Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
Hawaye,Domin bata da wani karfin Gwiwan Hana Anty Zaina kuka Domin Abun kuka ne ya sameta Dole abarta ta koka ko Zataji Saukin Abunda ke Damunta acikinn Ranta ita Fa kenan Data ke kanwarsa Taji Zafi Abun ya Raunana mata Zuciya Ballatana ita Matarsa Da ta kasance abokiyar Sirrinasa gabadaya. Umma na Shiga Cikin Dakinta Ta maida kofa ta Rufe Lokaci Daya Tana sakin wani Siririn kukan Daya ke neman kwace mata Tuntuni Tana Boyewa,Shi ta saki yanzu Domin Abun yana Fito mata Daga kasan Zuciyarta ne kukan Bakinciki da kuma Tsausayin Zaina Gefe Daya kuma Tana jin wani Daci acikin Ranta In ta Tuna Abunda Zain ya aikata a matsayinta ta uwa Dole ne Tafi kowa Shiga Tashin Hankali game da wannan lamarin Duk da Tana Boyewa bata son Kowa ya Fahimci Ta Damu da Abunda ya Danganci Zainullahi din. Nene Ta Dade tsaye kanta Tana kallonta Bata sani ba,Har Shigowarta Bata sani ba ballatana wamzuwarta acikin Dakinta Tana ganin Tana kuka Tasaki Mirmishin Takaichi kawai Domin ko Umma Taso Boye Damuwarta ita awajenta bazai Taba Boyuwa ba ba Tun yau ba tasan Cewa Duk Cikin Ya"yan da Umma ta Haifi Tafi Son Zainullahi kara ce kawai da kawaicin Dan Fari Da kuma Tasowar Da yayi ba ahannunta Ba yasa bata Shiga lamarinasa ammh Tabbas Soyayya Uwa da Da'nta Ko Uwa taso ta Boyeshi baya Boyuwa Allah zai bayannashi Wannan kukan Datakeyi bana komai Bane nashi ne Da kuma Bakincikin Matakin da Abba ya Dauka game da lamarin. Ganin Batama san da Tsayuwarta ba yasa tayi gyaran Murya Wanda  ya karkato da Hankalin Umma Zuwa Fahimtar ba ita kadai bace acikin Dakin Kafin ta waigo sai da Tayi Saurin Share Hawayenta saboda Bataso wani ya ganta Tana kuka kana ta Juyo Cikin Sanyi Jiki ta Sauke kallonta kan Nene wacce ta kura mata ido Tana kallonta Cikin Tsausayi da wani irin Girmanta Da Nene take gani acikin Idanuwanta. Yake Umma Tayi Tana Fadin"Ya akayi ne Hajiya Nene..? Tafada Cikin Zolaya Dama wani Lokacin Haka Take Kiranta Nene bata saki Fuskarta ba tace"Meyasa kika yin mgana kan Hukuncin da Alhaji ya yanke kan Zain..? Wani kallo Umma Tayi mata Tana Kokarin Boye Abunda ke Ranta Tana Fadin"Meyasa ni kuma zanyi mgana Nene..?Yana da Damar da zai iya yanke ko wani Hukunci Tunda Dagamu har shi muna Karkashin Ikonsa ne..Kuma Banga Illah kan Abunda ya yanke din ba Nene..Yana da gaskiya bai kamata ka kara Sauraran Wanda ka bama yarda ba ya Cutar dakai ba..." Ta Fada Tana kokarin maida kwallar cikin Idanuwanta Nene tayi Dariyan Takaichi kafin tace"Naji Hukuncin yayi miki Dadi Ammh Umman Zareena Meyasa kike kuka..? Umma Tayi Saurin Cewa"Ina kukan Tsausayin Halin Da Yata Halima Take ciki ne Nene...Ina Matukar Tsausayamata Tana da kananan Shekaru ayanzu haka Tayi kankanta da Daukan wannan Abun ko ni Da nake Babbar Mace in zan auna kaina a mizaninta yanzu haka Na Tabbata Raunina zai bayyana Soasai Ko ke baki Tsausayinta..? Nene Tace"Ina Matukar Tsausayamata mana..Ammh Shima Yarona Abun a Tsausayamai ne Umma ya kamata muyi wani Abu karki manta Zainullahi Danki ne da kika Haifa da Cikinki Taya zaki Shuru Rayuwarsa ta kara Lalacewa Da Hukuncin da Alhaji ya yanke ina zashi..? Wa yake Dashi bayan mu..? Da Sauri Umma Ta Juya Ma Nene Baya Tana Kokarin Shanye kukanta Lokaci Daya Tana Fadin'A'a Ni ba D'ana bane...Zainullahi Har Abada Dan'ki ne Aisha,Mganar kuma Shima Abun Tsausayi ne ban yarda ba..Karya yake Shi ba Abun Tsausayi bane..Mu  iyayensa da Danginsa da matarsa Daya Cutar da zuciyarmu Mune Abun Tsausayi  ba wanda bai ji Tsoron Allansa ba ya Dinga aikata Laifin da Allah ya Hana Sai Daga baya da komai ya Kwace mai sai ya Fara kuka Saboda a tsausayamai..? A'a Nene Kada ki Shiga Hurumin Alhaji a wannan Lokacin Shi kanshi yana Bukatar mai Lallashinsa Domin Abun akwai Ciwo wanda ka bashi Dukkan wani yarda ka karar da Lokacinka wajen bashi Tarbiya da kafashi Rana Tsaka Ya zo maka da Sakamakon Bacin Suna Haba Nene Zain fa Mata yadinga bi Hakan bai ishesa ba ya Dawo kasar sa ta Haihuwa ya Ijiye karuwa ko nace Dadironsa suna Shanshancinsu Har sai da yayi mata Ciki kana mu Danginsa aka zo aka Bamu shi a matsayin Sakamakon Abunda Da'nmu ya aikata Taya kike Tunanin inda Karfin Gwiwan kallon Alhaji nace Abunda ya yanke bai yi Daidai ba..? Ko saboda Halima Bana Son zain ya  kara Tunkaran Gidannan ina so Ta manta Dashi da komai nashi ammh In Tana ganinsa Tabon Da yayi mata bazai Taba gogewa acikin Zuciyarta ba..! Ta karishe Fada Tana Danne Abunda ke Taso mata Daga kasan Ranta Bata Jira Cewar Nene ba Ta Tura Kofar Tailet ta Shige Domim kaucema Nene Da ganin Halin Data ke Ciki Ita kuwa Nene Duk da Tasan maganganun Umma gaskiya ne ammh Kaunar da Take tsakaninta da Zain ta uwa da Danta ne ko Kowa bai goya masa Baya Ita zata Tsayamai ta Tallafeshi kada wannan Abun ya kara Jefa Rayuwarshi Cikin wani Hali ajiyar rai ta ijiye kafin ta Juya Ta Fita Daga Dakin,Ita kuwa Umma najin Fitan Nene Ta Sulale nan Kofar Tiolet ta Fashe da wani marayan kuka Kamar wata karamar yarinya Kirjinta Ta Dafe wanda ke Bugawa Tana Fadin'"Astagafurullah..Allah mun Tuba..Nidai bam kasance mazinaciya ba Haka mahaifinka na Tabbata bai yi wannan Shanshancin ba meyasa kai ka aikata..? Ka cutaar damu zain ka Cutar da zuciyar Uwa Wacce ta Sadaukar da komai saboda Kai kuma ka Cutar da zuciyar da Uwar data fi kowa sonka" Haka Take ta Fada Tana kuka Wurjajam kukan Daya Dade aranta Bata samu Fitar Dashi ba,Ta Dade tana wannan kukan kafin ta Share Hawayenta,wanka Tayi kana ta Dauro alwala Jin ana Kiran sallar Mangariba Bayan ta Fito ta Sauya kaya Tayi Sallah,Sai ta Fita Zuwa Dakin Zaina ta Sameta Tana sallah Tana kuka Zainab Bata Dakin Fita kawai Tayi Daga Dakin Ta Leka Dakin Zareena nan Taga su Junior da Saudart da Jalal suka taso suna mata oyoyo kansu Ta Shafa Tana Dan sakin Mirmishi Saboda su yasa ta Shiga Cikin Dakin Tana kallon Zareena wacce ke Sanya ma Umma karama kaya Inaga wanka Tayi mata Zareenan ne ta Dago Tana gaida Umma ta amsa Cikin sanyin Murya kafin tace"Yaushe zaku koma ne..? Itama Zareenan Cikin sanyinta Tace"Umma wata Daya zamu yi...Ammh Sati mai zuwa zan Je katsina Bikin Diyar kanwar Baban Jalal..Shima din ma yanzu muka gama waya Ranar Jumma"a zai zo ya Daukemu sai an gama Biki sai mu dawo kafin mu Wuce..''Kai Umma ta kada Tana Fadin"Ah akwai ma Sauran Lokaci Allah ya kaimu da rai da lafiya..,"Tafada Lokaci Daya Tana Dukawa tana ma Umma karama waasa da kallon Tsausayi Zareena tabi Umma Dashi Domin Taga alaman Tayi kuka ga Idanuwanta nan sun kumbura Kafin ta samu Zarafin mgana Umma Ta Dago Tana Fadin"Ki daina Saka mata kayan Sanyin nan Haka zareena garin akwai zafi zafi kuma ki Rage wannan A.C kar ya Cutar da ita.."Mirmishi Zareena Tayi kafin Tace"Umma ai ta saba..Tun muna U.S Da A.C muke kwana Da Farko ma na Fara Fada Abbanta yace gwara na barta ta saba Tunda dashi zata Rayu..Da Farko ni ban saba ba Har nazo na saba Hakama Jalal Babansa Daman ya saba ya  kwana Cikin sanyi ya Tashi Cikin Sanyi..'Umma tace"Ni Daman Baku nake ji ba..Takwarata nake ji kar Sanyi ya kamata atoh.." Zareena Tace"Itama ta saba Umma."Umma tace"Ta sabi me..? Kudai yaran zamani masu Jegon yan gayu kawai.."Sai ga Zareena na Dariya itama Umman Dariyan Tayi Nene ce ta Dago Labulen Dakin Ta Shigo Tana Fadin"Dariyan me nake ta Jiyowa..?Umma ta kai Dubanta ga Nene Tana Fadin"Ni da Diyata ce..Kuma sai kowa yaji..? Nene ta Tabe baki Tana Fadin"Naje Dakin ki ne Daman baki Ciki...Alhaji ne baya Jin Dadi Sai da yasha panadol.."Atare Umma da Zareena suka ce"Subhanallah..Allah ya sauwake..!Bari naje na Dubashi..' Umma ta Nufi Hanyar Fita Zareena ta Dauki Umma karama ta mika ma Saudart Tana Fadin"Umma bari na biki na Duba Abba.."Umma batace komai ba Suka Rankaya suka Fita Harda Nene bayan ta tsaya ta gyara ma Saudart Rikon Umma karama sun Fito Falon kenan Sai ga Sadiq ya Fito Daga Dakinsa Kallonsa Nene Tayi ganin baida Walwala tace"Kaci Abinci..? Kai kawai ya Girgiza mata yana Zama daya Daga Cikin kujerun Falon,Umma ta kalleshi ganin bai da wani walwala tace"Akwai abincin agidan ne..? Nene tace"Eh Nace Zainab Ta shiga Kitchen ta Girka ko Macaroni Da kifi ne.."Kai kawai Umma Ta kada ta wuce zuwa Dakin Abba Nene ta mara mata Baya Zareena ce ta Tsaya Tana gayama Sadiq Abba baya jin Dadin Jin haka yasa ya mike Shima ya mara musu baya Shi da Zareena. Ko da suka Shiga Sun iske Umma da Nene duk sun sakashi a Tsakiya,Suna Faman mai sannu Da kai kawai yake amsawa Domin Shi kadai yasan Halin da Zuciyarsa ke Ciki Shigowar Zareena da Sadiq ne yasa ya Bude Idanuwansa yana Kallonsu Gabansa suka Karisa Dukkansu suka Rankwafa suka gaisheshi suna mai Sannu Mirmishi Abba yayi yana Riko Hannun Sadiq lokaci Daya yana Fadin"Babana yaushe zaka koma ne..?ko dogon Hutu ka samu ne..? Cikin Ladabi Sadiq yace"Gobe zan koma Abba..Dama na samu Break ne na leko ku sauran wattani kadan ne na kammallah sai Defence.."Abba ya Jinjina kai yana Fadin"Allah ya Taimaka..Allah ya tsaremin ku aduk inda kuke.."Ya fada Cikim karaya Dukkansu suka amsa da Ameen Harda Iyayen Kallonsa ya maida kan Zareena yana Fadin"Diyar fatima ina Amaryata na ganki ke Kadai..? Zareena Tace"Tana Daki waje su Saudart Abba..Zan kawo maka ita sai ka ji sauki.."Kai ya kada yana Fadin"ki yi sauri ki koma kada Su Kada ita...Ina abokina Jalal ban ji Duriyansa ba..? Zareena Tace"Duk suna chan Tare dasu Junior.."Abba yace"Ok..Ina megidanki..? Kunsamu DogonHutu kenan..? Kafin Zarreena Tayi mgana Umma tayi saurin cewa"Eh wajen Wata daya zasu yi..Sati dai mai zuwa tace Jawaad din zai zo ya Dauketa Su Tafi katsina Bikin Diyar yayar shi Mijin nata..'Abba ya Jinjina kai yana Fadin"Yayi kyau..Dukkanku Allah ya yi muku albarka Ina Zainab ina Halimatu har yanzu bata bar kukan ba ko..? Cikin Tsausayawa Zareena Tace"Ameen Abba...Bata bari ba Abun dai yayi sauki ammh bata mgana Sai dai in ita da Umma ne.."Abba ya koma ya kwanta Yana Fadin"Fatima ki kula da ita..In Zazzabin nata yaki sauka kuje asibiti adubata..! Umma tace"Taji sauki..Sai dai yawan kukan ne..Yanzu hakama Tana Sallah na sameta Tana kuka Zainab kuma Tana Kitchen.."Lumshe ido Abba yayi yana Fadin"Ina Tsoron wani Abu..Ina Tsoron Yarinyar nan takamu da wani Ciwo sanadin Yaron nan Basan da wani ido zan kalli ahalinta ba..! Nene ta kada kai Tana Fadin"Sai Hakuri..Insha Allahu babu Abunda zai Faru....Zata warware Insha Allahu.."Mirmishin Takaichi Abba ya saki kafin yace"Allah yasa..Ku barni zan kwanta ko Ciwon kan zai sauka..! Dukkansu suka mike suna mai Sannu Ya"yan ne kan gaba sai iyayen Sai da suka Fita kana Abba ya Juya yana Share kwallar Data Silalo mai ta Bayan Kunnuwansa,Dama Dalilin Daya sa yace su bashi waje kenan kar suga Rauninsa ammh Tabbas wannan Al"amarin ya Girgiza shi Shi Usman Ne za"a samu Daga Cikin ya"yansa wanda ya ijiye karuwa Har da Sakamakon Cikin Shege..? Wannan Abun in ya Tuna sai yaji kunyar Duniya ta kamashi Ko Yan"uwansa ma Baya son Hada Ido da su saboda wannan Abun kunyar da ZAIN ya aikata. Ya samu Barci sai Wajen 10pm na Dare ya Tashi yayi wanka Ciwin kan ya sauka sai dai Nauyin Kirjin Bayan yayi wanka yayi sallar Isha"i Umma ta kawomai abinci yaci Ita kuma Nene ta gyaramai Shinfidar,Mganin ya kara Sha ya koma ya kwanta Umma Ta Tafi Dakin zaina ta bar Nene zata kwana da Abba. Dakyar da Lallashi Umma ta Lallashi Zaina taci macaronin nan Shima ba wani mai yawa ba ba Dadewa ta amayar Dashi Umma ta Fara Shiga Damuwa ganin kwana Daya Rak zaina Duk ta Fada kamar ba ita ba Idanuwana sun kumbura sun yi Luhu Luhu Sun kuma Fada Gabadaya Jikinta ba karfi saboda Rashin Cin Abinci,Ko Taci sai ta amayar dashi kuma taki yarda azo adubata ko kuma suje asibiti kada wata Cutar ta kamata. Kamata Tayi suka Shiga Tiolet ta wanke mata baki kana ta Dawo da ita kan gado ta kwantar da ita Ta koma ta gyara Wajen Da tayi aman kana ta koma Kitchen ta Tsiyayo Ruwa a Fulas na zafi Ta Hada mata Tea Shima Din Sai da Tayi mata jan Ido kana Tasha kadan Kafin ta kauda kai Cikin Bacin Rai Umma ke kallonta Tana Fadin"Meyasa kike son kashe kanki Saboda wanda bai damu Dake ba..? Ke sakaryan ina ne..? Kalli yadda kika Rame Cikin kwana Daya..? Kina so ki kashe kanki ne..? Girgiza ma Umma kawai takeyi takasa mgana sai Hawaye Dakyar Tace"Umma Bazan iya cin komai bane..Ko naci sai nayi amai,Umma kirjina da Zuciyata Ko"ina Ciwo suke ni nafi son ma na Mutu Umma da in zauna wannan Dacin Da nake ji acikin Zuciyata yayii ajalina"Gam! Umma ta make mata Baki Cikin Fushi Take fadin"Shi bai mutu saboda Abunda ya aikata ba ke zaki Mutu..? Kul kar nakara jin wannan mganar Ki Fitar da Abunda ke Ranki ki Maida komai ba komai hakan bashi ne Karshen Rayuwarki ba Indai ina Numfashi sai Zain ya sake ki ki samu wani mai Nagartan ki aura Kicigaba da Rayuwarki Shi kuma yaje chan ya karata da Dadiron tasa da kuma Dan Shegen Da zata Haifa masa Tunda Haka ya zaba..! Cikin Rauni da kuma wani Tsausayi Zaina tace"Umma kema baki yafe ma Firstlove ba..? Hararanta Umma Tayi tana mika Kofin Shayin Take fadin"Bana son na kara jin wata mgana Daya Dangance sa..Karbi ki Shanyeshi Duka ki bani Kofin kafin na Saba miki.."Umma ta Fada Fuskarta ba alamun wasa Dole Zaina ta karba ta kafa kai Duk da Bakinta kamar Madaci Haka Takeji ammh Saboda Ran Umma ya baci yasa ta shanye ta mika ma Umma Kofin Ta karba Tana Fadin"Ko ke fa..? Karki kwanta Tashi kisha Mgani naji kamar zazzabin ya Dawo..? Da Toh kawai ta amsa Umma ta ballo mata panadol Ta mikamata Hade da Ruwa tasha Ta koma ta kwanta Tana Sauke Numfashi,Umma ta gyara mata kwanciya kana ta Fice zuwa Kitchen ta maida komai,Zareena ta kwanta Zainab ma Haka suna gama cin Abinci kowa ya nemi makwanci,Shiyasa ta koma Dakin Zaina din Ta Shimfida Bargo nan kasa Ta kwanta Bayan ta Rage Hasken Dakin Duk Zaina na kallonta Wacce ke ta Sharan kwallah bata so Kukanta ya Fito Umma Taji ta. Washegari kuma Kafin Inna Hannatu ta wuce tazo ta Duba Abba Tunda Nene ta Kira Alhaji Tsoho Ta gayamai Abba bayajin Dadi yau ma bai fita aiki ba,Sai da Sadiq yaje yazo da Dr Imran Ya Dubashi Jininsa ne ya Hau yamai alluran barci Da kuma mganguna,Tunda Sadiq din yana ta Kiran Haddir bai Daga ba Sai daga baya ya Kirashi yace mai yana Gidan zain ne achan ya kwana Cikin Tsausayawa Sadiq yace"Ya Haddir ya Jikin Ya zain din..? Haddir ya Sauke Numfashi yana kallon Zain dake kwance yana Barci yace"Da sauki zamu ce Sadiq gashi kwance yana Barci.."  yanzu ya gama amayar da Tea din Da Haddir ya Hadamai yasha..Alluran barci ya sake mai ya kara Doramai Drip,Zazzabin da Ciwon kan ya sauka Jiya ammh Zuwa safiya kuma Sai ya Dawo,ba Domin Haddir gidan ya kwana ba baisan wani Hali zain zai Shiga ba yama ki yarda suje asibiti ne da Chan zai kaisa abashi gado adinga Kula Dashi Tunani yake Allah yasa wannan Damuwar da zain ya saka ma Ranshi bazai haifarmai da Hawan Jini ba Cikin Tsauyawa Sadiq yace"Allah ya bashi lafiya..In zan wuce zan Biyo na Dubasa Daman kiran da nayi maka Don kazo ka Duba Abba Shima ya kwana Jikin ba Dadi ganin ban sameka ba sai Alhaji Tsoho yace naje asibiti na Dauko Dr Imran har ma yazo ya Dubashi yamai alluran Barci ya samu barci.."Cikin Damuwa Haddir yace"Innalillah meke damunsa..? Cikim Damuwa Sadiq dake Haraban gidansu bayan ya rako Su Inna Hannatu ne Direban Abba ya Dauketa zuwa Filin Jirgi Dagachan zai wuce da Zainab makaranta Tare da ita suka Tafi yace"Yace Jininsa ne ya Hau sosai ya Haddir..! Cikin Salati Haddir yace"Subnallah yanzu ya Jikin nashi..? Sadiq ya numfasa yana Fadin"Da sauki har ya samu barci ma.."Haddir yace"Allah kara lafiya zan shigo zuwa anjuma na Dubashi in Jikin nashi yayi sauki Ina Halima..? Sadiq yace"Itama fa Tana kwance ba Lafiya ya Haddir.."Haddir kansa kawai ya Shafa yana Fadin"shikenan Allah ya bata lafiya.."Daga haka suka yanke Kiran Dafe kai kawai Haddir yayi yana kallon Zain Wani Irin Abu yake ji a kaasan Ransa zai iya Rantsuwa cewa Zain ne sanadin Hawan Jinin Abba Kaicho Dama irin wannan Abun yake ta Jiyema Zain Tun Suna makaranta ammh yayi kunun Uwar Shegu Da mganarsa sai yanzu da komai ya baci ne zai koma yana Nadama Gashi ya saka kowa Cikin Damuwa Iyayensa na Fushi Dashi haka Zakalika ma Matarsa Kuma Tana cikin wani Hali Saboda shi Yana Fatan Allah ya yayyafa ma Abun Ruwan Sanyi. Yana Tare da Zain ko"ina Baya zuwa ko Salla agidan yake yinta Daya Farka Shi zai Taimakamai yayi alwala yayi sallah yaci Abinci wanda Haddir din ke Fita ya Siyomai,Har zuwa Wajen bayan La"asar dai jikin na Zain yayi sauki Zuwan Sadiq ne wanda zai koma zaria Jikin ya kara Rikicewa Domin ya Fadamai Zaina na chan kwance kwana Take kuka Bata ci bata Sha Umma kadai take ma mgana,In ba ita ba sai dai ka gaji Dayi mata mgana bazata Tanka ka ba sai kuka Shima da zai Tafi ya Shiga inda Take ya Duka Har kan gadon Da take kwance Yana Mata mgana Tare da kalaman Lallashi gareta ammh Zaina sai kuka kawai take,Yayi kokarin yaga Tayi mgana ammh Taki cemai komai Umma tace ya Tashi ya Tafi kawai bazata mai mgana ba ya Fita da Tsausayin Zaina acikin Ranshi Zain yaji Hankalinsa ya Tashi Kwarai ya Fara Kokarin Tashi Dama Haddir ya Ciremai karin Ruwan Da cewa zai je GRA ya Duba Firstlove dinsa. Haddir na Kokarin Hanasa Da cewa"Ina zaka kana Cikin wannan Halin..? Shima Abba ba lafiya gareshi ba yau sai da Dr Imran yaje ya Dubashi Jininsa ne ya Hau.."Cak Zain ya Dakata Daga Sanya kayan dayake kokarin yi ya waiwayo yana kallon Haddir Lokaci Daya yana Fadin"Jininsa ne ya hau..? Ya Fada da Sigar Tambaya Cikin Muryan Ciwo da mamaki Kai Haddir ya kada yana Fadin"Kwarai da gaske...Na sani kuma kaima ka sani Kana da Nasaba da Hawan Jinin Abba In haka ne kuwa zuwan Ka gida yanzu ba alheri bane..Wlh Zain ko Alhaji Tsoho Dake matukar kaunar ka bai zo so ganinka yanzu ba Gwara ka Jira zuwa nan da Kwanaki kadan in Abun ya sake su sai ka Tunkaresu ammh yanzu akwai matsala Domin Sai Ciwon Abba ya kara Tashi in ya ganka..! Ya Fada yana kauda kai Saboda Bayason kallon Zain din balle har ya Fahinmci wani Hali yake Ciki Kuma baya so ya Furta masa Abunda ya Faru tsakanin Dadyn Abuja da Abba Jiya Shi kuwa Zain gabadaya Jikinsa sai ya kama Rawa wani Jiri na neman Gadashi ya Rike Jikin Wardrope yana Fadin"Firstlove fa Haddir..? Bazani naga Halin Data ke Ciki ba..? Nafi kowa sanin Halin Zaina bazata ci Komai ba Kuka zatayi Tayi har wani Cuta ta kamata Tana da Rauni indai akaina ne sosai...Ya kamata naje na lallasheta.." Ya Fada kamar yayi kuka Haddir ya kalleshi Cikin Jin Haushi yana Fadin"U are not Serious..Kana Tsammanin akwai Wata mgana da zaka gayamata ne ayanzu ta Saurareka..? Ka riga ka gama Zubar da Duka Kimarka da Soyayya da yardan dake tsakaninku..Da kake Fadin Kasanta Tana da Rauni akan ka Meyasa kasan da Haka Tun Farko baka Daina Abunda watarana In Taji Raunin nata zai bayyana ba..? Yafada Cikin Bakinciki Da Takaichin Zain din Wanda kawai ya Sunkuyar dakai bai kara mgana ba Rigar hannunsa ya Zura na wani Farin yadi ko hula bai saka ba Duk yayi wani Busu Busu dashi ya Nufi Haddir yana Fadin"Aramin key din Motarka..? Haddir ya nuna mai Gaban Dressing Mirror din Dakin yana Fadin"Ga Key din Taka Motar chan yau da Safe dana Shiga Cikin asibiti na Taho maka da ita.."Da sauri ya nufi wajen ya Dauka Yana Sauri kamar baya Cikin Natsuwarsa yana Shirin Barin Bedroom din yaji Muryan Sadiq yana Fadin"Kar kaje gida ayanzu Yaya Zain..! Ya Fada yana mikewa Haddir na Gefe yana kallonsa Zain ya Juyo Cikin Cije baki Da alamun Rashin lafiya yace"Kai Sadiq meka sani..? Baka san komai game da Dacin Da nake ji acikin Raina ba Dole zan je na Roki Abba dasu Umma gafara na kuma Dauko matata mu Dawo Gida na Tabbata ita mai yafiya ne gareni.." Daga Haka ya Juya zai Fita Sai kawai yaji Sadiq yace"Ko kaje Ba wanda zai maka mgana Ballatana ya Saurareka..In ma Abba ya bari ka Shiga Gidan kenan..! Yafada Cikin Wani yanayi Atare Zuciyar Zain Data Haddir ta amsa da Dam! Haddir ya Waro Ido yana kallon Sadiq shi kuma Zain da wani Sauri ya waigo yana kallon Sadiq Cikin Rashin Hayyaci kafin yace"Ban...Ga...ne ba..! Ya Fada muryansa na Rawa... Kada kai Sadiq yayi yana Fadin"Eh...Jiya nan Abba ya gama Tara su Umma da Nene yace bai yarje musu In kazo Gidan suyi maka mgana ba ballatana Har su Saurarekaba Daga karshe yace harta Anty Zareena na bai yarje mata ba kuma Umarni ne ba Shawara ba Daga Karshe yace Shi da kanshi zai gayamaka kada ka karo Tako mai Gida Tunda ba Da kudinka ya Siya Gidan ba..! *Shakira..* *ZAINAZAIN..!* _(Is a love Story and Betrayal)_ *Wattpad:Jamilaumar351* *Mallakar:Janaftyshakira*❤️ *BOOK 1*               2️⃣2️⃣ "Ba Zain kadai ya kad'u da jin Mganar Sadiq ba Hatta Haddir Shima sai da ya nuna Kad'uwarsa a Zahiri,Zain kuwa K'asa kasa Daukansa Tayi Domin Wani irin Jiri ne ya kwasheshi ya Tafi luu zai Fadi Atare Dukkansu Sadiq da ya watsar da Jakar Hannunsa ya Nufeshi Sai dai Haddir ya Rigashi isa Gareshi Tunda Shi yafi kusa Dashi Cikin Ikon Allah ya Tallafeshi ya Fado Jikinsa Cikin Fitan Hayyaci yake Fadin"Abba...Ne Abba ne yace kada na kara Shigomai gida .? Yafada wasu zafafan Hawaye suna Biyo Duka kuncinsa Atare Sadiq da Haddir suka Rikosa Zuwa Bakin gado ganin yadda Duka Jikinsa ke Rawa suna Zaunar Dashi Haddir ya kalli Sadiq yana Fadin"Jeka Kitchen ka Dauko Goron Ruwa mai sanyi a cikin Fridge..ka Hado da karamin kofi plz.." Jin Haka yasa ya Fita Da Sauri ba"a dau wani Lokaci ba ya Dawo da Ruwa a Hannunsa Da karamin Kofi ya mikama Haddir Shi kuma ya karba ya Tsiyaya Ruwan Fin Rabi acikin Kofin ya Mikama Zain yana Fadin"Karbi kasha..Zuciyarka Zatayi sanyi ta kuma Daina Bugawa Da Sauri Da Sauri.."Idanuwansa da Suka Sauya kala ya Watsama Haddir Dake mikamai Kofin Ruwan Cikin Bugun Zuciya da wata murya Cikin yanke Tsammani yake Fadin"Taya kake Tunanin zan iya Shan Ruwa ya Tsirgamin Haddir..?Kanaji fa Abba Da kanshi yace kada kowa ya Saurareni kuma Shima zai Fadamin kada na kara Takamai zuwa Gida..? Kaichona Haddir Wlh ban Taba jin na Tsani kaina ba Irin Jiya yau kuma kalaman Abba Gareni sun kara karyamin Duk wani Sauran kwarin Gwiwata yanzu ina zan saka kaina Duka iyayena da yan"uwana Suna Fushi Dani kuma suna kallona a mutumin da bai da wata kima..? taya zan kara samun Damar da Duka Ahalina zasu yarda dani..?Ga Firstlove itama Zata barni saboda wannan Bakin Fentin da na Saka ma kaina Allah na Tuba Allah ka yafemin Astagafurullah...! Yake Fada Cikin Kuka Lokaci Daya yana saka Fuskarsa Cikin Tafukan Hannayensa yana wani kuka mai cin rai Harda Sheshsheka kamar zai Shida,Sadiq baya ya koma Shima yana Sharan kwallah Domin Zuciyarsa bazata iya Juran ganin Jajirtatacen Yayansa na irin wannan kukan,ba Haddir kuwa kansa kawai ya Dukar yana Sauraran Duka maganganun Zain din Shima Ya gaji da kukan zuccin Da yake yine,Dagowa yayi yana kallon ZAIN Din kafin ya sake mikamai Kofin Ruwan yana Fadin'"Duk naji...Karbi dai kasha Ruwan ko bakomai zai Saka ka Natsuwa..! Bai yi gaddama ba ya karba ya kafa kai Domin gabadaya makoshinsa ya Bushe ne kamar bai Taba Shan Ruwa ba sai da ya Shanye Duka Haddir ya karamai kana yaji Bushewar makogwaransa ya Ragu Da Kofin da Ruwan Haddir ya mika ma Sadiq yana Fadin"Fita dashi Sadiq.." Ba Gaddama Sadiq ya maida Komai Kitchen din kana ya Dawo ya Iske Haddir ya zauna Kusa Da zain yana Fadin"Zain Dago kanka ka Saurareni..'Dole Zain ya Dago

Chapter 22 of 32