Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
karatu Daya suka karanta ba aikansu ya kawosu gari Daya kuma Halayyansu da Dabi"ansu tazo Daya Shiyasa Bond Din kawance su har yanzu yana nan Zakiya Babba ce awajen tana matsayin Matakiyar Md kenan Wato Manaja Shiyasa Tunda Dina ta Shigo ma"aikatar take ta samun gaisuwa yake kawai Take Tana Daga Hannu Domin bata Cikin Hayyacinta Gudu Gudu Sauri Sauri ta karisa ga Babban Office din zakiyan wanda ya zama Tamkar gidanta Wajen Zarya kamar yadda Shima Office din Dina na asibiti ya zama Dandalin Zakiya din. Tana Shiga ta isketa Hakimce kan Kujeran ta mai Juyawa da Mutum din nan katon Office ne wanda bayan katon Tuberin aiki da kujerun karban baki akwai Kujeran gida wadanda Suka karama Ofishin kwanya sai karamin Firaza sai Kofar Tiolet inda Mutum zai Shiga in Lalura ta kamashi. Dina na Shigowa ta Watsar da Key din Hannunta da wayarta Saman Daya Daga Cikin Kujerun wajen ta Nufi Fridge din ta Bude Ta Dauko Ruwa Swan mai Sanyi akwai kananan Kofuna a kife saman Fridge din ta zari Daya ta Tsiyaya ta kafa kai Tana Sha Cikij gaggawa Duk zakiya Dake Hakimce Tana Waya idanuwanta na kanta,Sai da Ta kusa Shanye Rabin Ruwa kana ta Dakata tana Sauke Numfashi Lokaci Daya kuma ta maida komai Cikin muhallinsa ta Baro Wajen zuwa Kujeran Dake Fuskantan Zakiya ta Zauna Tana maida Wani karamim Numfashi. Ita kuwa Zakiya kai ta Cigaba Da kadawa Tana kuma Wayarta Lokaci Daya Kusan Mintina goma da Shigowar Dina Office din ammh bata gama ba sai wani narkema wanda Take wayar Dashi Take tana Tsarashi Da kalamansu na yan Duniya Ran Dina ya Fara baci Ta kai Duba Zuwa ga Agogon Guccin Dake Tsitsiyan Hannunta Lokaci Daya Ta saki Tsaki Tana Fadin"Ko in koma Inda na Fito ne..? Tafada Tana Sakarma Zakiya manyan Idanuwanta Mirmishi ta Saki Tana Girgiza mata kai Kafin Tayi Saurin sallaman wanda Suke wayan Lokaci Daya Tana kallon Dina Cikin Shakiyanci Take Fadin"Dr Dina Gaddafi Sheerif...' Karamin Tsaki Dina Taja kafin Tace"Karki Batamin Rai..wai don Allah zakiya yaushe zaki Daina Harka da yan Barikin nan Tsoffin Banzan nan ne..? Me kike nema Kudi..? Suna..?matsayi..? Duka fa Allah ya baki Zakiya Wannan Rayuwar Da kikeyi sam Bata Dace da mace mai aji kamar ki ba..! Wani Shu"umin Mirmishi Zakiya Tayi kafin tace"Allah ko.? Ke bari ni nayi Tsoffin Banza Da kike mgana Duk fa yan Siyasan munr mu Dina gwara na karbe kudaden Tunda Duka kudin aikinmu da"aka basu suke Shashancin Dasu,gwara na karbi Rabona Domin ko Dangote na zama a kudi Wlh bazan hakura Da Nema ba Dina Kudi Sune Rayuwa Kinji..! Tafada Tana wani Rausayar Dakai Dina ta gyara zama Tana Fadin"Yan Siyasa fa kikace Zakiya..? Zakiya tace"Yes Sufa nace..Ai sune yan Harka ke bari nayi Miki gwari Gwari Wlh Duk yan Siyasan kasan nan namu Kadan ne na Allah Sauran duk yan Bushashe ne.."Da sauri Dina Tace"Ammh banda Ubana ko..? Wata Shegiyar Dariya Zakiya ta Saki Harda Buga Tebur kafin ta Dakata Tana kallon Dina Cikin Iya bariki ta Daga mata Gira Tana Fadin"Ammh ai kema kinsan Barewa batai gudu Danta yayi Rarrafe ba ko.? Cikin wani irin kallo Dina Tace"Bangane ba..! Zakiya ta kara wani Sakin Dariya kamar Wata Shashasha Tana Fadim"Dina kin sanni na sanki...Zan tsage miki gaskiyata kema zaki Tsagemin ita koda bazatamin Dadi ba ki Rantse da Allah me mahaifinki ki zuwa garuruwa yanayi da Sunan Taron Siyasa..? Shifa ba Dutse bane Tun muna yara sai ya Shafe sati Bashi agida to yana ina..? Ke Namiji fa sunansa Namiji Tawajena ni kin ganni nan Ko Ubana ban yarda Dashi ba Ballatana Uban Wata..! Ta karishe Fada Tana sakin Wata karamar Dariya Tsaki Dina Ta saki Kai ta Dauke tana Fadin"Zakiya bana som iskanci..Ni Dad dina ba irin Kazaman Da kika saba bi bane...Na yarda dashi Taron Siyasa yake zuwa Fakat..! Zakiya na Dariya tace"Yes Shima ya yarda Dake..Aiki kika zo Bauchi ba Sheke ayarki kikeyi keda Dr Zain ba ko...? Tafada Tana kallonta ido kawai Dina ta sakarmata ta kasa Mgana Ganin Haka yasa Zakiya ta kara saka Dariya Kafin ta Tsagaita Tana Fadin"Is Ok....Tuba nake Tawan Babanmu ba Dan isk..! Bata karisa ba Dina Ta Wawuri Wani Littafi ta wargeta Dashi kaucewa Tayi Tana karamar Dariya Tana Fadin"Ahh..Meyayi zafi haka..? Toh Allah baki hakuri ban karawa Tawajena..! Tafada Tana kokarin Hadiye Dariyarta Cikin Kufuluwa Dina ke Fadin"Ammh dai kinsan ance mu Nemi Duniya kamar bazamu barta ba ko..? Zakiya TaDaga kira Tana Fadin"Yes haka kuma muke Neman lahira itama kamar bazamu Risketa ba.."Hararanta Dina Tayi Tana Fadim"Toh ke Ai Duniyar kadai kike Nema kin manta da zaki Lahiran Wata Rana..! Zakiya Tace"Duniyan Dai muke Nema Ba nake nema ba..Duk wani Zunubi Danake aikatawa kema kina aikatashi Dina Kinga kuwa miye maraban Dambe da Fada ai Duka Sunansu Fada..! Dina Takadai kai Tana Fadin"A"a muna da Bambamcin Ni Tunda Nake wa Zain kadai na yarjema Gonata Zakiya kinsani ina Son komai nawa ya kasance Specail ne ke kuwa nayi nayi na Raba ki da Rabama kowa ni Jig and Jag Jikinki kinki jina Zakiya in ma Kina so ne kiyi irin nawa ki Zabi Wani Daga cikinsu kawai kice ya Fito kiyi auranki yafi Wannan Rashin Madafan..! Zakiya Ta Daga kanta Sama na wani Lokaci kafin Tace"Ai Duka Zina Zina ce Dina..Da wanda yasha Giya ta Dubu Daya da wanda yasha ta Dubu Dari Duka Dai sunanta giya sukasha.Dake da kike Harka da Mutum Daya Dani Da nake baza Hajata Duka A mizanin sunan Zunubai Daya ne Dina ko ki yarda karki yarda Tare zamu gyara Halinmu im ma Haka kikeso kice..mganar kuma na samu wani na Aura nifa ba wanda yamin ne..Dama zaki mim Hanya na samu wannan Cute and Handome Dan"uwan Farkan ki dinan Allah zan Tuba na Bishi muyi Aure na Tabbata yadda Zain yake Cika ki tsaf nima na Tabbata zai Cikani Har ya kure Kwadayina..! Tafada Tana yar Dariya Hararanta Dina Tayi Tana Fadin"Karma ki saka ma Ranki..Domin wannan Haddir din sai yafi Zain Taurin kai...Kullum.Fuskarsa ba Fara"a ba Ke ba,nikaina ya Tsanane kamar ya Fahimci da wani Abu Tsakanina da Dan"uwansa in ya ganmu Tare ya Dinga Hararata kenan Kamar na Tsaremai wani abu.! Zakiya Ta Tabe baki Tana Fadin"Kinga Abunda yasa naki yarda da Shawaranki kenan..Ka tsayama Namiji Daya ya zame maka Ciwon ido gwara ki barni Ahaka gida goma mganin kashe Gobara."Kai Dina ta Jinjina kafin Tace"Allah ko ya kyauta..! Zakiya Tace"Nagaba..Domim wannan ya Riga da ya Faru..Lafiya na ganki a Hanzarce..? Tafada Tana Tsareta da ido kai Dina Ta Dafe kawai batare da Tayi mgana ba Cikim Mirmishi Zakiya Tace"ZAIN again..? Kai Dina ta gyada mata Cikim Rauni Tace"Zakiya kin sani Kaf Duniya Ba Namijin Da nike so kamar Zain..Ammh kuma Shi yana Bani ciwon kai kullum Kalaman bakinsa bai Taba sona ba kuma bazai Taba Aurena ba Mace Daya yake so kuma itace Kadai matarsa Firstlove Halima Zakiya na Tsani jin Wadandan Sunayen zuciyata na kuna Jiya nan mukayi Fada dashi wai kamar ni Zaim zai kalla yace Bayajin Dadina Halimarsa na Sakashi Kuka Tundaga Farkon Dare Juz Imaging fa Zakiya Ni Wai Zaim ke Fadama haka Nida maza Dadama suke son na basu irin Damarshi ban basu ba ammh Shi ya samu yana min Wulakanci yana Hadani da wannan Banzar matar Tashi Wacce Daga ganinta Jikinta ba Ruwan da yake isanta ma Ballatana ta jika wani Dashi..! Tafada Cikin Jin Haushi da Kishi Dariya Zakiya ta saki Har tana Mikewa Tsaye Galala Dina Tayi Tana kallonta ganin Yarda Take Dariya kamar wani Abun Dariya ta gayamata Cikin Takaichi ta kauda kai sanin Halin Zakiya na Dariyan mugunta Tana Cikin dariyan ne ta kware Ta Fara Tari Cikin Kufuluwa Dina tace"Allah ya kara.! Da karfi Fridge Zakiya ta Nufa ta Bude ta Ciro Ruwa ta kafa kao Tasha sai da ya isheta kana ta Sauke Goran Ruwan Tana Sakin Ajiyar rai Cikin Mirmishi Dina Tace"Gud...Dama ai mganin mai Dariyan mugunta kenan..Nakawo miki matsalata ammh Sai kika Fara min wannan Banzar Dariyan Taki..! Zakiya ta murmusa kafin ta kariso Ta zauna Kujeran Dake fuskantan Dina gab Da gab Cikim Danne Dariyanta Take Fadin"Ya zanyi..? Wlh Nakasa Danne Dariyata ce Wai Shi Zain din yace ke baki sakashi kuka Daga Farkon Dare sai Matarsa..? Tafada Cikin som karta Saki Dariyanta Cikn Jin Haushi Dina Tace"Wlh..Jiyan nan ya Fadamun wai ya gaji da Tararrayanmu..Dama na gaya miki koda yaushe Cikin Fadin haka yake so yake na Rabu da Dashi yaci Bulus Zakiya ni kuma Kinsani Duk Duniya Zain kadai nake so kuma Shi nake mafarkin ya zama Mijina ko Ta Halin kaka...! Zakiya Tace"Ikon Allah ai bai Kamata ki Damu ba Sanin Dama Aikin Boka ne ke Tafe dashi. ammh ba Domin Haka ba da Tuni ya Rabu Dake..."Dina ta Rausayar Dakai Tana Fadin"Duk nasan wannan Zakiya plz ki gayamin ya zanyi..? Wlh bazan iya Rabuwa da ZAIN ba Shine kadai Namijin Dake gamsar dani..! Zakiya Tace"Dama ai bazaki Rabu Dashi ba sai mun kai ga Nasara.."Ido Dina Ta sakarmata kafim Tace"Taya..ya..? Help me kaina ya Dunkule waje Daya baya wani Motsi...! Mikewa Zakiya Tayi Ta kariso Kusa Da ita Lokaci Daya Ta Dafa kafadanta Tana Fadin"Alluran planning din da kikayi na How many Month ne..! ? Kai Tsaye Dina Tace"Harkin mata..? Tare fa mukayi na Six Six Month ne..! Zakiya Tace,"Ban manta ba So nake na kara Tabbatarwa..In ban manta munci Almost 4 month kenan Tana mana aiki ko..? Kai kawai Dina Ta Dagamata alaman eh Cikin Sauri Zakiya Tace"So ina so Indan Ta gama aikinta ajikinta karki sakeyi mujira mugani...! Da mamaki Dina ta Dago Tana kallonta Cikin som karin Bayani Lokaci Daya Tana Fadin"Kar na sakeyi kuma.? Kinsan me Hakan ke Nufi..? Zakiya Tace"Yes naasani..Ba Ciki kike Tsoro ba..? Kai Dina ta gyada mata Tana Fadin"Eh mana..Kinsan Zain ya gargadeni akan Hakan Tun Farko...! Wani Mirmishin Mugunta Zakiya Ta saki kafin tace"Toh ai da Cikin zamu Amfani mu Razani shi..Tunda na Lura yana Tsoron Danginsa Da Matarsa Wacce yafi so baya so Taji Labarin yana Tarraya da wata mace awaje..Duk Shaidar da zamu Tanada Bata kai Shedar ki Mallaki Kwan Haihuwarsa a maranki ba Dina Kuma Dole in Mgana ta kai kunin Manyansa su Zauna su sassanta mganar Domin na Tabbata baza su so wannan mganar ta Fita ko Domin kada kimarsu da Darajansu ta Zube akan Idanuwan Duniya ba..! Ta karishe Fada Lokaci Daya ta Juyo Tana kallon Dina Wacce tayi Shuru Tana kallon Zakiya kafin Zakiya tace"Ya kika ga wannan Salon..? In yasan wata bai san wata ba Tawan..Kuma kin manta Boka daman ya gayamana kafin Auranku yaga Turniku da Duhu..? Toh ai wannan yakin da zai Faru Shine Duhun Tabbas za"a kai Ruwa Rana Rayukan wasu zasu baci..Wasu zasu Raasa kimarsu Dayawa ammh mu bamu damu ba Koda mun Rasa namu kimar Daman chan ba wata kimar garemu Wajen Allah ba Indai Burinki zai Cika na mallakan Zain na yarda Duniya ta Shaida bamu da Wata Cikakkiyar kima Kura ce Lullube Daman da Fatar akuya..! Tafafa Tana wani kada mata Hannunta Ajiyar rai Dina Ta Sauke kafin tace"Hakan kina ganin bazai Taba Siyasar Mahaifina da kujeransa ba..? Zakiya Tace"In Macijin yayi mana Taurin kai ne Mganar zata Fasu saboda bamu da Zabi..Ammh in ya nuna yana son Sulhu zaku Sulhu iya ku Biyu ammh kuma ki Tuna Hakan bamai yuyuwa bace Dole ne Shima yarasa kimar Dayake Takama Dashi in ko Hakan ta Faru Dole ne Labari ya Fasu...indai kin Zabi Kujeran mahaifinki To ya zama Dole ki Yi Hakuri Da Cikar Burinki Dina..! Shuru Dina Tayi tana wani Tunani kafin ta Sauke Tagwayen Numfashi Tana Fadim"ammh kada muyi Saurin Datse ma Macijin kai Zakiya..Gwara mu Fara Datsan ganganar Jikinsa koda mu Rabasa da Kansa ne batare da Mun kashesa ba.' ! Zakiya Ta saki Dariya Tana Fadin"Wato Dai mu Fara Sare Macijin kafin mu Sare kansa kenan.? Kai Dina ta Gyada mata Kafin Tace"Haka nake Nufi..!kai kawai Zakiya Ta Jinjina kafin Tace"Shikenan komai na Hannunki..' Daga haka suka Cigaba da Tattauna mganar sun Jima Kafin Dukkansu su Shirya su Fita Tare Dina cikin asibiti Ta koma Ita kuma Zakiya Gida ta wuce Zatayi wanka Ta Shirya Tana da Bako. ***** Gabda Kiran Sallar mangariba Halima Tagama Komai Zobo Take Hadawa Taji Kiran wayanta Daga Falo Mirmishi Ta saki Sanin Firstlove ne ke kiranta Zobon Tagama Hadawa kana ta Dauka ta saka Cikin Fridge yayi sanyi Abincin Datayi kuma Farar Shinkafa Miyar ganye Mai kifi sai Ferfesun Pepe Kitchen wanda Tayi Saboda Firstlove nan Kitchen din ta bar komai Saboda Tana so Sai ta koma Daki Tayi wanka Tayi sallah kana sai Tazo Ta jera komai kan Dinning ta goge Kitchen Din Inda ta bata. Da Sauri ta Fita Daga kitchen Din Zuwa Falo Katon Talabijin Din Dake kafe Shi yake ta aiki Shi kadai kan Center Table Din Dake Tsakiyar Dakin Ta Hango Wayarta Da Sauri ta karisa ta Dauka kenan wani Kiran ya kara Shigowa Fuska Ta bata ganin Sunan mai kiran *UKTI ZAFEERA..*! Cikin Tura baki Ta Daga Kiran Tana Fadin"Dillah ji yarinyar nan ta sakani gudu nifa da naji Kiranki na Zata Firstlove ne....!Tafada Tana wani Tura baki kamar Wata karamar yarinya Dariya Dagachan Bangaran Zafeera Ta saka kafin Tace"Ehhe..Kaji masu Firatlove...Mu da bamu Dashi Allah ya bamu Ukti..! Halima ta saki Dariya Tana Fadin"Ameen Ukti kefa kikayi sanya Ina Barrister Ahmed yake..?Meyasa baki bashi Dama ba yana Sonki Wanchan Satin Alhaji Tsoho ke Fadamin yaje ya gaisheshi Da wani aiki ya Shigo Dashi Garin..'! Tabe Baki Zafeera Tayi Dagachan Bangaran Tana gyara Zaman System din Dake gabanta Cikin Basarwa tace"Yayi kokari..Ukti ya gida..? Ya kuma Yaya Dakta yake..? Naga Kiranki Dazu ina Cikin makaranta ne Shiyasa na bari sai na Dawo Gida na Kiraki..! Halima Tace"Komai lafiya Ukti to ya karatun.? Ya su Inna Rukayyah Ina Shema..? Zafeera Tace"Shema ta Shiga wanka..Nima yanzu na Fito Dayake ko Mintoi Ashirn bamu yi da Shigowa Gida ba.."Halima Tace"Allah ya Taimaka Ukti nayi kewarka yaushe zaku samu Hutu..? Zafeera Tace"Nima ina matukar Kewarki Ukti..Wlh sai nan da 2 Month inaga domim ko Test bamu Fara ba.."Halima Tace"Muma bamu Fara ba..Kuma ina ta ma Firstlove nacin yakai ni kano Wajenki yaki Maida kai akan mganar..! Zafeera Tace"Dama ai bazai barki ba Ukti..Kim manta Tun muna Gabansu Umma Sai inda ya Zabar Miki..? Dariya Suka saka atare kafin Zafeera Tace"Ahki Faruq na gaisheki Ukti Dazu ina School ya Kirani mukayi Vd call.."Tsalle ta Buga Tana Fadin"Don Allah..? Kice kinga Mutanen Chicago..! Zafeera Tace"Wlh..Kinga yadda ya zama ya kara Kiba da Fari.."Halima Tace"Allah Sarki Shine ni bai kirani ba.."Ta fada Cikin Shagwaba Zafeera Ta Saki Dariya Tana Fadin"Ho..Ni kuma Kishiyarki ba..Toh Yace ya Kirani bai sameki ba ya Kira Yaya Dakta kuma yace kina Gida Shi yana asibiti..! Halima Tace"Shikenan ya Fita...Nima zan Kirashi mu gaisa Wajen wata Biyu Rabon da muyi mgana Dashi.."Zafeera Tace"Nima kinsan yanayin karatunsu na lauyoyi Tunda ya Dage sai yagaji Dadyn Abuja.'Dariya Halima ta saki Kawai Lokaci Daya kuma suka Sarke Hiran Jin ana Kiran Sallar mangariba ne yasa Halima tace"ke wai hala baki Sallah ne..? Dariya Zafeera ta Sheke Dashi Tana Fadin"Au da kin zauna ne..? Nifa Shehi yayi min Tawa.."Halima tace"Banza Allah ya isana.."Dariya Zafeera ta kara sawa Tana Fadin"Dama Ai chan Allah ya Isa mana.."Halima Tace"Naji ni ba wannan ba Ukti Dama ina Son ganinki mgana nake so nayi Miki.." Zafeera Ta natsu Tana Fadin"Ko..? Toh ina jinki ko sai kinyi Sallah ne..? Halima Tace"Bari mu Fara mganar Tunda naji yanzu Wasu masallatan suke kira...! Jin Haka yasa Zafeera ta Ture Laptop Din gabanta ta mike Tsam Ta Fice ganin Shema"u ta Fito Daga Tiolet,ita kuma Zafeera macece mai Zurfin Ciki bata yarda kowa yasan Cikinta in ba Umma ko Halima ko Faruq ba,Koda Shema ta kasance Diyar Inna Rukayyah bakomai nata ta sani ba Fita tayi zuwa Falon ganin Duka yaran Mazan sun Tafi massallaci Matan kuma sum Shiga Dakumansu yin Alwala Inna Rukayyah ma Tana Dakinta kan Daya Daga Cikim kujeran Falon Ta zauna Tana Fadin"Ina Jinki Ukti..Na Fito Falo ne..! Mirmishi Halima Tayi kafin tace"Kan mganar Barrister Ahmed ne meyasa bazaki Bashi Dama ba Zafeera..! Naga yana sonki kuma Naga Dadyn Abuja da Alhaji Tsoho suna yabonsa Sunce Dan Gidan mutumci ne kuyi Auranki Ukti na Tabbata zai barki ki Cigaba da karatunki..! Numfashi Zafeera Ta saki Kafin Tace"Uhm..Ukti Nifa ba wai ina kin Ahmed bane..Kawai dai Mazan wannan zamanin ne baka gane kansuu baka san abunda ke cikinsu ba kuma Abun ke ransu dabam Abunda bakinsu ke Furtawa Dabam.."Da Sauri Halima Tace"Bangane ba..? Zafeera Ta gyara zama Tana Fadin"ina Nufin Acikinsu Dai dai ku ne keda Amana..Sai mace Ta gama yarda dasu Daga baya su Ci Amananta Ukti zuwana Kanon nan naga Casess na mazan da sukaci Amanar Matansu Daga Karshe suka bar matansu da Ciwon Zuciya Da Damuwa Shiyasa Maza suka Fita kaina na ke musu kallon Duka Halinsu Daya..! Da Sauri Halima Tace"Ammh banda Firstlove dina ko? Na Tabba Kin Shaida Bazai taba Cin Amanata ba.."Zafeera Tace"Ba zan iya sani ba Ukti bar ganin Yaya Dakta na yayana kema yar"uwata ce ta Jini Dole na gaya miki Gaskiya bansani ba Tunda Nidai Zahiransa nake gani ba Badini ba..Ammh dai karki saka komai acikin Ranki Ki kyautatamai Zato..' Jikin Halima yayi Sanyi Cikim Rauni Tace"Yanzu kina so ki gayamin kema kina Tunanin Wata Rana Firstlove zai iya yin wani Abu nacin Amana agareni Ukti..? Da sauri Zafeera Tace"A"a Ni wlh bance ba Ba kuma Haka nake Nufi ba..Nace bansani ba..Ammh Mu kyautamai Zato Ukti ni na Shaida Kaunar Yaya Dakta agareki Insha Allahu makamanciyar cin Amana bazai Taba gitwa tsakaninku ba.." Jin Tayi Shuru yasa Tace"kinji Ukti Don Allah karki Damu plz..! Ajiyar Rai ta Sauke kafin Tace"Shikenan...Zan kiraki zuwa gobe mu karisa mganar bari naje nayi wanka da Sallah Firstlove na Kan Hanyar Dawowa.."Kai Zafeera Ta gyada kafin tace"IS ok..Akulamin da Yayana Dakyau.."Dariya kawai Tayi ta katse Kiran Tsaye kawai Tayi Tana Tattara maganganun Zafeera gefe Daya kuma tana gamashi Dana Laila sai take ganin Kamar Abu Daya suke Nufi gabadaya Jikinta sai yayi sanyi Dakyar ta karisa Cikin Bedroom Dinsu ta Fada wanka bata Fito wanka ba sai da Ta Dauro alwala tazo Ta shafa Lotion Dinta Ta Zura Doguwar Riga ta Tada Sallah bayan ta Idar ne ta karisa gaban Wardrope Ta bude ta Dauko Riga da Sikat dinta na wani Atamfa mai kalan Ja ta saka ta karisa gaban madubi ta kashe Dauri ba wata kwalliya tayi ba sai dai kayan sun kamata kwarai sun Fitar mata da Sirrin kyanta,Turare ta saka a ko"ina na Jikinta kana ta Fito Daga Bedroom din. Karo suka kusa Yi da Zain wanda ya Sawo kanshi Cikin Bedroom dinsa Dauke da Suit dinsa a Hannun Dayan kuma yana Rike da wayarsa da Key din Motarsa Baya Taja Tana kallonsa Shima kallonta yake Cikin mamaki bai samu Zarafin mgana ba tace"Yaushe ka Shigo..? Kai Tsaye yace mata"Yanzu na Shigo..! Ido ta Rausayar Tana Fadin"Kwata kwata banji Bude get ba da Shigowarka ba."Cikin mamaki ya sakamata Ido kafin ya Fara taku zuwa gareta Cikin Tsare ta ido yace"Meke Damunki ne Firstlove..? Kai Ta Dago Tana kallonsa Tace"Me ka gani...? Cikin Sauri yace"U look so Silent Ba yadda nasan ZAINA ta ba.In taji Dirin Motatana zata Fito da Gudu ta kamkameni Abunda tasan yafi komai Sakani Farinciki kenan Fara Tozali da kyakyawan Fuskarta da kuma jinta acikin Jikina."Sai da ya Fada Taji Tayi wani Gibi Daga Abunda ta saba Cikin Sanyi Jiki kawai Ta Fada Jikinsa Batare da tace komai ba Shima azuciyar Zuciya ya saki kafin ya Saka Hannu Daya ya Rumgumeta yana Fadin"I Love u Firstlove In kika Bar Rayuwata Wlh zan lalace ne..! Tana Jinsa Saboda Jikinta a sanyaye yake bata iya cemai komai ba Sun Dade haka kafin ta Dago Daga Jikinsa Rigar Hannunshi ta  Karba Tana Fadin"Muje kayi wanka..Daman ban gama Jera abincin saman Dining ba..' Tayi gaba yana Binta abaya Cikin mamakin ganin yanayinta ayau kuma da Safe lafiya Kalau suka Rabu Har Tailet ta Shiga Ta Hadamai Ruwan wanka kana Ta Fito Ta Tayashi Ciro kayan Jikinsa Ta Daura mai Towel ta Rakashi Har Cikin bayin kana ta Fito Shidai da kallo yake Bita yana so ya karanci meke Damunta taki bashi Dama,tana Dawowa ta Tattara kayan Daya Cire Zuwa Cikim Wardrope dinta Bangaran inda Take Tara kayan wankinsa,Ta Rufe ta Fice Daga Bedroom Dim kichen ta koma ta Dauko komai ta Jera Bisa Dining kana ta koma ta Gyara Kirchen din ta Fito kenan sai gashi ya Fito da wata Bakar Jallabiya mai Gajeren Hannu Mirmishi ya sakar mata Itama ta maida mai Kafin ta karisa ta Riko Hannunsa Zuwa Saman Dinning Din Taja mai Dayan Daga Cikin kujeran ya zauna Ita Tayi Sarving Dinshi Har sai da yace Ta barshi haka kana ta koma Kujeran Dake kallonsa ta zauna itama Taja Filet ta zuba Daidai Cikinta. Cikin mamaki yakura mata ido Ganin Haka yasa ta Lamgwabe kai Tana Fadin"Bai yi Dadi bane abincin Firstlove..? Kai yaGirgiza kafin yace"Ko Daya....Kawai naga wani Chanji Tare Dake ne Firstlove wanda Banta gani ba..! Ido kawai ta sakamar Batare da Tayi mgana ba Shi kuma ya cigaba Da Fadin"Na Dawo ba"asan na dawo ba..Na biyu kuma Tunda mukayi Aure indai ina Gida baki da wajen zama sai kan Cinyata ni nake Ciyar dake Da Hannayena Firstlove ammh yau sai naga kin samu Kujera kin zauna kin kuma Dibi naki abinci ke kadai zaki ci..Sai na Fara Tunanin wani irin laifi ne mai Girma na aikata miki..? Wanda ni acikin Raina ina jin da na Bata miki gwara ke kin batamin Firstlove..! Ya karishe Fada yana Tsareta da mayun idanuwansa kai ta Kauda gefe bata iya Juran kallonsa Kanta na kasa ta Dago Tana Fadin"Allah bakomai Firstlove karka Damu..! Cikin Mamaki ya ijiye cokalin Hannunsa yana Fadin"Kinga bana son gaddama ban gane kada na Damu ba.? Ya bazan damu ba alhalin ga damuwa nan ta bayyana atare dake..?ki gayamin Abunda ke Damunki Firstlove in har kin Daukeni Abokin Rayuwarki..! Yafada Cikin Nuna Ransa ya baci Kai ta Rausayar kafin Tace"Babu Abunda ke Damuna Firstlove Belive me..! Fuska ba walwala yace"Na yarda Dake Fiye da yarda na yadda Dakaina..Ammh Damuwar Dake Fuskarki ta macece..? Ido Cikin Ido Ta Dago Tana kallonsa ba Zato ba Tsammani yaji tace"Firstlove don Allah zaka iya cin Amanata watarana..? Zaka iya barina Watarana saboda Wata.? Karishe Fada kai Tsaye Tana kallonsa wani irin Dam! Dum! Yaji gabansa ya amsa Cikin Waro Ido yake kallonta Tuni kuma yaji zuciyarsa ta sake Ta fara Tunanin kodai Tasan wani Abu Dake tsakaninsa Da Dina ne..? Daya shiga goma bama uku ba...! *Yan group din ZAINAZAIN BAND1&2 Bakwa sharhi kalilan ne masu Comments kuma gashi Kun cika Groups din duka ko ku gyara ko kuma Duka na kakkabe ku nayi Sabbin Zubi...* *Shakira...* . *ZAINAZAIN..!* _(Is a love Story and Betrayal)_ *Wattpad:Jamilaumar351* *Mallakar:Janaftyshakira*❤️ *BOOK 1*           0️⃣9️⃣ Cikin In ina da Tsoro da kuma Fargaba Hade da Faduwar gaba Zain ya Tattaro mganar da take Kan Harshen Bakinsa yace"Wa...n..wannan Wata irin Mganace ko nace Tambaya kuma Firatlove..? Waya gaya miki Watarana Ni Zainullahi zan Guje ki saboda wata...? Yafada kai Tsaye yana kara Tsareta da manyan idanuwansa Itama Shi take kallo Cikin Son karantar yanayinsa Ganin yadda mganar ta Dakesa ne sai yasa Ta saki Wani Kayattacen Mirmishi Tana Fadin"Kaima kaji Dukan Zuciya ko..! Kaji ka Razana da mganar ko...? Nima Haka naji Firstlove Lokacin da Laila Take Fadamin na Rage Sonka na Rage yarda Dakai saboda kai Namiji ne Watarana Duk Yadda ka kai da Rashin Son ganin Raunina zakayi Sanadiyar bayyanarsa..! Ta Fada Manyan Idanuwanta na kawo Cikar kwallah mamaki ya kama Zain da maganganun Zainarsa Cikim Mutuwar Jiki yace"Laila kuma..? Dama ita ta gaya miki Watarana Zan iya barinki Saboda Wata..? Ya karishe Fada yana wani Hade Rai Cikin Karaya da Rauni Tace"Bata ce bane....Misali Ta bani Da kuma jin Tsausayina kada Hakan ya Faru dani Watarana..! Cikin zafin Nama ya Daga mata Hannu yana Fadin"Kaji min Yarinya da Gulma..? Da ina kallonta yarinya mai Hankali Shiyasa na barki kike kawance da Ita Banta Zatonta Zatayi Sanadiyar Tsarwatsamin yardanan Danayi Shekaru ina gina ta ba Firatlove..! Ya karishe Fada yana wani karya mata Wuya Cikin Wasa da Spoon Din Hannunta Tace"Ba ita kadai Ta gayamin Haka ba..Ukti Ma na Tambayeta kan tana ganin zaka iya Cin amanata Watarana..? Kasan wata amsa ta bani..? Zuwa Lokacin maganganun Zainar Tasa Sun Fara Bashi Tsoro Cikin Tsoro da jarumta Duka Lokaci Daya ya Girgiza mata kai alaman bai sani ba Cikin Mutuwar

Chapter 9 of 32