Datayi Shirin komawa aranar Maryama Tatashi Da naguda aka kwasheta Zuwa asibitin Mallakin Dr Abubakar Saulawa.
Suna zuwa aka karbeta Sai Dakin Haihuwa Duka Gidan aka Tafi Umman Zareena da Nene,Sai Halima da Baba Abdullahi Da Direba Hajiya mama Tana Gida bata Taho ba Sai Dr.Saulawa Wanda Dama yana Cikin asibitin Alhaji Usman Daga baya Yazo Asibitin ganin Har Wajen Yammah Maryama Bata Haihu ba Sai Aka yanke Shawaran yimata aiki Zuwa Lokacin Hajiya Mama ta iso Ita dasu Zain Wadanda Tunda suka Dawo makaranta aka kaisu Wajenta Suke mata kuka Suna ta Kiran Sunayen iyayensu Dana Mama maryama ganin Haka yasa Ta lallashesu Ta Fada musu suyi ma Mama maryama addu"a Tana asibiti zata Haifa musu kani ko kanwa Jin Haka yasa Zareena da Haddir suka Fara Murna Shi kuma Zain sai ya Fara kuka yana Fadin Shi ba kanwa za'a Haifamai ba Mata da kuma kukan sai an kaisa yaga Mama Maryam Dole Hajiya Mama ta Tarkato su suka Taho Tare Duk da Dr.Saulawa Nata Fada ammh ganin yadda Yaran suka Sha kuka ne sai suka bashi Tsausayi.
Cikin Ikon Allah ana Kokarin Saka ahannu akan Takardan da za"ayi ma Maryama aiki Allah ya Sauketa Lafiya Inda ta Samu Haihuwar yarta Mace mai kama da Ita sak,sai Kuma Duhun mahaifinta Data Debo Saboda Maryama Faraace Sosai Sabani Abdullahi Dayake bakin Fata Sai da aka gama gyarata ita da Abunda ta Haifa kana Nurse Ta Fito da Jinjiran a Hannunta Da Halima ta Faracin karo Zata mikamata Zain yayi azamar Mika Mata Hannu yana Fadin Ta bashi matarshi Tsaye Tayi tana kallonsa Cikin Mirmishi Dr.Saulawa yace ta mikamai Tako mikamai ya karba kamar zai Fadi Halima ta tareshi suka koma Suka Zauna kowa ya Kura mishi ido ana kallon yadda ya kurama Jinjiran ido yana kallonta da wani Mirmishi Kafin ya Dago yana kallon Abbansa Cikin Yarinya yace"Abba me sunanta...?
Kafin Alhaji Usman ya bada Amsa Abdullahi ya bashi amsa da Fadin"Maryama Ta gayamin in ta Haifi mace Sunan Yaya Halima Take son asakamata Saboda Haka Alhaji Dakta kayi mata Huduba da HALIMATUS SA"ADIYA..!
Gabadaya Murna Ta kama Halima wacce ya"yanta ke Kiranta Goggo Halima Cikin Jin Dadi Take fadin"Masha Allah..Allah ya Raya Halimatu.."Zain kawai akaji yace"Ba Sunanta Halima ba Abba..Ni Matata irin Sunana gareta..!?
Cikin mamaki Nene tace"Irin Sunanka Da'n Nene..? Wani Suna kenan..?
Cikin Kura ma Jinjiran ido yace"Tunda Sunana ZAIN ita kuma Sunanta ZAINAH daga yau ba Halima ba...Kunga Zainazain kenan..!gabadaya al"ajabi da Mamaki ya kama kowa Dr.Saulawa yana kallon Zain da wani Farinciki acikin Ransa kafin ya Dafa kansa yana Fadin"Allah ya maka albarka...Karka Damu Sunanta Halima ammh Kai mijinta me kuma ka zaba mata Suna ai Shikenan kowa ya Shaida Sunan Matar Zain Zainah ko..?
Yafada yana kallonshi Washe baki yayi yana Daga sai Abun ya basu Dariya Dakyar Dr.Saulawa ya iya karbanta Suka Dunguma Dakin da aka maida Maryama Suka Iske ta Farfado agabanta yayi ma Jinjiran Huduba da Halima ya Dago Yana Fadin"Allah ya Raya Halimatus Sa"adiya..!
Karaf Zain yace"Ba Sunanta Halima ba Sunanta Zainah nace muku..!Maryama ke neman karin Bayani Nene ta Koramata yadda akayi Dariya Tayi Tana Fadin"Gaskiya ne Yarona..Sunan da aka Zabamata yayi Daidai da..Sunanka ina Fatan ko bayan Raina zaku Tabbatar da Halima amatsayin matar Zain..?
Tafada Tana Tsare Duka yan Dakin da Ido Kowa sai yaji Abun Wani iri Baba Abdullahi ne yayi Mirmishi yana Fadin"Kema yarintar Zain din zaki mana..? Kai ta girgiza Tana Fadin"Ba yarinya bace..Ku kalli Idanuwansa Tsabar gaskiyansa yake Fada..Nidai Nayi alkawarin Tun Kafin Ta Fito Duniya na Bama Zain ita amatsayim Mata Har Abada Ko Bayan Raina Abdullahi ka Tayani Sauke nauyin Dana Dauka..!
Kowa adakin Sai da Jikinsa yayi Sanyi Dr.Saulawa ne yace"Karki Damu Maryama...Insha Allahu da kanki zaki Hada Hannun Zain da Halima amatsayin ma"aurata."Wani Sanssayar Miemishi Tayi kafin tace"Allah yasa Ina Fatan Haka.."Daga Haka bata kara cewa komai Suma ba wanda ya kara mgana sai aka koma Raba Rigima Tsakanin Zain da Zareena Inda Take Rigiman sai ta Dauki Halima karama ammh Zain ya Dafe gadon da Maryama ke kai yace bamai Taba mai Mata Tun Abun nashi na basu Dariya Har suka zo suka Tabbatar ma kansu zain Da gaske Acikin Ran Dr.Saulawa kuma yana Ta auna Abubuwa afili ya Furta Haka Allah ke al"amarinshi Daman.
Kwana Daya Maryama Tayi a asibiti Aka sallamota ta koma Gida aka cigaba da karban yan Barka Gabadaya Kulawanta ya koma Karkashin Nene da Umman zareena Duk da suma Suna Fama da kansu Goggo Halima Sai dai kallo Domin ko Tace su barshi Sai suce sai sunyi ai maryama Tamkar kanwa Take garesu Hakama Hajiya Mama Tana iya bakin Kokarinta,Zain kuwa ansha Fama Dashi Domin Tunda akayi Haihuwan sai Ansha Fama Dashi yake zuwa makaranta sai ya Fara kukan Sai dai ya Tafi da ita da Dubara yake Tafiya yana Dawowa kuwa Shashen Maryama yake yada Zango Daga ma Karshe chan ya koma da kwana Saboda Zaina Ba Wanda ya Damu da Hakan Domin Kowa yana ganin Maryama da Mijinta yanzu Suna Cikin Ahalin Dr.Saulawa Tsudum.
Dr.Saulawa da ya"yansa sun ma Maryama kara Sosai Da Abun arziki Sai wanda ya gani Musamman ma Alhaji Usman da Matansa Sunfi kowa Rawan gani Haka da yan Gada suka zo Suna suka koma da Fadan Irin Dimbin karamci da Dattako irin na Iyalan Dr.Saulawa Goggo Halima ma Bayan Suna Ta koma Itama da Sha Tara na arziki Tana Ta Godiya Aka bar Maryama da yarta Halimatu Sa'adiya wacce Taji Tudu Biyu Sunan Goggo Halima kuma Sunan Baba Atine na gaskiya.
Kwanci Tashi ba Wuya awajen Allah Zaina nada Wata Shida Aduniya Nene ta Haifi Yarta mace Wacce taci sunan ZAFEERA bayan Haihuwanta da Kwana Hamsin Ita kuma Umman Zareena ta Sauka Wannan karon ma Namiji ta samu Yaci Sunan Mallam Umar suna Kiransa Faruq,kamar dai yadda Tsarin yake Nene uwar Maza Taja Nata itama Umman zareena Uwar mata taja nata Tunda Lokacin Zareena ta Girma Suna Cikin Shekaru na Goma da Haihuwa sai Tattalin ya koma kan Zafeera Yadda kukasan kwai haka Umman Zareena ke ji da Zafira kamar Tsoka Daya amiya Zain kuwa da karfi Da yaji ya zama Dan Shashen Maryama Saboda zainarsa Reno kuwa Tare sukeyi da Maryama Tun baya Iya Daukanta Har sai da ya iya Haka zai zauna yana ta mata wasa Tun Kafin ta isa Cin Abinci Zain ya Fara bata kayan zaki Ko Iyayen nashi na Fada Maryama Ta kanyi Mirmishi Tace su kyaleshi Mutum da matarsa Saboda Hakama Ta Riga ta ganeshi Da Taji muryansa zata Fara wuntsila kafa Tana Babban Dariya irin na Jarirai yana Daukanta kuma Shikenan Haka zasu yi ta Rigima da Zareena kan sai ya bata ta Dauketa In Kuma akaci Sa"a ya bata Zareena na Daukanta sai ta Fara kuka Sai Zain ya Fara Dariya Haddir dai yana Gefe Shi baima Cika cewa zai Dauka ba Ganin yadda Zain din ya mamaye komai Sai dai yayi tama Zareena Dariya ita kuma Taji Haushi Ta Fara kuka Maryama Ce mai Raba Fada ta kuma Shiga Ciki Tayi alkalanci.
Shekaran Halima Daya da Wattani Maryama ta kara samun Ciki Sai dai kuma yazo da matsala Tunda Tayi ta Ciwo sai da akaje asibiti nan aka gano Tana da Cancer Mahaifa Hankakula Suka Tashi barin ma Abdullahi,Ammh Dr.Saulawa da Alhaji Bashir sukayi Tsaye sai da akayi mata aiki taji Sauki Bayan an Fitar da wanchan Cikin,Dalilin wannan Ciwon sai Dawainiyar Halima Ya koma Hannun Umman Zareena Tunda Allah ya Doramata kaunar Yarinya Ta Hadasu ita da Zafeera Tana Rainonsu Tare Zain na Tayata Domin Dakyar ma ya bari Umman Zareenan ke Daukan Halimar har ta goyata Ganin Mama Maryaman Bata da Lafiya ne Shiyasa.
Bayan Taji Sauki ma Hakan bata Chanza Zani ba sai dai in Tana kuka akaita Maryama Ta bata Nono a maida mata Ita,Cikin ikon Allah ba Dadewa Maryama ta Sake samun Wani Cikin Wannan karon Da Sauki Abun Sun dai koma asibitin anyi Gwaje gwaje aka Tabbatar da Maryama zata iya Haihuwa ba Matsala Da haka tacigaba da Rainon Cikinta Gefe Daya kuma Dawainiyar Halima yana Hannun Umman zareena Cikinta na Shiga wata na Shida Ta Yayeta Ta Damkama Umman Zareena Ita,wacce ake ma Lakabi da mai Rainon Yan Biyu Sakamakon Zafeera akwai Girman Jiki Har ta kamo Zaina a Girma Ita har ta Fara Takawa Halima din ce Take Ta Rarrafe.
Acikin Wannan yanayin ne Wani al"amari ya Faru wanda iyalan Dr.Saulawa suka kasa mantawa Dashi Shine Wata Ranar Asabar da Misalin karfe 2:00pm na Dare yan Fashi Suka Shigo Gidan Alhaji Bashir da Manyan makamai Lokacin da Suka shigo Gidan Abdullahi ya Tashi gaban get ya Shiga Gidan Wajen Maryama Dama Hakan yake yi sai asuba kuma yake Dawowa,Duka ya Kulle get Din Haurowa sukayi suka Shigo kamar Wasa Dama Tunda ya Shiga Ciki bai kwanta ba,Alwala ya Dauro ya Fara Sallar Nafila yakai Raka"a na Biyu yaji motsin Takun Kafafu Da Sauri ya Sallame ya Dauki Fitilansa da Sandansa zai Fita Sai maryama ta Farka ganin zai Fita yasa Ta Tambayeshi sai yace mata yana Zuwa ya Fita da Sauri Yana Fita kawai yaci karo da Wani katon Mutim Cikin bakaken kaya ya Haskeshi da Fitila yana Tambayan waye Kafin ma yaji wani Abu Daga Bayansa yaji an sakarmai Harshashi aciki nan Take ya Fadi matattace Jin wannan karan Harbin Shi ya Rikita Maryama Ta Fito Da Gudu Ga Ciki Tana kuka Itama nan Take wani ya sakarmata Harshashi aciki Itama Ta Fadi ba Rai.
Innalillahi Wa"inna illairaju"un wannan ahali Sun ga Tashin Hankali kwarai yan Fashi Sun Shiga Har Shashen Alhaji Usman basu dai kashe kowa ba ammh Sun Karbi kudaden Daya Dawo Dasu Daga Tafiya yana Shirin Washegari zai kai Banki,sai kuma Dan kunnayen Zinaren su Nene da wasu kudaden Dake Hannunsu Sukayi ma Alhaji Usman Dukan Tsiya sai da ya Suma kana suka Tafi Su Nene suka Rude sai kuka Ga su Zain Suma kukan suke Zaina da Zafeera kuwa sai kuka Suke na Tashin Hankali Umman Zareena ita Tayi Hausan Kiran Wayar Dr.Saulawa ta Na kuka Tana gayamai Halin daSuke Ciki Cikin Tashin Hankali Shida Hajiya Mama suka Nufo Gidan Domin Daman Kaf an anguwan ba wanda bai ji karan Harbi Biyun Da sukayi ba.
Abun Tsausayi Suna Zuwa Gidan suka ga Get a wangale Hankalinsu ya Tashi ai basu Rude ba sai da suka ga gawan Maryama da Abdullahi kwance afarfajiyan Gidan cikin Jini Sai Zuciyoyi Suka Raunana Idanuwa Suka Zubda Kwallah Su Nene sun Rude matuka ga Halin da Suke Ciki ga mutuwar Maryama da Mijinta Sun Rasa Ina zasu Tare Hawayensu ne,Wanda ke zuba ba kama Hannun Yaro ganin Alhaji Usman baya Cikin Hankalinsa ne yasa aka Tattarashi Zuwa asibiti Dr.Saulauwa ya Kira yan Sanda suka zo Suna Ta Binciken gawan su Maryama Abun gwanin Ban Tsausayi Hajiya mama Kuwa Ta Rude sai kuka Take tsakanin ita dasu Nene an Rasa mai bama wani Hakuri.
Sai da yan Sanda suka gama Bincikensu kana suka Tafi da Cewar Insha Allahu za"a kama Yan Fashin da sukayi wannan aikin Sai alokacin Dr.Saulawa ya iya Kiran Chan Gada suma ya Sanar dasu wannan Mugun labari Fadar irin Tashin Hankali da Suka Shiga bata baki ne Mota Guda sukayo suka zo Goggo Halima da Hajiya Mama suka Yi ma Maryama Sallan gawa yayinda Wasu mazan Daga Gada sukayi ma Abdullahi wankan gawa aka Sallacesu Zuwa Gidansu na Gaskiya Allahu akbar.
Duka da su Bashir akayi Sallar gawan Domin Duk sunzo Hannatu ne kadai bata zo ba Ammh Rukayyah itama ta iso Tuni Zukata suka Raunana Sai ma in ka Tuna da Ciki Maryama ta koma ga Allah ga Yarta Karama wacce ko Shekara Biyu bata gama kaiwa ba Sai kaga yadda Zain da zareena da Haddir suke kuka Kamar Ransu zai Fita Duk da Suna Yara sun Fahimci Mama Maryama da Abdullahi Sun Tafi Tunda Hajiya Mama Ta gayamusu sun Tafi inda ba Dawowa Umman Zareena Goye da Zafira Zain kuma ya kama Halima ya kamkame yana kuka Abun gwanin ban Tsausayi.
Anan Gidan Alhaji Usman aka yi Karban gaisuwa Duk da Shi yana asibiti sai da akayi uku ya Dawo Gida Domin ba Laifi Ya Daku Allah yasa ba karaya sai Gocewar Kashi,Shi kanshi Yayi kuka Zuciyarsa ta Raunana da Wannan Mummunar kaddaran Data Fada musu,Sai da akayi bakwai kana yan Gada sukayi Shirin komawa nan Goggo Halima tace abata Halima ta tafi da ita ta Riketa,Tana ta kukan Bayan Maryama Bata da kowa Duka iyayensu Sun Rasu Su bata ita ko In ta ganta zata Dinga Tunawa da ita Da Farko Dr.Saulawa ya karbi Rokonta yace Umman Zareena ta Hadoma Halima kayanta ta bama Goggonta Tatafi da ita Umma Sai ta Fara kuka Tana Rokon Itama abar mata Ashe Zain yalura Da Sanda Goggo Halima Ta karbi Zainarsa Sai ya Fara kuka yana Kokarin son Karbanta Duk yadda akayi Tunanin Abun ya Wuce wasa Dr.Saulawa yabama Umman Zareena Hakuri yace Ta barma Goggo Halima Rikon Halima Tunda Ita ga Zafeera ma Tana Raina Hakanan ta Hakura Tana ji Tana gani Ta Hado kayanta tabama Goggo Halima Dakyar Aka Rike zain wanda ke kuka yana Birgima kan ba"a Tafi da Zainarsa ba Ganin Har Goggo Halima ta Shiga Mota sai Numfasa ya Fara Daukewa kafin kace kwabo ya Suma Wannan Dalilin Shi Ya Hana Goggo Halima ta Fasa Tafiya da Halima ta Sauko Ta Damkama Umman Zareena ita tana kuka Tana Fadin'Naga Soyayya da kaunar Halima I idanuwan wannan yaron Tun Ranar datazo Duniya..Bazan so na Raba wannan kaunar ba..Gata Hajiya Fatima Allah ya baki ikon Riketa da Amana..!
Ba wanda Baiyi kuka ba awajen Zain kuwa yana Farfadowa Daya ga Zainarsa sai ya Karbeta ya Rumgumeta yana ta kuka Zareena da Haddir ma suka Taru Kusa Dashi Suma Suna kuka ahaka yan Gada suka koma Chan garinsu daDacin Mutuwar Maryama da Abdullahi.
*Comments
*Share and vote*
*Janafty...*
*Intelligent writer"s asso..*
*ZAINAZAIN..!*
_(Is a love Story and Betrayal)_
*Wattpad:Jamilaumar351*
*Mallakar:Janaftyshakira*❤️
*BOOK 1*
0️⃣6️⃣
"Haka Halima Zaina Tatashi Ta ganta a Hannun Iyayan Rikonta,Musamman Alhaji Usman Daya kasance Kamar Uba Gareta Umman Zareena Ta zama Tamkar Uwar Data Haifeta Da Cikinta Saboda yadda Take Nuna mata kauna.
Alokaci Daya Suka Taso Su Uku Halima,Zafeera da Umar Faruq Duk da Ta Girme musu da Wasu Wattani Sun kawo Ta Girma Tunda Ita Haka Allah yayi ta mai karamin Jiki ce,Tunda Halima ta Fara Wayau Ta Fara Cin karo da matsancin Kauna Da Soyayyah da Zain ke Nuna mata Tun yana Lokacin kuruciya Shiyasa Ta Fara Bude Ido Dashi Duk Gidan Bayan Umman Zareena Halima Bata yarda da kowa ba Sai Zain Ko Makaranta Da karfi Da Yaji aka Sakasu Suna da Shekara Biyu da wani Abu basu Cika uku ba Saboda kukan da take yi Duk Sanda Zain zai Tafi makaranta ya Barta Wannan Dalilin yasa Alhaji Usman ya Saka su Nursing Section Saboda dai Halima da Zain su kasance Waje Daya Hakan kuma ba karamin yima Zain Dadi yayi ba ko achan makaranta Da ya samu Faraga sai ya Leka ajinsu Halima Lokaci kalilan Su kansu yan Makarantar suka Shaida Halima zaina yar gatace kuma Ta gaban Goshi a Wajen Zain
Kwanci Tashi ba Wuya awajen Allah...Yau da gobe bata bar komai ba Gashi Har Su Zain Sun kamallah Secondary School Dinsu Lokacin Zain nada Shekara 19 aduniya shi da Zareena da Haddir,ayayinda da ita kuma Zainarsa Take Cikin Shekara na Tara aduniya ita dasu zafeera Zuwa Lokacim kuma Abubuwan Duk Sun karu an samu Cigaba Sosai Ta Bangaran Haihuwa Nene Ta kara Haihu Yarta Mace mai Suna Zainab Wacce Tsakaninta Dasu Halima ba Nisa,sai Umman Zareena ta kara yin Bashir Wanda Suke Kira Junoir sai na Karshen Allah ya bata Ya mace Wacce Tacii Sunan Saudart.
Ayayinda kuma Bashir Wanda Suke Kira Da Baban kaduna Bayan Sadiq karami Sai Kuma Amina Wacce suke Kira Hajiya,sai Karaminsu Muhammed Amin,suna Kiransa Amin Kawai,Aliyu kuma Wanda Suke Kira Dadyn Abuja kuma Bayan Hamdiya,Ta kara Haifan Waleeda da Kuma Lauratu,yayan Su Inna Rukayya Ta kano da na Inna Hannatu dai ba Wacce Tayi Aure Dayake ya"yan nasu suna karatu mai Zurfi ne.
Zuwa Lokacin kuma Girma ya Fara kama Dr.Abubakar Saulawa,sai ya Damka Ragamar komai a Hannun ya"yansa Asibitinsa kuwa ba koda yaushe yake samun zuwa ba sai dai ya Damka Amanar komai Hannun Amintattun Likitocin Dake Asibitin Suna aiki..sai kuma Burinsa kan Jikikinsa Guda Biyu Haddir da Zain Wadanda suka ce zasu Karanci aikin Likitanci ammh kuma Bangare Dabam Dabam Wannan Abun yafi komai Mai Dadi Farincikinsa sai da ya kasa Boyuwa,Yana ji acikin Ransa ko ayau ya Fadi ya bar Gidan Duniya Allah ya Cikamai Burinsa.
Halima Tataso ba Hannun iyayenta ba ammh Babu Abunda Ta nema na Rayuwa ta Rasa,Umman Zareena,Nene, Zain,Da Alhaji Usman Kowa Sonta yake Kada Hajiya Mama Taji Labari da Dr.Saulawa Wanda Jikokinsa Ke Kiransa Alhaji Tsoho Har Duka ya"yan sa Suma sun kama ganin Girma ya kamashi Har ya Fara Farin gashi.
Ashekarun Halima Tara aduniya Ta Fahimci Tsanatsanin Son da Zain yake mata,Domin Tun kafin takai Haka Komai nata Zain ne,Tun Tana yar Shekara Biyu Tare suke kwana Shi ke bata abinci abaki Yayi mata wanka komai Shi yake mata ko Su Nene sun ce ya bari sai ya saka kuka Dole suka Kyaleshi Itama ta Bude ido da Wannan Kaunar Nashi ne Da Allah ya sakamai Tun Tana Cikin Mahaifiyarta.
Tun Tana yar Shekara 5 aduniya Zain yake kiranta da Firstlove Dinsa,itama kuma Sai Take Kiransa da Hakan,Duk wanda yake Cikin Wannan Ahalin ya Shaida wannan Kaunar Dake tsakanin Halima da Zain,Sai da Zain din ya Fara mallakan Hankalinsa ya kai Matakin Shekara Sha Hudu Umman Zareena ta Hanashi kwana Daki Daya da ita Saboda Halin Rayuwa Da Farko ya Nuna Fushinsa Sai da Mganata takai kunnan Alhaji Tsoho ya Kirashi yamai mgana kana ya Hakura Zainarsa Ta Daina kwana Dashi Shakuwa ce Wacce Bata da Karshe ta Shiga Tsakaninsu in Daya bai Ga Daya ba,ba kwanciyar Hankali In Daya na kuka Daya zai Fara ne komai nasu dai Daya ne in Daya ya samu Abu Toh bazai iya ci ba sai da Daya Suna Kara Girma Tsananin kaunarsu ga Juna na kara Tasiri acikin Ransu kuma Duk Wanda ke Tare da Zain Dole yasan Labarin Halima matarsa ko da Mutum bai Taba ganinta Ba ba"a zaman Minti Biyar Dashi bai ambaceta ba Haka Islamiyansu da Suke Zuwa Sai da Hukumar Makaranta ta kawo karar Zain kan yana Zuwa ajinsu Halima yana Daukanta zuwa ajinsu Baya barinta Tayi karatu Dalilin Haka Umman Zareena ta Saka aka Cire Zain din da Haddir da Zareena aka Sauya musu islamiya Saboda Zain ya samu kwanciyar Hankalin yin karatu Shima Din sai da aka Sha Fama Dashi kana ya Hakura ammh da yace Bazai bar makaranta ba Sai dai in inda aka maidasu Din Su koma Tare da Zainarsa.
In Homework aka bata Amakaranta Shi ke koyamata Komai in bata gane ba kafin Ta Fara Ma Umma mgana Shi zata Fara nema,Dama gashi da kwalkwalwa Zain irin yaran nan ne masu kaifin kwalkwalwa da Kokari Ita kadai yake koyama Karatu,Zareena Tayi ta Jin Haushi Shi kuwa Haddir Baya Damuwa,Tunda bamashi ba kaf abokansu na makaranta Sun san da Zaman Halima amatsayin matar Da Zain zai Aura in ya Girma ya gama karatu,Saboda koda yaushe ko kuma a ina ya zauna Bai da Labari sai nata Allah ya Riga ya Dasa wannan kaunar junan a Tsskaninsu.
Lokacin da sukayi Candy Zain yana Gida Tunda Batare da Saninsu ba akayi musu Cukun Cukun Fita Aborad Su Dora karatunsu Zareena kuma Alhaji Tsoho ya Hana yace ta zauna agida Nageria Tayi karatunta,Zain ya gama Sakankancewa ATBU bauchi zai yi Saboda Bayason Nisa da Zainarsa sai dai kuma Yaga Sabanin Hankalinsa Domin sai da komai ya kamallah Suna gabda Tafiya Shida Haddir suka Tsinci Labarin.
Haddir Kadai yake ta Murna Banda Zain wanda ya Fara cewa Shi ba Inda zashi Saboda Zainarsa Tun ana Dauka Wasa ne Har aka ga Da gaske yake Ganin Yaki ce shi bazashi ba yasa Baban Kaduna yazo Har Gida yana ta yimai Fada Daga baya kuma ya koma Lallashi ammh Sai da akayi mai alkawarim Daya Dawo Bayan ya gama Karatunsa Za"a Daura musu Aure da Zainarsa kana ya yarda akwanakin da suka Rage musu na Tafiya duk batasu yayi wajen Sallama da Zaina da kuma Daukan ma Juna alkwarinka da kuma Sharadai Sharadai masu Dama Da ba wanda ya sani sai shi sai ita Duk da Tana da karancin Shekaru ammh Ai tasan mai Sonta Ta kuma Shaku Dashi Tayi kuka Sosai Lokacin da zasu Tafi Ammh sai ya Lallasheta da Fadin Ta tsaya Tayi karatu Dakyau In ya Dawo Zai Tafi da ita Bayan An Daura musu Aure suje chan su zauna Allah Sarki Rayuwa Suna Makarantar Ranar Wata Talata Jirginsu Zain da Haddir ya Daga zuwa London Ta Abuja ya Tashi In da suka samu Rakiyan Dadyn Abuja da Mommy Iklima Sai Zareena Wacce tasha kukan Rabuwa Da yan"uwanta wannan Shine karo na Farko da zasu Rabu da juna Tun Bayan Haihuwansu....
Itama Din Tafiyarsu ba Dadewa Ta Tatattara zuwa Zaria Inda Ta Fara Karatunta na Aikin Jarida Wato Mass Com,a nan cikin ABU zaria Cike da kewar yan"uwanta Wanda suka Riga suka zama Jikin jikin Juna,Hakuri kawai Take Tinda Daman ko ba Karatu akwai Aure wanda Dole zai Rabasu.
Sai bayan Tafiyarsu Su Umma Da Nene suka Fahimci Yadda Shakuwa tayi mugun Shiga Jikin Halima Domin kwana Take kuka Tana Kiran Sunan zain Dalilin Haka sai da tayi zazzabi Harda kwanciya a asibiti Da aka Sallamota Sai ta koma Shuru Shuru bata Mgana sai dai ka ganta ta zauna Tayi Tagumi Kawai Chan kuma sai ta Fara kuka Sai a Hankali a Hankali Ganin Zafeera da Faruq suna Kokarin Janta ajiki Saboda ta Saki Jikinta da Ita kanta Umma da Abba Wadanda basa Son ganin Damuwarta Da akayi Hutun Makarantar Wannan Shine karo na Farko Da taje Gada Tayi musu Sati biyu ta Dawo,Domin Lokacin da Zain yana nan Baya barinta Taje ko"ina in ma Abba ya matsa Dakyar yake yarda Suje da ita tayi kwana Daya Su Dawo Goggo Halima Ta gaji da Mitan ta Zura ido Ammh Bayan Tafiyar Zain sai Alhaji Tsoho yace Taje chan Tayi musu Hutu Saboda yan"uwa su ganta Koda Taje Din bata wani Sake ba Duk da tasan Sune Dangin Mahaifanta ammh kuma Rashin Zain a gareta Tamkar wani Gibi ne na Rayuwarta.
******
Rayuwar Haddir da Zain a Jami"ar Oxford Universty London Tasha Bambam Domin Dama ko Ahalayya da na yau da kullum Suna da Bambamci Haddir Mutum ne mai Mugun Zuciya Kuma So Silent gashi bai Cika Shiga Shirgin mutane ba,In ka ganshi ya Sake to da Dan"uwansa Zain ne,Duk da ba Abu Daya Suke karanta ba,Shi Zain yana Bangaran Gyneacologist ne,ayayinda Haddir yake Bangaran Paediatric ne,ammh yanzu Suna Hade ne sai Tafiya Tayi Tafiya ne kowane Bangare zai Ware kanshi.
Tun Zuwansu Makarantar Basu Dade ba Sunan Zain Usman Abubakar Saulawa yayi Fice Saboda Zamowarsa Guru a bangaran Kokari Shi kanshi Haddir ya sani bai kama kafarsa ba Dalilin Haka sai ya Sanu Tarin Masoya da abokai kana kuma gashi Handome Matashin yaro mai Kokari,nan da nan ya Shiga Ran maza da mata kafin kace me Zain ya Shiga Click na mata da Maza ba Adadi Tunda Gaskiya Haddir yafishi irin wannan kamewar Ammh Shi Zain yana son Rayuwa da Jin Dadi.
Tun Farko Sai da Haddir yamai mgana kan ya maida Hankali ga Abunda yakai su Ammh Zain bai Ji ba,sai ma yayi Biris da Mganar Haddir din yana Ganin ai yana ganin Karatunsa bazai Hanashi Jin Dadin Rayuwa ba,Ganin Haka yasa Haddir ya Fita Batunshi Saboda karatunsu ba Koda yaushe suke samun Kiran Gida ba Sai bayan Wasu Satittuka Dama Shi Zain Ba da wanda yake waya sai Halima Waya Dakeki..? kina cin kaza..? Kin yi kuka..? Umma na baki madara..? Tambayoyi Dai gasunan sai Ta Rasa wanda zata amsa mai ma aciki Dama Shi yana Kiran Gida ne saboda ita Domin Duk Duniya bayan Iyayensa Itace agabansa kuma aransa.
Ko achan London zaku yi mamakin yadda Sunan Halima yayi Fice Sau Tarin Abokan Zain Turawan Suna mai lakabi da ZAINAZAIN ne kuma yana Jin Dadi Baya jin kunyar yace musu matarsa ce da zai Aura da zarar ya gama karatu ya koma Gida Shi Ba mutum bane mai ijiye Sirri A"a indai ya Hadu da kai ko na
All Chapters
Chapter 1
Chapter 2
Chapter 3
Chapter 4
Chapter 5
Chapter 6
Chapter 7
Chapter 8
Chapter 9
Chapter 10
Chapter 11
Chapter 12
Chapter 13
Chapter 14
Chapter 15
Chapter 16
Chapter 17
Chapter 18
Chapter 19
Chapter 20
Chapter 21
Chapter 22
Chapter 23
Chapter 24
Chapter 25
Chapter 26
Chapter 27
Chapter 28
Chapter 29
Chapter 30
Chapter 31
Chapter 32
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 6 Chapter of 32