maka son da babu mahalukin da zan iya yiwa kamarsa ,bazan iya cigaba da rayuwa babu kai ,ka tausaya min mijina .......
A matukar fusace ya buge hannuta dake bakinsa tare da tsareta da manya idanunshi yana sake jin matsanancin sabon 'bacin rai mara iyaka kafin daga bisani ya katseta ciki fushi da tsawa " you are very stupid dake da shegiyar soyayyar da kike min , "a duniya babu tozartacciyar masoyiya kamarki suhaima ...
"da na san haka kike Wallahi da tun farko ban takura kaina gurin aurenki ba ,nayi nadama wallahi amman babu komai , Allah daya haɗa ya raba sai kibi wani jirgin .......
yana gama fadar haka ya juya ya buɗe motarsa a fusace yana huci ya shiga ya murd'a key ya bar unguwar a guje zuciyarsa kamar zata tarwatse ...
Juyawa tayi da kuka ta shiga gidansu tana zunduma ihu tamkar wata mahaukaciya sabuwar kamu "wayyohlly Allah na shiga uku na lalace , karo suka ci da zulaihat dake ƙoƙarin fitowa sakamakon sautin muryarta data jiyo, da sauri zulaihat taja baya tana dafe goshinta , cike da matsanancin tashin hankali tace " suhaima lafiyarki kuwa kike wannan zunduma ihun waye ya mutu ?
"Wayyo Allah nah zulaihat na mutu na lalacewa ta faɗa jikin zulaihat tana sake fashewa da kuka ..
Zulaihat ta d'ago kanta daga jikinta tana sake tambayarta a rud'e kirjinta na bugawa da matsanancin karfi "ki faɗa min abinda ke faruwa mana kin tasani gaba kina risgar kuka, sai data ja majina tace "wayyo Allah ni suhaima na mutu karshena yazo tunda mah'ruf ya sake ni .....
"What ?"when ?
Tayi mata tambayar ajere tana girgiza kai jikinta na sake ɗaukar rawa " me kika ce suhaimai ?
" Mah'ruf ne ya sakeni, ya sakeni ,ni yanzu yaya zanyi da rayuwata ? "bazan iya rayuwa babu shi ba ku taimakeni yan'uwana kar na rasashi idan na rasa shi mutuwa zan yi nima zaku rasani har aba .....
zulaihat tayi saurin kamo hannunta tana toshe mata baki hakan yasa ta kasa k'arasa maganar suka k'arasa bangarenta dake zaman jiran gawar shanu dan kar mahaifiyarsu taji
hankalinta ya tashi ..
Ta zaunar daita a bakin gado tana cewa "garin yaya haka ta faru ?
"Akan wannan muguwar tsinanniyar yarinyar nan ce ummita shine ya ... ....
ta kasa k'arasa maganar saboda kukan daya ci karfinta "wallahi bazan iya rayuwa babu shi ba aunty tayi maganar tana fixge dankwalin kanta tayi cilli dashi a tsakiyar d'akin tana wani irin kuka .
jikin zulaihat na rawa ta janyo wayarta ta shiga neman layin hajiya rahma bayan ta ɗauka ta koro mata halin da ake ciki , ko cikakken minti ashirin ba'ayi ba ta bayyana a gidan , nan suka kulle kansu a d'akin zulaihat suka yita rarrashin suhaima daga karshe suka yanke shawarar zuwa gurin baba na isheri domin karkato da hankalin mah'ruf .
suhaima tayi shiru tare da rafka uban tagumi tana kuka cikin zullumi da rashin sanin abun yi, dan gabadaya maganganu y'an'uwanta basa shigarta duk da bata cire tsamammanin akan shawararsu na taimaka mata ba, tasan matukar suna da hali zasu taimaka mata ta koma gidan mijinta "yayarmu dan girman Allah kar a ɗauki dogon lokaci ,aiki nake so mai zafi cikin gaugauwa bana son na rasashi a rayuwata ."bazaki rasashi ba suhaima ki bani nan da kwanaki biyar zuwa sati da kanshi zai zo har inda kike nayi miki wannan alkawarin.
ta rungumeta a jikinta tana janyo numfashi da kyar "na gode yayarmu Allah ya bar mana ke ina alfahari da ke nasan zaki iya komai ,hajiya rahma ta shafa bayanta tana cigaba da rarrashinta sai gurin sha daya saura hajiya rahma ta bar gidan shima ɗan mijinta ya azalzala mata ne if not Sai ta kai shabiyu .
Mah'ruf zaune shiru akan kujera mai zaman mutun d'aya ya da'ura hannunsa ɗaya a saman goshinsa yayinda d'ayan hannun ke bayan keyarsa yayi pillow dashi, yana furzar da iska mai zafi daga bakinsa .
a hankali ya daura kafafunsa duka a kan Centre table din dake gabansa ya mike su yana girgizasu ,sosai ƙwaƙwaluwarsa tayi zurfi cikin tunanin sakin da yayiwa suhaima , gabadaya zuciyarsa babu dadi , sai dai bai yi nadamar sakin da yayi mata ba , cikin haka mama ta sauko daga samanta ta ganshi zaune cikin yanayi na damuwa da tashin hankali , kallo ɗaya tayi masa ta fahimci yana cikin zallar damuwa , take yar farar data sauko dashi akan fuskatar ta ɗauke ,ta karasa kitchen ta d'auko masa hollodian milk mai sanyi ta d'aura akan tire da glass cup ta fito ta d'aura tiren akan ƙaramin table ta tsiyayya hollodian a glass cup .
har sanda ta gama tsiyayawa bai san da zuwanta gurin ba , sai daya yaji tafin hannunta cikin sumar kanshi sannan ya motsa fuskar a murtike tamkar wanda aka yiwa mutuwa ,ya haɗe hannuwansa duka ya shafa fuskarshi batare daya yi magana ba ,
itama bata ce masa uffan ba ta mika masa cup din dake cike da hollodian data tsiyaya masa "ungo ka sha kaji sanyi .
jikinsa a matukar sanyaye ya kai hannunsa ya amsa yana sauke naunayen ajiyar zuciya sannan ya kai bakinsa ya kur'bi kaɗan ya ajiye cup akan table muryarsa a kasalance yace "na gode mamana "
"Me ke damunka baba babba ? Tayi masa tambayar tana tsareshi da idanunta ,da kyar ya buɗe bakinsa yace "
Babu komai mamana "
" babu komai shine duk jikinka ya sake haka? "ka faɗa min gsky karka min karya mana " hannuwanta duka ya kamo cikin nashi ya rike gam yana kirkiro murmushin dole "karki damu mamana zan sanar miki abinda ke damuna zuwa gobe inshaallahu , ya faɗa mata haka saboda yasan halinta matukar taji abinda ya faru tsakaninsa da suhaima tabbas zata takura ya dawo daita a daren, shi kuma abinda ba zai so faruwarsa kenan ba dan bai shirya dawo daita gidansa a halin yanzu ba, yafi son ko zai dawo daita sai ta taga rayuwa ta shiga hankalinta ta yadda zata san matsayinsa da darajarsa, bare baya tunanin sake rayuwa daita ,duk macen da zata iya kallon idanun mijin aurenta ta kirasa da kalmar bunsuru rayuwar aure daita bashi da faida ....
Murmushi mama tayi "fatan dai ba wata damuwar bace kou ?
Ya d'age mata girarsa d'aya alamun "eh .." to allah ya kai mu goben yasa muna da rai da lafiya , a hankali ya motsa bakinsa ya amsa da "ameen ..
Da sauri ummita take saukowa daga step har lokacin bata cire kayan dake sanye a jikinta ba , turus tayi sakamakon ganinsa zaune shiru tayi dan a tunaninta tuni ya dade a gidansa shi da matarsa .
mama na ganin saukowarta ta yunkura ta mike ta ɗauki abinda ya sauko daita tayi hanyar sama tana mata magana a hankali cikin muryar rada ta yadda mahruf ba zai ji ba "kije ki kwantar masa hankali da alamun yana cikin damuwa " tsuke ƙaramin bakinta tayi tana bin mama da kallo a ranta tace "haka kawai ya kwaso damuwarsa naje ni ya sauke akaina ....
Bayan barin mama parlour'n ya tsura mata idanunshi yana kallonta batare da yayi mata magana ba har sanda ta shige kitchen ta dibo abinci a plet ta fito ta wuce shi tana taka step da sauri sauri "fat lion .......
Ya kira sunanta da kasalalliyar muryarsa dake cike da tashin hankali , tsayawa tayi cak batare data juyo ba "ki daina irin wannan tafiyar da karfi plz ....."
Har lokacin bata ce masa qala ba ta cigaba da tafiyarta da karfi kamar yadda tayi niyya har ta sauka akan step tare da zancen zuci "ji min mutun da iyayi tsiya ko meye ruwanshi da tafiyata oho ?
"wayyohlly Allah ya faɗa da sauri yana dafe daidai saitin zuciyarsa a dalilin yadda ta k'arasa tafiyar da karfi .
ahankali ya tura hannunsa ɗaya cikin sumar kanshi yana chakud'awa tare da ciza lip's d'insa na kasa "i love you more than you know ya furta kalmarta ta karshe garesa a wanin da suka gabata daman yasan karya ne ba gaskiya ta faɗa masa ba ,kissa ne kawai irin nata ya san ba zata taba son shi ba gashi kai kuma ka kamu da matsanancin soyayyarta ba inji cewar kyakkyawar zuciyarsa..
A hankali ya shiga girgiza kanshi yana karyata zuciyarsa yana cigaba da jin abinda yake ji akanta ,yayinda ko wani part na jikinsa ke sake bud'ewa suna kar'bata acikin zuciyarsa da bata matsayi mai mahimmanci a rayuwarsa .... ..
Yana nan zaune har sanda kowa na gidan ya shigo , su meenal kuwa tuni an zarce daita gidan mijinta dake labak estate dake abulegba , ya mike akan kujerar ya kwanta yana tunanin ummita, yana son ya kice tunaninta a zuciyarsa amman ya rasa dalilin da yasa tunanita yaki barinsa hasalima sai sake kawo masa farmaki yake .... .
"to kod'an cikinsa dake jikinta ne ?
Yayi wa kanshi tambayar yana dafe goshinsa , take zuciyarsa ta amince da hakan ,yana son faɗa mata tana dauke da cikinsa ko dan tasan yadda zata dinga movement dinta amman yana fargaba bai san me zai faru ba idan tasan da zaman cikin , da karfi qirjinshi ke dokawa kamar zai fito waje saboda tsananin tunaninta daya addabi zuciyarsa, ya takure jikinsa guri daya tare da lumshe idanunsa yana shaƙar sanyayyen Kashim turarenta dake makale da kayansa ,
kusan karfe dayan dare yayi agurin yana kwance tana tunani batare da bacci yayi nasarar daukarshi ba.
bangaren suhaima kuwa itama kasa runtsawa tayi ko abinci daren kin ci tayi duk irin fama da zulaihat ta dinga yi daita taci abinci kin tayi har ta gaji ta kyaleta, ta barta da tunanin neman mafuta, gabadaya tunaninta kaf ya tafi ne akan yadda zata koma gidan mijinta da kuma yadda zata raba auren ummita da mijinta .. ....
ummita ta sake saukowa cin abincin dare tayi mamakin ganinsa kwance bai wuce ba ta k'arasa har inda yake kwance ta tsugunna gabansa tana kallon kyakkyawar fuskarsa mai tattare da haiba zuciyarta na sake samun natsuwa dashi , a hankali ta kai hannunta fuskarshi ta shafo kasumbarshi tana lumshe kyawawan idanunta , duk yana jinta ya sake lafewa yana sauke numfashi a hankali tayi kasa da hannunta zuwa faffad'an qirjinsa mai cike da yalwan gashi kwance luf ta soma shafawa tana cigaba da kallonsa .
a qalla ta ɗauki sama da minti goma tsugunne a gabansa tana shafa sumar fuskarshi zuwa qirjinsa tana kallonsa sannan ta yunkura ta mike tsaye da niyyar barin gurin on-expecting taji ya riko hannunta tare da fizgota ta fado saman fad'ad'd'en qirjinshi tana sauke numfashi haɗe da furta "wayyo cikina .....
ta soma ƙoƙarin mikewa daga jikinshi tana yatsina fuska da jin haushin abinda tayi gashi ya ka mata tana kallonsa da shafa jikinsa ,sake matseta yayi ajikinshi sosai yana fidda numfashi mai haɗe da shaukinta bai san sanda yace "sorry nayi kuskure bansan zaki ji ciwo a cikinki ba ya kike ji yanzu ko zamu hos.........
saurin datse harshensa yayi kafin ya k'arasa abinda yake son fadi ,
ta watsa masa wata ƙatuwar harara tana yatsina fuska wani irin kallo ta dinga masa kafin daga baya tace "plz ka sakar min jiki ta yunkura zata sake mikewa da karfi yayi saurin kai bakinsa cikin kunneta yana hura mata iskar bakinsa "plz ki taimakeni ki daina abubuwa da karfi irin haka ,da fa ba haka kike abubuwanki ba me yasa yanzu kike yin haka ne ?
"Ra'ayi ne ko dole sai na cigaba a yadda ka sani ?
"Yes ya faɗa tare da zarce wa da shafa jikinta , "kiyi hakuri ki daina zan ji dadi idan kika daina ,ba tayi ƙoƙarin dakatar dashi daga abinda yake mata ba,dan haka nan ta dinga jin wani irin dadi na ziyarar jikinta , kamshin turarensa da take shaka a halin yanzu yana sake haddasawa jikinta jin wani iri .....
yayinda feeling d'insa ke kawowa sansar jikinta farmaki ,fuskantar ya hade da nashi idanunsa na kallon cikin nata " "kallon me kike min har da shafani ko soyayyata ce ta hanaki runtsawa ?
tayi shiru haɗe da shigewa jikinsa tana sake shaƙar kamshin turarensa me kashe mata sansar jiki ....
" Fatlion ina matukar kishin aurena dake kanki fiyye da tunaninki haushinsa ya kamata ta tsani taji yace yana kishin aurensa dake kanta , kenan ita ba zai yi kishinta ba sai dai na aurensa ?tsaki taja a kasan ranta batare da tace masa komai ba
kusan minti goma suna haka yana yawo da hannunsa a sansar jikinta ita kuma tana faman lumlumshe idanunta alamun bacci, d'agata yayi suka bar parlour'n zuwa d'akinta ya kwantar daita shima ya kwanta ya zagaye cikinta da duka hannuwansa suna fuskantar juna yayinda hancinsa ke gugan nata, bakinsa daf da nata yana busa mata hucin numfashnsa me tafiyar da ruhi .
A tsanake ya dinga rabata da kayan jikinta yana ajiyesu a gefe haɗe da tabo wasu wurare ajikinta daya san dole idan ya ta'ba zata ji feeling d'insa ,taja numfashi da kyar ta sauke tana kokarin shigewa jikinshi, shi kuwa a tsanake ya dinga yawo da harshensa akan lip's d'inta kafin daga baya ya haɗe bakinsu guri daya ya shiga tsotsan bakinta tamkar wani mayunwacin zaki dan a matukar bukace yake daita sai dai ba zai iya kallon idanunta ya amfana da jikinta ba, yasan muddin wani abu ya shiga tsakaninsu tana sane kashinsa ya bushe agurinta .
kusan awa daya ya ɗauka yana juya harshensa cikin bakinta batare daya cire ba gabadaya ya manta da wata suhaima a rayuwarsa , itama ummita ya mantar da ita komai bata gane komai da kowa sai shi da sakoninsa a haka har bacci 'barawo yayi awon gaba dasu cike da shaukin juna sai goshin asuba ya farka ya maida mata kayanta ya shiga bayin dake cikin dakinta yayi wankan sarki dan a wasanin da yayi daita yayi realizing ya fito
ya qarasa inda take kwance ,kissing din goshinta yayi cikin zuciyarsa yace "mayya yarinya tayi nasarar dasa soyayyarta cikin zuciyarsa sannan ya fita zuwa masallaci ...
Yana fita ta sauke naunayen ajiyar zuciya dan ba wani bacci take ba , mikewa tayi a hankali ta shiga bayi tayi tsarki saboda yanayin jikinta daya ɓaci sakamakon hannunsa ɗaya kwana yawo a sansar jikinta sannan ta dauro alwala ta fito ta sauya kaya tana jin tafiyar tafukan hannunsa a fatar jikinta, tayi sallah zuciyar na makale da tunaninsa tana jin wani dadi na ratsa sansar jikinta da zuciyarta ," ina ma zasu kasance tare kamar yadda suka kasance a daren jiya ? duk da basu jiyar da junansu komai ba illa romacing dinta daya kwana yi .
Mikewa tayi ta faɗa saman katifa duk juyi sai ta tsinci kanta cikin yanayi na daban da bata taba tsintar kanta ciki ba sai akanshi ,ta san mijinta na daban ne acikin maza kuma na kece raini,sannan mijin yayi ne da kowace mace zata so mallaka har ma tayi alfahari dashi , "ki mika wuya kawai ummita ki rungume mijinki ,ki janyoshi jikinki ki bashi kulawar da zai soki ,ki manta komai kuyi rayuwarku ....
lamo tayi tana runtse idanunta da tunanin hanyoyi da zata bi domin mallake zuciyarsa da komai nashi ...
wuni ranar a kwance tayi shi cike da kewarsa sai dai har yammacin ranar bataji duriyarsa acikin bangarensu ba, shi kuwa yaki dawowa gidan ne saboda mama dan karta rutsashi da tambaya ..
Bashi ya shigo gidan ba sai gurin goma na dare kai tsaye part din mama ya shiga ya ganta kwance alamun ta soma bacci bai yi kokarin tashinta ba ya juya ya nufi dakin ummita, kwance ya isketa ta takure jikinta guri daya tana bacci cikin rigar bacci mai sharara kallo ɗaya yayi mata ya k'arasa shigowa da sauri ya haye saman katifa yana had'iye abinda ya tsaya masa a makoshi, ya kwanto jikinta ya kai bakinsa cikin kunneta ya soma hura mata iskar bakinsa kamshin turarensa ne ya kaiwa hancinta ziyara a hankali ta soma jin wani sanyayyiye dadi na shigarta ta sauke naunayen ajiyar zuciya sai dai ta kasa bude idanunta har sanda ya kamo ya kwantar daita ajikinsa suna fuskantar juna a hankali suke shaƙar numfashin juna kafin daga baya ya kai bakinsa dai-dai bakinta yana tsotsar pinky lips dinta har yayi nasarar cafko laulausan harshenta nan ta bud6e idanunta tarrrrr akan shi wata irin kunya yaji ta mamaye ilahirin jikinsa amman jin ta kai hannuwanta duka ta kamo fuskarshi tana busa masa numfashinta yasa ya sake rungumeta a jikinsa yana cigaba da sarrafa harshenta cikin bakinta cikin wani irin yanayi na shaukin juna suke exchanging numfashin , take yanayin fitar numfashinsu ya sauya suka rud'e tare da fita haiyacinsu , ya kai hannunshi kasanta yana shafa mararta zuwa pent dinta yana jin wani irin farinciki mara misaltuwa saboda jiyo tudun cikinta , cike da shaukinsa ta tura hannunta cikin sumar kanshi ta soma wasa da gashinsa tana sauke numfashi , wani irin numfashi yake fizgowa da karfi yana fitarwa, bai ankare ba ya ji ta cafke harshensa dake cikin nata ,ta soma sarrafashi tana tsotsar bakinsa kmr yadda taga yana mata , sai daya gama yamutsata sosai, da ragewa kanshi zafi sannan ya barta ya soma ƙoƙarin mikewa ta riko tafin hannunsa gam cikin nata tana narke masa ajiki tana fidda numfashi sama sama
da rausayar masa da fararen idanunta ,ya lura kwarai da zai dara daga abinda yayi zata bashi haɗin kai ,kokarin cire hannunsa yayi acikin nata amman taki sakar masa tana sake narke masa dole ya rankwafo jikinsa ya kai bakinsa cikin kunneta "menene fatlion ?
"Me kike bukata ?
Yayi mata tambayar yana hura mata iskar bakinsa cikin kunneta take tsigar jikinta suka mike gabadaya kamshin turarensa ya addabi hancinta da sake tunzira zuciyarta akanshi da matsanancin sha'awarsa ,yayinda iskar bakinsa da yake hura mata ya sake kashe mata jiki "kin yi shiru ki faɗa min idan akwai abinda kike bukata daga gareni saboda Ina son wucewa gida yayi maganar yana manneta da qirjinshi da tsura mata ido ,sai numfashi take fitarwa tana sake narke masa ajiki "baza kiyi magana ba ?
nan ma shiru tayi taki cewa komai duk da so take tace kar ya tafi ya barta ya kasance tare daita amman bazata iya furta masa haka ba ,
ta shige jikinsa sosai tana shaƙar kamshin turarensa ya daura hannunsa akan sumar kanta yana shafawa ahankalin zuwa gadon bayanta , ya zare hannunshi ya janyo blanket ya lullu'be mata jiki sannan ya sauko ya durkusa daidai fuskarta "zan wuce gida ki kular min da kanki ban da tsalle tsalle plz yayi maganar tamkar wani maraya "idan kina bukatar wani abu ki kirani tayi shiru tana mamakinsa "lallai namiji fa bai da kunya tsab ta gama karanceshi so yake ya mallaki jikinta cikin sauki sai dai ina bazata bari ba zata cigaba da rud'ashi kamar yadda yake rud'a mata jiki ..
*******
Hajiya rahma ke tafiya da baya da baya tana kokarin shigowa bukkan boka na isheri har ta karasa shigowa bukkansa sannan ta juyo da gangar jikinta tana kallo cikin bukkan inda ta iske bokan zaune babu komai ajikinsa daga shi sai wani dan kanfai da iya gabansa kawai ya rufe gabansa wani kasani acikin bakin dutse .
ya kalleta yana washe wakeken bakinsa tare da bushewa da mahaukaciyar dariya " shadiya yau kece a gari ?
"Nice aiki yanzu magani yanzu ta samu guri ta zauna can nesa kaɗan dashi tana kunshe miyon bakinta saboda warin da bukkan keyi "ya jikin alaja ? ya tambayeta cikin yaren yaroba yana jan layi biyu akan kasa da yatsun hannunsa .
" tana kan samun sauki dai "ai na faɗa mata abinda zatayi taki, daga karshe ma ta ɗauke kafafunta a gurina ,na faɗa mata zata samu lafiya amman lallai sai ta bada rayuwar mahaifinku domin nata rayuwar , hajiya rahma ta jinjina kai da girman al'amarin dan tasan wannan ba abu ne mai sauki ba , a yadda hajiyarsu ke son mahaifinsu ko farcensa ba zata iya bayarwa ba bare rayuwarsa ...
Boka ya soma buga kasa domin son sanin abinda ke tafe daita kusan minti goma yana aiki zana kasa sannan yaja wata ƙatuwar numfashi da ajiyar zuciya atare sannan ya soma magana cikin harshen yaroba "wannan yaron zai yi wahala ku iya mallakarsa kamar yadda kuke bukata saboda ta kowani bangare zagaye yake da tsari, iyayensa suna tsaye akanshi shima kuma haka babu yadda zaku iya dashi..
"yanzu babu abinda za'a yi yanzu ?
"Babu kuma duk inda kika je kudinki kawai za'a ci sannan ko anyi masa aiki daga karshe abun zai iya taba duka zuriaku saboda karfin addu'ar dake zagaye dashi ,dama baya tsaye gurin ibada ne akwai aikin da zanyi da kanshi zai dawo wanda
dawowarsa kuwa zai yi daidai da mallakarsa gaba-daya amman yanzu kije gida tukunna idan an kwana biyu ki dawo mu duba mugani "bama bukatar 'bata lokaci aiki mune bukata boka dan yar'uwata tana cikin wani hali taki ci taki sha ka sake dubawa idan akwai yadda za'a yi "babu shadiya idan akwai zan miki duk inda zaki akanshi kudinki za'a ci a banza irinsu asiri baya cinsu idan ma yayi tasiri na wani lokaci ne ..
Babu shiri hajiya rahma ta baro gidan boka tana surutai "yanzu me zata cewa suhaima bayan tayi mata alkwarin mah'ruf da kanshi zai dawo gareta ...
Jugun jugun sukayi a daki hankalinsu a tashe suna tunani mafuta dan kuka ma kasawa suhaima tayi sai dai idanunta sun kankace sun koma tamkar garwashin wuta naunayen ajiyar zuciya hajiya rahma ta sauke "ina gani mu dan dakata tukunan kamar yadda bokan yace "ni dai yayarmu kisan yadda za'a yi mah'ruf ya maida ni gidansa ta kowani hali ne ,ko kisa dady ya nemi abbansa ya bashi hakuri nasan muddin suka sa baki zai maidani.
"shikenan ki kwantar da hankalinki zan sanar masa idan Allah ya taimakemu ya maidake sai ki shiga hankalinki ,ki iya bakinki , kiyi taka tsantsa kiyi masa biyayyar karya na sha faɗa muku shi sihiri baya tasiri sai da biyyaya bawai da kun kama maza a hannunku shikenan ba ,ki kawar da idanunki akan duk abinda zai yi da yarinyar akwai makirci kala daban daban da zan koya miki ina tabbatar miki muddin kika rike biyyaya da waɗan makirci wallahi kina zaune zai dankarawa shegiya saki uku rasss ku matso kuji atare suka matso daga zulaihat har suhaima tayi musu rad'a kunne ,wani irin ihun dadi suhaima ta saki "dan Allah yayyarmu ki san yadda zaki yi na koma wallahi zanyi duk abinda kika ce nan suka cigaba da tautaunawa a tsakaninsu har yamma hajiya rahma na gidan, har sai data gana da mahaifinsu sannan ta bar gidan , faɗa dady yayiwa suhaima sosai sannan yace zai nemi Alhaji Ibrahim , bai yi sanya a gwiwa ba ya nemi Abba saboda shi kanshi baya jin dadin zaman ya'yansa gida gara sakin suhaima za'a iya gyarawa tunda saki daya ne , zulaihat ce dai sai hakuri .....
Abba yayi matukar mamaki jin bayanin dady daga karshe yace karya damu da izinin Allah kamar mah'ruf ya mayar da suhaima d'akinta ya gama ..
Karfe tara daidai Abba ya kira mah'ruf lokacin daya shigo parlour'n Abba , sai da gabansa yayi mummunar faduwa saboda ganin mahaifiyarsa da mama da injiniya har ma da Hajiya inna, guri ya samu ya zauna cike da biyyaya yana ƙoƙarin gaishesu inna tayi saurin katse shi "amman babana bansan tsami bane kai sai yau ta yaya dan rashin tunani , da rashin hankali zaka saki matar arzikinka, yarinyar mai biyyaya da sanin ya kamata da son yan'uwanka , shine dan ka iya wulakanci ka rasa wacce zaka saka sai ita sannan kayi mukut da bakinka da rashin hankali ...
tsaki yaja saboda takaicin maganar Hajiya inna ransa a matukar 'bace ya soma magana "kin san abinda tayi min da zaki zo kina damun mutane , wallahi idan kika hassalani zan mata mai gabadaya na huta .
" wanda ya fasa ya raina uwarsa da ubansa dan me shegen girman kan tsiya wa ka cuta kanka dan bazaka ta'ba samun kamarta ba ehee ..
"Hajiya dan Allah kiyi hakuri ki bari muyi abinda ya taramu anan kai kuma kar na sake jin bakinka idan bani na nace kayi
All Chapters
Chapter 1
Chapter 2
Chapter 3
Chapter 4
Chapter 5
Chapter 6
Chapter 7
Chapter 8
Chapter 9
Chapter 10
Chapter 11
Chapter 12
Chapter 13
Chapter 14
Chapter 15
Chapter 16
Chapter 17
Chapter 18
Chapter 19
Chapter 20
Chapter 21
Chapter 22
Chapter 23
Chapter 24
Chapter 25
Chapter 26
Chapter 27
Chapter 28
Chapter 29
Chapter 30
Chapter 31
Chapter 32
Chapter 33
Chapter 34
Chapter 35
Chapter 36
Chapter 37
Chapter 38
Chapter 39
Chapter 40
Chapter 41
Chapter 42
Chapter 43
Chapter 44
Chapter 45
Chapter 46
Chapter 47
Chapter 48
Chapter 49
Chapter 50
Chapter 51
Chapter 52
Chapter 53
Chapter 54
Chapter 55
Chapter 56
Chapter 57
Chapter 58
Chapter 59
Chapter 60
Chapter 61
Chapter 62
Chapter 63
Chapter 64
Chapter 65
Chapter 66
Chapter 67
Chapter 68
Chapter 69
Chapter 70
Chapter 71
Chapter 72
Chapter 73
Chapter 74
Chapter 75
Chapter 76
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 53 Chapter of 76