Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
Halima Dakinki ki gayamata komai Ya kamata tasani yanzu.."Ba musu goggo Halima Tabi bayan Hajiya Mama Daman Ta kosa Taji me ya Faru Ga kuma Tashin Hankalin Data ke ciki na Takardan Zaina,Suna Tafiya Alhaji Tsoho ya juya yana kallon su Mama safiya Lokaci Daya yana Fadin"Hannatu da Rukayyah da Wasu Cikin yan"uwanki su Dauki Hamdiya Zuwa Dakinta Saboda kunga suna Waje suna Jiranku ba Dadi..Ku Tafi ku kaita Dakinta Allah basu zaman Lafiya.." Suka amsa da Ameen Jiki a sanyaye kafin Alhaji Tsoho ya Juya Ya kalli Haddir yana Fadin"Kai kuma Hadiru ka kara Komawa ka Dudduba Hanya da kuma Tasha..In Allah yasa batayi Nisa ba Shikenan in kuma Tayi Allah ya Tsareta aduk Inda zata je...Kaddaran Data Fadamana kenan sai Hakuri.."Haddir ya gyada kai yana Fadin"To Alhaji Tsoho.."Ya mike kenen Zain Shima ya mike yana Fadin"mu tafi Tare Haddir..! Da Sauri Alhaji Tsoho yace"A"a Koma ka zauna..Ina zaka Cikin wannan Halin..? Cikin Karaya da Muryan kuka Zain yace"Taya Zakacemin na zauna alhalin Matata Ta bace ba"a ganta ba..? Bazan zauna ba din sai naje Wlh.."Yafada Harda Rantsuwa Cikin Fada,Alhaji Tsoho ya kada kai yana Fadin"Kai Bashir kamasa ya zauna..Ba inda zaka nace Zainullahi.." Zain zai kara mgana Baban kaduna ya Hanashi Da Fadin"Kaga koma ka zauna Jiri fa kake gani koma ka zauna.."Zain ya koma ya zauna yana Fadin"Baba Firstlove ce Fa tace wai Tatafi..? Ina zata..? Kuma fa Tace Tana da Ciki Baba Bata da inda zata Baba kabarni naje na Nemota.."Abba ya kauda kai yana Sharan kwallah Daddyn Abuja ne ya Dafa kafadarsa yana Fadin"Karka damu za"a ganta da ikon Allah.." Shuru kawai Zain yayi ya maida Fuskansa Kan Tafukan Hannuwansa yana Rera Siririn kuka,Haddir yamike zai Tafi Zafeera Ta Mike Tana Sharan kwallah Tace"Zan bisu Alhaji Tsoho.."Da Sauri Umma ta mike Tana Fadin"Nima zani.."Da Sauri Alhaji Tsoho yace"A"a ke Fatima ki zauna..Kai Hadiru ku Tafi da Zafeera.."Kuka Umma Ta saka Zareena ta Riketa Tana Lallashinta. Haddir da Zafeera suka Fice da Sauri Suna Fita Yan Kai Amarya suka Fara Fita Zuciyoyi ba Dadi ba wanda yabi Takan Dina Da Zakiya inna Rukayyah da Inna Hannatu sai Dangin Mama Safiya,da Mom iklima Suka Tafi da Hamdiya Kawayenta Tun dazu wasu abokan ango suka yi gaba Dasu Inna Halima kuma Tana Dakin Hajiya Mama tana ta Sharan kwallah Bayan Hajiya Mama ta gayamai komai Tana Fadin"Wauta ne ke Damun Halima in banda Sarkaci Data saka kafa Tatafi ina zata..?Tana da Inda yafi nan ne..? Allah Sarki Hajiya Fatima kin cika uwa Nagari.."Take Fada Tana kuka Hajiya Mama na bata baki Su Umma na Falo suma suna nasu Kukan Domin Zain banda kuka da sambatu ba abunda yake,Jin kiran salla yasa Alhaji Tsoho yace kowa yaje yayi sallah Su Umma suka koma Ciki su Abba suka Fita Zuwa sallah Harda Zain din wanda Baban kaduna yake Rike Dashi Gabadaya baya gani Sosai In ya sakesa zai iya Fadi Sambatun ambaton Firstlove kadai yake gwanin Tsausayi da kuka, Mama Safiya kuma Sauran yan"uwanta suka Fara Shirin Tafiya Alhaji Tsoho Dakinsa ya koma Cikin Damuwa Domin yayi sallah. Dakyar Umma Tayi sallah sai kuka Take Tana Rokon Goggo Halima Kan ta yafemata itace Sillan komai ita kuma Goggo Halima na basu hakuri Nene da zainab har sun Share Hawayensu Kowa kagani Cikin Damuwa Mama Safiya sai Fadi Take Allah ya bayyana wannan yarinyar,Dina kuwa da zakiya ba wanda yasan Fitansu Sai dai aka ga basu Ashe Zakiya ce Taja Dina suka bar Gidan ganin Tana kuka Tana neman kara ja musu Abun mgana Gidanta ta kaita Tana Mata Fadan meyasa Ta cika Mtaala ne..? Yadda yau gidan Ya Rikice Daman gashi ana Jin Haushinta sai ace itace ma Sanadiyar Tafiyar ma Halimar. Bangaran su Haddir kuwa haka suka Dawo ba wani Labari mai Dadi Wannan Labarin ya sa sai da Zain ya kara Suma Cikin Daukewar Numfashi Hankula suka kara Tashi an Daukesa Zuwa asibinsu Kenan Ita ma Umma ta Suma sai da aka sakamata Ruwa Gida ya Rikice ko abinci ba wanda yabi ta kai Dangin Mama Safiya ganin ba Lafiya suka yi sallama suka wuce bayan Sunyi Fatan Allah ya bayyana Halima. Zain ya Shiga Doguwar Suma ne Dakyar aka Daidaita Numfashinsa aka sakamai Oxygen su Dr.Imran ne sukayi Attending dinsa Domin Dr.Haddir ya kaasa Tabuka komai Saboda Tashin Hankali Daki na musamman aka kai Zain Su Abba Duk suna asibitin Tare da Zain harda Zafeera kowanne kagani Hankali atashe acikin Zukatansu kuma Rauni ne Da kuma Fatan Allah bayyana Halima Abba kuma Yaji Tsausayin Zain dayasani da Tuni ya yafemai inda yasan haka zai Faru Daya saka baki Umma ta bashi Matarsa da Duk haka bai Faru ba addu"a kawai yake Allah Tada kafada Baban Kaduna kuma wani Abokinsa ya Kira Dake aiki nan Gidan Tv na garin Bauchi Ya gayamai Bacewar Halima Bashi da Hotonra Haddir ya saka ya Turamai Hotonta da kayan Dake Jikinta da kuma Cikakken Sunanta,Shima bai da Hoton nata awayar Zain dake Hannunsa ya Cira ya Turamai da Cikakken Bayanin Zaina din ko Allah yasa za"a dace yadai ce yanzu zai saka Duka Cigiyan In da Rabo za"a dace ko kuma wani yazo yabada Bayanin ya ganta. **** Bangaran Zaina kuwa Tana Ta Tafiya sai da Taga tayi Nisa da GRA kana ta Tsaya Tana Haki Domin ta Dade batayi Tafiyar kasa haka ba,waige waige ta Farayi saI kuma Lokacin Tunanin ina ta Nufa yazo mata Tana Tunanin Bayan Gada da kano Bata Taba zuwa ko"ina ba sai ko Lagos kuma yanzu bai kamata Taje ko Daya Daga Ciki ba Tana wannan Tunanin ne Taji mai adaidaitan Daya Tsaya gabanta yana Fadin"Hajiya Tafiya ne..? Kallonsa Tayi Sai kuma ta Juya Bayanta Tana tsoron kada ayi Saurin ganin Takardan nan abiyo Sawunta Sai kawai Taji bakinta ya Furta"Tasha zaka kaini inda zan samu Motar barin garin nan.."Bai damu da yanayinta ba Yace ta Shigo ya kaita da Sauri ta Shiga yaja suka Tafi,Tun acikin adaidaitan TaFara Kuka Tanayi tana Sharan kwallah basu Dauki Lokaci ba sai gasu Cikin Tasha Suna Zuwa mai Adaidaitan yace"Gamu Tasha Hajiya ina zaki ne Hada..? Cikin Muryan data Shake da kuka Zaina tace"Ina zani kuma..? Nima bansani ba.."Da sauri mai adaidaitan ya waigo Yana kallonta kafin yace"Topha..Baki sani ba kuma..? Cikin Sharan kwallah Zaina Tace"Eh ammh nan Motocin ina ne..? Mai adaidaitan yace"Motocin Lodin Bauchi Zuwa Fambeguwa da garuruwan Dake wajen har Zaria sai kuma na Bauchi Zuwa Zaria da kuma ta Zuwa kano.." Cikin Wani Sanyi Zaina Tace"Zaria..? zaria ta kaduna State.."? Mai adaidaitan Cikin mamaki yace"Kwarai Hajiya.."Zaina na kara Kallon Kudin Hannunta Tace"Bari na Hau ta Zarian.."Da sauri mai adaidaitan ya Fito yana Fadin"To muje na sama miki Motar.."Jin haka yasa ta Fito Tana Bin Tashar da kallo Tunda Take bata Taba zuwa tasha ba yau ga Dalili ya kawota Dankwakinta Ta warware ta kara Nanndawa aka Ta Rufe Fuskarta Dakyau Tabi mai Adaidaitan zuwa wajen da Motocin ke fake suna zuwa wani Dan Union  mai adaidatan yayi mao mgana Shi kuma yace mai Motar zaria Ko me yaceme.?sai ya juyo ga Zaina yana Fadin"Kinji yace Ba Motar da Zata Zaria Direct sai dai ki Hau Ta kano in kinje chan zaki samu ta Zarian Direct.." Zaina Bata da Zabi Sai kawai Tace"Shikenan.."Mai adaidaitan Ta kallah Tana Tambayanshi Kudinsa yace"Dari uku ne.."Dubu Dayan ta Dauka Ta bashi ya Fasa ya bata Chanji yana mata Allah ya kiyaye Hanya tace Ameen ta Wuce Tabi Bayan Dan Union din yana Fadin ko Tana da kaya ne..? Tagirgiza kai kawai Har wajen Mota sukaje Kiran Sharron Ta kusa Cika Sauran Mutum Biyu Ta Cika akace ta Shiga ta zauna Ta Shiga Ta zauna Tana jin wani Hawaye na cika idanuwanta Tana Shiga sai ga Wani yazo Ya Shiga Ba Jimawa kawai suka Tashi Sun Fara Tafiya kenan kwandasta yace kowa ya Hado kudin Mota Cikin kasala lokaci Daya Tana kara Rufe fuskata tace"Nawa ne kudin Motan..? Cikin Sauri kwandastan yace"Dubu Biyu ne Hajiya  kudin Motanki zuwa Kano."Waro Ido Zaina Tayi Gabanta na Faduwa Lokaci Daya tana kara kallon Kudin Hannunta Dubu Daya da Dari bakwai,kallon Kwadastan tayi Shima yana kallonta yace"Yadai Hajiya..? Cikin In ina Zaina tace"Don...Allah...ka..min hakuri...Kudina bai kai ba Dubu Daya da Dari bakwai gareni na zata iyakarsa 1500 ne.."Cikin kallon Sannu ko Kwandastan ya Bita Dashi kafin yace"Lalle nema kaji wata yar rainin wayau oga..? Direban Dake gaba yana Driving ya waigo yana Fadin Lafiya nan kwadastan ya kwashe komai ya gayamai Direban daman Dan Shaye Shaye ne yace"Bari na Tsayamu Sauketa..Karya Take Yanzu haka irin yan iska nan ne Masu Zuwa bariki bada kafar Dama ba.."Kwasdastan yace.." Daga ganinta kuwa oga."Yafada yana kallon Zaina wacce ta Dukar dakai Tana Hawaye Gabadaya hankalin yan Motan ya koma kanta kowa sai Tofa albarkacin bakinsu suke Tun alokacin  Zaina Taji ta Fara Nadaman Wannan Fitowar Datayi ganin Direban na shirin Tsayawa ne yasa wani Dake zaune agaba Tun Dazu bai ce komai ba ya ciro 300 ya mika ma Kwadastan ta baya yana Fadin gashi nan ya cikamata Suje Allah ya kaisu lafiya Sai Lokacin Kwandastan da Direba suka yi Shuru ya karbi kudin yace Zaina ta kawo na Hannunta ta mikamai sai Hararanta yake maida kanta Tayi kasa kawai Tana Hawaye Lokaci Daya Tana Share Hawayenta da Gefen Damkwalinta. Cikin Ikon Allah Wajen 3:00pm na Rana suka isa kano Saboda Rashin Mutumcin Direban Nan ko Tasha bai kai Zaina ba ya Sauketa nan Bakin Hanya Da yan Motan suka mai mgana yace Shi haka kurum bai yarda da ita ba Tunda dai an zo kanon Shikenan Zaina Taji ta Muzanta Sosai ko Tsayaawa ma Batayi ba Ta Juya ta Fara Tafiya yan Motan suka Bita da kallo wasu na Fadin gaskiyan Diraben ne Suma basu yarda da Zaina ba kamar wata mara gaskiya nan dai suka wuce suka Barta Tana ta Tafiya akasan Abakin Titi Motoci nata wucewa da Adaidaita Tafe take kawai Tana kuka da Nadaman Fitowarta Tana Tunanin ko Ta koma gida ne..? Ammh ina Taga kudin Mota..? Ina zata..? Wa zata Nufa..? Inda ma take bata ma sani ba Kuka kawai take Tana Sharan kwallah kamar an ce ta Juya sai ga Wata golf da sauri ta saka hannu ta tsaidata ta Faka agabanta Sai taja ta Tsaya Direba ne amotan sai wani a agefensa sai Wata Mace abayan Motan ita kadai ta Hakimce,Dukowa Direban yayi yana Fadin"Hajiya ina Zuwa..? Da Kamar bazatayi mgana Ganin Abunda wanchan Direban yayi mata ammh sai tace"Za...Zaria zani.."Da Sauri yace"Ikon Allah muma ma chan muka Nufa..Hajiya Don Allah bari na kara Mutum Daya.."Daga Bayan tace"Bakomai.." Ya Bude Ma Zaina gaban Motan yana Fadin"Kai bawan Allah gyara mata..Ta zauna ke Shigo.."Zaina tayi kwalkwal kafin tace"Ammh sai dai ka Taimaka min bani da kudin Mota.."Wani sakaran kallo Shima ya Bita dashi kafin yace"Allah ko..? Daman har yanzu akwai masu wannan Taimakon..? Gaskiya kiyi Hakuri ni Sana"a na Fito ba Taimako..". Da Sauri Zaina Tace"Don Allah ka Taimakamin.."Ta Fada Tana Hawaye karamin Tsaki yaja kafin ya Taka Motarsa yana Fadin"Kiyi hakuri kila mai Taimakon yazo.."Yana Shirin Tafiya ne Matar Dake Baya wacce ke Kallon Abunda ya Faru Tace"Ka Dauketa..zan Biya.."Da Sauri ya juyo yana Fadin"Zaki Biya fa Hajiya..? Ta gyada kai Cikin Washe baki yace"Shikenan Hajiya..Ke Shigo ki godema Allah hajiya ta Biya miki.."Jin haka yasa Zaina ta Sauke ajiyan zuciya ta kama Murfin Motan ta Shiga Tana Sauke Numfashi Idanuwaanta duk sun kumbura saboda kuka Sai da Ta Daidaita zamanta Tana matsawa Domin Taga kafadanta na Gogan Namijin Dake kusa da ita sai da suka Fara Tafiya kana ta waiga Bayanta Tana Fadin"Nagode Haji...! Mganarta ta makale ne Ganin Wacce Direban ya ke kira da Hajiya Wata kyakyawan Farar mace ce mai kyau Gata Fara ga Dogon Hanci da Tsukikin baki,Tana Sanye cikin Shigar Doguwar Rigar material Buba wacce Taji Stone work Kayan Jikinta masu Tsada ne haka kunnuwanta da Hannayenta duka Sanye da Zinare,ta saka wani Jan Vail Ta yane kanta Dashi Kamar yadda Takalmin kafarta yake ja haka Jakarta ma Dake gefenta Ja ce mai Tsada Dogon Hancinta yana Sanye da Hudun Hanci,Kallo Farko in kayi mata zaka Fahinci Tana da Zubi Da Fulani,Sannan kuma karamar yarinya ce mai akallah Shekaru 25 aduniya Tana Zaune Cikin Mota ta Hakimce Kamar Wata Sarauniya. Kara Waro Idonta Tayi Tana kallon Zaina Bayan ta Kauda Idanuwanta Daga Taba wayarta Cikin Basarwa ta kalli Zaina wacce ta saki baki da Hanci Tana kallonta Haka kurum Taji Matar ta Burgeta Cikin Sanyin Murya Tace"Bakomai..karki damu..! Tafada Lokaci Daya Tana Cigaba da latsa wayarta Cikin Sanyin Jiki Zaina ta Daina kallonta ammh Lokaci Bayan Lokaci Tana kallonta Ta madubi kuma In Matar ta Dago suna Hada ido,Haka kurum taji Matar kawai ta Burgeta Ganin Farko Da Tayi mata Haka suke Tafiya Zaina na kallonta ta Madubi Itama in Ta Dago sai Su Hada ido Ganin haka yasa in sun Hada ido sai ta sakar mata Mirmishi Domin bata san Dalilin Yarinyar ba na yawan Nacin kallonta Shida Saura na yammah suka iso Zaria ta Sabon gari suka Shiga Wajen Bayan gidan iya ya Sauke wannan Namijin sai itama Ta Hajiyar tace ya Sauketa nan Fakawa yayi ta Bude Mota ta Fito Tana Bude Jakarta bandir din yan Dubu Dubu Ta Fito Dashi ta zari Guda 15 ta bama Direban ya karba yana Ta Godiya,Wucewa kawai Tayi Tana wani irin Taku Lokaci Daya Tana Tsaida mai Adaidaita Baki zaina ta saki tana kallon Mace iya mace wacce ta mallaki komai na ajikin Mata,Direban ne ya katseta da Fadin"Ke wai ina zaki Sauka ne..!? Da Sauri Zaina Tace"Nan zan sauka.."Kallon Mamaki yayi mata kafin yace"toh ki sauka mana ko kina Jiran sai nace ki Sauka.ne..?."Batama Tsaya Jinsa ba Ta Bude Murfin Mota Ta Fita Tana Kallon Kyakyawan matanan ta Tsaida Adaidaita ta Shiga Direban bai bi ta kanta ba ya Wuce yana Murnan ya samu kudi a asama. Tsaye Zaina Tayi Tana kallo Matarnan Adaidaitan Data Hau ya Fara Tafiya kamar Wacce ta santa sai Taji in ta Bari Tatafi Zata Rasa Madafa,Kuka ta Farayi Tana Bin kasuwar da kallo Kowa sai Harkan gabansa kawai yake ba Ruwan wani ma Da ita bata Taba Zuwa Zaria ba sai yau Tana Cikin wannan Halin Taji an Dafa kafadanta da Sauri Ta Waigo Sai kawai Taga Kyakyawan Hajiyanan Ganinta yasa ta Sauke Numfashi Ta saki Mirmishi. Cikim mamaki Tace"Lafiya..? Na shiga adaidaita mai Adaidaitan yace min ga wata chan tana kallonmu Tana kuka ko Tare muke..? Sai da nace ya Tsaya na Fito na ganki lafiya..? Ina ne Gidanku..? Wata anguwa zaki..? Duka Ta Jero mata Tambayoyin Cikim kulawa,Da Sauri Zaina Tace"Bansan ko"ina ba..Bansan ina zani ba.."Cikin mamakinta Tace"Topha..Wajen wa to kika zo..? Sai Zaina ta Fara Hawaye Tana Fadin"Bakowa.."Shuru Tayi Tana kallonta kafin Tace"Shikenan bar kukanan ki gayamin me sunanki kuma Daga Ina kike..? Zaina Tace"Sunana Halima..Daga Bauchi nake.."Haka kurum Taji bata son Ta gayamata karya Cikin Kallonta sama da kasa matar tace"Bazan matsa naji me ya Fito Dake Daga Gida ba...ina ganinki naji kin bani Tsausayi kuma zan iya Taimakonki ammh Zan Fada Miki gaskiya Domin Ita ke Rike Dani har yau har gobe..Ni sunana AISHA FARIDA mutane Suna kira da SHOLLY  ni ba yar garin Nan bace Yar Gombace ammh na Zama yar Zaria Domin nafi Shekara Hudu acikinta kuma ni ba Zaune nake gaban Iyayena ba Zaman kaina nake in kin amince zan Tafi Dake gidan Dana ke zaune Gidan Uwar Dakina ce Dake nan anguwan gwado Gidan UWAR MATA..! Zaina Taji gabanta ya Fadi ta kalli matar sai kuma Taji ta Natsu da ita Cikin Ranta Tana Tunanin ina ta Barta Tatafi ina Zata Cikin Sauri Tace"Shikenan zan Biki nagode Anty Farida.."Mirmishi Aisha Farida Tayi mata kafin tace"Ok...Shikenan muje gida Sa"adiya kiyi wanka kiyi sallah kici Abinci ki Huta ko Domin naga Duk kin gaji.." Murna Ta kama Zaina Ta fara Hawaye Tana Fadin"Nagode Sosai..Nagode.."Aisha Farida tace"Karki damu.."Daga haka Taja Hannunta Zuwa Cikin Napen Din Tana Fadin"Muje mallam...! *Tammat Bihamdulillah...* _Alhamdulillah nan na kawo karshen wannan Labarin ZAINAZAIN kashi na Daya kamar yadda na Fada muku Labarin yana da Shashe Biyu ne mun gama Shashe na Daya zamu shiga Shashi na Biyu,Tabbas Zainzain kashi Na Daya yazo akyauta ne kamar yadda kuka gani sai dai kuma ku sani Kashi na Biyu na wannan Labarin IS NOT FOR FREE..!,Na Tabbata indai Soyayyar da na gani ne Dalilin Rubuta wannan Labarin Ko nawa na saka kudin Labarin nan zaku Siyeshi har ku ninkasa ma Nasan da yawanku Masoyan Amana ne Kama Daga Wsop Zuwa Wattpad Na Tabbata Zaku yi TuruRuruwa wajen Siyan Kashi na Biyun wannan Labarin Kodomin ganin Yadda Zata kaya Ga Zaina ta bar Gida ta Fada Hannu Aisha Farida Sholly kuma Sholly Zaman kanta Take agidan Uwar Dakinta Uwar mata yaya Rayuwar Zaina Zata kasance atsakiyar karuwai..? Yaya Rayuwar Zain zata kasance ba Zaina..? Yaya Dina.? Shin Tana Haihuwa..? Xata samu Nasaram auran zain da samun Soyayyarsa..? Yaya Duka Ahalin Zain Zasu ji da wannan Salon al"amarin Daya Faru dasu..? Wacece Aisha Farida..? Yaya Rayuwar Zakiya da Dina Zata kasance Daga karshe..? Shin Zaina Zata Haifi Cikin Jikinta ko kuwa..? Zata koma Ma Firstlove ko Rabuwarsu kenan..? Duka wadanan amsoshin Suna Cikin ZAINAZAIN kashi na Biyu ne Wanda zaku sameshi Cikin Farashi mai Sauki da yardan Allah.._ *ZAINZAIN PART 2 KUDIN KARATUNSA ₦250 NE KACHAL GA MASU AMFANI DA BANKI ZAKU TURA SHEDAR BIYANKU TA WANNAN ASUSUN BANKIN 0552179550 JAMILA UMAR GT BANK SAI ATURA SHEDAR BIYA TA WANNAN LAMBAR 09069067488,KAI TSAYE MUTUM ZAI TSINCI KANSA A PAID GROUP,MASU TURO KATIN WAYA KUMA ZASU BIYA ₦300 NE KACHAL INDA ZASU TURO HOTON KATINSU TA WANNAN LAMBAR 09069067488,KAI TSAYE ZASU TSINCI KANSU A PAID GROUP DIN DA ZAMU FARA POSTING DIN ZAINAZAINA KASHI NA BIYU MUTANENMU NA NIGER KUMA ZASU TUNTUBI WANNAN LAMBAR WAYAR +22794775574 SAI KUNZO ALLAH YA BAKU IKON SIYA AMEEN...* *01/07/2021* *Janafty....* An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online, Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490 A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu, Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng You can download more hausa novels there Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online It is free we do not charge for uploading novel Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT This Novel is downloaded from https://taskarnovels.com.ng to download more hausa novels visits our site at www.taskarnovels.com.ng For feedback and support Facebook : https://facebook.com/taskarnovels Twitter : https://twitter.com/taskarnovels Telegram : https://t.me/taskarnovels

Chapter 32 of 32