ba zubawa dukiyar fulaninta idanunshi , tayi saurin lumshe idanunta tana zumburo masa baki "dan Allah ka bari na sa kaya , ya harareta yana dallare mata baki sannan ya kai bakinsa saitin nata ya fara tsotsan lip's dinta har yayi nasarar bude bakinta ya fara tsotsa tamkar ya samu lolly Popp yana shafa sumar kanta zuwa qirjinta shiru tayi jikinta na rawa tana jin dadin yadda yake tsotsar bakinta ya kai hannunsa zai shafa qirjinta ta rike hannunsa gam tana girgiza masa kai idanunshi cike da shaukin qaunarta ya zare bakinsa cikin nata yace "why me yasa baki so na
ta'baki ? " Bana son abinda zai saka mahaifiyata cikin damuwa "kamar ya ?"kamar yadda hajiya Inna take buƙata, ya ja tsaki ke yanzu idan na ta'baki wa zai sani ko zuwa zaki yi ki faɗa mata ? "Ni dai a'a banaso, bana so bana son damuwa da tashin hankali ,ganin bashi da niyyar magana ta janyo rigarta ta zara daga kwance da take yana kallonta ta rufe masa abinda yafi kauna daga gareta ya kai hannunsa zai zare rigar ta saka masa kuka dole ya kyaleta zuciyarsa na tafarfasa ya janye jikinsa yana janyota jikinsa ya k'arasa saka mata riga ya mike ta riko hannunsa ya juyo "meye kuma ya faɗa a fusace? "ka bari t shirt dinka da wandoka ya bushe "baza'a bari ba ya fixge hannunsa a fusace ya maida wandonsa ya dauki rigarsa ya kakkabe ya zira ya fita daga d'akin ta sauke nannauye ajiyar zuciya ta rufe kanta da hula dan kar mama ta fahimci wani abu daban, ta fito daga dakin zuwa parloun kasa gabanta na fad'uwa bata ga mama ba ta zauna akan kujera tana tunani kala kala can kamar minti goma sai ga mama ta sauko tayi saurin cewa "mama da wani aiki zan soma dan na gama da wuri ?"kinci dan wanke ne ? ta girgiza mata kai "ki ci tukun sai muyi aikin tare,ummita ta yatsina fuska yama fita araina wallahi da dai ma zan samu mangaro ko tsamiyar biri mama ta bita da kallon mamaki " mangaro ko tsamiyar biri anya kuwa ba ciki ga ummita ba ?" Tace wannan tace wancan Allah dai ya taimaketa ba wani abu ne ya shiga tsakaninsu da mah'ruf ba ta shiga uku a gurin hajiya Inna ,ta matso da sauri ta zauna kusa daita ta kamo yatsun hannunta tana dubawa da idanunta "ciki ne dake ummita ? Tayi mata tambayar hankalinta a tashe .
Wani irin luguden bugu qirjinta yayi da matsanancin karfi a tsorace ta kalli mama "a'a wallahi mama bani da komai "kinga samu natsuwa wani abu ya taɓa shiga tsakaninki da baba ne ? ta sake girgizawa mama kai "ki bude baki kiyi min magana mana "wallahi a'a mama, haba mama kamar wata wawiya ina ji fa ina ganin abinda hajiya Inna take miki acikin gidan nan dan me zan aikata wani abu wanda na san zan sakaki cikin wahala,shiru mama tayi batai magana ba , Allah ki yarda dani wallahi babu abinda ya taba shiga taakaninmu "ni ba wai ina yaki da aikata sunanh ma'aiki bane ina jin tsoron fitinar tsohuwar nan ne duk da Allah shine abun tsoro "karki damu mama Allah babu komai banida komai, naunayen ajiyar zuciya mama ta sauke "bazan hanaku ba tunda ba haram bane ... "kai mama wallahi babu wannan a tsakaninmu muje muyi aiki , idan zakiyi aike kasuwa kisa azo min da mangaro tana tafiya gama ta faɗa kitchen mama ta bita da kallo" ummita yanayinki ya nuna kina dauke da ciki ,idan kici abinci sai kinyi amai ga yawon bacci da za'bar abinci ,duk abinda bakya ci da shi kike ci yanzu ta zan yarda ?"ta yadda ta rantse miki mana ai tasan mahimmanci rantsuwa kuma ma ta yaya baba zayi mata a ciki a gidan nan ? Kitchen din ta biyota .
*****
duk sati suhaimai take zuwa gidan gaishesu wanda rabin yinin tana yinsa ne a bangaren inna ko ta shiga bangaresnsu ummita bata dadewa bisa umarnin hajiya inna kuma duk shigowarta bata haduwa da ummita har ta gama abinda zatayi ta fita , shi kuwa mah'ruf duk abinda take bata burgeshi yanzu gabad'aya hankalinsa baya gareta yana kan ummita da cikin jikinta, ya zubawa sarautar Allah ido ne har sanda cikin jikinta zai bayyana kanshi yaga yaya hajiya inna zatayi zata yarda ummita ta tare a gidansa ko kuwa ?
Sannu a hankali cikin ummita ke fitowa kasancewar lokacin ya shiga wata na biyar ,kowa ya ganta yaga me ciki sak , a wata ranar asabar din karshen wata , suhaima ta kawo ziyara , ta soma da bangaren mama tana shiga ummita na karasa saukowa a take gabansu ya fadi, tayi sororo tana kallonta da mamaki ganinta , tayi saurin murza idanunta tana sake kallonta cike da mamaki saboda ganin abinda ta gani ,ummita ta kawar da idanunta akanta ta soma tafiya zuwa dining area da sauri suhaima ta karaso gareta tasha gabanta "ke meye wannan ajikinki kamar ciki "ummita ta watsa mata katuwar harara " uwar ciki ne ba ciki ba , ta sake kura mata ido "ta yaya ga ciki ina gani ki karyatani "ina ganin kin soma soma shaye shaye ko kuma haukan gado ya soma taɓa tunaniki shiyasa kikaga haka dan Allah Malama ki ban hanya na wuce tayi maganar tana bin gefenta da sauri suhaima ta fice daga dakin ta nufi bangaren inna nan ta shiga labarta mata abinda ta gani "ke suhaima ba dai ciki ba cikin lafiya kar kishi ya rufe miki ido fa? "wallahi inna ciki ne ajikin yarinya kuma na haihuwa "bari naje na ganowa idanuna idan kuwa ciki gareta da gaske zataci bantar uwarta a gidan ta fadi haka tana gyara daurin zaninta ta fita ta bar suhaima da zullumi da faduwar gaba "wayyohlly na shiga uku Allah kasa cikin bana mahruf bane ta furta jikinta na rawa .
kai tsaye part din mama hajiya inna ta shiga ko sallama batayi ba ta soma kwalwa ummita Kira "ke ummita kina ina fito nan munafurkar Allah, ummita data shiga kitchen d'aura Ruwan zafi ta fito tana yatsina fuska "lafiya kike min irin wannan Kiran mafarautan "Kiran uwarki da wadan can dangin uwarta take nake miki tayi maganar tana kura mata ido wani iri razanannen ihu ta kurma
"Dan uwarki cikin waye ajikinki a she da gaske ciki gareki makira uban wa yayi miki ciki ?
Kan kace me parlour'n mama ya sauya da mutane har mama da hajiya umma da hajiya saudat
"ba zaki faɗa cikin uban waye ajikinki ba yar banza, wato abun kunya zaki janyowa mutane a gidan nan ?Inna ta sake kurma ihu wannan karon har injiniya da Abba sun shigo sukayi cirko cirko suna mazurai " wayyohlly Allah na shiga uku duk irin tarbiyar da Ibrahim ya baki ki rasa abinda zaki saka masa dashi sai da wanna ......
"kinsan Allah ko fadi uban da yayi shiri shiri ya dirka miki ciki ko kuma yau kubar min gidan dana ke da uwarki bayan ki amshi takardar sakinki daga hannun jikana, ita kuma wannan shashar uwar taki ta amshi sakinta daga dana daga yau bana son ganinku cikin ahlina ,dan wallahi bazan zauna gida daya daku ba ....
"Kai Ibarahim ka saki mairo ko na tsine maka albarka muddin bata fadi wanda yayi mata ciki nan ba gabad'aya jin haka yasa ummita ta rude ta gigice idanunta suka rufe dan tuni hawaye ya ɓalle a idanunta ta matsa kusa da inna Dan tasan yadda abbanta ke gudun bacin ran inna zai iya yi mata komai ciki kuwa har sakin mahaifiyarta, bata jin nata sakin bakinta da jikinta suna rawa tace "
wallahi inna bani da ciki bani da komai ta ina zanyi ciki ?
"Ta uwarki da ubanki ta fixge hannunta da ummita ta riko " na rantse da girman Allah inna bani da ciki idan kuma tabbas inda shi to bansan wanda yayi minshi ba ta k'arasa gurin hajiya umma "dan Allah ummah ki faɗa wa inna gaskiya wallahi bani da ciki karta sa Abba ya saki mama gara ni tasa ya mah'ruf ya sakeni "dukkaninku za'a saka kuma a yanzu, ina bazai yiwu ba cikin shege a gidan dana .. ......
TWO FRIEND'S (BSBS)
💗💗💗💗💗💗
WANNAN CE
QADDARARMU
💖💖💖💖
💗💗💗💗💗💗
~TRUE LIFE STORY~
FREE NOVEL
AL'QALUMAN
*AYSHA A BAGUDO*
*FAIZA HAMMADU*
~DEDICATED TO~
*MUHAMMAD AUWAL JININ JIKINA INA SONKA FIYYE DA SON DA NAKE WA KAINA, ALLAH YA RAYA MIN KAI YA KARE MIN KAI A DUK INDA KAKE ,GABA'DAYANMU MUNYI KEWARKA JIDDAH MENAL UWA UBA NI , ALLAH YA DAUKA YA HASKAKA RAYUWARKA YAYI MAKA SUTURA*
WATTPAD @HAUESH
bismillahirrahmanirrahim
PAGE 53
... Gabad'aya mutanen dake tsaye a parloun hankalinsu yayi matukar tashe sannan fuskokinsu cike yake da matsanancin mamaki furucin hajiya inna ga ummita .
" dan me hajiya inna zata dinga irin waɗan nan magangun mai tattare da cin zarafi da tozarci akanta ? " ta ya mace da aurenta zata dinga tuhumarta ? kallon hajiya inna suka ci-gaba yi babu wanda yayi magana a cikinsu gudun jaraba da bala'inta .
A gigice cikin tashin hankali tace "kai injiniya kira min Ummu salama a wayarka kace tazo yanzu yanzu ina son ganinta , injiniya ya kalleta yana son yin magana ta d'aga masa hannu da sauri" dakata bance ka karanto min dogon turanci ba , abinda na saka kawai zakayi min idan kuma bazakayi bane ka sanar dani nasa wani ya kira min salama ...?
Take injiniya ya soma neman number aunty Kira ɗaya ta ɗauka ya isar mata da sakon hajiya inna tare da katse kiran ya tsaya rungume da hannuwansa ya zubawa hajiya inna idanunshi hankalinsa ya rabu kashi biyu .
"Ko cikakken minti talatin ba'a ɗauka ba sai ga aunty ta k'araso gidan hankalinta a tashe tace " me ya faru na ganku haka duk kunyi cirko cirko? babu wanda ya buɗe baki yace uffan sai hajiya inna "ina fa lafiya salama wannan yar iskar yarinyar ce take ɗauke da ciki ,abinda ya bani mamakin shine a ina ta samo cikin ita da ba tarewa ta yi a gidan mijin ba ?
" gata nan ta tsaye ta kafe mutane da idanuwa kamar na agolar nufawa ta gaya miki uban da yayi mata ciki dan wallahil azim baza'a likawa babana cikin shege ba tunda nasan ko giya iyamurai ya kwankwad'a bazai aikata komai da wannan abar ba ..
a lokacin daya abba da hajiya umma har ma da mama suka runtse idanunsu tsabar bakincikin jin kalmarta ta karshe, wani irin numfashi mama ta dinga saukewa mai haɗe da tashin hankali jikinta na daukar rawa ta bude idanunta ta zubawa Ummita tana kallonta qirjinta na dokawa " tabbas ciki ne ajikinta .
Aunty da ranta yafi na kowa ɓaci tace" haba hajiya inna ta ya mace da aurenta zaki ce a ina ta samu cikin ?
" a matsayinki na babba bai kamata kiyi wannan tunanin ba ,sannan ba abun mamaki bane aga ciki ajikin ummita bare har ki dinga dangata jikarki da cikin shege ..
Ummita ta matso kusa da aunty ta riko hannuwanta duka hawaye na zubowa daga idanunta "aunty ki fahimceni wallahi bani da ciki , dan Allah karki yarda da maganar Inna wallahi sharri take son min saboda bata sona ,bancin haka ta ina zan samu ciki ?
"Ta gidan uwarki da ubanki shegiya mai kan maciji , wallahi idan baki fad'i inda kika kwaso wannan abun kunyar ba sai kun bar gidan d'ana yau ba gobe ba irin tsiya irin jaraba kawai irin danasani har kullum bazan daina bakinciki hada iri da uwarki ba ,Kallon inna ummita take hawaye na cigaba da gangaro mata jikinta na mazari tamkar mai jin sanyi .
Jiki aunty a sanyaye ta riko hannu ummita cikin nata saboda rawar da jikinta yake "kin kwantar da hankalinki saboda cikin jikinki zai iya samun matsala , ummita tayi saurin girgiza mata kai wasu sabbin hawayen na gangarowa bisa kuncinta "bazan iya ba ! Bazan iya kwantar da hankalina ba aunty ,ki taimakeni duk abinda zai faru karki bari abbana ya saki mamana gara ni tasa ya mah'ruf ya sakeni.....
"shikena amman kiyi shiru ki natsu ki bar kukan nan haka bari na kira wanda zai raba wannan gardamar domin inna ta tabbatar da gaskiyar lamari .
" Wa zaki kira ?
inji cewar hajiya inna da maganar ta kaiwa kunnuwanta ziyara
"Mah'ruf zan kira dan shi ne wanda zai faɗi uban cikin jikinta , nashi ne ko akasin haka "
"Ke salama fita daga cikin idanuna na rufe, Kema an koya miki munafurci da makirci ko ?
"na kiraki a matsayinki na diyar cikina shine ɗan munafurci zaki d'aurewa karya gindi kice sai ma'hruf yazo ,yaron da kin san halinsa ko cikin banashi bane haka zai kakabawa kanshi , wallahi karki soma kiran shi dan ko an kira shi cewa zai yi nashi ne ni kuma ko sama da kasa zasu haɗe bazan yarda a lika masa mugun iri ba, ki dai tambayeta uban da yayi mata ciki ....
nan take zuciya ta ɗauki ummita ta saki hannu aunty tayo gurin inna dake tsaye tana yatsina fuska "wai hajiya inna me na kashe miki a rayuwar duniya ?
"me nida mahaifiyata muka tsare miki a rayuwa?
" wace irin tsana ce wannan ? "wace irin kiyayya ce haka ? idan ma kina tsanar mahaifiyata dan ta kasance yare nifa me nayi miki tunda daga tsatson d'anki na fito ?
"Baki sona baki son ganina cikin farinciki ,kin fifita sauran jikokin akaina kin fifita bare akaina me nayi miki ? "Ban cancanci ki tsaneni ba saboda ni din jininki ce kece kika haifi mahaifina , kina kin mahaifiyata amman ita tana sonki kullum .... "mahaifiyarta tana miki biyayya, tana gudun 'bacin ranki duk abinda kike mata bata taɓa d'aga ido ta kalleki bare ta furta kalmar ta gaji dake ba , hajiya inna ya kamata a ce kin rangwanta mata wannan kiyayyar da ki ke mata wacce ta ja nima kike min ....
kuka take sosai tana farfad'awa hajiya inna duk magana da tazo bakinta mama ta k'araso gareta cike da sarewa "Ummita kiyi shiru bana son sake jin bakinki idan kika sake fad'awa hajiya inna wata kalma bazan yafe miki duniya da lahira ba, ta kare maganar tana zubar da kwalla mai zafi tana jin wani zafi a qirjinta bazata iya cigaba da ɗaukar wannan nauyin ba dole ta bar zuri'a hajiya inna haka ,koda kuwa hakan zai zamo sanadiyyar rasa rayuwarta ......
Baka jin sautin komai a parloun'n sai na sheshekar kukan ummita a hankali mama ta isa gaban hajiya inna zuciyarta na zafi "kiyi hakuri inna dan Allah bazata sake ba...
"Dakata........
hajiya Inna ta katseta tana kallonta shekeke "ni za'a kawowa gulma da munafurci da tsigudidi da annamimanci wanda aka gada sai da yarinya ta gama ɗebe min albarka sannan zaki ce baki yafe ba ,Allah yasa ki tsine mata karewa rashin yafiya wannan ba matsalata bace matsalarki ce da ita kadai gareki , ciki kuma sai dai kusan yadda zakiyi dashi dan wallahi babana bazai amshi cikin da banashi ba .
"hajiya Abba ya kira sunanta ban ce ka saka baki ba idan kayi kuskuren saka min baki zan tsine maka wallahi "Idan kuma kafi bukatar tsinuwar tawa ne bismillah , take Abba yaja bakinsa yayi shiru gumi na cigaba da tsatsafo masa ta ko'ina ajikinshi bai taɓa bakinciki da nadamar kasancewar hajiya inna mahaifiyarsa ba sai yau , zuciyarsa zafi take masa a hankali gefen kanshi ya soma sarawa ya kai hannusa ya dafe goshinsa yana jin wani irin zafi mara misaltuwa "ya Allah wannan wace irin uwace gareni ...? "Allah kaga halin da nake ciki Allah ka kawo min ɗauki da gaugawa..
"Haba Inna abinda kikeyi sam bai dace ba duk fa abinda kayi na alkhairi ko sharri kanka kayiwa ba wani ba , sakayyar duniya kuwa tun a nan duniya yanzu ake ramawa mutun "to zageni agabansu suji dadin zagina daman ai kune kuka fara bada kofar zagina a gidan nan , ku dana haifa kun zageni waye ma ba zai zageni ba ?"ku cigaba da zagina har muhammadu Abdullahi mahdi ya bayyana , Allah yasa kuma kun haifa duk abinda kuka min shi za'a yi muku, "inna lillahi wa Inna lillahi rajiun suke furtawa gabad'aya jikinsu na ɗaukar rawa tare da zubewa a gabanta injiniya yayi ƙoƙarin riko hannunta ta fixge a fusace haka ma aunty "karki soma kai hannunki jikina ke kaɗai Allah ya bani mace acikinsu amman baki da amfani agurina , har ki tsaya gaban waɗan nan kina faɗa ina faɗa ai ke kika bawa wannan jairar damar zagina ku cigaba da zagina karku daina ta karasa mgnr tana zubda kwalla katseta aunty tayi "kiyiwa girman Allah kiyi hakuri Inna ki fahimceni ,wallahi wannan cikin na jikin ummita na mah'ruf ne shi ....
"Dakata Allah ya isa ban yafe miki ba tunda kika ce cikin shi ne ,kuma kika sake cewa cikin jikinta na shi ne na rantse da girman Allah zan tsine miki salama ....
Babu abinda Abba da injiniya suke furtawa sai kalmar Inna lillahi wa inna ilaihi rajiun , idanunsu ya rikide yayi jazir , ita kuwa hajiya umma bakinciki da takaici ya hanata magana ta juya ta kalli inda suhaima ke tsaye kamar wata photo copy tana kallon kowa tana nad'e magana , a matukar fusace tace "tsayuwar me kikewa mutane, ana maganar family issues meye naki na tsayawa ?
"Maza kama gabanki ta karasa maganar da tsawa,tsawar da hajiya umma tayi ne ya dawo daita haiyacinta take jikinta ya kama rawa simi simi taja jikinta a sanyaye ta fice tana addu'ar Allah yasa cikin bana Mah'ruf bane dan idan cikin ya kasance nashi wallahi sunan shi zubabbe , tana fita umma ta bar parlour'n itama zuwa part dinta ..
Ko second biyu ba'a yi da fitar Hajiya umma ba sai ga ma’aruf ya shigo, a natse yake kallon kowa daya bayan daya sanye yake da blue jeans blueblack da t-shirt ja mai kwala, yayinda kwalar ke zagaye da kalar blueblack da bakin hannun rigar kamar yadda wandon jikinsa yake , kallo ɗaya yayi musu ya fahimci kalar tashin hankali da suke ciki .
Gaba-daya ya maida hankalinsa akan mama saboda fahimtar da yayi kuka take, da idanunshi ya soma tambayarta abinda ke faruwa bata iya ce masa komai ba har sanda ya maida idanunshi kan ummita wacce ta dawo tamkar wata zautacciya tana sambatu .
aunty ta kira sunanshi a tsanake "babana..........
ma’aruf ya waigo a hankali zuwa inda take durkushe gaban hajiya inna ka samu guri ka zauna, ya kasa bin umarnin aunty dan babu abinda yake son ji sai abinda ya sa mamansa kuka da fatlion dinsa ,kusan minti goma ma’aruf yaki zama yana tsaye qirjinsa na dukan tara tara .
A hankali aunty ta soma magana kamar haka "a halin yanzu hajiya inna taga ciki a jikin matarka shine take son sanin cikin waye a jikinta ,naka ne ko akasin haka ...?
Parlour'n ya sake d'aukar shiru baka jin motsin komai sai na sheshekar kukan ummita kowa so yake yaji abinda zai ce , ya tsurawa ummita idanunshi cike da tausayawa itama zuba masa rauraunun idanunta tayi wanda suka karaya cike da tashin hankali "kayi shiru kana kallon mutane cikin waye ajikin matarka ?inji cewar injiniya yayi maganar a fusace ......
"Karku matsa masa ku gigita shi ya fad'i abinda ba daidai ba ,kai babana kalleni nan ka faɗa min cikin jikin ummita na waye ?ya sake yin shiru yana kai hannunsa bayan keyarsa ya tsosa yana mai tsananin jin kunyar mama dake gabansa wacce ta langwa'bar da kanta idanunta cike da kwalla .....
"Karka cuci kanka ka faɗa min gaskiya duk da nasan cikin nan ba naka bane amman zan so naji daga bakinka ..
Idanunsa ya ɗauke akan mama ya tsaida akan hajiya Inna "nawa ne Inna ,cikina ne a jikinta na tsawon wata biyar da sati biyu wata irin zabura hajiya inna tayi daga zaunen da take ta mike tsaye tana dubansa jikinta na rawa.
"cikinka ?
Lumshe mata idanunsa yayi tare da d'aga mata kai alamun eh .
"Shikenan hajiya inna kin ji gaskiyar lamari daga bakinsa dan ha.......
tasss tasss kake ji akan kuncin injiniya daya soma magana , yayi saurin zaro idanunshi waje tare da dafe kuncinsa "kai na tambaya dan ubanka ? ko da kai nake magana ? Tayi maganar a fusace sannan ta dawo gaban ma'hruf ta tsaya kyam tana huci "kai kalli cikin kwayar idona ka sake maimaita abinda ka faɗa yanzu ,dakewa yayi yana kallonta cike da dakiyar zuciya yace " Allah Inna cikina ne ajikinta "Inna lillahi wa inna ilaihi rajiun "a gidan ubanwa kayi mata ciki d'aukarta kake zuwa hotel ko me ?
Ya watsa mata harara "ta ya zaki min irin wannan tambayar nida matata ta sunnah, koma a ina nayi mata tunda nace nawa ne ba shikenan ba nifa banason matsala da damuwa, to meye ma abun tara mutane kan ɗan wannan abu saboda Allah ? Kamata yayi ki kirani ni dake na fahimtar dake ba wai .....yayi shiru ya kasa karasa maganar saboda idanun mama dake yawo ajikinsa dan
tunda ya soma magana idanunta ke kansa sai data yayi shiru sannan ta sunkuyar da kanta tsabar kunya da farinciki daya lulku'beta, ta dinga jin kamar kasa ta tsage ta shige ciki sai dai me yasa ummita zata karyata maganar a lokacin data tambayarta ?" me yasa zata karyata hajiya inna alhalin tasan gaskiya, dan taya za tayi ciki batare da ta aikata abinda zai sa cikin kasancewa ba ? "Har da rantsuwa akan bata da ciki kai dan yau sai dai ka barshi kawai ,ta fadi hk a cikin zuciyarta .
ummita kuwa wani irin shock ne ya kama ilahirin jikinta ta tsaya tamkar wata wawiya tana kollon bakinsa da yake musu bayani cike da mamaki , take hajiya inna ta rusa ihu da kuka a lokacin daya .... ..
Abba da injiniya kuwa hamdala suka dinga yi a cikin zuciyarsu tare da bawa hajiya inna hakuri, katsesu tayi cike da maseefa "ku daina bani hakuri munafukan banza kawai tayi maganar kamar wata zautacciya ..
ummita na gama jin bayanin mahruf wanda ya tabbatar musu da cikin da hajiya inna take magana akanshi gaskiya ne ta sake shiga rud'ani da tashin hankali "yaushe hakan ta faru bata sani ba ? a sanita dole sai mace da namiji sunyi auratayya sannan za'a iya samun ciki ta ya ita nata cikin ya samu babu auratayya ?
"Kai impossible wannan cikin ba gaskiya bane ,dan haka bai taba faruwa a tsakaninsu da mah'ruf ba bare ya kai ga ciki ,ya dai faɗa ne kawai dan ya kareta daga maseefar hajiya inna amman ina ita ina wani ciki ana zaman kalau "
aunty tace " inna ki daina kuka yarinyar nan fa matarsa ce halak malak da jama'a suka sheida haka ,ciki kuma na faɗa miki gaskiya saboda ni na dade da tabbacin cikinshi ne saboda tun lokacin da cikin ya samu ma’aruf ya zo har gida ya faɗa min sai dai yace kar na sanar da kowa......
"Amman kuwa kin cuceni salama kinsan da wannan abu shine kika boye min saboda baki kaunata "ba haka bane inna sirrinsu ne wannan "ki min shiru munafukar Allah ,shi sirrin yaci kutumar ubanshi Allah ya isa ban yafe ba "kai kuma munafuki kana tafiya suki suki kamar mutumin kirki ashe sharri ne fal acikinka ya d'age mata girasa ɗaya yana cizan lip's d'insa na kasa alamun meye illar abinda yayi ...
"Ai dole kayita zariya a bangarensu tunda an yi maka d'and'ani haukaci kana zariya kamar zatiyar wando wallahi zaka san ni kake dagewa gira, dan wallahi sai na baka mamaki akan wannan ganganci da kayiwa rayuwata ,sau nawa ina maka kashedi akan haka ?" kace kiyi maganarki a banza na d'auketa .....
Juyawa Ummita tayi bayan ta gama jin bayani hajiya inna tana kuka ta nufi d'akinta nan take ma’aruf ya biyo bayanta yana kiran sunanta "fatlion ! fatlion !! taki tsayawa ta shige d'akinta .
ko da ma’aruf ya shigo dakin ya sameta tsaye ta bawa kofar d'akin baya tare da rungume hannunwanta duka a qirjinta tana kuka...
ya k'araso kusa da
All Chapters
Chapter 1
Chapter 2
Chapter 3
Chapter 4
Chapter 5
Chapter 6
Chapter 7
Chapter 8
Chapter 9
Chapter 10
Chapter 11
Chapter 12
Chapter 13
Chapter 14
Chapter 15
Chapter 16
Chapter 17
Chapter 18
Chapter 19
Chapter 20
Chapter 21
Chapter 22
Chapter 23
Chapter 24
Chapter 25
Chapter 26
Chapter 27
Chapter 28
Chapter 29
Chapter 30
Chapter 31
Chapter 32
Chapter 33
Chapter 34
Chapter 35
Chapter 36
Chapter 37
Chapter 38
Chapter 39
Chapter 40
Chapter 41
Chapter 42
Chapter 43
Chapter 44
Chapter 45
Chapter 46
Chapter 47
Chapter 48
Chapter 49
Chapter 50
Chapter 51
Chapter 52
Chapter 53
Chapter 54
Chapter 55
Chapter 56
Chapter 57
Chapter 58
Chapter 59
Chapter 60
Chapter 61
Chapter 62
Chapter 63
Chapter 64
Chapter 65
Chapter 66
Chapter 67
Chapter 68
Chapter 69
Chapter 70
Chapter 71
Chapter 72
Chapter 73
Chapter 74
Chapter 75
Chapter 76
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 55 Chapter of 76