kamar Auta ta sanya hannu a kai ta kurma ihu. Faɗawa jikin Yah Jawad ɗin ta yi tana ɓoye fuska tare da fara yin hawayen gaske, dan ranta ya ɓaci sosai, Chuchu ta kureta.
Wani irin kallo mai wuyar fassaruwa Yah Jawad ɗin ya jefawa Chuchun kafin ya sassauta muryarsa kasa sosai. "Me kika yi mata Jannat?".
Da sauri Autar ta ce. "Babu abin da ta yi mun Yah Jawad". Tana magana tana goga kanta a kirjinsa.
Izuwa yanzu ya fahimci abin sirri ne a tsakaninsu Chuchu take yi mata wasa da hankali take kuma sanyata kuka a banza. Dan haka sai ya ce. "Shikenan our Auta, jeki abinki yanzu zan bata punishment ba tare da na ji ma me ta yi maki ba". Ya yi maganar yana shafa kyakkyawa arab hairnta da ko ɗankwali bata ɗaura ba ta shigo room ɗin na Chuchun a ruɗe, dan a tunanin wani abin ne ya sameta.
Da sauri ta raba jikinta da na shi tare da nufar hanyar komawa room ɗin na Chuchun rike da pillown tana faɗin. "Allah Aunty Chuchu ba zan yafe ba idan kika gayawa wani".
Juyawa da gudu ita ma Chuchun ta yi da nufin ta bi bayanta dan ta ji Yah Jawad ɗin ya ce zai bata punishment, ba zata iya ɗaukar punishment ɗinsa ba.
Aikuwa bai bari ta bar wajen ba ya yi saurin riƙo hannunta tare da janyota ta dawo in da take tsaye ta tsaya. Ƙasa da murya sosai ya yi kamar wani na yi mashi laɓe, kamar kuma maras gaskiya ya fara magana, ita kuma Auta ta yi tafiyarta sai kumbure kumbure take yi.
"Me kika yi mata? Meyasa zaki saka mana ita kuka?". Yana magana yana kallon cikin kwayar idanunta, while ita kuma tana ɗan satar kallonsa ta wani yi ƙasa da kai kamar wata mai ɗaukar darasin hadisi a islamiya!.
"Babu fa komai Yah Jawad". Ta faɗa a sanyayye.
Shiru bai sake yin magana ba, domin ya shagaltu da kallonta, gaskiyar uncle Abbas da King da suke cewa in dai zai haɗu da chuchu sai ya karewa ƴarsu kallo tsab sannan yake kama kansa, ashe dai sun san komai.
Jin ya yi shiru bai sake yin magana bane yasa ta ɗago ido dan ta ɗan saci kallonsa. Ai kuwa tana ɗagowa suka yi four eyes.
"Yah Jawad in tafi?". Ta faɗa ba tare da ta kawar da kallonta daga saman fuskarsa ba, sai dai ba kallon cikin kwayar idanunsa take yi ba.
"Ban gama kallonki ba ai my Jannat". Ya faɗa ba tare da yasan lokacin da hakan ya fito daga bakinsa ba, sai da ya ji ta ce. "Kallona kuma Yah Jawad? Na yi kyau ne?".
Nisawa ya yi, kamar mai jin barci ya furta. "Over ma kuwa kika yi kyau".
"To Yah Jawad ka mun hoto". Cike da zumuɗi ta yi maganar.
Wani irin cool ajiyar zuciya ya sauke tare da ciro wayarsa ɗayar. "Where's my other phone da na baki jiya?".
Sai a lokacin ta tuna da wayar. "The phone is in my room, in je in kawo shi yanzu?". Murya a warware ta yi maganar.
Girgiza mata kai kawai ya iya yi alamar a'a, bai iya sake furta komai ba sai matsowa da ya yi kusa da ita tare da shiga camerar wayarsa, sannan ya ɗaura hannunsa ɗaya a saman shoulder ɗinta. Zafafan hotuna ya fara ɗaukarsu, ita da ta ce ya ɗauketa ita kaɗai ya ɓige da ɗaukarsu a tare.
Sai canza style suke yi sun manta da cewa a parlourn King fa suke, ga shi yau King yana da baki sosai saboda zuwan su Ramish da za su yi gobe, jama'a suna ta kai koma a part ɗin, already kun san dama akwai part na saukar muhimman bakinsa na kusa sosai a cikin part ɗin nasa, so su Jawad suna tsaye ne a tsakanin wannan ɓangare na saukar bakin da kuma hanyar nufa master room na King.
Canza style ya yi daɗi harda kwanciya a saman kirjinsa ta yi, yau abin nema ya samu, Chuchu mayyar ɗaukar hoto, to ga dama ya samu, mai hanata ɗaukar hoton ya takura mata yau da kansa yake ɗaukarta, ai style kuwa sai abin da kuka gani.
Suna tsaka da kashe hotunansu basu ankareba kawai sai tsinkayo muryar Akka suka yi a cikin kunnuwansu tana sababi, ta nufo parlourn ɗin ne tana ta surfa sababi da masifa, da alama wani ya taɓota. Tun daga nesa take faɗin. "Ai Zuhair shi ne ya mori aure, ku cigaba da yi, har ku kwanta a gadon ajalima kada ku dai'na, yo ni idan baku yi haka ba ai sai nace sam sam Zuhair ba mata ya aura ba, kuma idan baku yin haka ai sai na sa a bincika mun ku ko da wata munafurcin a ƙasa, dan cikakkun mata kam dole sai sun ɗana wannan kishi, shi kuma Abbas ba yadda ban yi da shi ba dan ya ƙara aure ya ji daɗin aure amma yaki, shi sam ba aure ya yi ba, dan idan baka haɗa mata biyu a gida suna nuna kishi karara kamar dai matan Zuhair suna faɗa a kanka ba to ba aure ka yi ba, ku ta yi abinku shi ne dai'dai, wadda ta fi sanin kan duniya ta kwace Zuhair ɗin ya tattare a wajenta". Sai sababi take yi.
(Jama'a kun ji mun wannan tsohuwa da bala'i 🤔 ita fa har dattijon arzikinta wato mijinta King Abdul Malik ya kwanta dama ita kaɗai ce matarsa, bata da kishiya, amma take cewa uncle Abbas ya karo aure, Akka sam bata son zama lafiya, ga rikicin tsufa, mata suna faɗa tana kara hura wuta 😅)
Jin motsinta tana surfa wannan uban sababin yasa Jawad yaja hannun Chuchun da sauri suka haura izuwa master room na King, domin idan ya bari Akka ta kama shi da Chuchu a ɗan wannan lungu to fa ya shiga uku, ai ta rinƙa takurawa rayuwarsa kenan, idan ma bata ce zai lalata mata jika ba, dama kun san ba shiri suke yi ba, kullum cikin faɗa da samun saɓani suke, kuma idan baku manta ba Akkar ta sha shiga tsakaninsa da Chuchun tana rabasu faɗa, so tasan basa shiri sam sam, yanzu kwatsam ta gansu a tare a wannan ɗan hanya na zuwa master room ai shikenan ya shiga uku a cikin wanna kingdom ɗin, ba zata barshi ya zauna lafiya ba, kuma abin da yake gudu na kada Jaish ya san halin da ake ciki na tsakaninsa da Chuchun fa to sai ya sani idan Akka ta gansu, bugu da kari Mammiensa ma sai ta sani, kuma ɓoye mata yake yi dan yasan bata son alƙarsa da ƴaƴan King Zuhair, shi kuma a part ɗin ya taso ya girma, ya fi sabawa da su fiye da ƴan uwansa su Sarina ɗin ma, amma bai san dalilin Mammaien ɗin tasa na bata son taga yana alaƙa da ƴan uwan nasa ba, jini ɗaya suke amma tana son raba jini da karfi da yaji.
Kai tsaye room na King suka nufa da gudu, wajen hawa ƴan ƙananan stage da suke a bakin kofar room ɗin na King Chuchu ta yi tuntuɓe ta faɗi, gudun da suke yi ne yasa bata lura da sun iso wajen ba.
Cak Yah Jawad ya ɗauketa suka ƙarisa shiga room ɗin. A lokacin da suka shigo kuma King yana wanka, bai jima da dawowa daga masallacin jumma'ar ba, so shi dama kayansa na zuwa masallaci daban suke da sauran kayansa, saboda daraja da girma da yake bawa ranar, a ranar kwalliya na musamman yake yi, saboda jumma'a babbar rana ce, kayan zuwa masallacin nasa ma na musamman ɗin na musamman ne, idan ya dawo daga masallacin kuma yana yin wanka ya canzasu izuwa wasu na musamman ɗin dan komawa fada ya zauna zuwa yamma irin karfe 5 ɗin nan bayan sallar la'asar kenan, sai a fita yin wannan gasa tasu da suke yi.
Coz yau ba zuwa fada zai yi ba, saboda abin da yake faruwa da Mama, yanzu haka idan ya yi wanka ya shirya wajen Mamar zai wuce, domin idan bai yi haka ba sai ta ce bai yi mata adalci ba, idan Momma bata da lafiya ko Dubai ta koma can yake tarewa, kunga kuwa idan yana son zaman lafiya dole ya zauna kusa da Mamar ma, idan ba haka ba a tashi gidan gabaɗaya da ruwan bala'i......... 😅
Akka dai ta ce idan basu yi haka ba to ba mata Zuhair ya aura ba, da alama fa Akka tana jin daɗin wannan diramar tasu, suna ɗebe mata kewa.
Ganin cewa King na cikin toilet yana wanka, ga kuma Akka a bayansu tana zuwa yasa Yah Jawad ɗin ya sauketa a tsakiyar room ɗin saman shinfiɗar tsakiyar ɗakin, sannan ya riƙo hannunta da sauri suka faɗa cikin dressing room na King. A bayan wajen glass na jera watch ɗinsa suka tsaya suna mayar da numfashi.........
Akka kuwa cikin room ɗin ta shigo tare da zama saman shinfiɗar King ɗin in da yake zama ya huta. A nan ta zauna tana jiran ɗan nata ya fito daga wanka, da alama su Momma sun bakanta mata rai ne yasa ta nufo wajen King dan su yi magana, har ta zauna saman wannan sofa da aka kawata da shinfiɗu na alfarma na gashin jimina bata dai'na zance su Momma ba, sai sababi take yi, aikuwa Allah ya rufawa Yah Jawad asiri, dan a yadda take kan tsini tana surfa sababin nan ta gansu shi da Chuchun a yadda suke ɗin nan ai shikenan rayuwarsa tana kwale kwale, dan ya shiga talatin ma ba uku ba.
Ni kam na ce to su yanzu da suka shigarwa King cikin dressing room ɗinsa ku gaya mun idan ya fito daga wanka zai sanya kaya ya kenan?.🤔 Ya zasu yi idan zai shigo sanya kayansa?🤔 Ga dai Akka a cikin ɗakin, King kuma zai shigo nan, my people's kuna ganin a gudun nan da suka yi sun tsira kuwa?🤔 To ni dai bari na leƙa Daular Abu Abdussalam wato Dubai in dawo, sai naga zasu tsira ne ko asirinsu zai tonu.
Abu Abdussalam empire🤍🔥
LEESHARH....✍️💘
A hankali ta ɗan waro idanun nata waje, from down ta fara kallonsa, a maimakon ta ɗaga idanu ta kalli face ɗinsa, sai ta fara kallon kafafunsa da suke sanye cikin cover shoe masu kyau da tsada launin baki. In a slow ta fara ɗaga idanunta tana binsa da kallon from down ɗin har up.
A tsananin razane ta miƙe tsaye tana zaro idanu waje kamar za su faɗi ƙasa. Domin kuwa a karya na idanunta face ɗin Ramish yake nuna mata, shi ya yi mata gizo a kan fuskar guy ɗin, wannan guy ɗin daban, amma da yake tunanin Ramish ne a ranta sai take ganin kamar shi ne.
Cikin harshen larabci wannan guy ɗin ya ce mata lafiya ta yi irin wannan miƙewa haka? Meyasa kuma ta tsorata da ganinsa? Ko dai ta san shi ne?. Bai san cewa face ɗin Ramish ta gani a tattare da shi ba. Wannan magana da ya yi ne yasa ta dawo cikin hankalinta, nan take idanunta suka kallan mata ainahin kamannin guy ɗin wannan da yake cikakken arab men, fari tas da shi kuma kyakkyawa.
Miƙa mata handkerchief ɗin ya yi yana mai sake ce mata lafiya take kuwa?.
Bata karɓi handkerchief ɗin ba sai dai ta raɓa ta gefensa da sauri domin ta wuce. A dai'dai lokacin kuma Guyson ya iso waje, zai je duba Yah Ramish da ya ki halartar taron ne, zai wuce sai ya hangota tana kuka, shi ne ya ce bari ya ƙariso ya ji me ya sameta ko dan Sharifat sai ya kulata.
Ganin Guyson a gabanta yasa ta ja birki tare da sanya hannu ta hau goge hawayen face ɗin nata da sauri sauri.
Wani irin kallo Guyson ɗin ya bi matashin da ya miƙa mata handkerchief ɗin nan da shi kafin ya ce da shi. "Meka yi mata?". Cikin harshen larabci ya yi maganar. Yadda ya yi maganar kuma sai ka rantse da Allah Bilal ko Ramish ne suka yi maganar, ya yi maganar a dake irin babu wasa a tattare da shi ɗin nan, ya yi ta kuma yana ɗaure fuska sosai.
Kai kai kai, Guyson fa akwai madarar kyau kam, kamar Gimbiya Zunaira yake, sai ma daya haɗe rannan, sai kyan ta kara bayyana so masha Allah, kamar ka yi ta kallonsa ba gajiyawa, da ya ɗaure fuska sai ga shin gerarsa suka haɗe waje guda, hakan ba ƙaramin kara tsatso mashi kyansa ya yi ba, waɗan nan fararen idanun nasa idan ya zaro maka su sai ka gudu saboda girma ga kyau.
Cikin girmamawa wannan matashi ya amsa mashi da babu abin da ya yi mata, haka ya iskota tana kuka shi ne yake rarrashinta. Da alama wannan matashi yasan Guyson sosai duba da yadda ya bashi amsa cikin girmamawa.
"Leesharh meyasameki kike kuka?". Ya yi tambayar yana maido da kallonsa a kanta.
Tana kan goge hawayen da suka ki dagatawa da zuba, ta ruɗe ta rasa wani amsa zata bashi. Shin ta ce mashi kewan babanta ne yasa take kuka ko yaya? Amma idan ta ce mashi kewar babanta ne zai iya sanyawa ya ce a kaita wajen baban nata ta gansa sai a dawo da ita, to a ina zata ga baban nata kenan? Ta sake jefawa kanta tambaya, ta rasa me yakamata ta ce mashi, tasan ƙaramin aikinsa ne duk abin da ta ce ga shi shi ya sakata kuka shi kuma ya ce a nemo wannan abin, ya zata yi kenan?.
Can wata wani dubara ta faɗo mata, cikin hanzari ta amsa mashi da. "Wani kwaro ne ya shiga mun cikin idona, shi ne ya sanya ni yin kuka".
Murya a ɗan kausashe ya ce. "Ta ya aka yi aka samu kwaro a cikin hall ɗin nan? Dole masu gyaran hall ɗin nan su sha punishment, domin kuwa basu yi aikinsu yadda ya dace ba ga shi suna cutar da mutane". Ya kai karshen maganar tare da ciro handkerchief daga aljihunsa ya miƙa mata a kan ta goge hawayen nata, sannan ya yi mata sannu kafin yasa kai ya wuce ya barta tsaye a wajen, ya sha alwashin in aka gama taro dukka masu aikin gyaran hall ɗin sai sun sha punishment, a kan me basu yi aikinsu da kyau ba har suka bar kwari suka iya shigowa cikin wajen suna cutar da bayin Allah?. Da alama Guyson yasan darajan ɗan Adam sosai da sosai.
Ita kuwa tsoro ne ya kamata na ganin cewa zata ɗauki alhakin masu gyaran wajen, bayin Allah basu san komai ba zasu sha punishment a banza, ta shiga damuwa sosai a kan hakan, danasanin yin wannan karya da ta yi ta fara yi, tana yi tana goge hawayen nata da handkerchief ɗin da ya bata, tana kuma shaƙar daddaɗar kamshin dake jikin handkee ɗin.
Katseta da yi mata sannu wannan matashi na bayan nata ya yi. A ɗan razane ta juyo da kallonta a kansa, da alama ta manta da shi yana wajen, hakan ne ya razanata.
Sannu ya kara yi mata yana wani binta da kallo kamar wani tsohon maye. Da yauwa kawai ta amsa mashi, cike da tsoro tasa kai zata bar wajen. Ƙoƙarin dakatar da ita ya yi, da alama yana da wani plan a kanta. Kin tsayawa ta yi domin idan baku manta ba ita Leesharh tana aiki ne bisa umarnin masu nikaf, sai abin da suka ce take yi, dan haka kula maza baya daga cikin tsarin aikinta, hakan yasa ta yi saurin barin wajen.
A hanzarce ta fito daga hall ɗin, tana tafiya tana waige waige kamar maras gaskiya, kirjinta sai dukan uku uku tara tara yake yi, addu'a take yi kawai Allah yasa wannan matashin kada ya biyota, sai zuba uban sauri take yi, a ƙagare take da ta isa wajen elevator ta koma sama ta je ta yi kwanciyarta a room nata dan yau dai aiki ba zai yiwu mata ba.
A garin waige waigen baya da take yi bata ankara ba sai ji ta yi ta yi karo da mutun. Har wani irin jiri ta ji tana ƙoƙarin faɗuwa saboda bata rike jikinta da kyau ba.
Da kyar ta iya kama kanta ta tsaya tare kuma da ƙoƙarin ɗaga idanu dan ta kalli da waye ta yi karo. Daddaɗar kamshin perfume ɗinsu ne ya daki kofofin hancinta. Kusan kamshin perfume ɗin irin na Ramish, hakan ne ya haifar mata da faɗuwar gaba tun bata kalli wanene bane.
Cikin tsoro ta ɗago idanunta da suke jajir har sun ɗan kunbura saboda kuka. Dai'dai lokacin da ta ɗago kai shi kuma Obaid ya yi yunƙurin kai mata mari saboda buge shi da ta yi, har ta sanya wayarsa ya faɗi a ƙasa.
Riƙesa Omaid ya yi dan yasan wlh marinsu ba shi da daɗi sam sam, idan ya mari yarinyar nan ai sai ta suma, duk wanda waɗan nan twins ɗin suka mara fa baya sha ta daɗi, sam marinsu bashi da daɗi. Hakan yasa Omaid ya riƙesa.
Ita sam bata damu da yunkurin kai mata marin da Obaid ya yi ba, ruɗani ma suka jefata, tunani take yi wai shin a gaban madubi take kallon mutun biyu maimakon ɗaya ne ko dai yaya ne? Taga sun yi muguwar kama, ka rantse da Allah mutun ɗaya ne, sun ruɗar mata da ƙwaƙwalwa...... Ni kuwa na ce ba ke kaɗai ba, yayyunsu ma ba iya rabesu suke yi ba bare ke bare, ai su kaɗai suke iya rabe kansu sai Mommarsu, ko King da yake matsayin ubansu baya iya rabesu, sai ya kira Obaid da sunan Omaid, ya kira Omaid da sunan Obaid, Allah ya yi masu halitta ne iri guda sak, ta wannan kamanceceniya da take a tsakaninsu suke amfani su ruɗar da mutane a kullum, baka isa ɗaya daga cikinsu ya yi maka laifi ka ce zaka iya gane wanda ya yi ɗin ba, wane kai, sai dai idan zaka haɗesu dukkansu biyu ka basu punishment, amma gane mai laifi a cikinsu ba abu bane mai yiwuwa.
"Who're you and what are you doing here?". Cewar Omaid ɗin, ya yi maganar kuma bai saki hannun Obaid da ya rike da kada ya mareta ba. Da farko dai sun cewa Guyson ba zasu zo gidan ba, amma daga baya suka ce zasu halarci walimar, shi ne fa Abu Abdussalam ya tura tawagar motoci aka ɗaukosu. Sun ci gayu cikin ƙananan kaya, ga wasu booth da suka sanya a kafafunsu masu kyau da tsada, already kunsan su komai masu iri ɗaya suke sanyawa, harta gyaran gashin kansu iri ɗaya suke yi.
"She looks like a criminal, ban yarda da ita ba". Cewar Obaid, ya yi maganar yana zame hannunsa daga riƙon da ɗan uwan nasa ya yi mashi.
Su suna ta maganarsu ita bata ma a tare da su, duniyar tunani ta luluƙa, ta ruɗe ta rasa gane wai mutun biyu ne a gabanta ko dai ɗaya ne a gaban mirror, sam bata jin abin da suke faɗe ma.
Na gaya maku waɗan nan twins ɗin giveted ne, ƙwaƙwalwarsu kaifi gare shi ga saurin gudun aiki, cikin lokaci ƙanƙani suke iya gane abin da babba baya ganewa, da kallo ɗaya Obaid ya yi mata ya ji ya fara zarginta, bai ma san wacece ita ko me take yi a cikin gidan ba, amma har cikin ransa ya ji tabbas wannan yarinyar maras gaskiya ce.
(Da su twin's a gidan Abu Abdussalam suke da kuwa akwai cakwakiya, dan kuwa cikin minti ɗaya zasu gano Leesharh.😅 Yara kamar wasu aljanu🤔😅)
"Yeah you're right blood, the way she's walking she's totally criminal, and see her eyes like she want to kill someone innocent". Cewar Omaid.
Tsawa Obaid ya daka mata a kan wacece ita?.
Can masu dai, ita bata ma jin me suke faɗe, hankalinta ya yi nisan kiwo. Wani irin raɗaɗin azaba da ta ji ya ziyarci dukkannin ilahirin sassan jikinta ne yasa ta dawo daga tunanin da ta afka. A wani irin mahaukacin razane ta sanya hannu ta dafe ƙuncinta in da Obaid ya sakar mata mari, ji take yi kamar ba'a duniya take ba, nan take ta fara ganin wani haske yana mamaye ko'ina a wajen, ɓangaren da ya mareta ɗin kunnenta ya daina jiyo mata sautin komai. Dama twin's basu shiga aikin special weapons and tactics bama ya marinsu yake da azaban zafi bare kuma su da suke karɓar horo kullum, ga aikin wahala, ai dama idan suka mareka sai ka ji kamshin lahira, to ita dai Leesharh ta ɗan ɗana.
Ƙoƙarin kara mata wani marin Obaid sarkin saurin hawa ya yi, dai'dai lokacin Guyson ya iso wajen, ya fito daga cikin gida wajen Yah Ramish.
"Kai Obaid me ta yi maka zaka mareta?". Guyson ya jefa masu tambaya, while shi kuma Omaid ya riƙe hannun Obaid ɗin dan kada ya kara mata wani marin, yasan idan ya barshi ya kara mata to fa sai dai a kwasheta ranga ranga bayan ta zuba kashi da fitsari a wando.
"Yah Omar who's she?". Cewar Omaid. Omaid fa da kuke ganin nan ya iya takunsa, ya fi Obaid iya tsiya, sai dai shi yana danne zuciyarsa baya saurin hawa, baya yarda ransa ta ɓaci har zuciya tasa ya fita hayyacinsa, sarai yasan me yake yi, da ƙwaƙwalwarsa yake aiki over, ya iya takunsa sanka sanka, yanzu dai kunga shi Obaid har ya arzuƙa, dan sun yi magana bata amsa masu ba har ya fusata ya mareta, shi kuwa Omaid kun ga kamar ma bai san ana yi ba, saboda tsabar iya taku da basaja.
"Ayya she's our new house girl, sabuwar maaikaciya ce fa, kuma innocent girl ce, bata da hayaniya, kawar Lil sister ce ma fa". Cewar Guyson.
Kawar da kansa Obaid ya yi tare da sauke hannunsa daga yunƙurin kara mata marin da ya yi niyar yi Omaid ya tare, cikin ɓacin rai ya ce. "Wannan ba house girl bane ba, criminal ce maras gaskiya, she looks like green snake under green grass".
Omaid zai yi magana Guyson ya riga shi da cewa. "Anyway, koma dai menene kuzo mu tafi cikin hall, wai bama kunce ba zaku zo ba? Ya aka yi kuma kuka zo?".
Guyson bawan Allah, yasan da cewa halin kannen nasa sai su, shi sam bai ɗauki zancensu da wani mahimmanci ba na kiran Leesharh da green snake under green grass da suka yi, dan yasan su fa yaran nan sam sam basu son zaman lafiya, idan basu kaunar mutun ba kalar sharrin da ba zasu yi mashi ba, dan haka sai ya ɗauki abin a zaman cewa basu kaunar Leesharh ce kawai yasa suka laƙa mata wannan suna. Bai san sun fishi gaskiya ba, su fa jami'ai ne, yau tsawon almost shekaru 8 suna a special weapons and tactics academy, a matsayin horon da suke yanzu zasu iya gane ɓarawo cikin dubbannin mutane, horo mai rai da lafiya suke samu, ba makarantace ta kananan kai ba, kun san su kuma da basira, hakan yasa makarantar take alfahari da su sosai da sosai, su ɗin su kaɗai ne tamkar ya dubu a cikin school ɗin nasu. Shi kuwa Guyson da yake karatun computer engineering ina zai gane hakan? Ai babu wannan magana, ba abin da zai gane, su kam sun san duk wasu lago na mutun maras gaskiya.
Da kyar Guyson ɗin ya iya jansu suka bar wajen, har suka bar wajen kuma Leesharh bata dawo cikin hayyacinta ba, ta maru kam ba karya, duk da take chocolate color sai da shatin yatsu biyar ɗin Obaid ya fito ruɗu ruɗu a face ɗin tata, ta ji hannun manya, wannan ma dan ba marin Omaid ta sha ba, da na shi ne ina ga suma zata yi ko mutuwa mai gabaɗaya, dan Omaid ya fi Obaid sanin gurbin mugunta, dama kunsan ko da twin's ɗin a mahaifa guda suka fito ba daban daban ba dole ɗaya yana fin ɗaya wasu abubuwa, to Omaid dai ya fi Obaid wayo, iya shege, iya taku, zafin zuciya, iya sarrafa zuciyarsa, kai da komai ma.
Ta jima sosai a wajen kafin ta fara jin kamshin dawowa cikin hayyacinta. Sai a lokacin kuma ta iya durkushewa kasa a saman gwiwowinta a wajen ta saki wani marayar kuka, wani irin zogi da azaba ne yake ratsa kashi da ɓargon jikinta, har yanzu kuma ta
All Chapters
Chapter 1
Chapter 2
Chapter 3
Chapter 4
Chapter 5
Chapter 6
Chapter 7
Chapter 8
Chapter 9
Chapter 10
Chapter 11
Chapter 12
Chapter 13
Chapter 14
Chapter 15
Chapter 16
Chapter 17
Chapter 18
Chapter 19
Chapter 20
Chapter 21
Chapter 22
Chapter 23
Chapter 24
Chapter 25
Chapter 26
Chapter 27
Chapter 28
Chapter 29
Chapter 30
Chapter 31
Chapter 32
Chapter 33
Chapter 34
Chapter 35
Chapter 36
Chapter 37
Chapter 38
Chapter 39
Chapter 40
Chapter 41
Chapter 42
Chapter 43
Chapter 44
Chapter 45
Chapter 46
Chapter 47
Chapter 48
Chapter 49
Chapter 50
Chapter 51
Chapter 52
Chapter 53
Chapter 54
Chapter 55
Chapter 56
Chapter 57
Chapter 58
Chapter 59
Chapter 60
Chapter 61
Chapter 62
Chapter 63
Chapter 64
Chapter 65
Chapter 66
Chapter 67
Chapter 68
Chapter 69
Chapter 70
Chapter 71
Chapter 72
Chapter 73
Chapter 74
Chapter 75
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 65 Chapter of 75