ita jikinsa a sanyaye " fat lion ya Kira sunanta muryarsa a kasalance tayi masa banza ya sake matsota sosai kamar zai shige jikinta dan har tana jin hucin numfashnsa a gefen wuyanta.
" nasan za ki ji babu dadi game da abinda ya faru da kuma abinda hajiya inna ta yi miki , tabbas kina dauke da ciki kuma wallahi cikina ne, nasan ban kyauta miki ba na aikata kuskure mafi muni agareki wanda sanadiyyar haka inna tayi maiki tonon silili da aibantawa , wallahi ban yi miki haka dan na kuntata miki ba ko nayi silar da za'a tozartaki ba , nayi ne saboda wani dalili nawa ,naki nasar miki ne saboda ban san yadda zaki ɗauki abun ba amma kiyi ha.......
Tun ka fin ya k'arasa abinda yake son fad'i ta juyu da sauri ta rufe masa bakinsa da hannunta ɗaya tana kallon cikin kwayar idanunshi dake cike da damuwa da ruwan kwalla ya cire hannunta "am really sorry ya faɗa yana kallon cikin idanunta dake zubar da ruwan hawaye ....
"ka daina bani hakuri sannan ka daina fadar ina dauke da ciki ,nasan ka fada ne dan ka kareni agurin hajiya inna ba wai da gaske cikin gareni ba ...
Ya matso jikinta sosai har suna iya jiyo numfashin junansu "it's true fatlion kina d'auke da cikin mah'ruf shuaib , nayi auratayya dake batare da saninki ba ,idan baki manta ba akwai ranar dana na iskeki a dakin kina daga kafa da kyar har na kaiki gurin wata nurse ta dubaki lokacin mama ta tafi cotonue , lokacin na kaiki gurin likita ta duba min ke saboda abinda na aikata miki , sannan ina lokacin da kika yita amai har doctor Husain ya zo ya dubaki ,shi kuma a ranar yake faɗa min ciki gareki shiyasa naki yarda yayi magana a gabanki ,na dade ina son fada miki amman zuciyata ta dinga kwabata saboda sanin halinki ..
Tayi sororo tana kallonsa kafin daga bisani ta soma girgiza masa kai "ko ka rasa tunaninka ne ya ma'hruf ta yaya kake cewa ina da ciki ?
Ya rungumeta tsam ajikinshi yana shafa bayanta bakinsa na kan sumar kanta daya gama wargajewa a bayanta "ta yadda nayi miki bayani .
a hankali take zubar da hawaye da sheshekar kuka "ki kwantar da hankalinki ,ki daina kukan nan haka, ba fa mugun abu mukayi ba ni burina yanzu bai wuce kiyi hakuri ki yafe min saboda nayi tarraya dake batare da saninki ba ta soma ƙoƙarin zare jikinta daga nashi "karka sake ƙara min damuwa akan wanda nake ciki ni bani da komai tayi maganar tana ja da baya tana ƙoƙarin juyawa ya riko damtsen hannunta ya manneta da bangon d'akin zuciyarsa na dokawa da sauri , ya kai hannusa daya jikin bango ya tokare ya matsota sosai yana ƙoƙarin shigewa jikinta ya haɗe goshinta da nashi hancinsa na gugan nata zuciyoyinsu ya dinga harbawa a tare ,a hankali suka sauke numfashi , ma’aruf ya lumshe idanunsa sannan yasa hannun shi daya ya talla'bo fuskarta yasa kwayar idanunshi cikin nata kana ya kira sunanta "fat lion ina me neman afuwarki please sannan ki yarda da cikina dake jikinki ummita ta marairaice fuskar tana dubansa "kice kin yafe min ko hankalina zai kwanta , jikinsa a sanyaye ya haɗe fuskarsu waje ɗaya "talk to me fatlion zuciyata na son jin wani abu daga bakinki ya k'arasa maganar yana goga hancinsa akan nata yana busa mata iskar bakinsa da numfashinsa kafin daga baya ya hade bakin su guri daya ya shiga tsotsa lip's dinta batare da ta shiryawa hakan ba.
kokarin hanashi take amman ta kasa aiwatar da komai dan tuni har ya zarce da romance dinta sun dade a haka rungume da juna gam gam yana tsotsan bakinta ...
Buga kofar d'akin da a kayi ne yasa mah'ruf janye jikinsa daga nata ya nufo bakin kofar ya bude ganin mama yayi tsaye rike da akwatin kayanta , mika masa tayi" muje ka rakani inda zan shiga mota zuwa kasar haihuwata ..
"What mama Ummita ta furta da karfin gaske tana karasa fitowa daga dakin da sauri "karki min haka mama yaya kike son rayuwarta ta kasance kina gidan nan ma yaya na kare bare baki cikinsa "akwai Allah sannan ga mijinki nan zai kula dake fiyye dani.
"wani miji mama ni bani da wani miji, wallahi ba zaki bar gidan nan ki barni ba kafarki kafata duk inda zaki ummita da hankalinta yayi kololuwar tashi ta fadi haka fuskarta tayi ja saboda kuka , jikin mama babu kwari ta soma jan akwatinta tana tafiya "haba mamana karki min haka idan kika barni yaya kike son nayi ta shiga binta tana rike da akwatin "ba tun yanzu ake bukatar na bar gidan nan ba , lokaci bai yi ba sai yanzu ,ni kaina na gaji da zama a cikin gidan nan tayi maganar a daidai lokacin da suka k'araso tsakiyar parlour'n inda mutane suke tsaye, jin abinda mama ta faɗa yayi mugun taga hankalin Abba take jikinsa ya kama karkarwa gumi na sake tsatsafo masa injiniya ne yayi karfin halin fita ya kira hajiya umma da baba sarki .
Hajiya umma ta shigo hankalinta a tashe, mama ta isa gaban Abba ta durkusa har kasa kanta a sunkuye "to Ibrahim lokaci yayi da zan bar maka gidanka da ahlinka zan tafi sai naji daga gareka Allah ya sadamu da alkhairi, idan nayi maka laifi a zamantakewar da muka gudanar ka yafemin ni dai baka min komai ba tana gama fad'ar haka ta yunkura ta mike ta isa gaban hajiya inna "inna kiyi hakuri dan girman Allah yau zan bar gidan Ibarahim dinki nasan kina kinsa da kuntata masa ne saboda ya aureni, a yau ki cigaba da son d'anki kamar yadda kike ada saboda zan barshi bari na har abada ..
Abba ya ja dogon ajiyar zuciya da karfi yana mai runtse idanunsa jikinsa na wani irin rawa, bai taba tunanin mama zata iya furta abinda ta faɗa a yanzu ba ,bai san ciwo da rad'ad'in barinsa zai daga masa hankali irin haka ba ,parlour'n ya kara rikicewa da kuka da rud'ani jin furucin mama mah'ruf kuka ummita kuka mama da sauran mutane kuka abun ya citura wata razananniyar
kara ummita ta saki mai karfi tace "nashiga uku Allah karka jarabi iyayena da wannan maseefar Allah idan hukunci ne ka hukatani amman ka bar iyayena su rayu kamar yadda suka d'auko rayuwarsu, "hajiya inna yau burinki ya cika amman da ikon Allah sai kinga ......
mama tayi saurin toshe mata baki tana girgiza mata kai "kul naji kince mata wani abu saɓanin alkhairi "haba mama me yasa zaki hanani magana "inna mahaifiyar mahaifinki ce , duk nan babu wanda ya isa ya faɗawa inna maganar daya gadama ban taka masa burki ba bare ke diyar cikina ta k'arasa maganar tana ƙoƙarin barin parlour'n Mah'ruf ya amshi akwatinta tare da rike hannunta "muje mama ai kinyi hakuri na tsawon shekaru tunda kin gaji babu mai takura miki ana aure dan ibada ne ,Allah daya halicci aure shi hassalata saki dan haka....
yayi kasa da kanshi yaki duban inda abba yake sannan ya cigaba da magana "Abba ka sawwakewa mama aurenka dake kanta kawai ta huta da wannan bala'in na hajiya inna ya karasa maganar yana sharce kwallar idanunsa tare da kallon hajiya inna yaji mai za tace , zata saduda ko kuwa tafi bukatar tafiyar mama ...
Wani irin ihu ummita ta zunduma "wayyo Allah na shiga uku karku bari mamana ta rabu da babana ,wallahi ina son su tare banason na rabu dasu , ta isa gaban mama tana hawaye wallahi idan kika tafi zan kashe kaina duk ku huta ..... .
a matukar tsorace mama tace "karki aikata sabo mana , rabuwa kaddara ce babu abinda zai sameki you will be fine ummita adduata tana tare dake dan Allah ki kwantar min da hankalinki kinji mamana kinga bake kad'ai bace ki zauna gidan ubanki tare da mijinki .
"mijin banza mijin wofi me zanyi dashi wallahi babu abinda zanyi dashi nafi bukatar ke da mahaifina tare ,yadda ta dinga wasu abubuwa kamar zararriya ya d'aga hankalin mama matuka .
Mama na kallon Ummita ta k'arasa kusa da ma'hruf ta fixge akwatin kayanta dake rike a hannunsa "dan me zaka goyin bayan tafiyarta? " kana bakinciki ganinsu tare ne ?
Girgiza mata kai yayi yana cewa "wallahl azim nafi son ganinsu tare "
"karya ne kai ga mahaifiyarka tare da Abba shine ni kake son raba tawa mahaifiyar da mahaifina ,wannan itace kalar taka soyayyar ga mama ?
"daman duk soyayyar da kake nuna mata shekara da shekaru karya ce ?
"Are you out of your sence ki natsu kiyiwa mutane shiru anan sannan ki shiga hankalinki kasancewarki diyar mama kawai kike amman soyayya dake tsakanimu ta wuce misali ,mama tayi niyyar tafiya da kanta I can't stop her wallahi bazan hanata tafiya ba dan nafi son rayuwarta akan komai , tsawon shekaru bata taɓa tunanin tafiya ta barmu ba ,ta ɗauki tsawon shekaru tana addu'a dan yau ta furta zata barmu sai nace a'a "bazan hanata ba sai dai na goya mata baya dan na samu kwanciyar hankalinta .
"to ni ban yarda ba ban kuma amince da wannan tsarin ba banason rabuwarsu nafi son na gansu tare "na rantse da wanda ya busa min numfashi matukar mama ta bar gidan nan sai dai ku farka kuga gawata tana gama fadar haka ta kwasa da gudu tayi hanyar step tana wani irin kuka da sauri ya saki hannu mama ya biyota aguje itama mama bata san sanda ta biyo bayansu tare da sauran jama'a ba.
Ummita na shiga dakin ta shiga bubbude dorowar bedside dinta ta dauko magani ciwonta , gabadaya ta zazzaga a tafin hannunta tana ƙoƙarin zubawa a bakinta ya banko kofar dakin da karfi ya shigo bai tsaya wata wata ba ya buge hannunta yana fuskantarta "kina hauka ne ko kin fara shaye shaye ne ?
" zan miki rashin mutuncin da baki taɓa especting daga gareni ba .. "dakata malam babu ruwanka da rayuwata waye ma kai meye hadinka dani ,mama ta k'araso gurin da suke ta d'aga hannu sama zata sauke mata mari , yayi saurin rike mata hannu "dan Allah mama karki mareta ki barta taji da halin da take ciki ,mama ta fashe da kuka tare da zama a gefen katifa, hajiya umma da injiniya da abba har ma da aunty suka shiga bata hakuri da bata baki .
"ku daina bata bakinku bafa zan zauna ana wulakantani ba meye aibuna ? "Meye laifina
"Me mahaifiyarku take son nayi mata?" iya biyyaya ina mata ko ita ta kawoni duniya iyakacin abinda zan iya mata kenan ,gara na kama gabana wallahi bazan zauna ba ......
jin furucin mama dake shiga kunnuwanta yasa ta soma yin kasa mah'ruf yayi saurin tarota jikinshi yana taɓa mararta jin numfashinta ya dauke yasa gabadaya a gigice ya soma kiran sunan mama "mama ta suma ....
gabadaya sukayo kanta, suna kiran sunanta "ummita ummita shi kuwa mah'ruf sai fatlion yake kira yana rungumeta daita tsam a faffad'an qirjinshi "dan Allah mama kiyi hakuri kice kin fasa tafiya wallahi idan wani abu ya sameta nima zaki rasani ,kiyi hakuri mama karki rasa yayanki alokacin ɗaya ...
Hannun ummita mama ta riko cikin nata tana kuka "ummita karki min haka ki tausaya min ganin yadda duk suka rud'e babu wanda yayi tunanin a yayfafa mata ruwa yasa aunty fad'awa bathroom ta dibo ruwa da sauri mah'ruf ya karbi roban ruwa, ya shiga shafa mata a fuska ,amman shiru bata motsa ba ,a matukar haukace mama ke girgiza ummita tana kuka tana kiran sunanta "ki tashi dan girman Allah wallahi na fasa tafiyar karki mutu ki barni idan kika mutu bazan taɓa yafewa kaina ba, saboda nice sanadi shima Abba a zabure yake girgizata wani ruwan ya sake tsiyaya mata amman shiru taki motsowa .
hankalin kowa yayi bala'in tashi fiyye da tunanin mai karatu sunanta kawai suke kira "shikenan ta mutu ta mutu "bata mutu ba mama mah'ruf ya faɗa a gigice yana sake janyota jikinshi ya zauna akan tayis ya rungumeta yana girgizata "fatlion karki mutu ki barni ki rayu saboda ni dan Allah . gabad'aya ya rud'e ya gigice ya d'ago fuskarta Yana busa mata numfashinsa a cikin bakinta da hancinta tare da zira yatsun hannuwansa duka cikin kunnuwanta a hankali ya haɗe bakinsu guri daya gabadaya ilahirin jikinsa rawa yake gumi na tsatsafo masa ..
Tsura masa ido sukayi suna dubansa kafin daga baya suka soma barin d'akin daya bayan daya saboda ganin abinda yake mata , waje sukayi gabadayansu suka tsaya cirko cirko suna addu'ar kowa hankalinsa a tashe yake ban da hajiya inna , wacce bata cewa kowa komai ba dan tasan ko tayi magana babu mai kulata ta nufi dakin inda ta iske Mah'ruf zaune rashe rashe rungume da ummita a jikinsa yana tsotsan bakinta da iyakacin numfashinsa mutuwar tsaye tayi tana kallonsu cike da mamaki idan ya tsotse bakinta sai zare ya sake maidawa haka ya dinga yi daga karshe ya zarce da romacing dinta yana tsotsan bakinta yana zuba mata sambatu, babu shiri ta juya da sauri ta bar dakin sai lokacin ta fahimci abinda ya fidda mutane daga dakin, tana fita ya sake damkar bakinta yana hura masa iska ta hancinta da karfi ..
Wani irin atishawa ta saki da karfi haɗe da sakin numfashi tare da kiran sunan mama "karki barni mamana karki tafi ki barni ina bukatarki ya mike tsaye rungume daita ajikinshi ya kwantar daita a saman katifa ya riko laulausan tafin hannunta ya rankwafo jikinta yana gyara mata kwanciya sannan ya zauna gefenta yana rike da hannu daya ,dayan hannunsa ya kai gefen fuskarta yana shafawa a hankali yana sauke numfashi, yafi karfi minti talatin a gabanta yana kallonta ya kai hannunta dake rike cikin nashi yayi kissing yana d'aura dayan hannunsa ya haɗe guri daya "ta matso ruwan hawaye "ina mamana ta wuce ko ?
Ya girgiza mata kai "ta fasa tafiya ki kwantar da hankalinki ki sanyawa zuciyarki natsuwa kinsan mama bazata iya barinmu ba.
"zata iya ya ma'hruf naga hakan a cikin kwayar idanunta ni dai ka dakatar daita duk lalacewar gidan nan nafi son ganita cikinsa, idan bata ciki rayuwata zata tagyyara "babu inda zata muna tare ya fadi haka yana kai hannunsa kan cikinta jin yana motsi har lokacin ya sauke naunayen ajiyar zuciya kana ya kai bakinsa cikin kunneta "am so happy cikina yana nan lafiya.
cikin kuka tace "ni ina ruwana da wani ciki ta zabura zata mike yayi saurin matseta gam a faffad'an qirjinshi "dole kuwa kiyi ruwa dashi wannan cikin rayuwata kenan ,akan cikin nan babu abinda bazan iya yi ba, babu wanda zan iya d'agawa kafa "To ni wallah ka rabani da cikin nan idan ma gaske ne dan banason shi ,me zanyi da cikin wanda bai sona bai kaunata . "okya kiyi hakuri sannan ki taimakeni ki bari ki haifa min cikina sai mu rabu tunda kinfi bukatar haka ...?
Tayi shiru zuciyarta na wani irin zugi "ai nasan zaki fi buƙatar rabuwar mu ko ba haka ba ? "ban sani ba matukar na tabbatar da cikin babu abinda zai hanani zubar dashi ,"karki soma wannan gangancin ,ayi ɗaya kacal na sameshi kinsa walahar da ake sha kafin a samar d'a ... ?
Taja tsaki tana kawar da fuskarta gefe "dan girman Allah ka rabu dani ka rabani da wani zance ciki "Bazan iya rabuwa dake ba fatlion saboda aurenmu auren zobe ne, bazan iya barinki ba duk runtsi duk wuya muna tare dan haka ki daina kawowa zuciyarki rabuwa a tsakaninmu ,
da kyar ta samu ta raba jikinta da nashi ta soma ƙoƙarin saukowa "ki kwanta ki huta babu inda mama zata,
ta girgiza masa kai "ina son ganin mamana bai ce mata komai ba ya riko hannunta suka fito yana rike da hannuta ..
Suna gama saukowa ummah ta nufo gurinsu" sannu ummita ta rungumeta ajikinta tare da manna mata kisss a goshi tana shafa gadon bayanta "kin kwantar da hankalinki mamanki ta fasa tafiya ta barki ,kuna tare muddin rai kinji diyata.
"inji uban wa ai tafiyar uwarta dan ada huta roro, dole ta wuce kuma tare da diyarta idan mutuwa zakuyi idan sun tafi sai ku mutu mu gani amma dole sai ta bar gidan nan kuma a yau daman nafi son barinta gidan sai gashi kuma ta bukata huta roro ta tafi na huta da jaraba ..
Abba ya motsa bakinsa zai yi magana hajiya inna tayi saurin dakatar dashi "karka sake naji bakinka ka rubuta mata takardar sakinta yanzu yanzu da zafi zafinsa ka bata dan ....
" Ba zai rubuta ba mah'ruf ya katse mata hanzarin ta hanyar faɗar hk " ko kin raba auren nan bazaki raba zukatan mutanen gidan nan da kaunar mama ba ..
" Da yarda Allah sai kin mutu ki bar wannan auren hajiya inna ,baki isa kisa Abba ya saki mama ba, ko da kika ga dazu na goyi da bayan ya sawwake mata bawai har cikin zuciyata nake son Abba ya saki mama ba ,na fadi haka ne saboda rabata da bala'in da maseefarki sannan na gani idan nace ya saketa zaki hana a she kema abinda ke ranki kenan ,to ko mutuwa zakiyi sai dai ki mutu amman abba da mama mutu ka raba suna nan tare daram .
"oho to bari kaga yadda karfin ikona ya kai yau idan bani da iko akanka ai ina dashi akan ya'yana Ibrahim sagiru ta kira sunan Abba da injiniya a tare suka d'ago suka zuba mata ido suna kallonta jikinsu na rawa "me ye matsayina agurinku ?
"Mahaifiya suka fadi haka jikinsu na sake rawa "to ina umartaku a yanzu
da ku sa ma'hruf ya saki ummita saki uku rasss .......kuma a yanzu idan ba haka ba duk sai na tsine muku albarka duniya tayi muku dumi sannan aljannarku dake tafin kafafuna zan danne bazan taɓa daga muku kafa ba, jin haka yasa hantar cikin mah'ruf kad'awa a hankali jikinsa ya soma rawa tamkar mazari yana kallon inna cike da mamaki.
Abba da injiniya kamar zasuyi kuka "ya mah'ruf kaji abinda Hajiya inna take buƙata ka aiwatar aikaina ka sakeni kamar yadda ta bukata kowa ya huta dan ni kaina bana bukatar zama da kai ,ya watsa mata kallon banza mai haɗe da harara hankalinsa bai tashi ba sai daya ji saukar Muryar abba cikin kunnenshi "ka sawwake mata baba Allah yasa hakan shine mafi alkhairi ...
kallon Abba ya dinga yi shesheke kamar wani mahaukaci tare da kallon sauran mutane dake gurin ,gabadayansu sukayo kanshi suna umartashi bai san sanda ya isa gurin Hajiya inna ya rike hannunta "haba inna karki min haka kiyi hakuri dan girman Allah karki sa Abba cikin wannan lamarin, ni ne fa babanki ma'hruf da kike so fiyye da komai .
"Ina sane da hakan ,sai dai tuni na soke maka wannan matsayin ba dai akan wannan matar ka rufe idanunka kana min tozarci ba ?
"na tuba Inna ki yafe ni , "baka isa ba sai ka rabu daita ya mike ya isa gurin ummita ya riko hannuwanta muje ki bawa inna hakuri ina bukatar rayuwa dake bazan iya rabuwa dake ba ..
"taja ta tsaya tana kallonsa sannan ta soma magana a tsanake "zaka min wata alfarma ?
Ya d'aga mata kansa da sauri yana sanya kwayar idanunshi cikin nata "ka sake ni kamar yadda ta bukata sannan ka fita cikin rayuwata bana bukatarka .....
"Idan kina bukatar na sadaukar miki da rayuwata zanyi fatlion amman bazan iya sakinki ba ya k'arasa maganar yana ƙoƙarin zubda hawayen dake idanunshi , cike da sanyi jiki take kallonsa ta kai hannunta fuskarshi tana shafawa batare da tasan ta aikata hakan ba tana kallon cikin kwayar idanunshi da suka canza kala tsabar tashin hankalin da yake ciki .
" dole ka sawwake min aurenka inna bata son zamana da kai ni kuma bazan iya rayuwar kunci ba ,bazan iya irin rayuwar da mahaifiyata tayi ba "Ki yarda ki amince ki kasance tare dani bazan bari wani abu ya sameki ba sannan bazan iya sakinki ba, ki kasance tare dani fatlion dan wallahi bazan iya barinki ba ,Allah ne kaɗai yasan abinda zai same ni idan kika bar rayuwata haushin furucinsa take ji ,a da taso tayi rayuwa dashi amman a yanzu bata bukatar haka cike da jin haushi ta fixge jikinta ta juya cikin sautsayi kafafunta suka gurd'e tayi kasa zata kifa kan cikinta yayi saurin tarota ya mannata da qirjinsa , wani irin bugawa qirjin inna yayi da wannan abu, ta zaro idanunta tana kallonsu zuciyarta cike da bakinciki a fusace yake kallonta numfashinsa kamar zai bar jikinsa "me yasa kike sakaci da kanki da rayuwarki ? "Me yasa bakya tunanin halin da zan shiga akanki ? ta hura masa hanci hawaye na zubo mata " hannun sa ya kai ya rike kafad'unta dashi yana sake kallon kwayar idanunta da tsare gira " I love you fatlion ! I love you fatlion !!
Yan wattapad Sai hakuri yan what's app zasu rigaku samu saboda matsalar network
TWO FRIEND'S BSBS
💗💗💗💗💗💗
WANNAN CE
QADDARARMU
💖💖💖💖
💗💗💗💗💗💗
~TRUE LIFE STORY~
FREE NOVEL
AL'QALUMAN
*AYSHA A BAGUDO*
*FAIZA HAMMADU*
~DEDICATED TO~
*MUHAMMAD AUWAL*
WATTPAD @HAUESH
bismillahirrahmanirrahim
PAGE 54
Tsaye ummita tayi tana bin mah'ruf da idanunta waɗan da suka koma jajaye tsabar hawayen dake zubowa daga cikinsu tana jin kalmar daya furta kamar almara tare da yin nazarin furucinsa mai kama da sake kusancinsu tare , wani sanyi ne ya dinga taso mata yana ratsa sansar jikinta ,jinin jikinta ya ninka gudun da yake fiyye da farko, hatta ɗan cikinta sai da yayi tsalle ya cure guri guda , gabad'aya ta kasa motsi dan kalmar i love you fatlion ba iya zuciyarta kaɗai ya tsaya ba har cikin jininta take jin tafiyarsu ..
"yau ita mah'ruf ya furtawa wannan tsadadden kalmar mai dadi da sanyaya zuciya ?"anya kuwa wannan drama ba'a mafarki yake faruwa ba ?
" tasan mahruf fiyye da kowa mutumin daya girma da kiyayyarta shine yanzu tsaye a gabanta yake furta wannan kalmar gareta anya kuwa ba yayi hakan dan hajiya inna taji haushi bane ?
Hannuwansa dake kan kafad'unta ya cire ya zuba cikin aljihun wandonsa haɗe da tsura mata idanunshi yana kallonta , da sauri ta share hawayenta dake sake turereniyar gangarowa haɗe da girgiza masa kanta yayinda soyayyarsa ke sake fixgarta da karfi ,tabbas tasan ita kanta ta kamu da mahaukacin qaunarsa sai dai duk runtsi baza yarda ta amince masa a karon farko ba ,zata adana nata soyayyar ba zata ta fito da nata fili ba ....
Shima zuba mata idanunshi yayi yana jin zallar farinciki da fargaba na ratsashi a lokaci daya qirjinsa ke wani irin mahaukacin dokawa kamar zai fito waje jikinsa a kasanlance ya buɗe bakinsa " babu ta yadda zan iya rayuwa babu ke ya furta yana sake kusanto jikinshi da nata qirjinsa na dokawa da matsanancin karfi ,still shiru tayi taki cewa komai tare da tsura masa idanunta dake cigaba da zubar da hawaye , " there's no way to survive without you fatlion I love you with all my heart banason na rasaki , banason rasaki a rayuwata saboda
All Chapters
Chapter 1
Chapter 2
Chapter 3
Chapter 4
Chapter 5
Chapter 6
Chapter 7
Chapter 8
Chapter 9
Chapter 10
Chapter 11
Chapter 12
Chapter 13
Chapter 14
Chapter 15
Chapter 16
Chapter 17
Chapter 18
Chapter 19
Chapter 20
Chapter 21
Chapter 22
Chapter 23
Chapter 24
Chapter 25
Chapter 26
Chapter 27
Chapter 28
Chapter 29
Chapter 30
Chapter 31
Chapter 32
Chapter 33
Chapter 34
Chapter 35
Chapter 36
Chapter 37
Chapter 38
Chapter 39
Chapter 40
Chapter 41
Chapter 42
Chapter 43
Chapter 44
Chapter 45
Chapter 46
Chapter 47
Chapter 48
Chapter 49
Chapter 50
Chapter 51
Chapter 52
Chapter 53
Chapter 54
Chapter 55
Chapter 56
Chapter 57
Chapter 58
Chapter 59
Chapter 60
Chapter 61
Chapter 62
Chapter 63
Chapter 64
Chapter 65
Chapter 66
Chapter 67
Chapter 68
Chapter 69
Chapter 70
Chapter 71
Chapter 72
Chapter 73
Chapter 74
Chapter 75
Chapter 76
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 56 Chapter of 76