Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
dasu yana gaya musu Gobe akwai Taron Family Duka iyayan nasu suna Tafe Inna Rukayyah ma Tana Tafe Daga kano Haka ma Baban kaduna da Mom Iklima Da Daddyn Abuja da Mama Safiya Da Hamdiya zasu zauna kan mganar Auran Hamdiyan daya Taso watan Gobe ne,Zain bai kara Jin Sagewar Gwiwa ba sai da yaga Sadiq babba ya shigo nan yake gaishesu tare da Shaida musu Dazu shima ya Shigo garin yazo gida yayi Hutun Sati Biyu ya koma Alhaji Tsoho nata Murna ganin Jikansa Haddir da zain sai dai suka kalli Juna kawai Kowa da Abunda yake sakawa Sai da Alhaji Tsoho ya gama Jawabinsa kana ya barsu suka Fita suna Fita basu koma ko"ina ba sai Cikin asibitin Office din Haddir din suka sake komawa Suna Kulla yadda zasu Bulloma wannan al"amarin Dake Tunkaransu Dirshan zain ya zauna yana kukan Haddir ya Taimakamai kada Asirinsa ya Tuni Ya bashi Tsausayi matuka kuma Har ga Allah baya Fatan wannan mganar ta fasu a kunnuwan iyayensu ko bakomai ya zama Silan Rufama Dan"uwansa asiri. **** Dina kuwa Da Fara Nadaman Biye ma Shawaran Zakiya Domin  Lokacin da Kwamishina ya Dawo Gida yaci karo da wannan Labarin sai da ya Kusa Fadi haka ya Zube gaban gadon Dina yana Jijjigata yana Fadin"Dina..?me kika nema kika Raasa..? Wani irin gata ne ban baki ba..? Wata irin Soyayya Uba ce ban baki ba..? Harda ta uwa na Baki Dina na Hana Dangin mahaifiyarki Daukanki Saboda ina sonki Ina son na baki Dukkan gatan Duniya..? Yanzu da Kanwar mahaifiyarki Maimunatu zata Zo sati mai zuwa Da wani baki zan mata wannan bayanin..? Na baki ilimi Na ingantan Rayuwarki saboda kada kice na zama mai Takura gareki ashe wannan sakewar har yakai ki kwasomin wannan Abun kunyar dina.? Nifa Dan Siyasa ne da wani ido kuke so na kalli mutane in wannan mganar ta Fita waje..? Ya karishe Fada Cikin zubar Hawaye Ita kanta Dinar kukan take Hajiya Batula ma sai da ta Share kwallah Zakiya ce kadai batayi kuka ba Cikin kuka Take Fadin"Kayi Hakuri Daddy..Plz Forgive me.Ba laifina bane Wlh Yaudarata yayi da Kalmar zai Aure ni ya lalatamin Rayuwa Shine kuma Daga baya yace sai dai azubar da Cikin bazai Aureni ba Shine na Gudo Gida.." Ta fada Cikin gunjin kuka Gefe Daya na Zuciyarta Tayi Rauni ganin Daddynta nakuka Hajiya Batula tace"Dama wani Namijin arziki ne zai yi Lalata da mace kuma ya aureta..? Ai Shima macen kwarai yake nema kinyi Kuskure Dina.."Kwamishina ya mike Tsaye yana Share Hawayensa ya kalli Zakiya yana Fadin"Wani asibiti kika kaita Kafin kuzo nan..? Cikin Ladabi Ta saka Hannu Cikin Jakarta Ta Dauko Farar Takarda Ta mikamai Tana Fadin"Asibitin Da take aiki ne Daddy....Gama sakamakon awajena.."Karba yayi ya Duba na wani Lokaci kafin ya Hada da wanda Dr.Bala ya Bada ya Tusa Cikin aljihunsa yana Fadin"Taga yamiki wanda yayi mata wannan Zaluncin..? Cikin Makirci Zakiya tace"Nayi nayi da ita Taki gayamin Daddy.."Tafada kanta na kasa Cikin Tsawa Kwamishina ya Kalli Dina ya Daka mata tsawa yana Fadin"Kimin Shuru anan wajen ki Fadamin wanda yayi miki wannan Abun kunyar..? Tsorata Tayi Tafara ja da baya zuwa Wajen zakiya Ita kuma Zakiya Fadi Take"Dina ki Fadama Daddy ko waye..Na Tabbata zai kwato miki yancinki na Zalunci da yaudaranki da yayi da kalmar zai Aureki yayi Miki Ciki kuma yake neman ya sake Jefaki ga Halaka.."Tafada Har tana matso kwallah Jin Haka yasa ta Fara Shesshekan kuka Tana Fadin"Likitan ne asibitin Dana ke aiki..! Kwamishina yace"Waye sunansa..? Waye kuma Ubansa a kasar nan..? Kan Dina na kasa tace"Sunansa DR ZAINULLAHI USMAN ABUBAKAR SAULAWA...! Tafada tana Rufe bakinta Waro Ido Zakiya tayi Tana Fadin"La Dr.Zain kike nufi..?Kai Dina ta Daga mata sai ta Fara Tafa Hannu Hajiya Batula tace"Kinsan shi ne..? Kodai wannan Saurayin da Dina take matukar so ne..? Da sauri Zakiya tace"Shine Wlh Anty...Tun suna London suke Soyayyah Tunda makaranta Daya Sukayi nasha cema Dina Ta Rabu Dashi ba Auranta zai yi ba sai tace Yace zai Aureta asibitin ma Datake aiki shi ya bata aikin fa asibitin mallakin Kakansa ne Dr Saulawa dake Garin Bauchi..' Hajiya Batula tace"Nifa banga laifinsa ba laifinta ne..Don Namiji yayi ma mace alkawarin Aure sai akace ta bashi Jikinta yayi yarda yaga Dama..?kwamishina ya Dago yana kallon Hajiya Batula kafin yace"Batula koma Miye Bai isa yaci Bulus ba...Na yarda Dina nada laifi Shima yana Dashi Saboda Haka Tunda ya Riga ya bari Haka Ta Faru..Wlh Tallahi ko Zan rasa Mikamina sai na kwatan mata yanci..Ke Zakiya kunsan gidan yaron..? Da Sauri Zakiya tace"Eh Daddy ai gidansu ba Boyayyen Gida bane agarin Bauchi kakansa Dr.Abubakar Saulawa yayi suna sosai.."Kai tsaye ya kada kai yana Fadin"Ku Shirya gobe daSafe zamu tafi Chan Bauchi zan je na gaya musu Abunda D'ansu yayi ma yata in ma basu sani ba gobe zasu sani..Batula kema ki Shirya dake zamu tafi sai Excort dina guda Biyu saboda Sirri yau ma Domin Anjima ina da ganawa da gwamma ne da a Daran nan zamu Tafi garin Bauchin..' Yana gama Fadar haka ya Fice Daga Dakin Kamar zai Tashi sama Hajiya Batula ta mara mai baya Suna Fita zakiya tatashi ta Rufe Kofar tazo ta Rumgume Dina Tana Fadin"Ina Tayaki Murna kin kusa samun Cikar Burunki..!. Wata Dariyan Farinciki Da Nishadi Dina tayi kafin tace"Da farko na Karaya..Ammh yanzu naji Kamshin na zami matar Zain..ammh kuma wani Fargaban Zakiya Shegiyar Firstlove din nan nashi zata yardada mganganunmu kuwa balle har ta Rabu Dashi..? Ta fada Tana kallon zakiya wacce ta Mike tana gyara zaman mayafin Kanta Lokaci Daya Tana Fadin"Karki damu da ita Tuni nagama da ita..Zatazama Comfuse mana Na wanda ka yarda dashi Fiye da kowa aduniya yaci Amanarka..Ammh Zan aika mata da Abunda Dole zata nemi karin bayani ni kuma zan gayyato inda zata ji gaskiyan komai kinga Daga Lokacin Zata ji Zain din yagama Fita Daga kanta Indai ita macece wacce ta amsa Sunanta..." Dina tace"Bangane Nufinki ba..? Zakiya ta Dauki Jakarta Tana Fadin"Ai Ba zasu zo Taji wannan mganar ba..Zasu yi Kokarin Rufa mganar kada Taji..Ammh ni zan gayyatota har zuwa Gidan kakan nasu da suke ji Dashi nayi Miki alkawarin aagaban Idonta zamu Fallasa Komai...Kin manta kin samo min Lambarta Awayar zain..?Hade kuma da aikin da na sakaki..? Kai Dina ta Daga mata Cike da mamaki Dariyan Mugunta Zakiya ta saki Tana Fadin"Ai Duka Shirin nata ne..Domin Ba lalle bane in wanchan Bomb din ya Fashe ba"a gabanta ba Mganar Daga bakin wasu Tayi mata Tasiri..Zata yi Tasiri ne Daga bakinki Da kuma Shaidunmu.."hannu kawai Dina ta Bata suka Tafa Tana Fadin"Aikin SS ya dace Dake Zakiya ba aikim kamfanin Sardawa ta Layi ba..". Dariya kawai Zakiya tayi mata kafin tace"Zan tafi Gida na kwana Dina..Saboda kinsan komai lalacewar gida gidanku ne kuma Tunda Tsoho nada Rai Bari na Leka Duk da wanchan Watan na Lekosu.."Dina ta kada kai Tana Fadin"Da safe kenan zaki Dawo..? Zakiya tace"Da yardan Allah.."Sallama sukayi Kana Zakiya ta Fice Koda ta sauka Kasa bata ga kowa kawai sai ta Fice Daga Gidan Security suna ganinta suka Bude mata get ta Fice Da Motarta Motar Dina kuma Tana kano Gidan Wata kawarta Teema suka kai Motar Dina Ajiya Tun Jiya Saboda kada Barinta ya bata musu plan dinsu. *Janafty...* *ZAINAZAIN..!* _(Is a love Story and Betrayal)_ *Wattpad:Jamilaumar351* *Mallakar:Janaftyshakira*❤️ *BOOK 1*             1️⃣6️⃣ "Zakiya iyayenta suna zaune a anguwar gadon kaya ne,Mahaifinta Mallam Nuhu Talaka ne mai Rufin asiri Tunda Sana"ar Dinkin Surfani na Hannu yake Da Saida Zaren Dinkin kala kala Tun yana da Samartkansa. Shago garesa a kofar gidansa Inda yake gudanar da Sana"arsa,Bayan Rasuwar Mahaifiyar Zakiya Adama Ya kara Auran Wata Samira yar garin Danbatta ne,Bayan ita ma ya kara Auran wata Lubabatu suna Kiranta Luba ita yar nan garin Kano ne, a kofar wambai. Mahaifiyar Zakiya yar asalin Kauyen Minjibir Dake kano ne,iyayenta ma ba masu Hali bane Kuma Dukkansu yan kauye ne Shiyasa bayan Rasuwarta da Mallam Nuhu ya hanasu Su Dauki Zakiya su maidata chan Minjibir din sai sukayi Fushi suka Fita Batun Zakiyar basu kara waiwayarta ba itama bata Damu ba Tunda ba wani Abun hannu garesu ba Uwa uba kuma Tana ganin ci baya ne ta koma Kauye da Zama. Sai ta tashi Hannun Kishiyar Uwa Samira irin mugayen Matanan nan ne da basu Dauki Ya"yan Kishiya ya"ya ba Dalilin ta shi yasa Zakiya ta Fara kangarewa,Da kuma Shigarta prine Collage da Haduwarta Da Dina lokacin Mallam Nuhu na Zamaninsa da Dinkin Surfani Shiyasa Zakiya tafi Sauran ya"yansa samun Ingancin Rayuwa mai kyau. Mtslanta Da Mahaifinta ya samo asali ne da Samarin da Zakiya ta Fara mu"amala dasu na Banza,Wannan Motan tazo ta Dauketa wannan ta Sauke sai manganganu suka Fara yawo kan Yana ganin Zakiya zata lalace bazai Dau mataki ba Da Zugan Samira yayi amfani yace In Zakiya ta gama Babban Sakandiri zai mata Aure ita kuma tace Bata so karatu zatayi,Rigima tayi Tsanani Har ya sako Dangin Mahaifiyarta Adama aciki Har zuwa sukayi suka samu Zakiyan suka mata Fada ammh Tace ita karatu zatayi ba Aure ba Ran Mallam Nuhu ya baci yace Taje duk inda zata ammh bada gwabonsa ba da wannan Dalilin Taje ta samu Dinar da kukanta itakuma ta Share mata Hawayenta ita ta Taimakamata ta Biya Jamb ta zana kuma taci Dayake duk Iskancinsu basu wasa da karatu Barin ma Zakiya Da take ganin Bayan karatu bata da komai Bariki bai sa ta sakar ma karatu ba Taana da Burin ta tsaya ga kafafunta wata Rana ABU zaria Tana daga Cikin Inda Ta nema kuma ssi gashi ta samu Bata Nemo kowa ba sai Dina Ita Tayi mata komai sai dai ita ta Rigata Tafiya Lagos inda ta Fara karatu kafin ta Wuce lagos,Ita kuma Zakiya sai Daga baya ta wuce Zaria Bayan ta gama Hada Abubuwan da zata Bukata wajen abokan Shashancinta Domin Zakiya Tun tana SS2 ta san Tabama Namiji Jikinta ya Biyata kaso mai Tsoka Gidan ma Datake Zaune azaria Cikin Samarinta wani ya kamata Zuwanta Zaria da Shigarta Jami"a Shiya Kara Sauya Zakiya Idanuwanta suka Bude tayi kawaye na Banza Dana arziki anan ne Takara sanin Rayuwa sanari kuwa ba adadi Tayi na Arxikin kuma Tayi na Banzan Kawayenta na nan Zaria suka Fara koya mata Harka da malamai kuma Tunda ta Fara take jin Dadin Haka zakiya ta kama kudi Sosai Wajen Abokan Shashancinta Shiyasa Har ta gama karatunta Sisin Mallam Nuhu bata Taba nema ba Shi kuma ya kawo ido ya saka mata. Zakiya Tana da kanne mata Sunfi Shida,kuma dukkansu sun yi Aure Tunda ba karatun suke ba,Bayan Tagama karatu ta Samu aiki a Bauchi Shima da Taimakon Mahaifin Dina kwamishina Gaddafi Sheerif,Ta tattara ta koma chan da zama bayan ta mallaki gidan zama da Motar Hawa In taje gidansu sai dai Tayi awa Daya zuwa Biyu,ta koma Bayan ta kawo musu kayan Abinci da kudi Mallam Nuhu baya karba sai ya kalleta yace"Zakiya ina Fatan wannan kudin bana Shanshancin kibane kika kawomin ba ko..? Yau ma Data iso Gidan Hakan ce ta Faru Tsskaninsu Bayan Ta Shiga Dakinsa sun gaisa Da zata Tashi Ta ijiye mai kudi a gabansa Tana fadin"Gashi Baba ku kara acefene..! Sai Tayi Dariya Tana Fadin"Ko Daya Baba..Daga cikin Albashina ne..."Sai kawai ya kada kai yana kallonta yana Fadin"Zakiya yanzu ina amfani ga wannan Rayuwar da kika Daukan ma kanki..? Kinga ma karatunki kin samu aiki me zai Hana ki nemi ko Cikin Abokan Shashancin naki ne kuyi Aure .? Mirmishi Tayi ta sadda kai Yana Fadin"Haba Baba meyasa kake Damuwa ne..?Aure fa wani Lokacin in baka yi sa"a ba Duk Wahala ce baga su Sahura ba Sunyi Auran ammh Suna Cikin Wahalan Rayuwa ba, yanzu da karatunsu sukayi irin nawa da Suna Tsaye ga kafafunsu Baba...! Carbinsa kadai ya Cigaba da ja yana Fadin"Ban taba la"antanki ba Zakiya kuma bazan Taba ba..Akullum Tsakanina Dake addu"an Shiriya ne Allah ya Shiryeki Zakiya.."Cikin Mirmishi Tace"Shiyasa nake sonka Babana..Ameen ya Allah..Bari na Koma ciki.."Dakai kawai ya yi mata mgana Har tatashi ta Fice ya bita da kallo yana mata Fatan Shiriya Tun zakiya na zuwa ana Gulmar ta zama karuwa Taje chan wani gari da Sunan aiki Tana iskanci tayi kudi ta sai Mota Har akazo aka Daina Domin Mallam Nuhu ya Toshe kunnansa ne Fatansa Allah ya Shiryeta yasa Ta gane Rayuwar da Takeyi ba Rayuwa bace. Tana komawa Cikin Gida Dakin Luba ta sauka Daman nan take Sauka Tunda ita take Rawan Jiki da ita Saboda Kwadayi ita kuma Samira Daman basa Shiri da Zakiya Tun baya ballatana yanzu da Girma ya kamata,Samiran ma ya"yanta Biyu an sakosu suna gabanta Zakiya bata Damu ba,Haka ta saki kudi Luba tayi lafiyayen Girki sukaci Ita dai Zakiya bata ci ba, tea ta Hada tasha ta kwanta kan Katifar da Luba ta mata Shinfida. ******* Haddir da Zain sun gama Tsaida mgana kan sai gobe da Safe zasu Tafi kano,Gidan Abba Suka koma Tunda Zafeera nata Kiran waya tana Korafin Bata gansu ba Duk wanda yaga Zain sai yasan wani Abu na Damunshi baya Cikin Natsuwarsa chan suka kara ganin Zaina dama Ta gayama Zain Zata wuce gidan Umma,Yace mata Toh. Ita kanta Zareena Ta Fahimci Wani Abu Haddir ta kalla Tana Fadin"Aboki Haddir meya ke Fauwa da Aboki Zain ne..? Naga ya Zama wani Shuru Shuru ne wani Abu ya Faru ne...?Haddir ya Juya yana kallon Zain wanda ya kura ma waje Daya ido kawai Daga ganinsa Baya Cikin Natsuwarsa. Yake yayi mata Lokaci Daya yana Dafa Zain din yana Fadin"Bakomai...Strees ne na asibiti.."Jin haka yaasa Zain ya Fahinci Abunda ke Faruwa Shima yake yayi wanda bai kai Zucci ba,Zareena dai bawai don ta yarda ba sai don Taga Basu san gayamata,Zain kuwa duk iya Kokarinsa na Kada agane yana Cikin Wani hali sai da aka gane Haka Nene ta Tusashi Cikin Daki Tana Tambayanshi meke Damunsa..! Ammh ya kasa Furta komai ba amsa Dayan ce Bakomai nan suka kai Dare Har Abba ya Dawo Daga Gidan Alhaji Tsoho Shida Baban kaduna Suka Shigo da Mom iklima Da Mama Safiya da suka Biyoshi zasu kwana gidan su Umma. Nan fa su Umma suka Fara maraba Da baki,Zain fa Hankalinsa ya Tashi Komai ma ya Riga ya kwacemai Haddir ne ke Zugurinsa in gaya yayi Tagumi ya Shiga Dogon Tunani,Sai wajen 10pm na Dare suka Rabu da Haddir Shi kuma Ya Dauki Zaina zuwa Gida,bayan sun yi Dinner agidan Umma wanda Zaina tana Lura da zain abinci ma Tsakura kawai yake yi batare ma Dayaci ba. Suna Cikin Tafiya Zaina sai kallonsa Take ganin sai Sakin Numfashi yake sama sama Tunda Suka Shiga Mota bai iya cemata komai ba Driving kadai Yake ammh Rabin Hankalinsa Baya Jikinsa Gefe Daya kuma yana ta gwada Kiran Layin Dina da Koda yaushe ake cewa akashe,Mamaki ya Cikata ganin kamar Baya cikin Natsuwarsa ne yasa  a sanyaye tace"Firstlove..! Waigowa yayi yana kallonta Batare da yayi mgana ba gyara zama Tayi Tana Fadin"Firstlove meke faruwa ne... ? U Look so silent.."Maida kansa yayi Ga Tukin Dayake yi kafin ya Sauke Numfashi kawai batare da yayi mata mgana ba Har ta Fidda rai Taga ya Riko Dayan Hannunta ya Damke Dayan kuma yana Tuki Dashi Cikin wata karyayiyar Murya ya Kira Sunanta..! "Halima..."Abunda ya bata mamaki Ita Tunda Take dashi Baza tace Tataba jin ya kira Sunanta na Gaskiya Halima ba Sai dai Firstlove ko Zaina,Ammh jin yau ya Kira sunanta da wannan Murya yasa Jikinta yayi Sanyi Cikin Damuwa da Faduwar Gaba tace"Na"am Firstlove mene..? Tafada Idanuwanta na Cikowa da kwallah Sai da ya juyo ya kalleta kana ya maida Hankalinsa kan Tukinsa ya Fara mgana Cikin Raunin murya"Halima wani Alfarma nake Roko awajanki Don Allah.! Cikin mamaki tace"Wata alfarma ne Firstlove..Na Dauka Tsakanina Dakai ba alfarma.."Cikin Dakiya yace mata"Akwai ta mana..Akwai Alfarma Zainata..! Yake Fada yana waniCije baki kamar ya Fashe da kuka yaje ji wata Zuciyar na ingizashi ya gayamata wata kuma na Hanashi kawai sai ya Bige da cemata"Don Allah kimin alfarman kowani Laifi zan aikata miki komai Muninsa kada Kice zaki barni...Wlh Tallah Na Rantse miki Da Allah ke kadai nake so kuma nake kauna..Kada ki barni Saboda wani kuskure nawa..In kika Barni Rayuwata zata Tagayyara kuma Bazan Taba Gafartama kaina ba.." Ya karishe Fada yana jin wani iri Rauni acikin Zuciyarsa Tun kafin yagama mganarsa ta Fashemai da kuka Cikin Rawan Jiki yake kallonta yana Fadin"Don Allah ki bar kukan nan Firstlove kukanki na sakani naji kamar zan Rasaki ne.." Dagowa Tayi Tana kallonsa Cikin Hawaye da kuka tace"Nima Haka nakeji..Zuciyata tana rawa Firstlove...Nakasa gane wani Hali nake ciki.."Take Fada Cikin kuka Daidai Lokacin da suka iso Gida Hon yayi Tanimu maigadi yazo ya Bude musu suka Sulala Ciki ya iso wajen Motan yana ta Barkwancinsa Daya saba sai dai wannan karon Ko ita Zainar bata kalleshi ba Tana Bude Mota ta Nufi Cikin Gida Tana hada Hanya,Shima Zain din ya Rufa mata Baya Abun sai ya Daure ma Tanimu maigadi mamaki ya Rike baki yana Fadin"Komai miye Allah ya Saukakashi..! Da gudu yabi bayanta Atare suka Shiga Falon suna Shiga ya Fizgota ta Fado Jikinsa Sai kawai ta kara sakarmai kuka ta kamkameshi tana Fadin"Nima bazan iya Juran rasaka ba Firstlove...Da kai kadai Zuciyata da gangan Jikina ta saba Rasaka Tamkar rasa wani Shashi na Jikina ne..Wanda kuma in bashi bazan iya Rayuwa ba.."Yana jinta in Tana mgana sai yaji kamar ya Duka gabanta ya gayamata komai ammh kuma sai yaji ya kasa Idanuwansa sun kala sunyi jajir yana Cikin Babban Tashin Hankalin da bai Taba Riskan kansa aciki ba. Ranar kwana sukayi suna gwadama Juna wata irin Soyayyah mai wuyar rubutawa,Ranar Zain bai ji ya gaji ba,ita kanta Salon da yake mata ya bata mamaki kamar irin wanda zai barta na wasu Shekaru,ga yagamata kalaman yana Sonta ba adadi ya kuma gayamata Duk duniya ita kadai ce yafi yarda da ita Fiye da kowa Daga karshe ma kuka ya saka mata yana Fadin bazai Taba iya cin Amanarta da gangan ba ta Tsorata Ta Fara Tunanin wani abu ya Faru ko kuma yana Shirin Faruwa,Sai Wajen 3 na Dare dukkansu suka samu Barci Sallar asuba ma agida yayi ta domin Haka kurun yau din ya Tashi yana jin kamar bashi ba Ita kanta Zainar Jikinta yana Sanyaye ne ga wani Faduwar gaba Dake damunta Tun kwana Biyu da suka Gabata. Karfe 7am na safe Zain ya samu Kiran Alhaji Tsoho inda yake gayamai ya Tabbatar da Shi da Halima sun zo Taron da zai Gudana agidanshi Cikin Hadiyan Miyau yace zasu zo ammh Zaina sai Ta Shiga makaranta zata kai Assigment ne kuma lacran yace Individual yake Bukata Shi kuma sai yayi mai karyar zai Shiga Cikin Asibiti Ya Duba patient ya gama Dasu zai zo Shidai Alhaji Jadaddamai yake ya gansu awajen kana suka yanke Kiran Tunda lokacin komai nashi yake Sukuku Zaina ta taimakamai yayi wanka ya Shirya itama ta Shirya Tunda Shi zata Bi Motarta ta lalace tana wajen gyara,Breakfast ma Dakyar ya yarda Ta Turamai Fadama yake bayajin Cin komai har ta Fara Tunanin ko Bashi da lafiya ne yace mata Kada ta Damu Lafiyansa kalau. Suna Mota zai kaita makaranta Kiran Haddir ya Shigo Wayarsa Dama ajiyan sun Rabu kan kada Zain ya Kirashi shi zai kirashi Da kanshi da Sauri ya Daga Kiran Shi kuma Haddir yace mai yana Cikin asibiti yazo ya Sameshi da Rawan Jiki ya amsa mai gudu gudu ya karisa da ita Cikin Makaranta ya ijiyeta Abunda ya bata mamaki ganinsa a gaggauce yau ko bakin Department dinsu bai kaita ba ya ijiyeta wai yana Sauri ne har ya bace ma ganinta Tana Binsa da kallo Haka kurun Take jin Tsinkewar Zuciya Jakarta ta saba ta Fara Takawa da Kafa Zuwa Department dinsu ammh Cikin Zuciyarta sam ba Natsuwa Tana Jinta kamar ba ita ba. Aguje ya Shiga Cikin asibitin yana Faka Motarsa sai ga Haddir ya Fito Daga Cikin Asibitin yana gyara zaman Suit din Dake Jikinsa Motarsa kawai ya Nufa yana Fadin"Shiga muje...Ya kamata muje mu dawo kan Lokaci Kafin Alhaji Tsoho ya Farga Damu.."Zain najin haka yaDauko wayarsa Ya zare key din Motarsa ya Rufeta kana ya Zagayo ya Shiga ta Haddir wanda yana Shiga ya Tasheta suka Bar Cikin asibitin Hanyar kano Suka Dauka Lokaci Daya Haddir na Fadin"Ka sameta..? Zain na Dafe kansa yace"Ban sameta ba..Tun da muka Rabu nake Kiran wayarta..Amsan Daya ne akashe take.."Haddir yayi karamin Tsaki yana Fadin"Kashe wayar ma wani Tsarinta ne..Nidai Fatana Allah yasa in mun isa kanon mu sameta agida Komai zai zo da Sauki In muka sameta.."Jin jina kai kawai Zain yake yama kasa Mgana Daka ganshi zaka Fahinci ya Riga yayi Laushi da Rauni. ****** Abunda su Zain basu sani ba Lokacin da suka Dauki Hanyar kano Lokacin Tuni Babban Jeep din Kwamishina Ta Tsufa kan Hanyar zuwa Bauchi Tun safe,Dagashi Sai Hajiya Batula sai Dina Su Waleed Da Waleeda agida aka barsu Tare da Zulai,Sai a Gaba Direbansa da Escort dinsa Guda Daya Sai Zakiya Dake Motarta ita ke gaban Bisa Tsarin ita zata musu Jagora zuwa Gidansu Zain din *10:00am...* *Falom Alhaji Tsoho..* Falon Alhaji Tsoho cike yake da ya"yansa da Matansu da Kuma Wasu Daga Cikin Jikokinsu irin su Hamdiya da kuma Sadiq babba,Baban Kaduna,Dadyn Abuja,Abba suna zaune waje Daya asaman Cafet din Daya mamaye Falon na Alhaji Tsoho Gefe kuma chan Umma ce da Mama Safiya sai Mom Iklima da Nene Daga yammah kuma Inna Rukayya ce da Inna Hannatu Chan kuma Daga Farko Sadiq ne Zaune Sai Zareena Dake gefensa Ita Da Jaririyarta Jalal yana gida Wajen Zainab suna ta wasa dasu Junior,Daga gefen Alhaji Tsoho kuwa Hajiya Mama ce da Hamdiya Dukkansu suma zaune saman Cafet din Sai Alhaji Tsoho kadai Dake saman kujeransa yadan Mike kafa saboda Ciwo Sandar sa na Gefensa yana Bin kowa da Kallo. Kafin afara Taron sai da yace a Kiramai Zain da Haddir sai dai kuma anyi Rashin Sa"a Suna Daji Lokacin Motarsu ta lalace musu Shiyasa akayi ta Kiransu ba"a samu ba,Ran Alhaji Tsoho ya baci Domin Dukkansu sai da ya Sheda musu Duk Taron da suke Gudanawa basa samun Hallata wannan kuma yana Sha"awarsu a wajen ko bakomai Su din Ababen alfaharinsu ne. Ganin yadda ya Damu ne Baban Kaduna yace"Alhaji Tsoho kayi Hakuri...Kila suna Cikin asibiti ne Wani Uzuri ya Rikesa ammh ka kwantar da Hankalinka kafin mu Tashi zaka gansu.."Da wannan kalaman Zuciyar Alhaji Tsoho Tayi sanyi ya Umarci Dadyn Abuja ya Bude Taro da Addu"a Haka kuwa akayi bayan ya Bude Taro da addu"an Alhaji Tsoho ya Fara Jawabinsa kamar ko yaushe Nasiha ne da kuma Tunatarwa kan su Hada kansu kana ya gangaro kan su Rike aman junansu dana Matansu su kuma yi Adalci A tsakaninsu Ya"yansu kana ya Gangaro Riko Da Zumuncin Dake tsakaninsu su zama Tsintsiya Daya madaurinsu Daya ko Da watarana Baya Raye Wata Baraka bazata Bullo a tsakaninsu ba,sai ya gangaro kan mganar Auran Hamdiya ya kuma Yi mgana da Kakkausan Murya kan Zafeera game da Mai sonta Barrister Ahmed yace tunda asan Nagartan yaro bai kamata azauna ana Biye mata Kamata yayi iyayenta Maza Baban Kaduna da Daddyn Abuja suyi wani Abu akai shi in yayi wata mgana ya"yansu zasu ga kamar yana matsa musu ne,Sai kuma yayi mgana kan Haddir da zamansa Har yanzu bai yi Aure ba kuma sun saka Ido Sunki cewa komai. Baban Kaduna ne ya Fara mgana Bayan Alhaji Tsoho ya gama Jawabinsa ya Dora da mai Alkawarin zasu kiyaye wannan zumunci kana Daga karshe yace"Game da mganar Zafeera Da Haddir...Ka bamu Lokaci Alhaji Tsoho kafin Taro nagama zakaci Labari mai Dadi.."Daddyn Abuja yace"Insha Allahu.."Shima Abba ya Tofa albarkacin Bakinsa haka ma su Inna Hannatu Daganan kuma sai suka karkata kan Bikin Hamdiya Dake gabansu sun yanke Shawaran anan Bauchi Za"a Daura Dauran da Bikin Gabadaya Tunda Kaduna Hamdiya zata zauna wani Navy zata Aura,Inna Hannatu ce ta Fara kawo mganar azo nan ayi Bikin Sai Baban Kaduna yace Shu bai ga Fa"idar haka ba gwara atsaya chan ayi wannan mganar tajawo cuceku cikin Falon Matansu dai sunyi Shuru Tunda wannan ba Fagensu bane,Alhaji Tsoho na zaune yana kallonsu bai kuma katsesu ba. Ana Cikin Haka ne sai ga Sallamar Megadi Daga bakin Falon Sadiq ne ma yaji Sallaman ya amsa ya tashi ya Leka nan Megadin ke Shaidamai agayama Alhaji Tsoho Yana da Bako yace ace mai kwamishinan Ilimi ne Alhaji Gaddafi Sheerif. Mamaki ya kama Sadiq sai dai kuma Bai yi mamaki ba sanin Kakansa ai ba Boyayyan Mutum bane,Komawa

Chapter 17 of 32