Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
kansa daya maida kasa yana Sharan kwallah Cikin Sanyin Murya Haddir ya Dafashi yana Fadin"Abunda Muke Gudun fa ya Riga ya Faru..Fake gaba kawai zamu yi sai Abu na gaba yadda zaka Shawo kam iyayenmu su yafe maka da kuma yadda zaka Gyara Mu'amalanka da Matarka Domin fa mai afkuwa ta Riga ta afku bamu da yarda da zamu yi wannan koke koken naka bazai kaika ko"ina ba Wlh Gwara Tun Wuri ka Ijiye wannan gefe Tunda komai ya Faru kai ne Sila Tun Muna London nasha Fada Maka kabar wannan Muguwar Dabi"an Bata Dace da Dan Musulam kwarai ba Zain kaki jina Na Dauka Da muka Dawo Gida zaka Daina Abunda kakeyi Ko Domin Tsoron Allah da kuma Darajan Mutumtakan iyauyenmu ammh baka Daina ba ka Biyema Yarinyar nan Dina Wacce Tun ganin Farko Dana yi mata na gayamaka ka Rabu da ita Shedaniya ce kaki jin mganata,Wlh na Tabbata ba sai nayi kaffara ba Da gangan ta bari Ciki ya Shigeta Saboda ta Fallasaa ka Aureta Tun Farko sai da na gayamaka in Sonta kake ka Aureta mana ka Hadasu ita da Zaina da kabi Shawarata Hakan zata Faru..? Kamar karamin yaro Haka Zain ya Girgiza ma Haddir kai alaman A"a,Haddir yaci gaba da Fadin"Toh ka gani ka kijin mganata Lokacin ma Saboda ina Gaya maka gaskiya gaba ka Farayi Dani Da auranta kayi Da Duk Abunda ya Farunan bazai Faru ba Gashi yanzu Dalilin Son Zuciyarka da kuma Shedan din Daya Dinga kawata Maka aikata zina yasa ka Cikin wani Halin Ka samu mumaa Damu da Duka Yan"uwanka da makusantanka Don Allah ina Dadinsa..? Ni babban Damuwa ta ma Fushin iyaye akan ya"yansu Bala"i ne Uwa uba ayanzu bamai Shiga mganar nan Tunda kowa ma yana Cikin Bakincikin Abunda ka aikata ga Zaina Ka saka yarinya karama Dandanan Dacin Bakincikin Cin Amanar Da Namiji ni kaina ina Jin kunyar mu Hada ido da ita bansan me zan ce mata ga Ga Babban ma Tashin Hankalin Cikin Da ke Jikin Dina kuma Alhaji Tsoho yace sai ta Haifeshi yanzu haka Acikin Zuru"armu zamu samu Dan gaba da Fatiha..?Kai son Zuciya bai yi ba sam Wlh.." Ya karishe Fada yana Dafe kansa Sadiq Dake gefe kai yake Jinjinawa alamun gamsuwa da kalaman Haddir din Shi kuwa Zain Kansa kawai ya Tusa Cikin Gwiwoyinsa Yana Kuka kamar wani karamin yaro Mikewa Haddir yayi yana Fadin"Nasan Damuwa ta zama Dole Gareka ammh u Hv To become Very Strong Tunda daman kasan Duk Abunda kake aikatawa watarana asirinka sai ya Tonu kuma Wannann Lokaci zai zo,ina Jiyemaka Hawan jini Ko Ciwon Zuciya yazo ya kamaka Domin Duk wanda zai ji wannan mganar kukan ka bazai Taba bashi Tssusayi ba Illah ma ya karama da kalmar Allah kara kai ka jawo ma kanka komai miye yake Faruwa Dakai." Ya karishe Fada yana Sakin Numfashi kafin yace"Zan je Gidan Na Duba Abba da Jiki Daganan zan Biya Gidan Alhaji Tsoho na gayamai nagani ko zai iya Saka baki Abba ya sauko ammh Shima din ba yanzu ba saboda Kaga Halin Daya ke Ciki Yanzu ba"a son yasa ka wani Damuwa aransa kaima ka sani.."Da Sauri Zain ya Dago yana Fadin"'Don Allah Haddir ka Tayani Lallashin Firstlove kace mata Tazo ta ganni muyi bankwana na Roki gafaranta kada na Mutu ka Shaidamata Wallahi Summa Tallahi Duk Duniya Ita ce macen da nake so Kuma Itace in ta barni Rayuwata zata Lalace ka Fadamata Ta Dawo Gareni Don Allah ka Tahomin da Firstlove na Rumgumeta akirjina Nayi kukan da Haryanzu ya kasa Fitowa Daga Cikin Kirjina.." Yafada yana Runtse Ido Saboda yadda yakejin Zuciyarsa na Bugawa Daga Sadiq har Haddir sai da suka kusa mai kwallah Cikin Muryan Lallashi Haddir ya Dafashi yana Fadin"Karka Damu I Will Try my Best Insha Allahu naga komai ya Daidaita..Yanzu ka kwanta ka Huta ka Cire komai aranka da Izinin Lahi Tunda kayi Tuban gaskiya Komai zai zo ya wuce kamar ba"ayi ba zan je nyi mgana Dasu Umma itama Zaina zan yi mgana da ita komai zai Daidaita kaji ko..? Kamar Haddir yamai Gafara Haka yakeji Cikin Gyada kai yace"I Trust u...Kuma Wlh da Gaske na Tuba...Nama Dade da Tubam ma Allah Dina ita ce Ke maidani Ruwa Shiyasa na Tsani Jin Sunanta ma na Tsaneta na Tsani mai kaunarta Tayi sanadiyar Jefani Cikin Bala"i Tsakanina da ita sai Allah ya isa kawai zence Shegiya macuciya..'Haka kawai Zain yake Sambatu yana Zagin Dina Haddir ya gyada kai yana Fadin"Koma miye ya Faru da Taimakon wannan Shedaniyar kawar nata...Shiyasa akomai kada kayi mu'amala da Mutumin Banza Domin Aiyukansa Watarana zasu iya Shafanka..Bari Naje ka kula Da kanka kafin na Dawo in Tabawa Tayi Tuwo nazo maka Dashi..? Da Sauri ya gyada kai yana Fadin"Allah yasa ta bada in Taji ance ni za"a kawo mawa.."ya fada kamar yayi kuka Mirmishi Haddir yayi yana Fadin"Zata baka mana...Har yau har Gobe kanan nan amatsayinka na Zain Usman Abubakar Saulawa Babu Abunda ya Sauya wannan kuma Abunda ya Faru Jarabta ce kuma Allah ya bamu ikon Cinyeta Watarana zata zama sai Labari Insha Allahu.."Cikim Karfin Hali Zain yace"Allah yasa.." Fara Tafiya Haddir yayi yana Fadin"Da yardan Allah...Kai Sadiq in ka Tashi muje na ijiye ka Tasha naga ma kamar kayi yammah.."Sadiq ya Fara Tafiya Wajen Jakarsa ya Dauka ya Rataya yana Fadin"Yauwa Ya Haddir nako gode....Banyi ba ko agida Abba yagaji Da Fada ya kyaleni nafi son Tafiyar Dare.." Haddir na Barin Bedroom din yana Fadin"Tab lalle...Yarinta ke Damunka Allah ya Shiryeka muje.."Daga haka ya Fice Shi kuma Sadiq ya Tsaya gaban Zain yana Fadin"Ya Dakta Allah kara Lafiya zan koma Zaria sai an kwana Biyu kuma.."Cikin Rinannun Idanuwansa ya Kallesa kafin ya mike ya Riko Hannayensa Duka Biyu yana Fadin"Sadiq kai kanina ne Ka ga Dai Abunda ya Faru dani ko..? Ina baka Shawara karka yarda ka Kusanci aikata Badala Kai ko mata ma kadaina sakar musu Fuska Da yawansu Shedanu ne sai sun kai ka sun baro su kyaleka Cikin Bala"i ka Tsare Kanka Don Allah.."Yafada Cikin Fitan Hayyaci Tsausayinsa ya kama Sadiq ya murmusa yana Fadin"Insha Allahu Ya Dakta..Ni Bana Shiga Harkan mata Mazan ma ni ba Shiga Harkansu nake ba Allah ya Tsaremu Daga aikata Abunda zamu zo muna Dana sani Daga baya.." Da Sauri Zain yace"Ameen Ameen Nagode..Allah ya kiyaye Hanya.."Ya amsa da Ameen Har Falon ya Rakosa kafin ya koma Shi kuma ya Fita Zuwa Haraban Gidan Inda Haddir ke Jiransa bai ma kai ga Shiga Motar ba Tanimu maigadi ya Tsareshi Da Tambayan ina Gimbiyar Dakta ko Tayi Tafiya ne bata Dawo Gida ba..? Shidai Haddir cemai kawai yayi bata lahiya Tana Gra Shine fa ya Fara kwararo Addu"o'i wata addu"ar ma baisan me yake Fadi ba Mirmishi kawai Haddir yayi ya zaro 1k ya bashi yana ta Godiya kana ya Bude mota ya Shiga Sadiq ma ya Shiga Gidan Gaba Yayi Hon Tanimu ya Bude Get suka Fice Daga Gidan. Sai da yakai Sadiq Tasha kana ya Wuce Gidan Abba Sadiq din kuwa yayi Sa"a yana zuwa Motar Zaria Ta kusa Cika Saura mutum Biyu yana Shiga sai ga wani Shima ya Zo Basu Dade ba Suka Tashi Haddir kuwa Koda ya isa Gidan Abba  ya iske Har Abba yaji Sauki ma ya Farka yana Cin Abinci Bayan ya Gaisheshi da Jiki Su Umma da Nene Duk suna Dakin Abba ya Kallesa yana Fadin"Ka koma bakim aikib ka ko..? Cikin Ladabi Haddir yace"A"a sai zuwa gobe Abba..Jikin Zain din Har yanzu ba Dadi.."Zaro Ido Nene Tayi Lokaci Daya Tana Dafe Kirji Cikin kaduwa Tace"Na Shiga uku me ya sami Zain din..? Kafin Haddir ya Bata amsa Abba ya maka mata Harara yana Fadin"Na manta ban Fada muku ba ko Sunansa na Kashe ambatonsa acikin Gidan nan..! Wannan Karon Har Umma sai da Ta kalli Abba kamar zatayi mgana sai kuma ta Fasa,Nene kuwa Idanuwanta Ne suka cika da kwallah ammh batayi mgana ba Abba ya kalli Haddir Fuskarnan nashi ba Annuri yace"Ka koma wajen aikinka ka Rabu Dashi..Babu jin kai ga wanda baya jin kunyar aikata Abunda yaso..! Kan Haddir na kasa yace"Kayi Hakuri Abba...Nasan Zain yayi Laifi matuka ammh.."Ammh me..? Me zaka Fadamin wanda ban ji ba kuma ban Fahimta ba..? Abba ya katse Haddir Lokaci Daya Da Dagamai Hannu sai Haddir yaji Gwiwansa Tayi sanyi Cikin Dauriya ya Dago kansa yana Fadin"Nasani Abba ammh In ka Lura da komai yadda ya Faru Zain ya Hadu da Shedaniyar mace ce ita ke Ribantanshi koda ya Tuba kan Abunda yake aikatawa.." Abba ya Dade yana kallon Haddir kamar bazai yi mgana sai kuma ya Murmusa kafin yace"Kaji wata mgana..? Ai Shine Babban Shedan din Hadiru.."Haddir ya Bude baki zai yi mgana Abba ya Dagamai Hannu yana Fadin"Kaga Hadiru Tashi kaje sabgoginka nagode..Ammh Matukar mganar Zainullahi zai kara kawo ka kaima na Yanke maka zuwa Gidan nan Allah bada lada.." Daga Haka ya Mike Daga kan gadon Bayan ya Ture Filet Din Abincin Daya gama ci Ya Taka ahankali ya wuce Tiolet,Dukkansu suka Bishi da kallo Cikin Tsausayawa ganin Duk ya Rame ya Fada Kada kai kawai Umma Tayi Tana Fadin"Komai ya Faru Zuciyarsa Data Rinjayensa itace Silan komai.."Daga haka ta Fice tana Kokarin Boye Damuwarta Dakin zaina ta Wuce Domin ta Dubata sai ta Iske ta samu Barci Hamdala Tayi ma Allah Domin Jiya Tana Jinta kwana Tayi bata yi Barciba Tana kuka Yanzu ko Hakkin Yarinyar nan Allah ya kama Zain Dashi zai ga Daidai arayuwarsa..? Nene kuwa Umma na Fita ta kalli Haddir Tana Fadin"Hadiru ya Jikin Zainullahi din..? Fata dai da sauki ko..? Bai mata mgana ba Jin kamar Abba na Shirin Fitowa Daga Tiolet Da Sauri Nene ta wuce Gaba Tana Fadin"Biyo  ni muje Dakina Hadiru..Alhaji ya Riga yayi Fushi Da Zain kuma Fushin da bamu Taba ganin yayi kamarsa da wani ba.." Ba Musu ya mara mata Baya zuwa Dakinta suna Shiga Ta Rufo Kofar Tana Fadin"Hadiru ba dai wani Cutar ne ta kama min D"ana bako..? Haddir ya Girgiza kai yana Fadin"A"a Bata kamashi ba ammh in ya Cigaba da saka Damuwa zata iya kamashi Har tamai illah.." Salallami Nene ta Fara kafin ta zauna Gefen gado Tana Fadin"Oh ni Aisha..Ina zan saka Raina Wlh Hadiru Tun Shekaran Jiya Rabona da samun Barci mai Dadi agidanam Hankalina na wajen yaron nan babu Kowa awajensa bamai Sauraransa sai kai Ba Domin Alhaji yana mana iyaka ba Da Tuni naje naga Halin Dayake Ciki.." Haddir ya gyara Tsayuwa yana Fadin"Haka sadiq ke Fadamana yanzu Daya Biya kafin yanzu mu Fito Tare nakai shi Tasha ya Hau Motan Zaria,Zain din ne ma ya matsa bayan yaji Sauki kan zai zo gida da na Hanashi yaki Hanuwa Shine Sadiq yake Fadin Abunda Abba yace..Abun bai yi Dadi ba Nene Kinsan Fushin Iyaye kan ya"yansu fa Ba kyau sam.."Nene na Sharan kwallah Take fadin "Na sani Hadiru ya zanyi..? Wlh ni kam bana Fushi da zain sai dai in na ganshi zan mai Fata fata na Nuna mai Bacin raina kan Daukan Tarbiyan da ban Taba mai Shi ba..Ya na iya Alhaji yayi Fushi sosai wanda kuma sauko Dashi kan wannan Fushin sai Alhaji Tsoho kuma Shi din na Tabbata ba zai saka baki yanzu ba kuma Fushin Alhaji Duk da Yarinyar nan Halima ita ke kara Sakashi Jin Takaichin Zain Wlh Domin Kuka fa Take kwana yi Ta Wuni Yi Tunda Abun nan ya Faru.." Haddir yace"Ai da wuya ma Alhaji Tsoho yace wani Abu yanzu..Mganar ma Zainar  Duk da ita ta kawoni Nene,Ku saka Baki ta koma Gidan Mijinta Wlh Zain yana Bukatarta Sosai kuma Abu ya Riga ya Faru ai sai Hakuri Bawa bai isa ya kaucema Kaddaransa ba.." Nene tace"Hakane...ammh kam banajin Hakan zai yuyu gaskiya..'Haddir yace"Saboda mene Nene..? Nene tace"Saboda Ba wanda zai ce Dole Sai Halima ta koma Gidanta..Alhaji kuma bazai yi mgana ba Alhaji Tsoho kuma yasan Tana nan gidan ammh bai ce komai ba Uwarta ce kuma Bazata Yarda Ta baka ita ba.." Cikin Sauri yace"Wai Umma..? Nene tace"Eh..."Haddir ya Sauke ajiyar rai yana Fadin"Bari naje nayi mata mgana in tayarda ta bani ita shikenan Abba da Alhaji Tsohi basu da yarda Zasu yi indai sukaji Ta koma Wajen Mijinta ai ba wanda ya isa ya Raba Tsakaninsu sai Allah Nene.." Nene Ta Mike Tana Fadin"Kwarai mganarka Haka Take muje Dakin Halimar Umman Tata tana Chan Tunda Ita ke kwana da ita.."Daga haka ya Fita itama tabi Bayansa Sun Fito Falo kenan suka ci karo da Zareena Tana Zaune afalo Tana bama Takwaran Umma Nono Jalal na Gefenta yana Game acikin Tap dinsa,Ganin Haddir yasa Ta saki baki Tana Fadin"Aboki Hadiru Tazuru kuma kanina Yaushe kazo gidanan..? Tafada Tana yar dariya Ba laifi Itama Ta Fara sakewa ba kamar Jiya ba Tunda Har tayi wanka Zataje gidan Alhaji Tsoho ne Hararanta yayi yana Fadin"Ni sa"anki ne wai Abokiya Zareena..? Kin Raina ni ko..? Cikin Shakiyanci Tace"ji wannan yaron..? Ban girmeka bane nifa yayarka ce ko kaki ko kaso.."Haddir yace"Wata Hudun da kika bani Shine kin Girmeni..?Ki sake Tunani yarinya akwai malaman da suka ce komai kankantar Namiji shine Shugaba akan mace saboda Haka ki Dawo Cikin Hayyacinki Maza Bisa kanki yarinya.."Yafada yana Kashe mata Ido Daya Bata rai Zafeera Tayi Tana Fadin"Da aurena da ya"yana kake cemin yarinya..? Yace"Au Ai harta wanda ya ijiyeki Engnear Jawaad din yaro ne..."Duka Zafeera Takaima ya kauce yana Dariya Nene ta Tayasu Sai ga Jalal ya Saka Dariya ashe Tun dazu yana Kallonsu kumatunsa Haddir ya Kama yana Fadin"Ai gaskiya na Fada ko Son..? Da sauri yace"Is Truth Uncle.."Dariya ta kama Haddir har Sai da ya Bashi Hannu yana Fadin"Dat my Son Plz Give a Five.."Yako bashi Hannu suka Kashe Zareena tacika kamar ta Fashe Nene sai Dariya Takeyi Haddir da Jalal na Tayasu. Kukan Little Umma ne ya katse Zareena ta koma ta zauna Ta Cigaba da Bata Nono Tana Fadin"Ka samu sa"a ne Aboki Zaim baya nan Da shi zai Taremun Tunda kafini baki.."Ambaton sunan Zain Da Tayi ya Dauke duka walwalansu Cikin Damuwa Haddir yace"Yana Gida ba Lafiya Abokiya Zareena.." Cikin Damuwa Itama Zareenan tace"Ayyah..Allah ya bashi lafiya..Zan je na Dubashi ammh Nene Kada Abba yaji labari.."Nene tace"Wa..? Ba wanda zai ji kinji na Rantse Miki anjuma kije ki Dubamanashi Don Allah kice ya kwantar da Hankalinsa Nenensa na Tare dashi komai zai Wuce.." Zareena Tace"Insha Allahu...Zan Tafi Gidan Alhaji Tsoho na kai mai mai Sunan Umma Shi da Hajiya Mama da Tabawa Daganan sai na Biya na Dubashi..Allah sarki wannan Kaddaran bata kyauta mana ba sam Nene..'"Haddir yace"Uhm...Bari dai na ga Umma kam mganar Zaina.." Zareena Ta kalleshi Tana Fadin"Tab...Anya kuwa..? Da kun bari zuwa akwana Biyu Lokacin Abun ya saketa.."Haddir ya kama Tafiya Zuwa Dakin Su Zaina yana Fadin"A"a Barin zuwa Wani Lokacin ta wannan bangaran abun kara Tabarbarewa zai yi..Zain na Bukatarta ahalin Dayake Ciki.."Zareena Tace"Allah yasa ku dace..' Nene Tace"Ameen Ameen..."Daganan Itama ta mara ma Haddir Baya zuwa Dakin Da zaina Take,Haddir ne kan Gaba ya Tura Kofar ya Shiga Nene na Binsa abaya Da Umma suka ci karo ta Riko Zaina sun Fito daga Tiolet kamar Wanka Ta Taimaka mata Tayi da alwala Tunda dai Wasu masallatan Har sun Fara Kiran Sallar mngariba. Atare Umma da Zaina suka kai Dubansu kan Haddir da Nene Cikin mamaki Umma ke binsu da kallo har suka kariso Cikin Dakin,Haddir ne ya Fara gaisheta Cikin ladabinsa Lokaci Daya yana karema Zaina kallo ganin Tayi wani Fari fayaut kamar bata da jini ajiki kuma Ta Rame bakinta ya Bushe akallon Farko sai yaga kamar Tayi wani Danye Danye kamar wata mai Shigar Sabon Ciki Ita kuma Sau Daya Ta kalleshi kawai ta kauda kai kan Gado Umma ta zaunar da Ita Tana Fadin"Zauna ki Huta kafin ki shafa mai ki saka kaya sai kiyi sallah kici Abinci ko..? Kallon Umma kawai Tayi batare Da Tayimgana ba Umma ta maida Hankalinta kan Haddir tana amsa gaisuwansa Nene ta kalli Zaina Tana Fadin"Sannu Halima Ya Karjin Jikin..? Bata amsa ba illah kanta Data maida kasa Daman bata saka Rai zata amsata ba Domin Tunda Abun nan ya Faru Bazata ce taji mganar Zaina ba ko sau Daya ba sai dai in da Ummanta,Umma ce ta kalli Nene Tana Fadin"jikin nata da Sauki ba zazzabi sai dai Rashin karfin Jiki Shi kuma wannan Rashin Cin Abinci ne Tunda ko Taci sai ta amayar dashi..? Nene tace"Toh yanaga Idanuwanta sun kumbura ne bata bar kukan bane..? Umma ta Rausayar Dakai Tana Kokarin Daukan man Vaseline saman Madubin Dake dakin Tace"Bata bari ba..Kuma Harda ma da Rashin barci Da Rana tana samu tayi kadan ammh Da Daddare bata barci Kwana Take kuka.." Umma Ta Fada Fuskarta na Sauyawa Haddir ne ya sauke Numfashi yana Fadin"Allah ya Sauwake ya kamata Taga Likita Gaskiya.."Umma tace"Bata so..Bazata asibiti ba tace..Ni kuma bana som matsamata Na kyaleta Ko Taje asibiti Basu da mganin Damuwarta Hadiru.." Haddir yace"Hakane Umma..Ammh Kuka ma da Amai Da Rashin barci ai Wata Cutan ne na Dabam ko..?Umma batayi mgana ba illah mika ma Zaina Man Data Dauko mata Datayi wacce ke sanye da Hijabi Dogo na wajen zainab ne Umma ta Dauko mata Karba Tayi Ita kuma Umma tace"Ki shafa.." Haddir ne yaga Umma na Shirin Shiga Tiolet yace da Sauri"Umma wajenki fa nazo.."Dakatawa Umma Tayi Ta waigo Tana kallonshi kafin tace"Wajena kuma..? Allah sa lafiya..? Haddir yana kallon Zaina wacce Ta Dago Tana kallonsa da Rinannun Idanuwanta yace"Lafiya lau..Dama mganar Zaina ce Umma" Umma Ta Juyowa Gabadaya Tana Fadin"Ina Jinka.."Tafada Tana kallon Nene wacce ta marairaice mata Tun Daganan Ta gano Inda suka Dosa Sai dai bara Ta katse musu Hanzari ba gwara Taji Daga bakinsu lalle zasu ga Fushinta nan take kuwa. Idanuwan Umma sun ma Haddir kaifi ya kasa mgana sai da ya Sunkuyar dakai kana ya iya Fadin"Dama..Dama..Umma mganar Komawar Zaina Gidan Mijinta ne kinga Zain yanachan kwance ba lafiya kuma Yana Bukatarta ayanzu gaskiya.." Har ya gama mganarsa Umma na Jifansa da wani kallo na lalle nema kun Raina mutane Zaina kuwa Tun mganar Haddir Taji Dan Jinin Jikinta ya Daina Gudu Bata Sha"awar kara ganin Ya zain ma Ita acikin Idanuwanta ammh akasan Ranta Tsausayinsa Sonsa Sun Hanata Sukuni Kamar Daga sama Taji Umma na Fadin"Ok Shi ya aiko ka kenan...? Shine kuma Da zaka zo Fada ka Dauko Uwarsa kuka zo Tare ko..? Nene tace"Eh yazo yagamin komai..Nace yazo muje mu Taru mu Roke ki Umman Zareena Hannunka fa baya Taba Zama Cuta gareka,Bamu da yarda zamu yi da wannan kaddaran kuma Hana Zain matarsa kamar kara Tabarbara komai ne,ki barta ta koma Gidan Mijinta Suyi Jinyan Juna Ya bata Hakuri sai Kiga komai ya Daidaita.." Umma Ta Tsuke Fuska Tana Fadin"lalle nema..Wato yanzu ne Take da kima da Daraja acikin Idanuwansa ko..? To kaje ka Fadamai Wlh Tallahi kunji Rantsuwan Musulmai yata bazata Je ko"ina ba.." Daga Haddir Har Nene kasa Mgana sukayi jin Umma ta Rantse,Cikin Jan karamin Tsaki Umma tace"Ina Dadiron nashi ko nace karuwan nashi Da bai Kirata tazo Tayi Jinyarsa ba Ko nace Uwar Shegen nashi..? Sai yata Zata Dinga Wahala kansa ko..? Hadiru ka Fita idona karka kara Zuwarmin da wannan mganar Banzan Daga kai har Uwarsa Wacce bazata ga Illah Da Abun Tir din da D'anta ya aikata ba.." Tafada Cikin Bacin rai Da Sauri Haddir ya Rankwafa yana Fadin"Don Allah Umma..Ko Sau Daya ki bani Dama nayi mgana Da zaina kila ita ta Fahimceni.."Kamar Umma zata mareshi Haka ta taso mai Tana Fadin"Anki abaka Daman..? Nace an ki abaka daman..? Ba inda Zata ka wuce ka bamu waje kafin Raina ya baci Na Tsinke ka da mari Hadiru.." Jin Haka yasa bai yi gaddama ba ya Juya yana Fadin"Allah Huci Zuciyarki Ummah.."Da Sauri Tace"Ameen.."Nene bata ma yi mgana ba ta kada kai ta Juya Tabi Bayan Haddir kawai Umma Ta Rakasu da Harara Tana Fadin"Kaji min iskancin banza iskancin Wofi..Wani wai Ta koma Gidan Mijinta..? wato ta koma Taje Chan ta Cigaba da zama Dashi karshenta ya Auri Karuwarsa Tasa tazo Tana Tayasu Renon Shegen nasu Rayuwarta Ta kare Cikin Bakinciki Wlh bazata sabu ba indai ina Numfashi Halima Ta bar Auran Zain har Abada.." Zaina Dake zaune bata san Sadda Karshen kalmar Umma ta saka Kukanta Fitowa ba Cikin wani Takaichi Umma ta Isa Gareta Tana Fadin"Rufemin baki Sakara mara wayau...Ana Neman yadda Zaki Rayu Cikin salama kina ma wanda ya ci Amanar zaman tare da irin Soyayyar da kika nuna mai kuka..? Ki Min Shuru yanzu ko na Kikkifa miki Mari yanzu yanzu nan.." Jin yadda Umma ke Sababi ne yasa Zaina Tayi gum da bakinta bata kara Bari kukanta ya Fito ba ma Ta Dinga Hadiyeshi Tana Sauke ajiyar Zuciya kamar wata karamar yarinyar da Uwarta Ta Tsigeta Tana Cikin Shan Nono Tsaki Umma Taja ta Nufi Hanyar Tiolet tana Fadin"Kafin na Fito ki Saka kaya ki Tada Sallah in kina so mu Shirya.." Da Sauri tace"Toh Umma."Tana Kokarin Goge Hawayenta da Danne kukanta Sai Lokacin Umma Taji Tsausayinta ammh kuma Dole ne tayi mata haka In ba Haka ba Haka Zatayi ta zama Cikim Kuncin zuciya har wani Cutan ta kamata Kofar bayin ta Bude ta Shiga Ta bar zaina na Kokarin Mikewa Lokaci Daya tana saka Hannu tana Danne bakinta kada kukanta ya Fito Umma Taji ta Fito taci kaniyarta. _Godiya Ta musamman ga Dimbin Masoyan ZAINAZAIN,Ina ganin Tarin Sharhinku da Comments Dinku Musamman yan Group din ZAINAZAIN 1&2 ,da Gidajen Janafty Shakira,Duka ina gani Kuma ina Jin Dadi Sosai kuke sakani Nishadi Kuyi hakuri bana samun Lokacin Maida muku martani Abubuwan ne sai a Hankali ammh ina gani kuma ina Godiya Da ku da yan Wattpadians Fans dina suma Ina ganin Sharhinsu Alhamdullahi kawai Zance Allah ya bar Zumunci Ameen..!_ *Janafty...* *ZAINAZAIN..!* _(Is a love Story and Betrayal)_ *Wattpad:Jamilaumar351* *Mallakar:Janaftyshakira*❤️ *BOOK 1*               2️⃣3️⃣ "Haddir ne kan gaba Nene na Biye Dashi Zuwa Falo,Zareena na ganinsu Fuska ba walwala Tasan ba"a Dace ba Domin Taga Umma Ta Dauki Fushi Sosai kuma Bata ma da Niyar Barin Zaina Ta koma Gidan Mijinta a Take takenta Datake gani. Cikin Kallonsu Tace"Ba"a Dace ba ko..? Nene ce ta zauna Gefenta Tana Fadin"taki ma Sauraranmu...Naga Bacin rai naga Tsausayi na Soyayyah da Jinkai duka acikin Idanuwanta na Farko Tana Tsausayin Zain Tana kuma Tsausayin Halima Tana kuma Jinta kamar yarta Data Haifa Da Cikinta,Wannan Dalilin yasa Ta nuna bacin Ranta Sosai wanda ban Taba gani ba.." Nene Ta Fada Cikin karaya,Zareena Tace"Hm...Allah ya kyauta nagaba.."Haddir ya amsa da Ameen yana Fadin"Bari naje na samu Alhaji Tsoho muyi mgana in anci Sa"a ya saka Baki mgana Ta kare.."Nene tace"Shima din bana Jin zai ce wani Abu awannan Lokacin Hadiru.."Haddir yace"Zan Jaraba Dai na gani yadda mukayi Dashi ko ban Daawo ba zan Kiraki awaya na Shaida Miki.." Nene tace"Shikenan..Sai na Jika.."Zareena kuma tace"Ka gaida Zain din sai nazo.."ya waiwayo yana Fadin''Ke ina zaki da Daddaran nan..? Baki bari sai gobe..? Nene tace"Nima Abunda na gayamata kenan.."Jin Haka yasa Zareena tace,"Shikenan bari na Bari sai goben Dama zan Jira in Zainab Ta Dawo Daga makaranta Direban Abba ya kaimu ne ammh Bari dai na bari sai gobe da safen.."Haddir ya wuce yana Fadin"Yadai kamata kam...Ni na wuce.."Suka Rakashi da Allah kiyaye Hanya. Yana Fita Haraban Gidan yaci karo da Zainab Ta Dawo Daga Makaranta Cikin Ladabi Ta Ramkwafa Tana gaisheshi ya amsa Sama sama ya Fada Motarsa ya Fice Daga Gidan Ta Bishi Da kallo Bata samu Fuska bane Taso Ta Tambayeshi Ya Ya Dakta yake ne..? Sai dai baima saki Fuskan ba Ballatana ta Tambayeshi Tana Shirin Shiga Cikin Gida ne sai ga Motan Abba ta Dawo Daga Dauko su Saudart Daga Islamiya bata ba Tsaya ba Taja Jakarta Ta Nufi Cikin Gida Domin yau din agajiye ta Dawo Wuni Tayi Cikin Makaranta Suna Kokarin Fara Test din Zangon Karatunsu na Farko ne. Haddir kafin ya isa gidan Alhaji Tsoho sai da ya Tsaya masallacin Kusa da Gidan yayi Sallar mangariba kana ya karisa,Alhaji Tsoho Na cikin Dakinsa saman Kujeransa yana Karatun wani katon Littafi da Siririn Gilashinshi mai kara mai karfin gani,Gabansa Haddir ya Zube bayan sun gaisa Ya Shiga Rarrafomai Abunda ke Tafe Dashi na game da Fushin da su Abba suke da Zain da kuma Halin Da yake ciki da kuma Yadda sukayi da Umma yau din.. Har ya kamallah maganganunsa Alhaji Tsoho na kallonsa bai ce komai ba,Ganin Alhaji Tsoho yayi Shuru ne yasa Haddir yace"Nazo na gayamaka ne Tsoho Saboda ka saka baki Abba ya Janye wannan Fushin Da yakeyi Ko Zain zai ga Daidai Arayuwarsa..Umma kuma

Chapter 23 of 32