabci ya fara faɗin. "Shareee.... Shareee zo ki bani drugs ɗina, kada ki kira su Ummie kin ji?". Yana magana ne a tunaninsa Sharifat ce, da alama ya ji shigowarta kenan.
Kamar zata gudu, dan tana tsoron kada ace ita ta yi mashi wani abin, bare kuma yadda ta ji kowa a gidan yana yawan maganarsa tasan tabbas ɗan gata ne da ake ji da shi, to tana tsoron kada wani abin ya haɗasu tun bata fara aikinta ba ta shiga uku. Amma kuma tana da tausayi da raunin zuciyar da ba zata iya tafiya ta barshi a cikin wannan hali ba.
Juyowa ta yi a hankali tare da kai kallonta saman gadon, har lokacin yana murkusoson nan dai yana ambatar sunan Sharifat come and give me my drugs. Shiru ta ɗan yi tana tunanin Sharifat dai bata nan, tana school, koda kuma tana nan ita a ina tasan zata nemota a cikin wannan gida har ta kira mashi ita? Yau watan ta guda kenan a gidan idan ba time to time ba ko Ummie bata wani samun damar gani sosai a wannan hawa da suke, Sharifat ɗin ma ita take zuwa in da suke dan ta ce Leesharh na yi mata kyau, yarinyar tana da saukin kai, so ita take zuwa wajen Leesharh ɗin ta ce ta zo su ɗan yi hira, Leesharh ta bata labarin ƙasarsu, so dani da ku duk mun san a kan dokar da Leesharh ɗin take na ja mata kunnuwa da aka yi a kan kada ta yarda ta yi hira da kowa, hakan yasa bata taɓa yarda ta saki jiki da Sharifat ɗin bare ma har su yi hira, bata yarda da hakan, sai dai ta yi shiru.
Idan Sharifat ɗin ta ce mata to ki yi magana mana, sai ta ce ai bata san me zata ce ba, murmushi kawai Sharifat take yi ta ce na lura baki da yawan magana amma zan koya maki, iya murmushi kaɗan kawai take yi daga haka bata sake yin magana, to haka suke rayuwa a cikin gidan, Leesharh tana yawan janye jikinta ga mutane sosai, bata taɓa yarda ta buɗe baki ta yi magana, izuwa yanzu voice ɗinta ya koma yadda yake sosai da sosai, maganarta na fita da kyau da kyau, tana da daɗin murya sosai, ta gama shanye magungunan da Dr Suhail ya bata.
Sanin cewa ba zata sami Sharifat bane kuma tana da zuciyar tausayi sosai, ta ji ba zata iya guduwa ta bar shi a cikin wannan mawuyacin halin ba ne yasa ta juyo da sauri ta dawo wajen bed ɗin. Kaɗan ta sake janye duv ɗin kasa. Sosai da sosai yake kuka, har wa lokacin kuma idanuwansa a rufe ruf.
Matsowa kusa da shi kaɗan ta yi tare da duƙowa kansa, cikin kwararriyar laraɓcinta tare da yi mashi magana ƙasa ƙasa a tawajen kunnuwansa ta tambayi ina magungunan nasa suke?.
Duk da yana cikin raɗaɗin ciwo hakan bai hana ya gane cewa wannan ba voice ɗin Sharifat bane, hakan yasa ya ɗan yi jim kaɗan kafin kuma ya ce. "Who're you?".
Dum dum ta ji gabanta ya bada bugu, sai ta ji ta yi nadamar zuwanta wajen nasa ma, a cewarta da ta gudun kawai abinta, ta tsorata sosai saboda bata kullo gaskiya ba. Kai ya Allah kasa mu kasance masu gaskiya a duk in da muke, rashin gaskiya bai yi ba, domin kuwa idan baka da gaskiya ka rinƙa shiga fargaba da faɗuwar gaba koda sunanka kawai aka kira a waje, duk karasa sukuni ka takura kanka, ka rasa walwala ka kasa iya rayuwa kamar kowa, koda iya wannan kawai aka barka kana cikin masifa wlh, jama'a mu riki gaskiya da amana domin samun rabauta duniya da lahira!!.
Jin ta ɗan yi shiru ne yasa ya sake maimaita mata tambayar da ɗan kausasshiyar murya tare kuma da fara ƙoƙarin buɗe idanuwansa da suka yi mashi tsananin nauyi saboda ciwo, ga kuma kukan da ya sha, har wani sara mashi kansa yake yi.
Ƙoƙarin juyawa ta yi dan ta gudu, a shirmenta zata je ta tonawa kanta asiri, ko me abin guduwa a wajen oho, ta tsargu ne.
Bata bar wajen ba ya damko hannunta da ɗayar hannunsa tare kuma da ƙarisa waro waɗan nan manya manyan idanuwan nasa masu kama da na Auta Gimbiya Zunaira.
Idanun nasa sun yi jajir da su kamar wuta saboda kuka. Nutsuwa ta yi tsit tare da sunkuyar da kanta ƙasa, tsoro ne karara a saman face ɗinta, sai dai hakan bai hana ta rinƙa satar kallonsa ta ƙasan ido ba, kullum ma idan ta shigo babbar parlourn sai ta yi ta karewa hotonsa kallo, yana yi mata kyau sosai da sosai, bare ma iya ɗaukar wankarsa, guy ne sosai, in dai ɗaukar wanka ne to daga kansa an rufe kofa, gwani ne, kowani irin kaya ya saka zama mashi suke yi ɗas a jikinsa kamar dan shi aka yi su.
"Who're you?". Ya sake tambaya yana ciza laɓɓansa, alamar yana jin azaba. Ga hawayen kuma suna cigaba da wanke mashi fuskarsa.
Cikin in'ina ta gaya mashi wacece ita da kuma matsayinta a cikin wannan gida nasu. Sake mata hannunta ya yi tare da mayar da idanunsa ya datsesu gam. Shiru ya ɗan yi na ƴan sakani kafin ya ce ta buɗe drawers ɗinsa ta ɗauko mashi drugs ɗinsa and bottle water mai ɗumi ba mai sanyi ba.
A hanzarce ta amsa mashi da okey, har lokacin jikinta yana ɗan kerma ta fara bubbuɗe drawers ɗin, dan bai gaya mata a cikin wanne drawer magungunan suke ba, ya
All Chapters
Chapter 1
Chapter 2
Chapter 3
Chapter 4
Chapter 5
Chapter 6
Chapter 7
Chapter 8
Chapter 9
Chapter 10
Chapter 11
Chapter 12
Chapter 13
Chapter 14
Chapter 15
Chapter 16
Chapter 17
Chapter 18
Chapter 19
Chapter 20
Chapter 21
Chapter 22
Chapter 23
Chapter 24
Chapter 25
Chapter 26
Chapter 27
Chapter 28
Chapter 29
Chapter 30
Chapter 31
Chapter 32
Chapter 33
Chapter 34
Chapter 35
Chapter 36
Chapter 37
Chapter 38
Chapter 39
Chapter 40
Chapter 41
Chapter 42
Chapter 43
Chapter 44
Chapter 45
Chapter 46
Chapter 47
Chapter 48
Chapter 49
Chapter 50
Chapter 51
Chapter 52
Chapter 53
Chapter 54
Chapter 55
Chapter 56
Chapter 57
Chapter 58
Chapter 59
Chapter 60
Chapter 61
Chapter 62
Chapter 63
Chapter 64
Chapter 65
Chapter 66
Chapter 67
Chapter 68
Chapter 69
Chapter 70
Chapter 71
Chapter 72
Chapter 73
Chapter 74
Chapter 75
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 53 Chapter of 75