ka mata Mgana Ta bashi matarsa Tunda dai mai afkuwa ta Riga ta afku Sai dai muyi kokarin kada Hakan ya kara Faruwa..!
Mirmishi Alhaji Tsoho ya saki kafin ya Ijiye littafin Hannunsa Saman wani karamin Tebur Dake gabansa Lokaci Daya Yana Fadin"Toh ni yanzu da kazo kana Gayamin me kake so nayi maka..?
Cikin Mamaki Haddir yace"me nake so..?kaifa Tsohon nan ka iya Nuna ma Mutane Boko fa..? Ai nayi maka Bayanin komai.."Dariya Ta kama Alhaji Tsoho wanda Tun Faruwar Al"amarin nan bai yi Dariya Haka ba baki Sake Haddir ke kallonsa kafin ya koma kawaai ya Hade Ransa sai da Alhaji Tsoho yayi Dariyansa Son Ransa kana yace"Yaro yaro ne...Yaro Man kaza bai san Wuta ba sai ya Taka.."
Cikin Haushi Haddir yace'"Ammh dai bani kake Nufin yaro man kazan ba ko..?Alhaji Tsoho yace"A"a Ba da kai nake ba...Karin mganace tamu ta Hausawa.."Yafada yana Dariya Lokaci Daya yana Daga Hannu Alaman yayi saranda Mirmishin Lebe kawai ya saki Yana kallon Alhaji Tsoho Daman ya sani Alhaji Tsoho so yake ya Hukuntashi Shida Zain alokaci Daya.
Ganin yadda Haddir din yasha Kunu ne yasa Alhaji Tsoho ya Dakata da Dariyan Dayake ya Fuskanci Haddir yana Fadin"Kasan abunda kai baka Fahimta ba Hadiru..!? Bai bashi Zarafin mgana ba yacigaba da Fadin"Duk Cikin ya"yana Usmanu Yafi kowa Hakuri da kawaici Sai Mahaifinka Aliyu..Sai Rukayytu..Dama masu Zafin Da Zuciya Sai Babana da Hannatu uwata Daman kuma so Gado sukayi wajen Uwarsu Amina ka gantanan nayi Fama da Ita Tun Lokacin muna da Kuruciya.."Yafada Cikin Zolaya Murmusa kawai Haddir yayi batare Da yayi mgana ba Shima bai Damu Daya Tanka din ba ya Cigaba Da Fadin.
"Tunda kaga Usmanu yayi irin wannan Fushi Ka Tabbata Babban Abu ne...Mutun ne mai kawaici da Boye damuwa Naji matukar Tsoro Lokacin Danaji Labarin Damuwar da Zainullahi Ya sakashi Ta kaishi Har kwance bai iya zuwa aiki Daganan nasan Zainullahi ya Gama Raunana Zuciyar Usmanu na Wanda banta gani ba Tunda na Haifeshi Saboda Hakurinsa da Kawaicinsa..!
Ya fada Idanuwansa na kan Haddir wanda ya natsu yana Sauraransa Cikin Takaichi Alhaji Tsoho ya Cigaba Da Fadin"Me kake so nayi akai Hadiru..? Karka manta Usmanu Shine Mahaifin Zainullahi Shine Babban D'a Namiji cikin ya"yansa Wanda ya Dorama Son Duniya da kuma Burin Watarana In Bashi Shi zai Gejesa ya Rike Iyayensa da kanninsa..? Ya bashi yarda yana ganin Ya Sauke Nauyin Dake kanshi Wajen Bashi Dukkan Tarbiya da Ilimi na Arabi da na Zamani Saboda Watarana ya Tsaya Da Kafafunsa bayan Gama Dukkan wananan bai ga Sakamakon komai ba sai wannan aikin da Zainullahi ya aikata na Ijiye karuwa suna zaman Haramci Harda Tsaraban Ciki,Ni na isa na Hanashi Nuna Fushinsa da Damuwarsa akan Abunda ya Haifa..?
Ya Fada yana kallon Haddir Wanda kalaman Alhaji Tsoho suka Sanyayamai Jiki Kai ya Girgiza Cikin Mutuwar Jiki Kafin Alhaji Tsoho ya Cigaba da Fadin"Toh ka gani bani da wani Abunda zan iya yi kan wannan Lamarin Hadiru Zainullahi ya gama Bamu kunya gabadayanmu..Na Riga nayi iya Abunda zanyi sauran kuma sai mu bar ma Ubangiji mganar ita yarinyar ma Mahaifinta ya Kirani yace nayi Hakuri Dayake ya karbi Lambata Ranar kafin su Wuce kan Gobe ne Suke sa Ran Zuwan ita Uwar yarinyar Daga Sudan in tazo yayi mata Bayani Insha Allahu zasu zo da mai Dakinsa su kawo ta Wajena kamar yadda nace..Sai godiya yake min abun gwanin ban Tsausayi..!
Haddir bai samu Damar mgana ba yaji Muryan Hajiya Mama Dake Kokarin Shigowa Dauke da Farantin Kololin Abincin Alhaji Tsoho tace"Nifa wannan Hukuncin naka baimin ba Sam Taya za"a ce kuma tazo ta zauna Cikin mu Har ta Haihu ai sai in muna ganinta Bakinciki watarana ya Nemi kashemu daka sani Ta tsaya chan gaban Uban nata ta Haife Shegeen..'
Tafada Cikin bayyana Takaichinta Da Sauri Haddir ya mike ya karbi kayan Hannunta yana Fadin"Kamar kin Shiga Raina Hajiya Mama..Wlh nima Haka nace..!
Yafada yana Sauke Farantin Gaban Alhaji Tsoho wanda ya murmusa yana Fadin"Mata mata..Sai abarku..Nan din Shine mafita ai Aminatu..Mahaifinta Dan Siyasa ne zamanta gabansa akwai mtsala Gwara tazo nan ta Haihu sai a Daura musu Aure suje chan su Cigaba da Renon Abunda Suka Hadu suka samar baShikenan ba.."
Hajiya Mama na zama Gefen Haddir Tana Fadin"Bafa Shikenan ba Mallam..Su mun Rufa musu asiri mu kuma mun Tona namu kana Tunanin mganar nan bazata Fita bane in Har yarinyar ta Dawo gabanmu da wannan Abun kunyar..? Alhaji Tsoho yace"Zai fita mana...Alheri ke Buya banda Sharri Aminatu..Kuma Wanda ya rufama wani asiri Allah Shima zai Rufamai Duniya da Lahira,Muma ai ya Rufamana Tunda bai kai mu kara Kotun musulunci ba Inda chan yakai Allah Jikanki jefasa za"ayi har ya Mutu Tunda da Auransa yake Zina.."
Hajiya Mama tace"Ita fa sai a kyaleta..? Alhaji Tsoho yace"In ta Haihu ita kuma Bulala 80 za"ayi mata Tunda ita batayi Aure ba.."Hajiya mama Tayi Tagumi Tana Fadin"Ba wacce nake jin Tssusayinta Har Raina sai Yarinyarnan Halima Dazu mukayi mgana da Fatima Take Fadamin komai taci sai Ta Dawo dashi kwana Take kuka Ga Rashin Barci..'
Alhaji Tsoho ya kada kai yana Fadin"Nima Wlh Aminatu..Kamar kin Shiga Raina da Yarinyar nan marainiyar Allah nake kwana ina Tashi..Ina Fatan Allah yasa ya zame mata kaffara.."Gabadayansu suka amsa da Ameen,Kafin Alhaji Tsoho yace"Mganar da Hadiru yazo min da ita kenan kam in saka Baki Takoma Gidan Mijinta Shima yana chan kwance ba lafiya Hadirun ma ke Kwana chan yana Kula Dashi..".
Hajiya Mama tace"Oh ni Amina...Allah ya kyauta na gaba..Me kace kan mganar..? Alhaji Tsoho ya sauke Numfashi yana Fadin"Me kuwa zan ce..? Bazai yuyu Ta koma yanzu ba saboda Halin Datake Ciki Gwara ta zauna anan Uwarta na Kula da ita Zuwa akara kwana Biyu ni dakaina zan saka Fatimar tazo Da ita nan na kara mata Nasiha Da Lallashinta Mganar Usman kuma Shima sai zuwa bayan an kwana Biyu zan mai Mgana kan ya Sausssauta Fushinsa Hakan bai da wani amfani Kai kuma Hadiru in ka koma Wajen Zainullahin in Jikinsa yayi sauki gobe ka kawomin shi nan ina son mgana Dashi.."
Haddir yace"Allah ya kaimu.."Daga Haka ya kalli Hajiya Mama yana Fadin"Me kuka Dafa ne Tsohuwa..?
Cikin Haushi Hajiya Mama tace"Uwarka Safiya ce Tsohuwa don kaniyarka.."Baki ya Rike yana Fadin"Me yayi zafi Kika sako Sunan uwata Gatse haka..? Karkace kai Hajiya Mama Tayi Tana Fadin"Don ma Bance Aliyu Kai Tsaye ba..?
Baki ya kama yana Mikewa Lokaci Daya yana Fadin"Kirashi mana ai ke kika Haifi Abunki ni miye nawa..? duk Tsiyarki dai baki haifeni balle kice zaki Dakeni Ni kinga ma Tafiyama basai kin ga mutum bama ballatana ki gayamai mgana.."
Yafada yana Bayyana yadda yaji Haushin Kiran sunan Mamarsa Datayi,Alhaji Tsoho na Gefe yana Mirmishi Cikin Tura Haushi Hajiya mama Ta Rakashi Da Fadin"Kwarai na Haifeka kuwa..Tunda na Haifi Uban daya kawoka Duniya kaga kuwa bama Duka ba zanyi sakaka Cikin Daki nayi maka Dukan Tsiya sai na barka kwance.."Ko Tankata bai yi ba ya Fice yana Fadin"Sai kuma kiyi..Ji dai da wannan Rudadden Tsohon Mijin naki.."
Da karfi Tace"Bana ga Rudadde ba..Rudadde ya wuce Ubannanka Bashir ko Aliyu.."Yana Jinta Daga Falo kai ya Girgiza yana Fadin"Gaskiya Tsohon chan ne Daya ce Rigimarki su Baban kaduna suka kwaso.."Abayyane yayi mganar Dakinsa ya Shiga Wanka yayi ya Sauya kaya kana ya Fito Kitchen ya Shiga wajen Tabawa suka gaisa Cikin Sanyin Murya Take Fadin'Ya zainullahi yake ne Hadiru..?
Tura baki yayi yana Fadin"Kai Tabawa..Wai kema Hadirun nan Har dake.."Dariya Tayi Tana Fadin"Eh mana wannan Shine zamu kira namu na Mutan Da..Ko Bakin ku na yan zamani ne Hadiru..'Kai ya Rausayar yana Fadin"Ba wani kuna dai Batamin suna kuma ba kowa yaja ba sai Tsohin chan Da matarsa.."Tabawa Tayi Dariya kawai Haddir yace"Zain yana nan Lafiya..Bai dai jin Dadi ne yanzu ma Shi nazo samar ma wani Abu Allah yasa kinyi Tuwon nan naki mai Dadi Tabawa..'Cikin alhini tace"Allah Sarki..Allah bashi Lafiya Jarabawa ce Allah ya bashi ikon Cinyewa damu gabadaya..!
Haddir ya amsa da Ameen Kafin Tabawa tace"Akwai Tuwon Shinkafa Miyar Danyan kubewa Wanda nayi ma Alhaji Tsoho ne.."Da sauri Haddir yace"Alhamdulillah..Saka mana Cikin Kula nayi gaba Dashi Daman na Dade banci Tuwon ki ba Tabawa.."Tana Dariya tace"Na Dumaman Alhaji Tsoho ne fa ko nayi muku wani ne..?
Da Sauri Haddir yace"No..Samana wannan Tafiya zanyi na bar zain Shi kadai..Yaci yanzu banda Hadama yace harda wani Dumaman Safe..? In yayi mgana gayamasa Manyan Jikokinsa na Bukata kin basu.."Tabawa na Dariya tace"Shikenan kuwa..!
Saka musu Tuwon Tayi Cikim kula Miyan ma Haka wacce Taji Kashin Rago da manshanu Dauka yayi ya Fice yana mata Godiya Ta Rakashi da Allah kiyaye Hanya da kuma sakon Gaisuwarsa ga Zain ko Dakin Alhaji Tsoho bai kara Lekawa ba Saboda yadda hajiya mama Ta gama bata mishi Rai abayan Motarsa ya Jera komai ka fin ya Shiga ya Tasheta ya Fice Daga Haraban Gidan Bayan Maigadi ya wangalemai get.
Yana Bisa Hanya Dadyn Abuja ya Kirashi sukayi mgana ya kara gayamai Halin da ake Ciki Daddyn Abuja ya Sauke Numfashi yana Fadin"Yanzu muka gama mgana Dashi ya Usman Din..Dama na sako mai nganar Zain din kashe wayarsa yayi ya Riga yayi Fushi Dashi ne sosai na kuma Kira Ya Bashir namai mganar Shima ya nuna Ma Ya Usman din yayi Daidai ne bazai saka baki ba..!
Haddir acikin Ransa yace"Daman ai wannan haka zai ce.."Haryanzu bai manta zafin marin Dayayi mai ba Cikin Damuwa yace"Daddy meye Abun yi Kenan..? U hv to do Something fa..'Daddyn Abuja yace"Karka Damu...Muna ta Shiryan Shiryan Dawowa nan Bauchi Dukkanmu gabadaya Har sai an gama Bikin Kanwarka Hamdiya kafin mu koma Insha Allahu i will Tary may Best naga komai ya Daidata kaji ko..?
Ajiyar rai Haddir ya Sauke Kafin yace'"I Truth u Daddy...."Daddyn Abuja yace"Tanque Son..Ina zain din bani shi a waya nayi mgana Dashi..?Haddir yace"Yana Gidansa yanzu haka ina kan Hanyata ta zuwa ne naje na Karbomai Tuwo Gidan Alhaji Tsoho..'"Jinjina kai Daddyn Abuja yayi kafin yace"Alrigh in ka isa Call me Ina son nayi mgana Dashi.."Haddir yace"Ok Daddy..Ka gaida Mom..!
Daga Haka suka yanke Kiran Shi kuma Haddir ya Cigaba da Driving Dinsa Bai jima ba ya isa Gidan yaji Dadin ganin Zain yaji Sauki Har ya sake yin wanka ya Fito Falo Har ya Shiga Kitchen ya Dafa Ruwan Coffea,Haddir ya Nuna Jin Dadinsa Sosai ganin Zain din ya Taahi da kafarsa ba kamar kwana Biyu nan Dayake Wuni Kwance ba Tare sukaci Tuwon Suna santi kafin Haddir ya maida Sauran ya saka Cikin Fridge,Shima irin na Alhaji Tsoho zai yi Dumame kenan Bayan ya wanko Hannu ne ya Dawo ya Kira Dadyn Abuja yabama Zain sukayi mgana Sun Dade yana ta Fada Cikin Hikima da Salama yana kuma Nuna mai Kuskusaransa kana ya bashi Tabbacin zai zo Bauchi bazai koma ba sai komai ya Daidaita Zain nata Godiya yana kuka kafin Wayar nasu ta kare sai alokacin ne Haddir ke Fadamai Sakon Alhaji Tsoho Duk da Zain yaso yaji me ya Faru Dayaje Tahowa da Firstlove..? Ammh sai yaki gayamai komai Illah cemai Da yayi Zareena da Nene na Gaisheshi Cikin mamaki yace"Ashe Har yanzu suna Sona..?
Dariya Haddir yayi yana Fadin"Ai ba"a sauya ka ba..Kanan nan amatsayin Yaya Daktan ka.."Sai da Zain ya Murmusa da kalaman Haddir Cikin Sanyin murya yace"Ya jikin Abba..? Haddir yace"Yaji Sauki Shima.."Daga haka ya yanke mganar ya Dauko wayarsa ya Fara Latsawa Shi kuma Zain ya koma ya Jingina da Kujera ya Fada Zurfin Tunani yana so ya Tambayeshi Zaina kuma sai ya kasa Domin baya so yaji wani Labari mara Dadi akanta,Shiyasa yayi Shuru da bakinsa Ammh Abun nacin Ransa da Zuciyarsa..
*****
Washegari kuma Tun Wajen karfe 10am na Safe Zareena da Zainab da Little Umma da Jalal suka zo Gidan Zain sun iskeshi Shi kadai Haddir baya nan ya Fita Zuwa Cikin asibiti,Yaji Dadi da kuma mamakin ganinsu Domin bai taba tsammanin Wani Daga Ahalinsa zai zo Dubashi ba Karban Little Umma yayi yana Kallon Zareena yana Fadin"Ammh Abba bai san kun zo ba ko..?
Kai ta gyada mai Tana Fadin"Bai sani ba..Gidan Alhaji Tsoho nace zani..Umma ma bata sani ba Nene ce kadai ta sani tace na Gaisheka kwarai ita tabamu ma wannan Ferfesun Kayan Cikin Tace mu kawo maka.."Idanuwansa suka Ciko da kwallah yabi kulan Dake Hannun zainab da kallo kafin yace"Allah Sarki Neneta..Na Saka Zuciyarta Ta Raunana saboda ni..Allah na Tuba Allah ka yafemin.."Suma cikin Tsausayawa sukace Ameen Jalal ne ya Hau gadon yana Fadin"Uncle baka da lafiya ne..?
Kumatunsa ya Shafa yana Fadin'"Eh Sojan Jaawad...Ina Babanka.? Zareena ne tace"Yana katsina ya samu Hutu ne...Daman kuma akwai Bikin Diyar yayarsa Jibi ma zai zo yaDaukemu mu Tafi Chan Family House dinsu sai an gama Biki zamu dawo insha Allahu.."Yana Mika mata little Umma yana Fadin"Allah ya kaimu ya kuma kaiku lafiya.."
Ta amsa da Ameen Shuru ya Biyo Baya Kafin ya Dago yana Fadin"Ya Firstlove take..? Tabar yin kukan...?
Zareena tace"Tadai Sauki kam..Nadai jita dazu ita da Umma Tana ta yi mata Fada kamar zata Dageta kan Kukan Da takeyi..'Cikin karaya da wani Irin Soyayyarta Dake Cikin Zuciyarta yace"Bazan iya kwana ban je na ganta ba.."Da Sauri Zareena tace"Ya zakayi da Abba..? Umma ma bazata barka ka ganta ba Domin Jiya marin Aboki Haddir ne kadai batayi ba kan yace yazo Tafiya da ita.."
Ido ya sakarmata yana Fadin"I know.."Yafada Cikin wata Murya Kamar yayi kuka kafin yace"Zan je koda zai Koreni ne..Zan je na Duka na Bashi Hakuri..Shi da Umma na kuma Dukama Firstlove na kuma Roketa Data Yafemim.."Zareena Tace"Shikenan ammh karka kaje kai Kadai..Ku Tafi Tare da Aboki Haddir.."
Kai ya gyada mata yana Fadin"Eh Tare zamu..Yanzu ma Shi nake jira zamu je gidan Alhaji Tsoho yace yana son ganina Ko bama Haka ba ni da kaina Zani Shima na Rokeshi Gafaran Abunda na aikata da kuma Kuncin dana sakasu Shi da Hajiya Mama..'Cikin Sanyin Murya Zareena tace"Ya kamata..Allah daidaita komai.."
Ya amsa da Ameen basu wani Dade ba suka wuce Zasu Biya School su kai Zainab Da Zareena Ta Fadamai haka ne ya Kalli Zainab yana Fadin"Zee Kun Fara Test ne...? Kai ta Girgiza mai kafin tace"Bamu Fara ba mu..Ammh wasu Duk sun Fara Yaya Dakta ina Jin ma Harda su Anty Zaina Domin na Hadu da kawarta Anty Laila take cemin yanzu zasu Shiga Test ne.."
Cikin Karfin Gwiwa yace"Dole zan je na Roki Firstlove gafara..Na Dawo da ita Gida ta koma makaranta bazan yi Sanadiyar Ruguza Burinta nayin karatu mai Zurfi ba.
******
Su Zareena basu kai awa da Tafiya ba sai ga Haddir ya Dawo Daman Zain ya Riga ya Shirya Cikin Riga da wando na Wata Blue Din Shadda Fitowa kawai yayi suka Wuce,Suna Hanya ne Haddir ya juyo yana kallonsa yadda Duk yayi Zuru Zuru ga Kasumba Tayi mai yawa Cikin Damuwa yace"Ko zamu Biya Shagon aski ne ka Rage wannan Gashin..?
Kai kawai Zain ya Girgiza kafin yace"Bashi ne agabana ba Haddir...Muje gidaanmu Dagachan sai mu wuce Gidan Alhaji Tsohon
Da Sauri Haddir ya kalleshi kafin yace""A"a ba yanzu ba Zain..Abba nacikin Fushi bazai Saurareka ba.."Zain Cikin Takaichi yace"Banga Laifinsa ba..Ko Bazai Saurareni ba Zanje na Duka na nemi gafaransa Koda zai min Koran karene..'
Haddir zai yi mgana Zain ya Dagamai Hannu yana Fadin"Komai ya Faru ninaja..Abaya Abba yamin haka..? Amsa ita ce A'a Saboda Naji na Dauka zan Tunkarin wannan Yakin Insha Allahu da Tsarkakken Zuciya Allah na Tuba ka yafemin.."Yafada yana Jin Taruwar kwallah acikin Idanuwansa Haddir bai kara mgana ba yayi Shuru yana Fatan in sun isa Allah ya Kwantar da Zuciyar Abba.
Allah kam bai amshi Addu"an Haddir ba Domin Suna Shiga Falon suka ci karo da Umma da Nene,Dukkansu Mikewa sukayi suna Bin Zain da ya Shigo abayan Haddir da kallo Cikin wani yanayi Umma kallonsa Take Tundaga sama Har kasa ganin yadda ya Sauya Cikin kwana Uku kachal,Nene kuwa Har ta Fara Hawaye ganin yadda yayi wani Baki ya Rame kamar bashi ba Cikin Dimuwa da Tsausayi ta Nufeshi Tana Fadin"Zain...!
Bata karisa Gareshi ba Shima ya Taho da Sauri Zuwa gareta Da Murnan ya samu kafadan da zai Kwanta yayi kuka Yaji Muryan Abba yana Fadin"Kul...Aisha karki Sake ki karisa kusa Dashi..Kinji ma nagaya miki..!
Yafada Cikin Kakkausan Murya,Gabadayansu suka waiga suna kallonsa yana Tsaye Daga Gaban Korodon Dakinsa Cikin Bakar Jallabiya Shi kanshi ya Rame din ganinsa yasa Zain ya Zura mai ido yana Jin Tahowar kwallah Cikin idanuwansa cikin Takun Rauni ya Fara Taku Zuwa gareshi Sai dai mai Cikin Tsawa Abba yace"Kul..Karka kuskura ka kara somin nan...Bana son ganinka..!
Yafada Cikin Tsawa da Fushi Wanda Harta Zaina Dake kwance Ta Fara Barci Ta jita Ta tsshi afirgice Tana Raba ido Shi kuwa Zain Cak ya Tsaya Idanuwansa Sun Fara Zubda da kwallah Cikin Raunin murya yace"A...Abb...!
"karka ka kara Kirana da wannan Sunan Kirani kai Tsaye da Usman Dina zai fin Dadi da naji kana Kira da Sunan Ubanka Zainullahi."Ya fada bayan ya Tarema Zain din Numfashi,Yanayin yadda yake mgana zaka Fahimci Ransa kuna yake Domin Shi kanshi Idanuwansa sun kala sun yi Ja Cikin Sagewa Gwiwa Zain yaji Kafafunsa sun kaisa kasa ya Zube Bisa Gwiwoyinsa yana kuka kuka mai Cin ran Mai Sauraro Cikin Fada Abba ke Fadin"Wama ya baka izinin Shogomin Gida...?baka ji Sakona bane..? Na sallama maka na Nace ka Tafi Chan ka zauna da karuwarka Dadironka Domin Ita ce Rayuwarku ta Dace da Juna bamu ba..!
Yafada Jijiyoyin kansa na Mikewa yana Numfarfashi Da Sauri Haddir yace"Abba kayi Shuru hakanan Saboda lafiyarka.."Abba ya juya kallonsa kan Haddir yana Fadin"Kai da ka damu da lafiyata..Toh in kana so nayi Shuru kace ya Tashi ya Fitarmin Daga Gidana Tunda bada Kwabonsa aciki na Siya Gidan ba.."
Jin haka yasa Zain ya Fara Rawan baki yana Fadin"Zan...Zan Fita Abba ammh sai na Rokeka Gafara..Don Allah Abba Don Annabi ba Domin Halina da Tarin Laifuka na ba..Ka yafemin Wkh Abba na Tuba bazan kara ba Na Tuba nabi Allah Abba bazan kara ba..."yake fada yana wani kuka mai Cin rai Nene da Gudu ta karisa Kusa Dashi itama ta Zube Cikin kuka Take Fadin"Don Allah kayi Hakuri Alhaji ka yafemai..Shifa Bawa ne kuma Bawa zai iya aikata Kowani irin Laifi Alhaji Don Allah karka Koresa Daga Gidanka in ka koresa ina zashi..?...
Itama Ta Fada Cikin kuka Ganin Haka yasa Haddir ma ya Isa Kusa da Zain Shima ya Duka yana Fadin"Don Allah Abba kayi Hakuri..ZAIN yayi Laifi kuma ya Gane Kuskuransa Don Allah Abba ka yafemai.."Umma Dake Tsaye Kai kawai ta Kauda Tana kuka Zaina kuma Dake Kofar Dakinsu k'asa Kasa Daukanta Tayi Sai da Ta Jingina da Bango tana wani kuka mai Cin rai Lokaci Daya Da Tushe Bakinta kada Kukanta Ya Fito.
Abba kuwa kai ya kauda Cikin Tsawa yace"Ya tashi ya Fice Daga Gidana nace..? Zan kira mai Jami"an Tsaro Wlh in bai Fita ba."Ganin Zain Bashi da Niyyar Tashi ne yasa kawai ya Fara Laluban wayarsa Dake Aljihun Jallabiyansa Ya Zarota Ya Fara Kokarin Kiran waya Nene da Haddir sun ma kasa Mikewa Ballatana Zain da kansa ke Duke ya Hada Hannayensa alaman Roko Idanuwansa na Zubar da kwallah
.
Cikin Bazata Suka Ji Abba ya Daga waya yana Fadin"Dpo....!Bai Karisa ba,ZAINA ta bayyana Afalon Tana Dingishi Lokaci Daya Tana Dafa bango Tana Fadin"A'a ABBA...DON ALLAH KADA KA KIRAMA DA'N DA KA HAIFA DA CIKINKA YAN S A.N.D.A..'Tafada Cikin Rarrabe mganarta Saboda kuka Cak Abba ya Tsaya da mganar Da yake yi ganin Zaina wanda Ya kwana Biyu bai sakata a ido ba.
Haka ma Zain Cak Kukansa ya Tsaya Nene da Haddir ma suka Dago suna kallonta Haka ma Umma Ganin Abba ya Tsaya ne yasa Zaina ta isa Gabansa ta Zube Tana kuka Tana Fadin"A"a Abba Hakan bai kamata ba...Duka Abun na Cikin Gida ne Don Allah kayi Hakuri kada ka Koreshi Daga Gidanka Da jikinka Gabadaya..!
Tsura mata ido Abba yayi Cikin Tsausayamata yana Ganin itace ma Abun Tsausayi Wayarsa ya kashe ya maida aljihun gaban Jallabiyansa Ya Saka Duka Hannunsa ya Tallabo kafadunta Ya saka Kuma Hannunsa Duka Biyun ya Daukemata Duka Hawayenta Yana Fadin"Naji bazan kiramai Jami"an Tsaro ba..Ammh ya Tashi ya barnin gida..!
Zatayi mgana ya Hanata Da Daga mata Hannu Lokaci Daya Ya Kai kallonsa ga Zain wanda ya Kura musu Ido Shi da Zaina wacce yake jin kamar yaje ya Rumgume Zaina ya Fashe mata da kuka Ta Fahimci Nadamarsa Da Yadda yayi kewarta.
Cikin Kakkausan Murya Abba ya kalli Zain yana Fadin"Wlh Tallahi Ko Saboda Cutar da wannan Marainyar Allah da kayi Zainullahi Allah bazai barka ba..Kuma nima bazan Taba yafe MAKA BA...!!!
Kowa Abba yabi da kallo Wanda ya Juya yana Tafiya Yana Fadin"Aisha Ki gayama Dan'ki ya Fita yabarmin gidana..In na kara Fitowa na ganta Abun bazai mana kyau ba.."
Ya Fadin haka ya Shige Dakinsa ya Banko Kofarsa,Kawai sai Zaina Ta Sulale nan ta Fashe da kuka Zuciyarta na wani Rawa Saboda ita Abba bazai yafe ma Zain ba..? Ta Shiga uku Kar tayi Sanadiyar Raba D'a Da Mahaifinsa..? Ina zata saka kanta In haka ta Faru..?
Zain Da ya Fara Rarrafe kamar karamin yaro yana kuka zuwa ga Zaina sai da Taji kawai Numfashin Mutum Gabda da Ita Tana Dago Fuskarta Datayi Jabe Jabe da Majina Da Hawaye suka Hada Ido Hudu, da Zain Kowa tsayawa yayi yana Kallon Kowa..Kuma kowa da Abunda Yake Sakawaa cikin Ransa,Yana kallonta yana Zubar kwallah itama Tana kallonsa Hawayenta na Bulbulowa kamar an Bude Famfo.
*Shakira...*
*ZAINAZAIN..!*
_(Is a love Story and Betrayal)_
*Wattpad:Jamilaumar351*
*Mallakar:Janaftyshakira*❤️
*BOOK 1*
2️⃣4️⃣
"Ita Zaina Tana Kallonsa ne Da Dukkan Zuciyarta Mai cike da Soyayyarsa Kaunarsa da Kuma Tarin Tsausayinsa da kuma yardansa Idanuwanta na Fidda Hawayen karaya da Rauni Ganin yadda ya Rame ya Fita Hayyacinsa Cikin kwana Uku Kachal.
Shi kuma ZAIN yana kallonta ne Cikin Raunin Zuciya,Karaya da Ban Hakuri da kuma Soyayyah da kaunarta Hade da Tarin Tsausayinta ganin yadda ta koma Kamar wacce bata da Ishashan Jini ajikinta,Gabadaya Jikinsa Rawa yake wajen Saka Hannunsa ya Riko Nata Hannu Cikin Rawan baki Dana Murya ya Furta..
"FI...rsT....LO..ve...'Ya fada Gabadaya Jikinsa na Daukan Rawa Dukkansu sai da Zukatansu suka amsa Cikin Fitan Hayyaci da wani irin Muradi mai Girma da kuma Nenan sauki da Waraka ga Halin Dayake Ciki Taji ya afka Jikinta kawai ya Rumgumeta da wani irin karfi Wanda ba Domin Ta saka Dayan Hannunta ta Tallafe kasan Cafet din ba babu Abunda zai Hanata batayi Bayaba ya Bita sun baje atsakar Falon ba Saboda Tsabar irin Karfin Rumguman Da yayi mata.
Da karfi ya matseta Har sai Da Taji bata iya Fitar da Numfashi,Kansa yake Tusawa Saman Kirjinta Lokaci Daya yana sakar mata wani marayan kuka wanda Sai ya Tada Hankalin Mai Imani Nene da Haddir kuwa Wani irin Abu Suke ji akansa Ransu na Tsausayin Duka Zain din da Zaina,Ita kuma Umma Kuka take kawai Batare ma Da tasan kukan Me take yi ita ba,ta dai sani Zain ya kasanace mafi soyuwa acikin Ranta Tun yana karaminsa Bata iya Juran kukansa Sai dai ta Boye ko kuma ta kauda kai Saboda Nene.
Jin yadda yake kukan ne yasa Raunin Zaina ya kara Bayyana Cikin Wani irin azama ta Dago Hannunta zata Rumgumeshi,Sai kuma ta Fasa Domin Alokacin Hotunan Zain da Dina ne Cikin yanayin Da ita kadai ta sanshi yake Gilma mata Gefe guda kuma Tana Tuno mganarsa na Yarda da cewa Cikin Jikin Dina nashi ne da Sauran mganganu,Gabadaya Jikinta ya Fara karkarwa Cikin Sarewa Da Duk wata yarda da Tsausayi kawai Ta Janye Hannunta Lokaci Daya ta Fara ja da baya Tana Kokarim kwace Jikinta,Ganin Tana Mutsu mutsun kwace kanta ne yasa ya Dago Da kansa Fuskarsa Duk Ta baci Da hawaye yana kallonta Itama Shi Take kallo Cikin mamaki yaga tana ja da baya Hannu ya mika zai Rikota da Sauri Ta kara matsawa Baki ya Bude yana Fadin"Firstlove...!
Kai ta girgiza mai Tana Fitar da kwallah,Sai kuma ta Fashe da kuka kawai Tana Girgiza mai kai tama kasa Mgana Zain ya Duka Hannu Bibbiyu ya Riko Kafar zaina yana kuka yana Fadin"Firstlove...Matata Farincikina...Halimatu Abdullahi Gada..My Firstlove my World,Kece Rayuwata Zaina In baaki bazan iya Rayuwa ba..Naji na yarda naci amanar Soyayyarmu naci Amanar yardan Da kikamin ki Taimakeni ko ki kara bani Dama ta Karshe Don Allah..Ni zainullahi Abubakar Saulawa nayi Miki Alkawarin bazan kara Dabi"ata ta neman mata ba,ammh Plz Don"t Leave me i Can"t do Without u..!
Ya karishe Fada yana Kife kansa Jikin Kafanta yana kuka,Itama kukan Take Lokacin Har Jikinta ya Fara wani irin Tsuma Umma ce Ta Lura da haka da Sauri Ta Share Hawayenta ta isa Garesu Cikin Fushi ta saka Hannu ta
All Chapters
Chapter 1
Chapter 2
Chapter 3
Chapter 4
Chapter 5
Chapter 6
Chapter 7
Chapter 8
Chapter 9
Chapter 10
Chapter 11
Chapter 12
Chapter 13
Chapter 14
Chapter 15
Chapter 16
Chapter 17
Chapter 18
Chapter 19
Chapter 20
Chapter 21
Chapter 22
Chapter 23
Chapter 24
Chapter 25
Chapter 26
Chapter 27
Chapter 28
Chapter 29
Chapter 30
Chapter 31
Chapter 32
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 24 Chapter of 32