Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
Wuni Daya ne Dole ka Shaida Wacece Firstlove a Wajen Zain. Ba Dina Bace Sanadiyar Fara Lalacewar Zain ba Ita Dina Daga Baya tazo makarantar Domin Zain na gabanta da Shekara Daya sai akaci Sa"a kuma Duka Course Daya zasu karanta,Zain yana da Sakewa da Mutane Both Mata da Maza Sabanin Haddir Dake da kamewa da kuma Daraja Mutumtanka Gidansu da kuma Tarin Nasihun Iyayansu har ma Gargadin Alhaji Tsoho Garesu na su Tsarkake Zuciyarsu Suji Tsoron Allah Suyi Abunda ya kaisu ammh Zain ya watsar da Wannan Farkon Abun da ya Fara kaishi ga Kusanta ZINA shine Biye ma Matan Turawa Wadanda muke da Bambamcin al"ada dasu da kuma addini. Tun Zuwan Zain makarantan Yayi yanmata da Kawaye mata Wadanda bai san iyakarsu ba In suka ce Suna sonsa baya Taka musu Burki Saboda Shedan ya saka Mishi Sha"awarsu Banda Son su Saboda So Daya ne Tak kuma Zainarsa yake ma Wannan Son Da wannan Abun yasa ya kan kyale su Tabashi Har ma Suyi Hugging Dinshi Su kuma yi Kissing Dinsa baya Damuwa Tunda ya gani a nan Duk Normal ne. Dalilin Fara aikata Zinarsa Ta Farko Suna Shekara Na Biyu a Landon ne Wata Kawarsa Gloria,Baturiyace yar kasan London din ce itama karatu ya kawota makaranta Tun ganin Farko Da Tayi ma Zain ya Shiga Ranta Ta Dinga Neman kusanci Dashi Dayake bashi da Wuyar Sakewa Nan da nan ya Saki Jiki Da Ita suka Shaku suka zama kawaye suna Fita yawo Tare da Zuwa Wurare Dadama Kwatsam Ranar ta gayyaceshi Gidanta Cin Abincin Dare Wato Dinner Daya nemi Haddir yazo suje yace bazashi ba sai yayi Fushi ya Tafi shi kadai Ashe ta Shiryama Ranar Mganin karfin Sha"awa ta sakama Zain a Alemi yasha Domin ya Biya mata Bukatunta Tunda Tayi kokarin Hakan ta kasance ammh kuma Shi Zain din yana kwace ma Hakan. Ranar Zain yayi Zina da Gloria kuma Abun Takaichi ma Bashi ne ya Fara saninta ba Ranar agidanta ya kwana Bayan komai ya Lafa yashiga Nadaman Abunda ya Faru yana kuka yayi mata Kaca kaca suka Rabu koda ya koma Gidan da iyayensu suka kama Musu Shida Haddir baya Cikin Natsuwar,Dama bai da Rike Abun Aranshi yana komawa ya kwashe komai ya Gayama Haddir Suka zauna sukaci kukansu Tare ammh Haddir yayi ta ma Zain Fada kuma yayi mai alkawarin Rufe wannan Sirrin ba Wanda zai Ji Bayan Shi Zain din yamai alkawarin zai Guji Faruwan haka. Kamar Gaske Zain ya Fitar da kansa Cikin Wani Shashancin makaranta ya koma ya maida Hankalinsa kan karatunsa sai dai kuma Waasa Farin Girki Tunda Gloria ta Dandanamai kamar ta Jona mai Bala'i sai ya kasa Sukuni yayi yayi ya Danne Abun ya kasa Bayan Faruwar Haka da wattani kadan Zain ya Koma Ruwa Harka da Mata kaca Kaca Duk wacce ta saki kanta zai Taya kuma yayi Abunda yaga Dama da ita Tun Yana Boyema Haddir har Abun ya Bayyana ya sani Ranar ya kwana Cikin Bakincikin Halin da Dan"uwansa ya saka kansa Yayi mai Fadan da Nasihan ammh Duk Abanza Sai ya koma mai addu"an Shariya Abu Daya ne yamai Dadi ganin bai wasa da karatunsa ba kusan yana Jerin masu Tafiya da manyan point aset dinsu. Addu"an da Haddir ya keta mai da kuma Nasihan Dayake ta mai a kullum yasa Kuma Abun yayi sauki Zain din ya Rage Neman matansa Ba kamar baya ba Duk da yana yi ammh ba Sosai Haddir nata jin Dadin sai dai kwatsam Suna Shekara ta uku a London har kuma Lokacin basu je gida ba Sai da Abba yazo Dubasu Shida Alhaji Tsoho da Dadyn Abuja Wanda suka Rako Alhaji Tsohon wani Asibitin aka Dubashi bayan Tafiyarsu ya Fara Fama da Kafa Da sukazo Haka Zain ya Dinga Rokon Kar Haddir ya Fada musu Halin Da yake ciki Shi kuwa mai zai kaishi Fadan wannan Abun..? Ya gwammace koma me zai Faru ya Faru ammh Zai Rufama Amininsa Kuma Dan"uwansa asiri Ahaka suka zo suka gansu suka koma Batare da sun Fahimci Zain din ya Chanza Daga yadda suka Shanshi ba. A Daidai Tsskanin ne kuma Dina Gaddafi Sheerif ta Shigo Rayuwar Zain wanda ta kara Tabarbara komai Daga Tarbiyansa Gabadaya. Dina Gaddafi Sheerif Haifaffiyar Garin Jahar Kanon Dabo ce Mahaifinta Gaddafi Shareef Dan garin Bama ne Dake Maidugurin Nageria,Mahaifiyarta kuma Sarah Balarabiyar Sudan ce Auran Soyayyah suka yi da mahaifinta Wanda ya kasance Dan Siyasa ne,Tun bayan Auransa da Sarah suka Fara samun Matsala kan Rashin Kulawa ga iyalansa Yafi maida Hankali kan Harkokinsa na Siyasa Suna Haka har Allah ya basu Dina Ita kadai kwara Daya Allah ya basu Shiyasa ta tashi Cikin Gatan Duniya ta kowani Bangare. Abunda yasa Ta kara Sangarce Shine Rasuwa Mahaifiyarta Sara Tana da Shekara goma aduniya Dangin Mahaifiyarta Sun so su Dauketa Su maidata Sudan su Riketa Tunda Rikon Diya Mace sai mace ammh Alhaji Gaddadi Shaeerif ya Hana Adauketa Saboda yadda Gabadaya ya maida Soyayyar Sarah ga Dina din Dole suka Bar mai Ita Ba Domin Ransu yaso ba Sai Domin Tsausayinshi na Ganin Rasuwar Sarah din Ta Tabashi Sosai. Da farko kamar zai iya kula da Ita sai kuma ya gaza Saboda ya kara Shiga Harkan Siyansa Sosai,Sai ya Dauko mata mai Reno ya kawo Gidan Tana kula da ita Tunda Wani Lokacin Tafiya Tana Kamashi Wannan Dalilin Shine Dalilin Dayasa Dina Tatashi bata Da Tarbiya Ga kuma Sangarta Datayi mata yawa Tatashi ba"a gaban Uwa ba Ba kwaba Uba kuma bai da Cikakken Lokacinta Ballatana ya Tsaya Tsayin Daka Wajen bata Tarbiya Sai Rayuwarta Tatashi Sai Abunda Dina Taga Dama Take yi kuma Duk Abunda Tayi Niyya Shi take aikatawa bamai ce mata Domin komai Ko Chan Sudan bata Cika zuwa ba sai dai su suzo su ganta Ko su Suna Cikin Takaichi da bakincikin Yarda Dina Ta sangarce Ta kuma Tashi ba Wata Tarbiya Tare da ita. Duka Karatunta Har zuwa matakin secondary a Frine Collage Tayi Dake garin kano Sai kuma alokacin Alhaji gaddafi ya kara Aure,da Wata Mata Itama Ta taba Aure Mijinta ya Rasu Sai dai bata Taba Haihuwa ba mai Suna Hajiya Batula,itama yar nan garin kanom ce kanwar Wani abokin Siyarsa ne ya bashi ita ya Aura Saboda Suna samun suka Wajen abokan Siyarsasu kan Rashin Auren na Alhaji Gaddafi. Bayan kamallah karatun Dina amatakin Secondary University of Lagos Dina ta Fara ammh ganin Kokarinta da Hazakarta Yasa Mahaifinta ya Dauketa Daga nan ya kaita London Domin Tayi Karatunta achan Ita kuma da Kanta Dinar Ta zabi Bangaran Likitan mata a fanni da zata karanta Duk wanda ya ganta Sai ya san cewa Dina yar gatace ta gaba da Baya Domin Gida sunan gida Mahaifinta ya Siyamata ya Zube mata ababen Jin Dadin Rayuwa Gata kyakyawa Son kowa kin Wanda ya Rasa Da wannan kyan nata Take jan Hankalin da yawan Maza da mata zuwa gareta Duk da Iya Rumguman Namiji da kissing Abunda dai ba"a Rassa ba Ammh bata Taba jin zata iya bama Wani Martabanta ba sai Haduwarta da zain wanda Taji zata iya Bashi komai saboda Son shi da Allah ya Dora mata. Tun Shigowarta makaranta ta Fara Sanin Labarin kwazon zain da kuma Kokarinsa sai dai bata maida kai akansa Ba Tunda Itama Tana Ji da kanta ammh Sai kuma ta kasa Saboda kowa Tadinsa yake Duk da yana Gabanta Sai da ta Shekara a makarantar kana Tataba ganin Zain Ranar da Ta Fara ganinsa Wajen Buga Table Tinnes ta Raina kanta Domin akaron Farko,Ta Raina kanta Saboda ganin Haduwar Zain da kuma yadda komai nashi ya Tafi da Imaninta Bata Tunkareshi ba Saboda Itama Tana ji da kanta sai dai kuma ta kasa Sukuni da Tunaninsa Abu kamar wasa ya Zama gaske karfi da yaji Zain ya kaasa bace ma Dina acikin Zuciyarta da Haka ta Fara Neman saninsa Dayake Tana da kudi Cikin Lokaci kalan Ta samu Labarinsa Garinsa da kuma Abunda yake karanta da kuma Wasu Daga Cikin Hallayarsa ta Hannun Wani Saifkhan wani abokinsa Dan Indiya ne Wanda Yake ta Shigema Dina Saboda yana Sonta ita kuma sai Tayi amfani da wannan Damar tasan komai game da Zain din Harda Neman matansa Hatta da Labarin Haddir ta samu. Jin Labarin yana Harkan Mata sai Ranta ya baci kishi ya kamata Da Farko Taso ta kyaleshi Sai kuma ta kasa Dole ta Nemi yadda suka Fara Haduwa da Zain din Ta Hanyar abokinsa Saifkhan,wanda Taje da Niyyar wani karatu ya Shige mata Duhu ya koyamata Ganin Farko da Zain yayi ma Dina yaji Kyanta da komai nata ya Burgesa Cikin Lokaci ya Saki Jiki Da Ita Har ta Fara sanin Wasu Sirrinkan nashi Ciki kuwa Harda Labarin Zainarsa Wanda Tun alokacin Dina Taji ta Tsaneta Saboda Ko karatunsa Zain baima Maimaici kamar Mganar Wannan yarinyar. Haddir Rana Tsaka yaga Kawance da Wata Shakuwa ta Sarke Tsakanin Zain da Dina Wanda Tun ganin Farko da yayi ma Dina tazo gidan da Suke zaune yaji batamai ba Domin Daga ganinta Bata da Wani Cikakken Tarbiya Da yayima Zain mgana akan ya Rabu da ita sai da sukayi Wani gagarumin Fada da suka kusa Sati basa mgana Sai Daga baya suka Shirya Ganin baya son Ana mai mganar kan Dina sai Haddir din ya Tattarasu kawai ya Watsar Ita kanta Dina Tasan Haddir baya yinta Domin ko Gaisheshi Take Dakyar yake amsawa yana wani Cin mgani Har Zain din Tataba mq mgana kan Shi Dan"uwanshi bai son Wayewa bane..? Ya takura kansa Shi kadai Dariya yayi mata yana Fadin Haka yake Tun muna Yara Haka yake baida Hayaniya Bazaki iya Chanzashi ba Daga haka Itama ta Fita Batunsa ta Dinga Jan Zain din ajiki Domin Ta Rabashi da Hulda Da Sauran mata. Zain Shi ya Fara sanin Dina a Ya mace,Kuma Bashi ya Roketa ba Ita da kanta Ta bashi Saboda ta kamashi da Wata Budurwann Shashancinsa Ta koreta Bayan Tatafi sai ya Fara mata Fadan Bayason Haka Data koreta zata Bashi Abunda wanchan zata Bashi ne,Ita kuma saboda Lokacin Tagama mutuwan a kansa Tana Jin zata iya komai akansa kawai batare da wani Nadama ba ta bashi kanta Tun kuma daga wannan Lokacin su ka koma suka kulle kamar mata da Miji,Dayake shi Zain yasan kanshi Da Condom yake amfani Da Dina Tamai mgana sai yace Mata Tana so ya kwasan ma Firstlove dinsa Cuta ne..? Ita kadai ce Yake so Duk Duniya Shiyasa bayason yayi Abunda Zai Bata mata Rayuwa Ranar sai da sukayi Kaca kaca da Zain a Kan Zainarsa Ta Shareshi shima ya Shareta Ammh Daga Baya ita Ta Nemeshi kana Suka Shirya Domin Bazata iya Jurewa ba Kalaman Zain sun fi komai kona mata Rai Dayace mata Halima ce kadai yake ma Sona Na Hakika Sauran matan kuma Da Taga yana Harka dasu Sha"awarsu kawai yake Da Tace mai Harda ita Kai Tsaye yace Kwarai Tana Cikinsu Wannan Dalilin yasa Ta kara Tsanar Zaimah Din Tun ma bata Taba ganinta ba,ta kuma gane in Tana Son Zama da Zain Dole ta Daina Nuna bata kaunar Halima in kuma ba Haka zai iya Rabuwa da ita akanta.   Koda Haddir ya Farga da irin Kullewan Zain da Dina yaji Takaichi Yayi ta ma Zain Fadan meyasa yake Kokarin Sauya kansa,ya manta da iyayensu da Abunda suka Turosu suyi..? Yaya Halimar tashi zataji in Tasan Abunda yakai aikatawa zata yadda ta Aureshi kuwa..? Wannan kalaman na Haddir sunsa Zain ya Dawo Daga Hayyacinsa har yayi kokarin yakice komai Hatta ko da Dinan yace Rabuwarsu tazo Saboda Halimarsa Bayaso ta Samu Raunin Zuciya in Taji Abunda yake aikata mata na cin Amana Anyi Haka ba Dadewa suka samu Dogon Hutu suka Dawo Nageria wanda ko Sallama bai iya ma Dinar ba Sai Bayan Tafiyarsu Taji Labari alokacin Idanuwanta ya Rufe Basu samu Hutu ba su itama Ta Tattaro ta Dawo Gida Saboda Tayi Shiri Sosai kan Zain Domin bata Fara Sonshi Domin Ta Daina ba alokacin Daya Nuna baya son Harka da ita,ita alokacin Take Kara Jin Dadin Harka. Tana Komawa Gida Babanta bai Tsaya Tambayanta meya Dawo da Ita ba Itama bata Tsaya mai Bayani ba Tunda Alokacin Siyasa Tayi zabi Har yana matsayin House af Rep na kano alokacin ba Zama Tana Dawowa Taje ta Nemi Wata kawarta Zakiya Nuhu Wacce sukayi Makaranta Tare a Frine Collage Kawancensu ya samu asali ne Tunda kaf Hallayansu yazo Daya na Rashin ji da kuma Rashin ishashiyar Tarbiya Itama Zakiya Bata da Uwa Hannun Muguwar Kishiyar uwa Tatashi Shiyasa batajin Mgana Ita Taje har Chan Zaria inda Zakiyan take chan Tana karatunta,Ta sameta ta Zayyane mata komai ita kuma ta Dauketa Ta kaita Hanyar kaduna Wajen wani malami Dayake mata aiki kan Samarinta Tana Juyasu yayi mata aiki kan Zain akan komai Runtsi bazai Taba Rabuwa da ita kuma Kuma Tana so ya Daina Son kowacce mace da Sha"awarta sai Ita Malamin ya gayamusu zasu yi Nasara ammh Akwai Wani Taurari Dake Tare da Taurarin Shi zain din Yana da Karfi kuma yaga Aurattaya Tsakaninsu Toh Ita din bazai Taba Daina sonta ba kuma Ita Din Tana Daga Cikin kaddaransa Ko bai Fadi Suna ba Tasan kowacece Halima ce Zainarsa. Malamin ya gayamusu zatayi Nasaran Rabashi da Sha"awar kowacce mace,zai Dawo nata ita kadai kuma Bazai iya Rabuwa da Ita sai dai kuma a Tarrayansu yaga Duhu Sosai,Kuma Zasu yi Aure da Juna bayan ya Auri Wacce yake so Sai dai yaga Tashin Hankali Soaai da Turniki acikin lamarin Dina ta yadda da komai Da malamin yace daga Haka suka Zubemai kudi suka Tafi akan cewa Zain din da kansa zai Nemeta Su sasanta. Dawowarsu Zain Lokacin Halima Tana Cikin Shekaranta na Sha uku ne Ta Fara zama Budurwa Tunda Har ta Fara Kirgan Dangi,Zain yayi matukar murna ganin yadda Zainarsa ta kara Girma sai dai yayi ma Su Umma Korafin Zafeera tafi Zainarsa Kiba ita sai Tsaho Yana ta Kunci wai basa kula mai da Ita,Sudai sai Dariya suke mai Ita kuma alokacin Ta Fara Fahimtar komai sai ta koma Jin kunyar Zain din Duk da Tafi kowa Dokin Dawowarsa . Lura Da hakan da yayi sai ya Fara Janta ajiki Sosai yana kara nuna mata Salon Soyayyarsa Wanda Daman itama Dashi ta Bude ido Tsaraba kuwa Rabi da kwata nata ne kantin London sun Shaida Haka Domin Tun Farkon zuwansu Duk Abunda ya gani sai yace zai ma Zainarsa kyau sai ya Siyamata Zafira nata Jin Haushi ita kayanta kadan ne Ita kuwa Halima sai murna Take tana musu gwalo Ita da Faruq. Sun Dawowa ba Dadewa Zareena ta Dawo Gida Hutu da kuma zata Tsaya tayi Wata Shiga agidan Radiom Bauchi Saboda koyon makaman aiki Murna Wajensu ba'a mgana sai Gida ya Sake Rudewa Duk da Tunda Suka Dawo Gidan Alhaji Tsoho Suke yada Zango Kafa Tayi Dadi yanzu baya zuwa Ko"ina Kafafun sun gaza Don ma Hutu da Jin Dadin Suna Tare dashi Zareena ta Dawo ba Dadewa Zain yabi Haddir suka Tafi Abuja kwamansu uku da Zuwa zain ya kasa Jurewa ya Nemi Dina sai da taga mai Wulaknci kana Tace mai Tana kano Haddir bai san ina Zain yake Saurin zuwa ba Suda sukayi Niyyar yin Sati kafin su Tafi ammh Zain yaki zama Yace zai Fara Tafiya Haddir din yazo Daga Baya Da Haka ya Barsa a Abuja yaje Kano wajen Dina Chan ya karishe mata Kwana Hudun acikn gidansu da Hajiya batula ta Yi mgana sai tace abokinta ne bata Damu ba nan sukayi ta Shedancinsu Babu Wanda ya Damu Dasu,har kuma ya Tafi Basu Hadu da Mahaifin Dina ba wai yana Abuja. Koda ya koma Bauchi ya iske Haddir ya Dawo Daya Turkeshi yana Tambayansa Bai iya karya ba ballantana Rike Sirri ba,sai kawai ya gayamai Wajen Dina yaje..Ranar Sai da Suka kusa Dambe da Haddir Daga Karshe akayi Rabuwan Baram Baram Washegari kuma Haddir din ya Hada kayanshi ya koma Abuja Wajen iyayensa Bakuma wanda yasan Abunda ya Faru Tunda Haddir din bai gayama kowa ba Shi ma Zain din Ammh Su Umma sunyi mamakin Abunda yasa Daga Dawowan Haddir Jiya Jiya kuma Gari na Wayewa yace musu zai koma Zareena Tayi Tambayan Duniyan Yaki gayamata komai saboda ya Riga yayi alkawarin zai Cigaba da Rufama Zain wannan Sirrin Har Abada ba wanda zai ji Sai dai yana Fatan ya Daina Abubuwan Dayake yi kada Bacin Rana tazo Ranar da kuma zai yi Nadaman Abubuwan da yake yi. Sun Samu Hutu mai Tsawo Wajen Watansu Hudu agida kana suka koma Wannan karon ba Dawowa sai sun kamallah karatunsu,Wannan karon ma Halima Tasha kuka ammh ya Lallasheta Tare da mata alkawarin Daya Dawo za"a Daura musu Aure Duk inda zashi Sai Su Rika Tafiya,Sun koma da kwana Biyu Itama Dina ta Dawo Domin Taki yarda Ta koma Saboda Zain bai koma ba Kuma ahakan ma yana Zare jiki ya bita chan kano su lalacewarsu sai yayi karyan yana gidan Baban Kaduna ko Gidansu Haddir wanda Har suka koma basu samu wani Fahimtar juna ba sama sama. Tunda suka koma Suka maida Hankali ga karatunsu ganin Abun yazo ganganra,Bamgaran Halima kuwa suna mgana Lokaci bayan Lokaci Game da Birthday Dinsa Ita da Nenensa basa manta Wannan Ranar ko bai kunna Wayarsa ba zai zo ya Samu Sakonninsu na Tayashi Murna Achan Gida kuma su Taru Su Tayashi Murna Suna Cikin Shekara na Shida a London ne Halima da Zafeera suka Shiga Catering School and Snack kuma Shima sai da ta gayamai ya amince kana ta Shiga Na wata uku ne suka gama aka yayesu Bayan an Basu Takardan gamawa. Sai da suka Shekara Bakwai a London kana Suka Tattaro suka Dawo bayan sun kamallah karatunsu Duka Iyayen nasu Sunje musu Murnan gamawa Alhaji Tsoho me kadai da Hajiya mama Basu zamu zuwa ba ammh Baban Kaduna da Mommy iklima Sai Dadyn Abuja da Mama Safiya Umma ce kadai batazo ba Tana Gida Nene ce Gaba Gaba da Abba sai Zareena Wacce Har ta gama karatunta Tayi Bautar kasa ta samu aiki a Gidan Radion Bauchi Sai Zafeera da Halima da Umar Faruq,sai Sadiq babba bai zo ba yana Makarantar Chan Univesrty of Ibadan,Hatta Da Inma Hannatu Taje London Inna Rukayyah ce bata samu Zuwa ba. Wannan Shine karo na Farko Da Dina Taga Zaina ido Ido ta kuma Shaida Irin kaunar da zain yake Fadin yana mata ta ganin ma Idamuwanta Tun da ya samu Tarin kyauttukan kan Hazakarsa da Kokarinsa Duk inda ya saka kafa Zainarsa tana Gefensa baya Yarda Hannunta ya Rabu da Hannunshi Gabadaya kyauttukansa Ita ke Rikemai kowa kuma ya ga Zainar Zain wanda suka Dade suna Jin Labarinta Dina Tayi Bakinciki ganin aranar Zain yama manta da ita ganin yan"uwansa da Halima Wacce ta kara Ninka Tsanan Data ke mata,Zain bai Tuna da Dina ba Sai bayan komai ya kamallah Da Daddare kana ya Saci Jiki yaje Gidanta Bata barshi ya Fito ba Sai da ta Hillaceshi suka aikata Haramun kana ta barshi ya Dawo Sunyi sallama Tunda gobe da Safe zasu koma Gida da Iyayensu,tayi tayi Zain yayi mata alkawarin zai Aureta ammh yaki Kalma Daya yake gayamata Bata ga Matarsa bace Shi Daman bai Taba Cewa yana Sonta ba wannan Harkan ce ta Hadasu kuma Ita ta Nuna tana Ra"ayi Shiyasa Har suka kawo iwar Haka,sallam nasu dai ba wani Dadi Tana kuka tana komai ya Tafi ya barta koda ya Dawo Iyayensa da Ita kanta zainar nashi Tana Ta Nemansa Ba"a ganshi ba sai yayi karya Dayaje sallaman Wasu abokansa ne,Kowa ya  yarda banda Haddir wanda ya kalleshi kawai Shi kuma ya Banka mai Harara nan ya Ja Hannun Zaina suka Kebe Gefe suna ta Hiransu Cikin So da kaunar junansu. *Comments* *Share and Vote..* *Shakira...* *Intelligent writer"s asso..* *ZAINAZAIN..!* _(Is a love Story and Betrayal)_ *Wattpad:Jamilaumar351* *Mallakar:Janaftyshakira*❤️ *BOOK 1*              0️⃣7️⃣ "Shekara Daya Zain da Haddir suka yi a Bauchi Suna housemanship Dinsu a asibitin Dr.Saulawa Wanda Dama Dole alhakin komai na asibitin kansu zai koma,Gaskiya sun yi kokari Sosai sai yabama Kokarinsu yake ashekara Dayan da sukayi Sun bada gudummuwa Sosai Wanda ya kara Farantama Alhaji Tsoho rai Wanda Yaji ko Cikinsu ba"a samu Wanda ya Karancin Bangaran kwakwalwa ba akallah ya samu Wadanda Suka karancin Bangarorin da zasu Taimaki Talakawa Wato Yara da kuma Mata. Bayan sunyi Shekara Daya Suna Internship Dinsu Sai kowannensu ya Tafi Yin Course akan Abunda ya karanta na Shekaru Biyu Zain Wata Medicine School ya Tafi Dake Garin Mumbai Shi kuma Haddir ya Tafi Cyprus,wanman karon Iyayensu sunyi mamakin Yadda Suka Raba Wajen karatun nasu ammh Dalilin bamai jin kansu ba Wanda ya Matsa sai yaji Dalili ko Zamansu na Shekara Daya ba wata Jituwa suka samu ba Duk da Tun Suna London Suna Gabda gamawa Zain yayi ma Haddir alkawarin Insha Allahu in suka koma Gida ya Daina Duka Abubuwan da yakeyi Shi kuma Haddir din yana Fatan Haka toh koda suka Dawo Kunsan Bambamcin Ra"ayi Da kuma Yadda Shi Haddir din ko Fita zain yayi sai ya Dora Zargin wajen Wata yaje sukayi Shashancinsu sai Suna yawan Fada da Samun Matsala Dalilin Dayaasa Haddir ya bar Zama Gidan Abba Usman kenan ya Koma Gidan Alhaji Tsoho da kwana Sai dai su Hadu da Zain a Asibiti kowa ya kalli Juna Su Dauke kai kamar ba Aminan Juna Ba Wadanda suka Tashi Tare Koda Abba Usman ya Farga da Barin Haddir Gidansa Har Gidan Alhaji Tsoho ya Bisa ga Shi ga Hajiya Mama ga Alhaji Tsohon Ga Haddir din ya Tambayeshi ko anyi mai Wani Abu ne..? Domin Tun yana Yaro Shi ya Rikesa har ya kawo Girmansa Bai Taba ganin Sun Raba Wajen kwana da Zain ba sai yanzu da Girma ya kamasu ko Sun samu matsala ne Tun da yasan Halin Zain din da saurin Fusata,Ammh sai Haddir din yaki yarda yace komai Ya nuna ma Iyayansa kawai yana Sha"awar zama agidan Alhaji Tsohon Tunda ko da Zain Da Zareena Tun Suna yara nan Gidan Alhaji Tsohon kamar gidansu ne sai Hajiya Mama Ta gaji da Kirniyansu ta Kadasu Gida da Haka ya Kashe bakin kowa ammh bawai Domin sun yarba ba Sai Domin Daga Zain din Har Haddir din sunki basu Damar Fahimtar wani yasa suka Fita Batunsu Suna Tunanin koma Miye Chan Tsakaninsu ne. Dan zaman da Zain Yayi agida kafin Tafiyarsa Mumbai ya Tada Tsiyan sai an Daura mai Aure da Zainarsa Domin alokacin Da Ita da Zafeera Suna Cikin Shekarunsu na Sha bakwai kenan a Duniya Har da Umar Faruq,Duk da Zafeera tafini Girman Jiki ni na Fita Tsawo Da kuma Cikar Hallitan Ya Mace,Kuguna da Kirjina Tun ban kai Haka ba Kuguna da Kirjina yake aciki in ka kalleni zaka Fahimci Allah yayi Mace anan Wajen Allah ya sani ni Ba Fara bace kuma ba wata Chan mai kyau ba ammh kuma in da Tsarina Fuskata Daidai Misali ,Zafeera ce Fara ni kuma Bakin Fatar Mahaifina na Dauko Inji Goggo Halima Wanda Bansansu ba sai dai a Hoto Tabbas dana Biyo Hasken Fatan Mahaifiyata ko Zafeera bazata Nuna min Haske ba. Ina da Sanyin Hali da kunya da kwaici Wanda Umman ke Fadamin Duka Hallayan Mahaifiya tace na Dauko,Zaman Zain agida yasa ganin yadda na koma sai ya Fara Kafa min Dokokin Rashin Fita Saka Hijabi da dai Sauransu Daga makarantar Boko sai Islamiya kadai yake yarda naje sai Kuwa Gidan Alhaji Tsoho,Da muka samu Hutun makaranta naje Abba Ya barni Tafiya Gaga Wajen Dangin iyayena Musamman ma Goggo Halima Wacce koda wani Lokaci Tana Zuwa Dubani ita nake gani kamar Uwa gareni Dakyar Zain ya yarda yabarni naje Da yace na Jira Weekend yakai ni ya Dawo Dani sai da Umma ta Hadashi da Abba yamai Fata Fata kana ya yarda ya barni na Tafi ammh Ko Sallama bai yarda Munyi dashi ba yana Fushi ya Fita Zuwa asibiti kuma nayi ta Kiransa awayar Nene Tunda ya Dauka Yaji muryata ya kashe Nayi ta Kira bai Daga ba Zafeera tace Zata Rakani Tare muka Tafi Da ita. Kwanamu Goma agarin gada a gidan Goggo Halima muna Shan na kauye,Mu zazzaga Gidajen yan"uwa da abokan arziki Sai mamakin Girmama Suke da yarda na Zama Cikin Hakane Wani Abokin Wasa na ya ganni yace yana Sona Hisham Wanda Yake karatu a Usman Dan Fodiyo University Sokoto yana Shekaran Karshe Lokacin Daya Tunkare ni da Mganar na Nuna mai Ni ina da Mijina yaki yarda Har

Chapter 7 of 32