Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
bamu alheri su Nene kuwa ko kallo Kowacce da Abunda Take Sakawa. Dina kuwa Zuciyarta Kamar Farar Takarda Saboda Haske Ta gaban Zain tazo ta wuce Tana Fadin.."Ka bar kuka..In ka Rasa Wata matarka..Ga wata nan kuma Uwar ya"yanka ce Insha Allahu.."Tafada a Hankali kasa kasa ba wanda zai jita sai Zain din Wanda ya Dago yana kallonta Cikin Wani irin Tsana da Bakinciki yake Jifanta da wani matsiyancin kallo Mirmishi ta sakamar Lokaci Daya Da gamai Gira kafin ta wuce Zakiya ta mara mai Baya Tana mai kallon Sorry For u Self Dr Zain. Sai da suka gama Fita kafin Alhaji Tsoho ya yunkura ya mike yana Dogara sandanshi yace"Sallar azahar ta Kubucemana Kowa yaje ya gabatar..Mu Dawo aci Abinci Ayi addu"a kowa yaje ya Huta.."Daga haka ya Fara Dingisawa zuwa Dakinsa Su Baban Kaduna suka Bishi da kallo Har ya Shige,Baban kaduna ne ya Mike Tsaye sai Daddyn Abuja wanda ya saka Hannu ya Mikar da Abba suka fice Batare da sun ma kowa mgana ba Suna Fita Haddir ya mike yabi Bayansu Sai Hajiya mama Tabi bayan Mijinta,Sai Zaneera da Hamdiya suka Shige Dakin Hajiya Mama Daganan sai Inna Rukayyah da Inna Hamnatu da su Mama safiya suka Mike suka Nufi ciki Ko kallon Zain dake zaune Dirshan ba wacce Tayi Laila kuwa kawar Zaina Tun Saddan Zaina ta Shiga ciki Tana kuka ta mike ta Fice Daga Gidan Ta Nufi Gida Tana kuka da mamakin Halin Namiji Damam Abunda Take jiyema zaina kenan Tuni. Nene ce kadai Ta Rage afalon sai Share kwallah Take ganin haka yasa zain ya Rarrafa gareta Zai Tabata Tayi Saurin Janye kafarta ta mike Tana Juyamai Baya cikin Fitan Hayyaci Da Muryan kuka Yace"Nenee...! Bata ma Jira cewarsa ba ta wuce Ciki Itama Tana Sharan kwallah Da kallo ya Bita Yana Jin Tsiyayan Hawaye lalle kuwa yau yayi Nadamar aikata Zina gashi Dalilinta Mutane Biyun da basu Taba gujemai ba Sun gujeshi yau wato Fitstlove da Nenensa Duniya Abun Tsoro ne. Nan ya Durkushe yana kuka Shikadai kamar zai Shide Yana cikin kukan yaji an Dafa kafadansa yana waigowa zatonsa Nene sai gaya Tabawa ce bai san sadda ya Rike hannunta ba ya kara saka kuka yana Fadin"Tabawa na Cucu kaina...Dalilin Biyema zuciya da Shedan yau Firstlove taki Dubana Nene ma haka Umma kuma Ta Daga Hannu ta mareni Wanda Tunda ta Haifeni bata Taba Koda Dungurina ba sai yau.."... Yafada yana kuka Kansa Take Shafawa Tana kuka Lokaci Daya Tana Fadin"Kayi Hakuri...Jarabawa ce..Allah ya baka Ikon Binta..Zasu sauko Dukkansu kuma zasu yafe maka Bacin Rai ne yanzu.."Kuka kawai yake Kamar karamin Yaro kafin ya mike Zumbur yana Fadin"Ina jin kunya..Ina Jin kunyar kara Haduwa da wani Ahalina ayanzu Tabawa..". Daga haka kawai ya saki Hannunta ya Fice kamar walkiya yana zuwa Haraban Gidan yaga su Abba na Sallah sunyi Jami"i ne Dadyn Abuja ke Bada Sallar Haddir ma na Cikin Sahu Hango Key din Motar Haddir yayi agabansa yasa ya karisa da Sauri ya Dauka Duka suna kallonsa ba Halin mgana Tunda suna sallah suna Ji ya shiga Motar Haddir ya Fice Daga Gidan da Gudun Kamar zai Tashi sama. *Shakira...* *ZAINAZAIN..!* _(Is a love Story and Betrayal)_ *Wattpad:Jamilaumar351* *Mallakar:Janaftyshakira*❤️ *BOOK 1*            1️⃣9️⃣ "Zain na Fita Daga Gidan Alhaji Tsoho Sai ya rasa Duka Natsuwarsa Tuki yake ammh ba  Cikin Hayyacinsa ba Kuka yake kukan Nadama da Danasanin Abunda ya aikata yau gashi ya Girbi Abunda ya Shuka. Iyayensa Da Duka Danginsa yau ba wanda ya kalleshi Matarsa yau Ta shiga wani Hali Saboda Shi Daman irin wannan Ranar yake ta Tsoron gashi yau tazo mai acikin yanayin da bai kamata ba, Tafe yake yama Rasa ina Zashi ayau ya Tabbatar da kansa Duk Abunda zaka aikata kada ka kaucema Umranin Allah In baka Kauce ba kowani Hali zaka Shiga zakaga Allah ya baka Mafita in kuma ka Kauce ma Umarnin Allah Zaka Dade kana Yadda kaga Dama Ranar da Allah yayi Niyar kamaka bazakaji Da Dadi ba Kashima sai yafika Daraja kuma Haka Rayuwarka zata Shiga kilaWakalan Bakinciki Da Damuwa na Har Abada. Yana Tafe yana kuka Lokaci Daya kuma yana Tuki Haka ya Dinga Zagaye Titunan garin Bauchi Yarasa Ina zashi..? Wajen wa zai Nufa.? Allah kawai ke Tsarewa ammh Wajen Sau Biyu yana Buga ma Mutane Mota Saboda baya Cikin Natsuwarsa,Daya gaji ne yasa ya samu Wani masallaci ya shiga yayi sallar Azahar da La"asar nam ya zauna Cikin Masallacin yana ta Rokon Allah Gafara ga Cikinsa na Jin yunwa ammh kwata kwata Bakinsa bayajin Zai iya saka wani Abu. Ya Dau Tsawon Lokaci Cikin Masallacin kafin ya Mike ya Fita Mota ya Shiga ya Tadata Rasa Wajen zuwa yasa yayi Tunanin zuwa Cikin asibiti Sai kuma yayi Tunanin Kila suma Labari yaje musu yanzu baida wata Sauran Kima Dole yasa ya Maida akalan Motan nashi Zuwa Gidansu dake Lowcost. ***** Bangaran su Kwamishina kuwa Suna Fita Zakiya Daman bata koma Kano ba Gidanta ta wuce saboda Zata koma bakin aiki Daganan Tayi musu sallama ta Hau Motarta ta Nufi Cikin Gari Su kuma suka Hau Hanyar Komawa kano Cike da Damuwa Wanda kaso Kadan Daga Cikin Damuwan Ta Ragu Tunda komai yazo da Sauki. Suna Tafe Ahanya Hajiya Batula na yabon Ahalin Dr.Saulawa Musamman ma Shi kanshi Cikin Mganarta Take Fadin"Gaskiya Dattijon arziki ne...Naji ba Dadi Danaga Daya Daga cikin Ahalinsa ne ya aikata Haka...Daga gani Suna da kyakyawan Hadin kai...Yayi Adalci Sosai Domin in har yaronsu nada laifi kaso mai yawa Daga ciki laifin Dina ne.."Tafada kai Tsaye Tana kallon Dina wacce ke Tura baki Tana Hararan Hajiya Batula kasa kasa Cikin Takaichi Ta kalli Dina Tana Fadin"Eh na Fada laifinki yafi yawa..Domin ai ba"a Shege sai da aka Farayin Shegiya..Babu mutumci Ba kuma So bane mace ta watsar da kimarta yanzu wa gari ya waya..? Ko banza zaki Haifi Abunda ke Cikinki bata Hanyar Aure ba..Don Allah ya Tarfama Garinki Nono Wlh Haka Zaki Haifi Cikin arasa Ubanshi..' Kwamishina ne ya katse Hajiya Batula ganin Dinar Ta Dago Tana kallonta kamar zata yi mgana Cikin Damuwa yace"Ya isa Haka Batula..Don Allah ki bar wannan mganar...Naji da laifin Dina nima da laifina kuma kema da naki..Tunda matsayin Uwa kike gareta in kin sakama Tarbiyanta ido baki laifi ba.."Kai Tsaye ta bashi Amsa da Fadin"Baka bani wannan Damar haka ba..Kaida kake mahaifinta ka bata damar Rayuwar sakewa waye ni da zan Hanata..? Kuma kai yafi Chanchanta ka fara Bincikan Halin Da yarka ke ciki ammh kayi wannan..? Baka yi ba sai Siyasa sar ka kawai ka saka agaba Ta wannan Gabar Kada ma ka Doramin wani Laifi..! Daga Dina har kwamishina Sun San Gaskiya Hajiya Batula Ta Fada Shiyasa ba wanda ya kara mgana Daga Cikinsu Ita Dina Bata Damu ba Lumshe ido Tayi Tana Mafarkin gatachan Ta Ganta agidan Zain a matsayin Matarsa Farinciki ya cikata Shi kuma kwamishina Nadama da kunyar in yau ya Mutu me zai Fadama Allah..? Hakika Barewa bazai Gudu Danta ya Rarrafa ba wannan Abunda ya Faru Da Dina kamar Dawowamai Yayi Domin bayan Rasuwar Sarah mahaifiyar Dina ya Fada Harkan Neman mata sosai Sai Daga baya ya Rage bayan ya Auri Batula,Ya bar Harkan ne Tun Watarana da wani Abokinsa Shima Dan Siyasan ne,yanzu ma Haka sanata ne aawani yankin Yake bashi labarin Wata yarinya mai zafi Daya samu,Tun yana Bashi Labari Har watarana Da sukaje Abuja wani Taro Sai Sanatan ya gayyaceta Tazo mai Sai ya nemi ya Hadasu da kwamishina yaji Matukar kunya Lokacin da yaga Zakiya kawar Dina amatsayin Karuwan Sanata Abun yayi matukar Bashi kunya yaji ya Tsani Harkan Bariki Yaji Neman mata ya fita kansa,Abun da yafi bashi kunya shine Zakiyan tasan komai Domin har Sanatan na Fadi zai bashi Fagen shima ya Dana Ammh Dayake yar Duniya ce sai bata nuna komai ba ta Basar kawai,Yaji kunya Sosai ace yau Kawar yarka ta kamaka Da Dabi"ar kwartanci Abun ba Riba Tundaga Ranar ya daina Harkan Banza da Biyema Shawaran abokai yan Siyasa,Da kuma wannan Dalilin ya Fara Fargaban Kar yazo Itama Dina Halin Datake ciki kenan yaso ya Fara saka ido da Bincike kan Dinar sai kuma wani abu ya Daukemai Hankali ya watsar da Komai,Ammh Yayi Tuban Gaskiya Domin Tundaga Lokacin bai kara Bin yar wani Ba Tsoron Allah ya Shigesa ashe an Gudu ne ba"a tsira ba Shi yana chan yana Bin Diyan wasu Shima wani na bin bashi yar,Nadama ta kara Shiganshi Yaji Komai ya Fita kansa yana jin Da zai iya Daga murya Daya Daga ya gayama Maza masu Bin Ya"yan wasu da su Daina In ba Haka ba zasu gani Domin Sharri kamar Dan Sako ne zaka aikashi kuma zai Dawo maka. Wannan Dalilin yasa Zakiya Take Sakama Dina mgana in ta ambaci Wasu Daga cikin yan Siyansa sai a hankali,Sai ta nemi kare Mahaifinta ita kuma Zakiya Sai ta gayamata Barewa bazai Tayi Gudu Danta yayi Rarrafe ba ammh ita kam ta sani Allah ya Fitar da ita cikin Ya'yan Babanta Domin Tana da Tabbacin bai aikata makamcin Abunda take aikatawa ba yanxu..Ammh Tabbas Abunda Uban Dina yake aikatawa ne yarsa ke aikatawa Shiyasa bata ganin Laifin Dinar,Bata Taba gayama Dina Wani labarin daya Danganci Dadynta Domin Tsakani Ga Allah take zaune da ita Kawa ta Dauke sosai Abokiyar Sirrinta alokacin ma koda Ita da Daddy suka Hada Farka Cikin Rashin Sani bazata Taba Yarda Tayi wani Mu"amala Dashi ba Inda Amana Ruwa bazai Dafa Kifi Ta sani Batajin mgana kuma Tana Bariki ammh Barikin ta bai kai Tayi Harka da Uban kawarta ba Balle kawa ma irin Dina ta wace komai awajenta. Da wanman Tunanen Suka Isa Gida Kwamishina da Hajiya Batula suka Nufi Barayinsu Dina kuma ta Haura Sama Ta Shiga Wanka saboda Gajiya Bayan ta Fito ne ta Hada Salollolin Da suka Kubcemata, Ta koma Tabi lafiyan gado Ranta Fes Wayarta Ta jawo Tana Laluban Zakiya Tana jin Hayaniyar su Waleed a Falo da Tashin Mganar Daddy da Hajiya Batula..! ***** Salolli suka Gabatar kamar yadda Alhaji Tsoho ya Umarcesu,Ita kam Sallah ya zama Dole ammh mganar Abinci Ba kowa ya iya ci ba...Mom Iklima ce Da Mama Safiya suka Tsakura abincin sai Inna Rukayyah Inna Hannatu dai Bata ci ba Tagama sallah Tan kan Sallaya Tana Jan Carbi Ta Zab Tagumi Umma kuwa da Nene Suna zaune waje Daya Umma ce Tayi Sallah Nene na hutu Sai Zaneera Dake Gefe Zaune Tana Shayar da yarta Itama Bayan ta Idar da Sallar Idanuwanta sun kala sun ji Jajir Saboda kuma Sai Hamdiya Dake kan Sallayan Tana Sallah Dukkansu Suna Daki Daya ne Dakin Hajiya Mama Sai Zaina Dake Kwance kan gado Wacce Kuka da Damuwa ya sakarmata Zazzabi,Umma ce ta karbo panadol Wajen Tabawa ta bata Tasha Shine Allah ya Taimaka Ta samu Barci Sai Dai Daga ganin yadda Take Sakin Numfashi zaka Fahimci a Wahale take. Duk yawansu acikin Dakin Babu Wanda ke mgana da Dan"uwansa kowa da Abunda yake sakawa acikin Ransa,Shi kanshi Alhaji Tsoho Tunda ya Shiga Ciki bai iya Fitowa ba Tunda ya Idar da sallah yake zaune kan kujeran yana Ta Can Casbaha yana istigifari,Domin Hakikanin Gaskiya Abun ya Tabashi Yanzu ace acikin Zuru"ansa asamu wanda zai kawo Irin wannan Tunaninsa ya Tsaya ne ta gano Inda suka Kuskure. Yana nan zaune har akayi La"asar ya tashi ya koma kan Sallayansa ya zauna Yayi Sallar La"asar ya idar kenan sai ga Hajiya Mama ta Shigomai da Abinci ta Iskeshi ya kurama Waje Daya ido yana kallon Hotonsa Lokacin Dayake Matashinsa,Har Hajiya Mama Tayi mai mgana ga Abinci bai Jita ba sai da Ta zauna kusa Dashi Ta Dafa kafadansa kana ya Dago yana kallonta Cikin Damuwa tace"Ka daina Saka kanka Cikin wannan Dogon Tunanin ba Ishashiyar lafiya Gareka ba..! Gyada kai kawai yayi yana Fadin"Damuwa ta zama Dole Amina..Sai dai Zamuyi Kokarin Mu ki bata Muhallin Zama acikin Zuciyoyimmu.."Jinjina kai Kawai Tayi kafin tace'Ga abincin ka..! Kallonta yayi kafin yace"Anya zan iya cin Abincin nan Amina..? Barshi Dai zuwa anjuma..' Batayi Musu ba Sanin Halinsa Tunda yace haka Tasan bazai ci ba,Sai ta kauda Farantin Abincin Gefe Ta Daawo Ta zauna Tana Fadin"Anya Alhaji Hukuncin Daka yanke Kan Wannan al"amarin nan Daidai ne..? Nifa Wlh gani nake Yarinyar nan Tana Sane bafa Dole Zainullahi yayi mata ba Da Amincewarta Suka Fara wannan Shanshancin.."Alhaji Tsoho na Jinta bai mata mgana ba Shuru kawai yayi mata yana Cigaba da Jan Carbinsa. Sallamansu Baban Kaduna da Daddyn Abuja sai Abba ne ya Dago da Alhaji Tsoho yana amsawa Cikin son kare musu kallo Dukkansu Waje suka samu suka zauna Dukkansu Sannu Da Gida sukayi musu Hajiya Mama kadai ta amsa Shi kuwa Alhaji Tsoho Abba yake ta kallo ganin Irin yadda Lokaci Daya ya zama Wani Iri Cikin Muryan Sanyi da Salama Alhaji Tsoho ya Kira Sunan Abba.. "Usmanu Bin Fodiyo.."Dagowa Abba yayi Araunane yana kallon Alhaji Tsoho Cikin Rauni Da Hannu ya yafitoshi alamun yazo ba Musu ya Tashi ya isa Kusa Dashi,Ya zauna Kansa na Kasa Hannu Daya Alhaji Tsoho ya saka ya Dafa kanshi yana Fadin"kayi Hakuri Usmana...Nasani Abun akwai zafi da Ciwo samun Wannan Abun kunyar Daga Abunda ka Haifa kuma kake alfahari Dashi..Sai dai ina so ka sani Fushi ba namu bane..Mai Faruwa ta Faru sai dai Kuma Mu nemi Hanyar da zamu gyara kar hakan ta kara Faruwa.."Kansa na kasa yana jin Shigar wata natsuwa da kalaman Alhaji Tsoho Cikin Girmamawa ya Dago kansa yana Fadin"Insha Allahu Alhaji...Da farko ina cikin Bakinciki da wannan Abun da zain ya aikata ammh kuma zuciyata tayi Fari da kalaman Uba nagari..Hakuri ya zama Dole ammh kuma Don Allah  Karka Hanani nuna mai Fushina Domin ya Ruguje yardan Dake tsakanina Dashi.." Alhaji Tsoho yace"Bazan Hanaka ba Usmana..Domin kai Uba ne Nuna Fushin kuma Tamkar Hore ne...Ammh kada yayi yawa kaji ko..? Dakai ya amsa yana Fadin"Insha Allahu.."Mirmishi Alhaji Tsoho yayi kafin ya Dago yana Yafito Su Baban Kaduna da Hannu suma suka Taso zuwa gareshi Dukkansu suka zauna agabansa Kallonsu yayi yana Fadin"Ina Shi Zainullahin da Hadiru..? Baban Kaduna yace"Muna sallah Zain ya Fita da Mota...Haddir kuma yana Haraban Gida Shi da Sadiq.."Jinjina kai Alhaji Tsoho yayi kafin ya kalli Hajiya Mama yana Fadin"Aminatu Kiramin su Rukayyah da Hannatu.."ba musu Hajiya Mama ta Mike zuwa Dakinta nan ta iskesu Jugum Jugum Gaisheta suka Farayi Ta amsa Tana kallon Zaina Dake kwance Tana Sauke Numfashi Ahankali Cikin Tsausayawa Ta kalli Umma Tana Fadin"Fatima ya Jikin Haliman..? Tana ta barcin ne Har yanzu..? Umma Ta Dago Kanta Idanuwanta Har sun kumbura Tace"Eh Hajiya Mama bata Tashi ba Har yanzu..Saukin mata na Taba Jikinta zazzabin ya Sauka.."Kada kai Hajiya Mama Tayi Tana Fadin"uhmm..Allah kara afuwa..Rukayyah da Hannatu ku Taho Alhaji na Kira..Ku kuma ku saki Ranku kuci Abinci Haka Allah ya Tsara..Bamu isa mu Gujema Kaddaranmu ba..! Mama Safiya tace"Hakane kam Hajiya Mama..Bawa bai isa yaGujema Kaddaran Allah ba,..Allah ya kara Shiryamana Zuru"a Nima yanzu Da kika Shigo Su Nene nake ta ba Baki kan suyi Hakuri kada Fushinsu yayi yawa in yayi yawa Zasu saka Zain din ya kara Shiga Wani Hali Uwa uba ga Yarinyar nan Abun Tsausayi Wlh.." Hajiya Mama Ta jinjina kai Tana Fadin"Allah Miki albarka Safiya...Naji Dadin mganarki Fatima da Aisha Don Allah ku bar wannan kukan..Ke kuma Zareena Ji da yarinyar nan Sai kukanta nake ji Tun dazu ku kuma kuzo mu tafi yana Jiranku.."Daga haka ta Fice Daga Dakin Inna Rukayyah da Inna Hannatu suka Rufa mata Bayan Sun iske Alhaji Tsoho nata Lallashin Ya"yansa da Nasihu Sai gashi Lokaci Daya Sun Warware sun kuma ji Damuwarsu ta Ragu Suma Su Inna Rukayyah suka nemi Waje suka zauna suna Sauraransu Cikin Mganar Alhaji Tsoho ya kallesu Yana Fadin"Kun gano Inda muka Kuskure kan wannan Al"amarin..? Gabadayansu kai suka Girgizamai alaman A'a Cikin Hikima Yacigaba da Fadin"Kuskuran mu kadan ne .Bazan ce Saboda mun kai ya"yanmu kasashen Ketare karatu ne ya Jawo mana wannan Abun ba A"a Abun ba Haka yake ba Duk da wasu Dalilin Haka Suna Lalacewar ammh Hakan ba zai zama Hujja ba Tunda Nima nayi wayon Kashashen Ketaren kuma Wlh Allah ban yi wannan Lalacewar ba Kuma gaku kunyi kuma har yau wani Abu mai kama Da haka bai Faru ba..Nayi Tunanin Sakacinmu da kuma Rashin Bibiyar ya"yanmu akan lokaci Ko kuma nace Rashin Saka Ido Inda ace muna Kokarin Saka ido Sosai koda basa gabanmu Achan Kasar da suke mu Samu wani mai amana wanda zai Dinga Kula da Shige da Ficen ya"yanmu na Tabbata in da Muna Haka zamu samu labarin wani Abun kafin ya Girmama kun gane Abunda nake nufi..? Gabadayansu suka ce'Hakane Tabbas..Alhaji Tsoho.."Mirmishi yayi Cikin Jin Dadi yana Fadin"Yauwa..Tunda mun gano haka Sai muyi Kokarin Kiyayewa Yanzu akwai Ragowan Yaranmu da Basa gabanmu Bana jin Ta zafeera Tana Gaban Rukayyah ne kuma nasan ita da Shitu bazasuyi Sakaci Da Tarbiyansu ba.." Da Sauri Inna Rukayyah Tace"Insha Allahu Alhaji Tsoho muna iya bakin Kokarinmu.."Alhaji Tsoho yace"Yauwa sai Abubakar karami ko..? Yana ma wata kasa ce .?Da Sauri Daddyn Abuja yace"Shi yana Cyprus ne Alhaji ammh ya kusa kamallawa.."Alhaji Tsoho ya gyada kai yana Fadin"Masha Allah...Sai mai sunan Manya Umaru Faruq shima yana Chicago ko..? Baban Kaduna ya gyada kai yana Fadin"Hakane..! Alhaji Tsoho yace"Allah ya tsare su..Dukkansu zamu saka musu ido.."Baban kaduna ya Jinjina kai yana Fadin"Insha Allahu Alhaji Tsoho.."Kallonsu yayi Dukkansu yana Fadin'"Mganar Hamdiya kuma inda yafi Sauki za"a Daura auran.." Daddyn Abuja ya Kada baki yace"Nan za"a Daura Alhaji Tsoho.."Jin haka yasa Kowa yayi Na"ama Da mganar,Alhaji Tsoho yace"Sai Mganar Zafeera Zan bata Lokaci Zuwa bayan Bikin Hamdiya in bata kawo wani ba zan bama yaro nan Ahmed Dama.."Kowa yayi Na"am Da mganar nan sukaci ba Da Tattaunawa,Kafin Alhaji Tsoho ya Hada kan ya"yansa sukaci Abinci Suka koshi suka Sha Ruwa Su Inna Rukayyah kuma suka koma Dakin Hajiya Mama Kowacce Tana hada Kayanta Gobe zasu wuce. Sai Gabda Mangariba Zaina ta Farka Daga Barci Tana kuma Tashi Da kuka ta tashi kamar yadda Ta kwanta Dashi,Mganar Duniyan bata Tanka kowa ssi Umma da ita kadai Take mgana Dakyar ta Lallasheta Ta Rakata Tiolet tayi alwala tazo Tayi Sallolin Dake kanta azaune Tana Sallah Tana kuka Domin kamar Magiji Haka Abun ke Dawo mata. Abunci kuma Umma Tayi Tayi ammh Taki ci Zareena Ta kalli Zaina Tana Fadin"Kici Abinci Zaina..Don Allah.."Tana kallon Cikin Idanuwan Zareena Sai Hawaye ta kasa Mgana ganin Haka yasa Handiya Taje ta Kira Hajiya Mama tazo Tana ta Fada kan Zaina Taci Abinci ammh Sai Taki ci sai da Tayi mata jan Ido kana Ta yarda Ta karbi Abincin Daga Hannun Umma ta Tusa Ko Loma Goms Batayi ba Zuciyarta Ta Fara Tashi sai Amai Tun Tanayi da karfinta Har ta kasa Umma da Mama safiya suka Riketa ganin Bata da karfin Jiki yadda Take kuka ne Tana Hawaye yasa Tsausayinta ya kara Shiga Ransu Ruwa aka kawo Umma ta wanke mata baki Hamdiya kuma ta Tsaftace Wajen kafin kace me Jikinta ya Sake Daukan zafi Ta kwanta Jikin Umma Tana Rawan Sanyi. Abba ne ya aiko kan su Umma su Fito su Tafi Gida,Dole Nene da Umma suka Mike Kowacce Fuska akode,Hajiya Mama Tace Umma ta Kwantar da Zaina kan Gadonta su Tafi sai dai me Tana Mikar da ita ta makalkaleta Cikin kuka da Rauni Karo na Farko Datayi mgana.. "Umma...Zan...Zan biki..! Tafada Cikin Fitar kwallah gabadayansu da kallo suka Bita Lokaci Daya Ta maida kanta Jikin Umma Tana Sauke Numfashi Ganin haka yasa Hajiya Mama taje ta gayama Alhaji Tsoho Halin Da Ake ciki Cikin Nazari yace"Barta su Tafi da ita..Taje gidan ta Huta na wani Lokaci Shima ai zainullahin baya cikin Natsuwarsa yanzu haka zuwa gaba in komai ya Daidaita za"a samu Masahala.."Da haka Taje tace Umma su Tafi da Zainar gida Inji Alhaji Tsoho. su Mama Safiya da Mom Iklima suka Taya Umma Kama zaina suka Rakasu har Haraban Gidan Inda Direban Abba ke jiransu,Zareena ma Ta Goya yarta Tabi su Umma,Su Baban Kaduna Duk suna Waje nan sukayi sallama Kowane ba Farinciki ammh Da Sauki ba kamar Dazu ba,Abba ya kalli Umma yana Fadin"Fatima Har yanzu Jikin Halimar..? Kai Umma Ta Dagamai Tana Jin Taruwan kwallah Saman Goshinta ya Taba wanda yasa Ta Bude Kodaddin Idanuwanta Tana kallonsa Cikin Tsausayawa Yake Fadin"Sannu Halima..Sannu kinji ko..? Nima Hakurin zan baki Allah ya kiyaye kawai.."Yake Fada haka su Baban Kaduna Sallama sukayi Suka Shiga Mota Nene dai ba Baki sai dai kaga Tayi Shuru Kawai Tana kallon Mutane Abun ya Daketa Sosai.. Koda su Umma suka Koma Gida sun iske Sadiq ya koma Labari kuma Tuni yakaima Zainab Tunda Sadiq daya Dawo yake Fadamata itama taci kuka bata ma Kara Jin Wani kukam ba sai Da Taga Shigowarsu Umma haka Tazo ta Rumgume Nene Tana kuka Gefe Daya kuma Tana kallon Umma Dake Rike da Zaina wacce ke Kuka kasa kasa..... Dakinsu Ita da Zafeera Umma ta kaita ita da Zafeera da Nene Abba kuma ya wuce Dakinsa,Kwantar da ita sukayi suna Mata sannu Jin Jikinta yayi zafi Zareena ce ta Dago Tana Fadin"Umma ko zan kira Aboki Haddir ne yazo ya Dubata..? Wannan zazzabin yayi yawa ajikinta..! Numfashi Umma ta Sauke Tana Fadin"Kirashi in zaki sameshi.."Tafada Tana kallon zaina wacce ke kara Shiga Cikin Bargo Tana Kudundune kanta Jin za"a Kira Haddir yasa ta Dago kanta da Idanuwanta da suka Kumbura Tace"A"a Umma..Kada ki kira kowa..Ki bani panadol kawai .Domin wannan Ciwon Da nake ji acikin Kirjina Bashi da mgani Har Abada..! Tafada wasu Tagwayen Hawaye na Zubomata kafin ta koma ta kwanta Tana maida Numfashi Umma Ta Dade Tana kallonta Batayi mgana ba Nene ta kada kai Tana Fadin"Dole azo adubaki Sa"adiya Dare muke gudu..Dama ba mganin Damuwarki zai baki ba, na lafiyarki ce Domin Damuwa ko Mu bamu da mganin Tamu sai Hakuri kawai.." Zareena Ta Ijiye Jakar Zaina Wacce Ta tattaro mata Daga Gidan Alhaji Tsoho nan Gefen Gado Jakarta ta Dauko Tana Laluban wayarta Cikin karamar Jakarta Take fadin"Kuma Nene Zazzabin yayi yawa fa..! Hannu Umma Ta Dagama Zareena Tana Fadin"Kyaleta Zareena Ayi mata Abunda take so..Ina Jin Tsausayinta Fiye da yarda nake jin Tsausayin kaina Bari nayi sallahr Mangariba nazo na Taimaka mata tayi sallah Tayi wanka sai na Bata mganin Ta kwanta.."Ba suyi mata gaddama ba Suka Fice Daga Dakin Umma dai Kofar Tiolet ta Tura ta Shiga ta Dauro alwala Tayi sallah Ta Tada Zaina wacce Zazzabin ya karayin zafi Ta kaita Tiolet Ta Taimaka mata tayi wanka Tazo Ta Taimaka mata ta zura mata wata Doguwar Riga Umma Ta kasa Daina Jin wani iri game da Kukan da zaina keyi ta kasa ma Lallashinta,Dakyar ta sakata Tayi sallah azaunr kamar ta Kife Fita Tayi zuwa Kitchen ta Iske Zainab na Hada Fruit Salad shi ta Diba Ta kai ma zaina Dakyar ta iya Bata tayi Cokali Biyar ta kauda kai Allah yasa batayi Aman ba wannan karon Ta Balla mata panadol Ta bata tasha Ta koma ta kwanta Fadi Take"Umma Rufamin Bargo..Sanyi..Sanyi.."Hakoranta na Haduwa Rufamata Tayi Tana Tofa mata addu"a bata barta ba sai Da taga kamar makyarkyatan ya Ragu kamar zatayi Barci kana ta Fita Zuwa nata Dakin Tayi wanka Lokacin ana Kiran Sallar Isha"i Tayi Kan sallayar ta zauna kawai Domin Gabadaya Gidan yau ba Dadi Nene ma na Dakinta Haka ma Abba Zareena ma Tana Dakin Datake sauka ita da Jalal Zainab Kuma dasu Saudat suna Falo duk da su Yara ne basusan Komai ba Sun Fahinci gidan Ba kamar yadda yake ba Sadiq ma yana Dakinsa bakajin Motsin kowa. Babu Wanda ma ya Nemi Wani Abu Zainab ce Tayi Tunanin Hada Fruit salat Saboda Ruwa Ruwa ne zai yi Dadin sha Toh banda Wanda Umma ta bama zaina Ko Kitchen din ba wanda ya kallah Zareena ko Tana Dakin Datake sauka Bayan tayi Wanka Tayi sallah Ta Kira Haddir Sai da tayi mai Kira Biyu ya Dauka Sama sama suka gaisa Take Tambayanshi yana ina..? Yace mata yana cikin asibiti..Cikin Jimami tace ina zain Ya bata amsa da bai sani ba Tunda ya Fita da Mota Dazu bai kara ganinsa ba,Kuka ne yaci karfinta ta yanke kiran Shi kanshi Haddir kukan yake Tun Dazu yazo cikin asibitin ya kulle kanshi Cikin Office dinsa yana ta kuka Kukan Tsausayin Iyayensu da Zain din Shi kansa da kuma Uwa Uba Zaina wacce Yake Tunanin wani Hali Take ciki yanzu..? Shi kanshi yayi kuka kan wannan lamarin Ballatana ita. *Shakira..* *ZAINAZAIN..!* _(Is a love Story and Betrayal)_ *Wattpad:Jamilaumar351* *Mallakar:Janaftyshakira*❤️    *BOOK 1*              2️⃣0️⃣ "Zain kuwa Tunda ya koma Gida ya Shiga Cikin Bedroom dinsu

Chapter 20 of 32