warning a kan kada ya sake, kuma ya sani shi ɗin bawansu ne, a karkashinsu yake, dole a kasansu zai zauna ba wai ya jera da su ba. Amma da yake gimbiya Chuchu ce, sai bata wani damu ba, bama ta bi ta kansa ba, zama kawai ita ma ta yi.
"Aunty Chuchu meyafaru naga kina ɓata rai ne?". Cewar auta.
Kara tsuke ɗan bakin nan ta yi kafin ta ce. "Ni da Yah Jawad ne mana, na je wajen daddy yanzu dan na roke shi zan je Dubai, shi ne Yah Jawad wai na tafi daga nan babu in da zan je, kamar shi na je tambaya".
"Yauwa kin ma tunaninmun bari na je wajen Yan Jaish ya gaya mun ya gama tunanin da zai yi, nima dai ina son zuwa Dubai ɗin ne ai"
Ta kai karshen maganar tare da yunƙurawa ta miƙe.
"Jirani mu fita tare, daga nan na wuce wajen Akka, Allah zan je na gaya mata ta sa daddy ya barni na je".
(Chuchu dai bata daddara ba zata sake kai karan Yah Jawad wajen Akka, da alama ta manta punishment ɗin ne😅 mu dai namu ido)
A tare suka miƙe. "Hoorain zan je wajen Yah Jaish, zaka jirani a nan ne ko zaka tafi?".
Ta faɗa tana kallonsa.
Ƙasa ya yi da kansa kafin ya amsa mata da cewa. "Yadda kika ce ranki ya daɗe".
"Auta sunana ba ranki ya daɗe ba, ko kace mun Zunaira". Ta faɗa a ɗan ƙule.
"Ai babu wanda zai kiraki da Zunaira sai mara kunya". Cewar Aunty MieMie da ta shigo cikin lambun a yanzu.
A hanzarce suka kai kallonsu a kanta, tana shirye cikin kayan masu bala'in kyau da tsada, ga wani dankareran alkyabbarta a sama, daga wuya zuwa hannunta dukka gwala-gwalai ne masu tsada ta kawata kanta da su, ga wani haɗaɗɗen ɗan kunnen hancinta na gold shi ma da ta sanya ɗan karami, sai kyalli yake yi, hakan ba ƙaramin kyau ya kara mata ba, cover irin na hamshaƙan matan sarakuna ne a kafafunta launin golden color, haɗuwa iya haɗuwa, jinin larabawa.
Da sauri auta ta taho ta faɗa jikinta tana sakin murmushi, ita ma Chuchu a hanzarce ta ƙarisa wajenta tana faɗin. "Aunty MieMie ina kika je two days?".
Rungume auta ta yi tare da sanya hannu tana shafa kan Gimbiya Chuchu ta basu amsa da. "Na je na halakci taron makarantarsu Omar da aka gudanar ne na kammala secondary school ɗinsu, yau na dawo".
"Shi ne Aunty MieMie baki tafi da mu ba?". Cewar Chuchu.
"Ban san kuna son zuwa ba ai, nima na wakilci daddy ne, saboda ba zai samu zuwa ba, akwai abubuwa da suka sha mashi kai sosai, uncle Abbas ma bashi da lokaci shi ne na wakilcesu duk da su uncle Rahab sun je".
Gimbiya Zunaira zata yi magana wata kuyanga da ta shigo cikin lambun a yanzu ta katsesu da cewa. "Allah ya kara sawon kwana ranki ya daɗe, Momma tana kiranki, wai ki je parlourn mai martaba ki sameta".
Har suna haɗa baki wajen tambayar waye ake kira? Dan ranki ya daɗe ta ce, kuma dukkansu haka ake ce masu.
"Princess Aunty MieMie ke ake kira".
Kuyangar ta basu amsa.
Shi dai Hoorain yana zaune yana binsu da kallo, sai dai ba kowa zai iya gane cewa yana binsu da kallon ba, baza ma kataɓa yin tunanin yana kallonsu ba.
Raba jikinta dana auta ta yi tare da riƙo hannunta tana faɗin su je su ji me ake kiransu. Ta yi maganar tare da riƙo hannun Chuchu da ɗayan hannunta.
Kai tsaye part ɗin King suka nufa, suka bar Hoorain a zaune a wajen bawan Allah.
Sun sha madarar mamaki na ganin gabaɗaya family a wajen, harda su Sarina, ga Yah Jaish da Yah Jawad ma nan, dukkansu manyan suna zaune a saman tsala tsalar sofas dake a cikin parlourn, su Sarina kuwa suna zaune a saman Dubai carpet dake a tsakiyar sofas ɗin, ga twins Obaid and Omaid a kusa da Gimbiya Fanan.
Cikin mutuntawa Aunty MieMie ta yi sallama tare da wucewa ta zauna a saman sofa mai zaman mutun biyu da yake a kusa da King, tare da zaunar da auta a gafenta kafin ta ɗagawa su Momma gaisuwa.
Kowacce tana dake a cikin alkyabbarta, kowacce kuma tana zaune a saman nata sofar na daban, Mama ta wani tsare gida kamar hakan ce zai sa su ji tsoronta, har da Mammie Yah Jawad a wajen, kowa yana cikin shiga ta alfarma.
Gimbiya Chuchu kuma kusa da King ta zo ta zauna a saman carpet ɗin, ta kwantar da kanta a saman laps ɗin King ɗin. Tana turo baki kamar anyi mata wani abin, sai dai rashin sa'arta na yanzu yasa ta zauna a in da suke fuskarta juna ita da Yah Jawad, da zarar ta ɗago kai shi zata fara kallah, shi ma kuma haka, sam bata lura da hakan ba har sai da ta ɗan ɗago da kanta da nufin ta kalli su waye da suwaye ne ma a cikin parlourn, tana ɗago kai kawai karaf suka haɗa idanu da shi, a dai'dai lokacin shi ma ya ɗago idanu dan ya saci kallonta, dan shigarta ta yi mashi kyau.
Cikin sauri ta yi ƙasa da nata idanun ta fara ƙoƙarin matsawa daga saitinsa ko da kaɗan ne.
Shi ma kawar da nasa kallon ya yi izuwa kan King, ga mamakinsa sai ya ga King ɗin ma shi yake kallon, abin gwanin ban dariya. Duk sai ya ji ya tsargu kuma, sai yake ganin kamar kallon tuhuma King yake yi mashi, alhalin kuma ba haka bane, shi ma King ɗin ya ɗago ido ne kawai sai kallonsa ya sauƙa a kansa, ba wai haka kawai ya kalle shi ba.
Kamar dai wani mara gaskiya sai ya yi saurin kawai da kallonsa daga kan King ɗin yana jin gabaɗaya a takure yake, izuwa yanzu shi da kansa ya fahimci ba iya burgesa kawai Chuchu take yi ba, sama da hakan ne, akwai dai abin da yake ji dangane da ita.
Shi kam Jaish da tun ɗazun yake aikin latsa waya bai ma san me ake ciki ba.
Twins kuwa sai wani ƙus ƙus suke yi ƙasa ƙasa, wani lokaci su yi ƴar kurma kurma kamar wasu munafukai.
Gyaran murya King ya yi tare da fara yin magana a nutse. "Nataraku a nan ne kan abubuwa biyu zuwa uku. Na farko shi ne akan abin da ya faru da Sarina, abin sam bai yi daɗin ji ba, ga shi har ya saka mun ɗan uwana (uncle Abbas) ciwon kai, sam ban ji daɗin hakan ba, shiyasa na taraku domin na ja maku kunne a kan ban yarda wani ya sake zuwa wa wani daga cikinku da zancen yana son ƴaƴana har kuma ku yi mashi jagora zuwa cikin gida na wajen ƴaƴan nawa ba, ban yarda da hakan ba! Ku kyaleni idan sun kai munzalin aure ni zan zaɓa masu maza da kaina, koma ya kuke da mutun bana da buƙatar ku kawo mun shi cikin gidan nan da sunan wai yana son ƴa ta, dukka dukka ma nawa Sarinar take da Abbas zai takura kansa da zai ta yi aure? To ni bana da buƙatar irin hakan ta sake faruwa, ku kyale mun ƴaƴana su huta, sai dai ni ina tunanin wannan yaro Yusuf ba lafiya yake ba, amma dai koma menene Zafar zai yi masu abin da ya dace, wannan shi ne maganata ta farko. Ta biyu kuma Obaid and Omaid zasu koma Dubai gobe, duk da ba'a buɗe makarantarsu ba ko ma nace basu wuci sati ɗaya da yin hutu ba, amma za su koma bisa son hakan da mahaifiyarsu take yi, ta ce tana son su koma yafi mata, so zasu koma. Sai magana ta uku, Omar zai dawo nan da kwana uku, Mommynku ta buƙaci da zata shirya mashi gagarumin walima na murnar dawowarsa, na kuma bata izinin yin hakan, ina gaya maku ne domin na fita hakkin kowa".
Ɗan dagatawa ya yi da maganar yana sauke numfashi tare da bin fuskokin matan nasa da kallo.
Shi dai Jaish har ga Allah bai ga wani abin da zai sa a kirashi cikin wannan al'amari ba, shi ba aboki yake da shi bama bare ace ko abokinsa zai ce yana son kanne nasa har ya yi mashi jagora zuwa gidan, to shi ko da ace yana da aboki ma ya isa ya yi mashi jagora zuwa neman aure ne? Wlh bai ga wanda ya isa ya sanya shi ya yi mashi jagora zuwa wajen mace ba, a ganinsa ba'a haifi mutun ba.
"Akwai wani mai abin faɗa ne?".
King ya katse su da wannan tambayar.
Siririn tsaki Mama ta ja kafin ta ce. "Ranka ya daɗe ni ina son a gaya mun menene banbancin su Chuchu da su Obaid da duk wanda Rahilarh zata haifa sai ta ce bata son ya zauna da ƴan uwansa a nan sai dai a Dubai? Menene a gidan da nata ƴaƴan ba zasu zauna ba sai namu? Ko mu namu ƴaƴan ba mutane bane? Ko dai nata ƴaƴan sun fi namu daraja ne?".
Da iya gaskiyarta ta yi maganar.
Ita kuwa Momma ba wani dalili bane yasa ta buƙaci su Obaid su koma Dubai face wannan matsala dai da take fuskanta a cikin gidan, kwana biyun nan tana yawan mafarkinsu a cikin wani mawuyacin hali ne yasa ta buƙaci da su koma kawai ko hankalinta zai kwanta.
(Ni kuwa na ce bama dole ki gansu a cikin mawuyacin hali ba, yara basu ji, sai dai su yi ta kwasa wa kansu alhakin mutane suna biyewa Sarina suna kwasan hakkin waɗan da basu ji ba basu gani ba, yara kamar an canza maki su lokacin da kika haifesu🤔 ai in a kansu ne ma fin haka zaki gani baiwar Allah😅)
Da yake Momma jinin Modarawa ce ba'a masu su kyale, sai ta ce da Mama ɗin. "To ai naga duk tushe ɗaya ne ko? Kina iya mayar da su Chuchu ɗin Dubai ɗin kema idan kina da buƙata, saboda suma ai kakaninsu ne a can ɗin, babu wanda ya hanaki yin haka, dan haka sai ki cire idanunki a kan rayuwata, haka nake son ƴaƴana su kasance, tun da ba ke kika haifa mun su ba kina iya jan baki ki yi mun shiru".
Akka dake zaune saman nata sofar ta wani dake tare da ɗaura kafa ɗaya bisa ɗaya ne ta karɓi zancen da cewa. "Idan ma baku yi haka ba ai sai na ce Zuhair ba mata ya aura ba".
Karo na farko da Yah Jawad ya ji dariya ta so ta kubce mashi, wannan tsohuwa Akka akwai iya tada bom, a maimakon ta shiga cikin lamarin ta sasanta, amma kun ji wai idan basu yi hakan bama ba mata bane.
Shi dai Jaish haushi har wuya yake ji ta iso mashi, dan shi sam baya son zama a taron mata, yasan fin haka ma zasu aikata, su yi abinsu su bar mutun da ƙuncin zuciya ba abin da ya damesu, ai mata duniya ne, kome za'ayi masu kishin nan dai yana nan, ba zai taɓa tafiya ba, kai ko cire zuciyar mace ka yi ka wanketa fes da ruwan zam zam ka sake dawo mata da shi a kan kishi gobe sai kaga wani bakin halin........😅
"Daddy zamu iya tafiya?". Cewar Yah Jawad, dan ya lura abin na mata ne take shirin motsawa, wato kishi, dan haka gara su kama kansu kada a kashesu da kuncin zuciya.
Shiru King bai basu amsa ba, ya dai zuba masu idanu yana ganin su, dama haka yake yi, sai sun yi sun gaji yaje saka baki.
"Bayan kin asirce shi ya zama ƴaƴanki kawai yake gani da daraja ta ina muke da ƴan cin zaɓarwa ƴaƴanmu in da muke son su yi rayuwa? Ai ke kaɗai ce mai wannan dama, zalunci dai komai daren daɗewa yana da karshe". Cewar Mama.
Omaid ne ya kalli Mama ɗin cikin ɓacin rai ya amsa mata da. "Mama ko Momma ta zaɓa mata in da zamu yi karatu ko bata zaɓa mana ba mu dama bamu da ra'ayin yin rayuwa a cikin kingdom ɗin nan, wajen su mai ran karfe su Uncle Rahab and uncle Abu Abdussalam muke son zama, dan haka ba laifin Momma bane, kuma..........."
Wani irin ɗan iskan kallo da Yah Jaish ya wurga mashi ne yasa ba shiri ya haɗiye sauran maganar nashi, dan sun san Jaish ba kanwar lasa bane, ba shi bashi da hakurin Yah Jawad, yanzun nan zai sa su ji kamshin ma'aika azarailu, dan haka sai ya yi shiru tsit kamar babu shi a parlourn.
Ita kuwa Mama kallon walaƙanci ta wurgawa Momma ɗin kafin ta ce.
"Kina iya yin fin hakan ma ai, kisa yaranki basu daraja kowa".
Shiru gabaɗaya parlourn ya yi, kallon Obaid ta ƙasan ido Omaid ɗin ya yi, burinsu kawai su bar parlourn nan su je su shiryawa Mama ɗin nan wani munafurcin da sai ta yi kuka, dan wlh idan ba haka suka yi mata ba ba zata rabu masu da Mommarsu ba, shi kuma Yah Jaish zai taka masu birki, wlh ka ana ha maza ha mata basu ga dalilin da zai sa su bar wata banza tana yi wa mahaifiyarsu kutse a cikin al'amura ba, a cewarsu sun lura Yah Jaish ɗin nan baya son Momma sam sam, tun da yana zaune Mama ta zageta bai iya cewa komai ba, to su dai ba za su ɗauki wannan iskanci ba, dole kowa ya san matsayinsa a gidan, kafin su koma Dubai sai sun yi maganinta....... Hmmmm lallai akwai kura!.
Shi kuma Jaish ya ja bakinsa ya yi shiru ne saboda King yana wajen, koma dai menene yasan da cewa King zan yanke hukuncin da ta dace, kuma dama a matsayinsa na babba mai ilimi da hankali me ruwansa da faɗan kishiyoyi fisabilillahi? Ai wanan ba layinsa bane, amma fa sosai abin ya sosa mashi zuciya, ji ya yi tamkar ya buge Mamar sai ta sume ko ta mutu a wajen, amma ya danne saboda kannensu dake a cikin parlourn ga kuma King and uncle Abbas sannan ga Akka a kwana!.
Miƙewa tsaye ya yi ba tare da ya bi ta kan kowa ba ya nufi hanyar fita, domin idan ya ce zai cigaba da zama a wannan tattaunawa ba makawa tsab zai yi wa Mamma one slap seven death, so gara mashi ya yi gaba tun bai hasala ba.
"Where are you going Jaish?".
Cewar uncle Abbas.
Duk yadda yake kaunar uncle Abbas ɗin ya kasa iya bashi amsa, dan zuciyarsa a kusa take, idan ya ce zai buɗe baki ya yi magana zai iya haɗiyar zuciya ya mutu, so sai ya yi kamar bai ji me uncle Abbas ɗin yake cewa ba, a hanzarce ya fice daga cikin parlourn dan ma kada King ya dakatar da shi. Already shi kuma King dama bai yi niyar dakatar da shi ɗin ba, saboda yasan halin ƴaƴan nasa da zuciyar bala'i, shi kansa ya ji zafin maganar Mamar bare kuma ƴaƴan Momma, ai dole abin ya sosa masu rai.
"Sarina, Fanan, auta, Jannat, Obaid and Omaid duk ku tashi ku tafi".
Cewar Aunty MieMie.
A hanzarce kusan a tare suka miƙe suka nufi waje.
Mummy kam tana zaune kamar mutun mutumi tana binsu da kallo, ita sam sam ma bata son hayaniya a rayuwarta, ba zaka taɓa jin maganarta a irin wannan abin ba, da girmar kujerarta hajiya uwargidan King Zuhair Abdul Malik ba.
King ya ɗauki a kallah 5 mins yana kallonsu tun bayan fitarsu Sarina, kafin ya ɗan nisa tare da fara yin magana cike da bada umarni da kuma izza.
"Kada wanda ya sake yin magana a kan hukuncin da Rahilarh ta yankewa ƴaƴanta na girmansu a hannun ƴan uwanta, kowacce a cikinku tana da damar da zata ce mun Zuhair a wajen kakaninsu nake son ƴaƴana su girma, iyayena da yayyuna haɗe da kannena sai kakanina ne fa a Dubai ɗin, me dan ƴaƴana sun girma a hannunsu? Ƴaƴana mata ne na ce bana buƙatar su matsa daga kusa da ni, amma maza ina iya turasu ko'ina su je su yi karatu, ita Zunaira da take mace ba ga shi tana gabana ba? To me wani sabon abu a ciki? Me abin ta da hankali? Bana son wannan hayaniya dukka, ba'a kan haka na taraku ba, abin da na tara ku a kai shi ne, kada ku kuskura ku gayyato mun wani cikin gidan nan da sunan yana son ƴaƴana, sannan Obaid and Omaid zasu koma Dubai gobe, Omar yana dawowa nan da kwana uku, Mummynsa zata shirya mashi walima, idan akwai wadda take buƙatar wani abin ta yi mun magana zan shiga ciki".
Ya kai karshen maganar tasa cikin nuna cewa tsantsar umarnin yake basu.
Mummy baiwar Allah, Omar dai ba ɗan ta bane, ɗan Momma ne yayan Zunaira, amma kun ji har walima ta nemi izinin shirya mashi dan zai dawo, ita dukka ƴaƴan nasu abu guda ta ɗaukesu saɓanin Mama.
"Zan iya tafiya?". Cewar Mama, da alama ranta bai so maganar da king ya yi ba sam.
Akka ce ta ce "Kowa ma zai iya tafiya a yanzu".
A hanzarce Mama ta miƙe ta yi waje, Momma ce ta biyu a fita ta rufa mata baya, sai Mummy ta uku, princess Aunty MieMie ta rufa masu baya. Parlourn ya rage daga Akka, uncle Abbas sai King. Uncle Abbas ma miƙewa ya yi tare da sanar da su zai je ya shirya dan zai koma baƙin aikinsa. Sallama suka yi ya wuce, ya rage saura Akka da King, su kuma suka cigaba da hira na tsakanin uwa da ɗa.
🤍KADA KU MANTA WANNAN DADDAƊAR LABARIN DAGA ALKALAMIN FATEEMA ZAHRA MUSA A-K-A PRINCESS TEEMA TAKU TA AMANA YAKE🔥💘
Share fisabilillahi 👏
ALLAH KA KARA MANA SON MANZON ALLAH 🔥🤍
🤍🔥𝗥𝗔𝗪𝗔𝗡𝗜𝗡 👑 𝗭𝗔𝗟𝗜𝗡𝗖𝗜🔥🤍
🔥CROWN OF INJUSTICE🔥
𝗠𝗔𝗟𝗟𝗔𝗞𝗜𝗡
❤️🔥FATEEMA ZAHRA MUSA ❤️🔥
(❤️A-K-A 𝑷𝑹𝑰𝑵𝑪𝑬𝑺𝑺 𝑻𝑬𝑬𝑴𝑨🔥)
🔥🤍T🔥🤍T🔥🤍W🔥🤍......💻
❤️𝑫𝑨𝑻𝑬 5/8/2024.....✍️📚🌹
For information 08161390581 Whatsapp me only!!.
🤍𝑺𝑻𝑬𝑷 1......✍️📚🔥
اللَّهُمَّ صَلِّ عَلَى مُحَمَّدٍ وَعَلَى آلِ مُحَمَّدٍ، كَمَا صَلَّيْتَ عَلَى إِبْرَاهِيمَ وَعَلَى آلِ إِبْرَاهِيمَ، إِنَّكَ حَمِيدٌ مَجِيدٌ، اللَّهُمَّ بَارِكْ عَلَى مُحَمَّدٍ وَعَلَى آلِ مُحَمَّدٍ، كَمَا بَارَكْتَ عَلَى إِبْرَاهِيمَ وَعَلَى آلِ إِبْرَاهِيمَ، إِنَّكَ حَمِيدٌ مَجِيدٌ❤️
E____________28🔥
🕊️🌼🕊️🌼🕊️🌼🕊️🌼🕊️🌼🕊️🌼🕊️🌼
AAJ YARI.💔😥
Shiru Leesharh ta yi, gabaɗaya ta shiga ruɗani, kanta ya ɗaure, duk ta rasa me yake yi mata daɗi, yanzu ya zata yi?.
Dafa shoulder ɗinta da kyau Jasrah ta yi tare da fara magana cikin nutsuwa da ƙoƙarin nuna mata illar da abin da zata aikata zai haifar mata ita da danginta gabakiɗaya, dan wlh idan aka kamata ko mahaifinta da take burin take ikirarin ta koma gida ta je ta gani ba barinsa za'ayi ba, babu wanda zai iya tsira daga cikin familynta, babu wanda zai tsallakewa Sheikh Abu Abdussalam bin Badeen, duk sai ya ragargazasu, to babban abin tambayar ma a nan shi ne wanenen shi wanna Ramish ɗin kam? Ya yake? Meyasa ake farautar rayuwarsa har haka da ake ƙoƙarin leƙar asirinsa? Kuma kun ji matar ta ce suna da ma'aikata a gidan, hakan na nufin ba ita Leesharh ɗin bace ta farko, kenan an jima ana sanya mashi idanun? Da alama har yanzu haƙarsu bai cinma ruwa bane yasa suka buƙaci Leesharh a wannan aiki, idan kuka yi duba da yadda matar ta ce ma'aikatan nasu a iya harabar gidan suke ba su sami damar shiga ciki ba, hakan yasa basu iya sanin me Ramish ɗin yake ciki, ita kuwa Leesharh karamar yarinya ce da ba za'a barta a harabar gida ta yi aiki ba, dole idan za'a ɗauketa aiki a can cikin gida zata yi aikin, kila ma a ta fannin kitchen ko kuma gyaran ɗaki or wani abu makamancin haka, babu wanda zai kawo wa ransa ita ɗin leƙar asiri ta zo yi, kunga zata sami damar sanin wanenen Ramish da kuma motsinsa a cikin gidan, ina ga tabbas kafin su tunkari Leesharh da wannan magana sai da suka yi gagarumin bincike a kanta, sai kuma da suka shirya sosai.
Amma kuma matsalar a nan shi ne, ita Leesharh idan ta amince ta karɓi wannan aiki da ankamata fa shikenan ita da danginta ne zasu girbi laifukan da basu suka shuka ba! Domin bata san wannan mata ba! Tab akwai cakwakiya na gasken gaske kuwa, yanzu nasu wasan kuma zai fara kenan, zamu ga wanene zai yi nasara a wannan game ɗin da za'a buga kuma!!!.
"Leesharh a wannan magana babu wani tunani da zaki yi, domin kuwa baki da wata mafitar da ya wuce ki ce mata ba zaki je ba, idan kuma kika ki, to wlh karnikan gidan Sheikh Abu Abdussalam bin Badeen ne zasu cinye gawarki a ɗanyarta, kuma ki sani sun cinyeki sun cinye banza, ke bama wannan ba, wlh duk danginki babu wanda zai iya tsallakewa, babu wanda zai sha a hannun Ramish idan asirinki ya tonu, kuma yadda suke da mahaukatan cameras a gidan kin san kuwa dole asirinki zai tunu, ke ta ina ma zaki fara yin wannan aikin fisabilillahi Leesharh? To ina mai tabbatar maki ganin waɗan nan mugayen fusatattun securitys ɗin da suke gadin kan titin da zata ratsa ta shigar dake unguwar da gidan yake ma ya isa ya sanya ki saki fitsari a wando, duk rashin tsoron nan naki da ƴan gidan nan suke faɗa wlh baki ga abin tsoro bane, bare ace ki ga securitys ɗin da suke gadin ainahin gidan, ina ga daga nan zaki sume, ke ni fa ban ma yarda matar nan zata iya shigar dake wannan gida ba, gidan ɗaya daga cikin ƴaƴan the most powerful King Badeen da duniya take magana a kansa, kowa idanunsa naa kansa, ga karfin iko kamar shi ya bawa kansa, kuma defence minister da duk wani mai kaki yake a ƙarƙashinsa, sai da izininsa kaki zata motsa, lallama kam, ni dai a matsayina na ƴar uwarki ban baki goyon baya ba, ko da bamu da alaƙa ta jini addinin Musulunci ya haɗa mu mun zama ƴan uwan, kuma ba zan zuba maki idanu ina ganin abin da zai cutar dake da familynki na yi shiru ba, dole na gaya maki gaskiya koda zaki gujeni".
Ta kai karshen maganar tana mai cigaba da kallon fuskar Leesharh da tsoro ya gama bayyana a samansa sosai. Bata taɓa shiga irin wannan yanayi ba, ko lokacin da aka kawota gidan da sunan ta kashe mahaifiyarta babu irin makamancin wannan tsoro a face ɗinta, bata taɓa tsorata a cikin wannan gida ba duk da ta san hukuncin kisa ne a kanta, tasan kasheta za'ayi, amma babu tsoron hakan a ranta, yau dai ta tsorata da jin wannan irin bala'i na aikin da zata je.
"Ke fa Jasrah baki da mutunci, yanzu saboda mugunta ne kike son hanata fita daga cikin wannan gida, kina ji Leesharh? Wlh duk abin da Jasrah take faɗa karya ne, kawai bata son ki kuɓuta daga hukuncin kisa da yake a kanki ne, bata son ke kifita ita a kasheta ne, shiyasa take ƙoƙarin sare maki gwiwa, dan haka kada ki yarda, ki je kawai Allah ya bada sa'a, zamu tayaki da addu'a". Cewar Sahra dake makale a saman gado kamar wata mage........ Mugunta dai babu kyau Sahra!!.
Taɓe baki Jasrah ta yi tana mamakin irin wannan kiyayya, kiyayya ido da ido suke nunawa Leesharh babu ko sakayawa! Sai ka ce ba musulmai ba, yaran nan sam sam basu da mutunci, sun tsani Leesharh over, duk wani munafurci ƙoƙari suke yi suga sun kullah mata, su basu ki ba ma a matso da hukuncin kisan da yake a kanta ya dawo yau yau a kasheta su huta, ko me ribarsu idan an kasheta?..............🤔
"Sahra laifin me kika yi ma aka kawo ki gidan nan?".
Cewar Leesharh, daga jin yadda ta yi magana ƙasan zuciyarta ta gama karaya, gwiwowinta duk sun sage, ta tsorata sosai da wanna al'amari, ita tunaninta ma ɗaya shi ne ya zata yi ta cewa wannan mata ba zata yi wannan aiki ba ta,
All Chapters
Chapter 1
Chapter 2
Chapter 3
Chapter 4
Chapter 5
Chapter 6
Chapter 7
Chapter 8
Chapter 9
Chapter 10
Chapter 11
Chapter 12
Chapter 13
Chapter 14
Chapter 15
Chapter 16
Chapter 17
Chapter 18
Chapter 19
Chapter 20
Chapter 21
Chapter 22
Chapter 23
Chapter 24
Chapter 25
Chapter 26
Chapter 27
Chapter 28
Chapter 29
Chapter 30
Chapter 31
Chapter 32
Chapter 33
Chapter 34
Chapter 35
Chapter 36
Chapter 37
Chapter 38
Chapter 39
Chapter 40
Chapter 41
Chapter 42
Chapter 43
Chapter 44
Chapter 45
Chapter 46
Chapter 47
Chapter 48
Chapter 49
Chapter 50
Chapter 51
Chapter 52
Chapter 53
Chapter 54
Chapter 55
Chapter 56
Chapter 57
Chapter 58
Chapter 59
Chapter 60
Chapter 61
Chapter 62
Chapter 63
Chapter 64
Chapter 65
Chapter 66
Chapter 67
Chapter 68
Chapter 69
Chapter 70
Chapter 71
Chapter 72
Chapter 73
Chapter 74
Chapter 75
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 38 Chapter of 75