Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
Jiki ta Cigaba Da Fadin"Wai itama cemin Tayi bata sani ba..Zahirinka ta sani ba Badini ba ammh Tana da kyakyawan Shaida akan ka..Firstlove kalaman Laila dana Zafeera suna min amsa kuwwa acikin kunnina sun sakamin Raunina ina Ji ajikina in Hakan Ta Faru wani Hali zan Shiga..? Wlh zan iya kashe kaina indai na Wayi Gari Zaka barni Saboda Wata Firslove..! Ta karishe Fada Cikin kuka kamar Wata karamar yarinya kana ganin yadda Take kukan zaka san Daga karkashin Zuciyarta yake Fitowa Da Sauri Zain ya mike Daga Inda yake ya Isa gareta ya saka Hannu ya Dagota Tsaye Cikin Wani Sanyi Jiki dana Zuciya yake Fadin"Kinga Firstlove..Stop Craying..Kinga Mganar Zafira Data Laila Hasashe ne kawai Zainata Bazai Taba Faruwa ba..! Yafada yana Dauke mata Hawayenta Da Tafin Hannunsa Cikin Tsuramai ido Tace"In Hasashensu ya zama gaskiya fa Firstlove..? Tafada Cikin Kuremai Idanuwanta masu Cike da wani Rauni da neman Tallafi Jikinsa ne ya kara Mutuwa Sai kawai ya kauda Kansa Lokaci Daya Ya Jawota jikinsa ya Rumgume ya kamkameta yana Sakin Zuciya kamar wani karamin yaro Itama Jinta acikin Jikinsa yasa kawai ta Kara sakin kukan Dake Cin Ranta Tuni Shi kuma sai aukin Shafa bayanta yake Cikin Sigan lallashi kafin ya Dagota ya Share mata Hawaye yana Fadin"Kin yarda Dani..? Kai Tsaye Tana kallonsa Tace"Sosai ma Fiye da yadda na yarda Dakaima ma kuwa Firstlove..! Cikin wata murya yace mata"To indai kin Yarda Dani ki saka Ranki Har Abada ni Zainullahi bazan Taba barinki saboda wata ba..Duk Duniya mace Daya nake so kuma kece..Bayan ke ba Wata Firstlove mganar Laila da Zafeera kuma Suna Dora mizanin Haka kila sun ga Wani Abu ya Faru achan wani waje da Nisa wanda bamu da alaqa da Hakan Ki daina Kokwanto akaina Kinji Insha Allahu ko Mutuwa Tare zata Daukemu..! Ya karishe Fada yana Sakar mata manyan Idanuwansa Sun Dade suna kallon Juna kafin ta kada kai Tana Fadin"Na yarda Dakai Firstlove...Ina Sonka Abun alfaharina..! Rumguma ya kaima ta Cikin Wani yanayi yake Fadin"nima ina Kaunarki Zainata...! Yake fada yana Shinshinar wuyanta itama makaleshi Tayi Sun Dade ahaka kafin ya Dagota yana Fadin"Kuka ya kare ko..? Kai ta gyada mai bai yi Wata Wata ba ya Dagata Cak yana Fadin"Muje muci Abinci....nagode ma Allah dana iya Shawo kan wannan Matsalan da Zafeera da Kawarki Laila suka so su kunnomin acikin gidana..! Yafada yana yar Dariya itama Dariyan Take kan Cinyarsa ya zaunar da ita bayan ya zauna ya Jawo Filet din Abincin da Cokali ya Fara bata tana karba Har sai da tace ta Koshi kana ya bata Zobo da Ruwa Tasha kafin Shima ta Ciyar Dashi Har sai da ya Koshi suna kamallawa ya Tashi ya Tayata suka kwashe komai suka maida Kitchen jin ana Kiran Sallar Isha'i yasa ya Tafi Bedroom yayi alwala Ita kuma ya Barta Tana kara gyara Kitchen din. Minti Talatin ya kwashe sai gashi ya Dawo Lokacin Har ta sake wanka ta Chanza kaya Zuwa Wata karamar Riga ta Shan a Iska Falo,Suka Yada Zango Ta Nannade ajikinsa Tana Shagwaba Shi kuma yana Biye mata Wayarsa na Gefe Yana ganin Dina nata Kiransa Allah ya Taimakeasa Wayar Tana Silent ne Da bai da kuma amsan da Zai bama Halima in ta Fahimci wani Abu Dama Dayan Layin da suke yawan mgana da Dina Dr.Dogara ya sakamata Saboda in yana Gida tana yawan Kiransa Dayan layinta ne ya Sakamata Dr.Dina kuma ya Tabbata Kiran ta bana alheri bane Halima na kan Jikinsa ya Jawo Wayar ya Kasheta Gabadaya,ya Biye mata Basu wani Dau Lokaci ba Ya Tattarata Zuwa Cikin Bedroom dinsu,chan suka kwakwame Juna Cikin so da kauna Cikin Lokaci kalilan Ya mantar da ita Duka wasu manganun Laila da Zafeera ta saki Jiki kan Duk Duniya ko kowa zai iya Juya mata baya Toh Banda Zain aciki. ***** Washegari Tun Karfe 7:45am na Safe Zain ya Fice,A gida ya bar Halima ita sai 9 take da Lactures,Gida ya Fara Biyawa ya kaida Umma da Nene Koda yaje Abba ya Fita Tun 7 shima yana da Meeting bai jima ba yayi musu sallama ya Fice Daganan Gidan Alhaji Tsoho ya Biya suka Gaisa Bayan sunyi Wasan Jika da kaka Dashi da kuma Hajiya Mama Baba Tabawa tazo Suka gaisa Bai jima ba yayi musu sallama Yana Sauri zai Shiga Cikin Asibitin Kusan Tare suka Shigo Cikin Haraban asibitin da Haddir kusan kuma Waje Daya kowanne ya Faka Motarsa Suka Fito Dukkansu a Tare,Sakamakon yau jumma"a Dukkansu Shigan Manyan kaya ne ajikinsu,na Shadda Fara kowanne kuma ya Daura Hular zanna Bukar Bisa kansa kafafunsu kuma Kamar hadin Baki Duka Suna sanye da Rufaffan takalma ne na Fatar Damisa,Kallo Daya zaka musu kaasan Sudin Jini Daya ne Saboda yadda Suke Diban kama Sai dai Haske kawai da Zain ya Dara Haddir ammh har yanayin Tswonsu da kuma Sumar kansu da kuma Sajen Fuskarsu iri Daya ce Komai nasu Cikin Tsari ne Shiyasa Mata da yawa Suke Zencensu Suna kuma Jinjina ma Tarin baiwar da Allah yayi ma wadanan Zaratan samarin. Da Farko Dauke kai Zain yayi Daya ga Haddir zai wuceshi yana Tusa key din Motarsa Cikin aljihun wandonsa Da Haddir yaga Haka sai ya Murmusa ya Bishi Suka Jera Tare Lokaci Daya yana Mika mai Hannu da Fadin"Assalamu alaika...! Cikin Basarwa ya Dakata da tafiyar dayake yi ya Bashi Hannu yana amsa Sallamanshi Fuska ba Fara"a Haddir bai Damu ba Sukayi Musabaha yana Fadin"Ya gida..? Ya kwanan Halima..? Cikin Son kauda mganar yace"Komai Normal....! Daga Haka ya sa kai zai Wuce Haddir yace"Zareena Tace Tana ta Neman wayarka Bata samu...In ka samu Lokaci ka Kirata..! Waigowa yayi zai yi Mgana kenan Daidai Lokacin Motar Dina ta Shigo Cikin Asibitin Dukkansu da kallo Suka Bi Motar har ta karisa Parking Space ta samu waje ta Tsaya Bata Jima ba ta Bude Murfin Motan Ta Fito Cikin Shigar alfarman na Riga da Sikat na Wani lees mai kyau da Tsari,Dinkin ya kamata Sosai sai karamin mayafin Data yane kanta Dashi karamar Jakarta ce a Hannunta Da wayarta sai key din Motarta Kwalliya ta Chaba Sosai kuma Yayi mata kyau Sosai Sai Tashin kamshi Take kafarta Sanye Cikin Takalmi mai Tsini Ta Fara Taku Daya bayan Daya kowani Sassa na Jikinta na Motsawa Kai Tsaye kuma Inda su Zain ke Tsaye Suna kallonta Haddir Dai Kai ya kauda Daga kasan Ransa yana Jinjina Shedancin Dina Zain kuwa ya kasa Dauke ido Daga kanta Haka kurum yaji kamar wani manadigosu na Jansa Zuwa ga kallonta. Har sai da Ta kariso kusa Dasu yana kallonta ganin yadda Haddir ya kafeshi da ido ne yasa ya kauda kai Lokaci Daya yana Sakin karamin Tsaki Haddir ya kallah yana Fadin'Ok zan kirata..Ok..! Daga haka kawai ya Wuce Cikin Asibitin da Sassafar Dukkansu da kallo Suka Bisa,Shi Haddir kallon Takaichi yake Bin Zain Dashi Ita kuma Dina kallon Soyayyah da kauna Tana jin kamar ta Bishi ta Rumgomsa Saboda yadda yayi mata kyau kwarai yau din da Shigar Jikinsa. Maida Dubanta tayi kan Haddir Wanda ke Kokarin Fiddo wayarsa Daga Gaban aljihun Rigansa Cikin Kissa Tace"Mrning Sir...! Bai kalleta ba ya Juya zuwa Cikin aasibitin Lokaci Daya Yana Fadin"Mrning How are u..? Daga Haka ya Dora Wayarsa a kunni ya Fara mgana kuma yana Tafiya Cije bakinta Tayi Tana kallonsa har ya bace ma ganinta kafin Ta Murmusa Tana Fadin"Hmm baka da yarda Zakayi Watarana Haka zaka ganni agidan ku a matssyin Matar Zain..! Daga Haka itama ta Nufi Cikin Asibitin Cikin Takunta na Goggun mata Tana Shiga Da Dr Imran ta Fara cin karo ya Fito Daga Office din Dr Peter,Da wasu Folder a Hannunsa yana ganinta ya Washe baki Lokaci Daya yana Sakarmata manyan Idanuwansa kamar zai Cinyeta Danya,Ganin haka yasa Ta Zabgamai Harara maimakon Ta Nufi Hanyar Office dinta kawai sai ta Fada Office din Dr Aisha Saboda Gujema Haduwa da Bakin Maye Dr Imran. Shi kuwa Zain yana Shiga Office Dinsa Daman da Folders Din Mutane yaci karo Wata Nurse ta Shigo Tana gaisheshi Cikin Daure Fuska ya Zauna kan kujeransa yana Jawo Folders Din gabansa Lokaci Daya yana Fadin"Wadanan Folders din fa..?cikin girmamawa tace"Na Patient ne masu ganin Likita Sir...Dr Imran yace na Tara maka Su Kafin ka iso..! Karamin Tsaki kawai yaja kafin ya zari Biron Dake kan Teburinsa ya Bude Folder Din Farko yana Fadin"Hannatu Bashir Call her.." daga haka ya Juya yana kallon Folder din matar yana Nazarin Abunda ke Damun matar yar Shekara 41 da wani Abu a Duniya,Da Sauri ta Fice Zuwa Gaban Office din nashi Inda Masu Jiran ganin Likita ke Taruwa takira Sunan Hannatu Bashir wani yaro Dan kimanin Shekara 20 ya Mike Lokaci Daya yana Tada wata mata Dake gefensa Cikin Kulawa Nurse din tace"Itace ko..? Yaron ya Daga mata kai da Sauri Tace"Ok ku Shiga da Sauri Dr.Zain ne bayason Jira..Ku kuma ku Tsaya ayadda na Tsaraku Daga na Daya zuwa na Goma,In wannan ya Fito wannan ya Shiga ku kuma Sauran ku taso muje Nakai Folders din ku Office din Dr Imran ne..! Daga Haka tayi gaba Sauran Majiyanta Suka Bita abaya,Yaron nan kuma ya Shiga da Mamansa office din Dr Zain ya zaunar da ita Shima ya zauna Zain ko Dago kansa bai yi ba ya Fara Fadin"Hawan Jini ke Damunki Mama..! Yaron ne ya bashi amsa da Fadin"Eh likita.." sai Lokacin ya Dago kansa ya Sauke kan yaro na Dan Lokaci kafin ya kada kai yana Fadin"Sannu Mama bari na gwada Bp ki..! Yafada ganin Tana ta Numfashi Sama sama. Cikin kwarewa ya Fara aikinsa ya Gwada Bp Dinta Bayanan kuma yana ta mata Wasu Tambayoyi Tana Bashi amsa,Rubuta mata mganguna Yayi ya basu,yace su dawo nan da 4weeks bayan ya dan bata Wasu Shawarwarin na Rage Tunani Tayi ta mai Godiya Tana Sakamai albarka Cikin Mirmishi yake Fadin"Bakomai Mama Aikinmu ne..! Suna Kokarin Fita ta Sawo kanta Cikin Office Din,Kallo Kallo akayi Tsakanin Matar nan da Danta da Dr.Dina Tabe baki kawai Tayi ta wucesu suma suka Fice suna mamakinta,bai ma san ta Shigo ba ya Dukufa Duba Dayan Folder Dake gabansa Na wata mace ne kamar kuma Zuwanta na Farko kenan,jinjina kai yake Dazu matar da ta Fita bashi ya kamata ya Dubata ba Dr Imran ne,ammh Tunda Fayels dinta ya Fado gabansa kuma ganinta Babba Tayi Sa"ar Nene yasa ya Dubata ammh Shi yafi Duba Wadanda suka Shafi Ciwon mata kamar su Ciki haihuwa,Mtsalan Bari,sanyi Da Sauransu. Azatonsa Itace kai Tsaye yace"Aisha Jarma meke Damunki..? Zan iya Taimakonki..? Yafada kai Tsaye Yana Dora Bironsa Bisa Folder Din zai Fara Rubutu wani Mirmishi Dina ta saki ganin bai Fahimci ita bace Siririyar Dariya ta saki mai kara wacce Har Zain ya Jita da Sauri ya Dago Suka Hado 4eyes yana kallonta Lokaci Daya kuma kamshin mayen Turaranta ya Shigemai Hanci. Cikin Hade Rai ya ijiye Biron Hannunsa yana Fadin"What..? Baki ganin ina kan Duba patient ne Dina..?meke damunki..? Yafada yana Tsare ta da idanuwansa Cikin Kayattacen Mirmishi Tace"Nima Patient din ne Dubani zakayi..! Tafada Tana Kafeshi da mayen kallonta Wani karamin Tsaki yaja kafin ya maida kansa baya bai samu zarafin mgana ba aka Bude Office din aka Shigo Ganin su Su biyu yasa Ta Juya zata Fita da karfi Zain yace"Aisha Jarma..? Bafullatanan ta Daga kanta Tana Fadin"Eh Dakta...! Kai Tsaye yace mata'"Shigo Ciki mana..! Yafada yana maida kallonsa kan Dina Lokaci Daya Yana Fadin"Plz Dina Get out...In ke baki san Darajan aikin ki ba Ni na sani ki Fitarmin daga Office Tun kafin Raina ya Baci..! Mamaki ya Cikata tayi Galala Tana kallonsa Cikin Taushin Murya tace'Buh Zain mgana...! I said get Lost....Ke Dakikiyar ina ce da baki gane mgana..? Ya Katseta Cikin Wata Gigitaciyar Kara wacce ba ita kadai Ta Razana ba Har Bafullatanan Dake tsaye sai da Taja Baya,Daskarewa Dina Tayi Tana Bin Zain da kallo Idanuwanta Sun Cika da kwallah ganin Taki Tashi ne yasa ya Mike ya Nuna mata Kofa yana Fadin"Fita..Fita Tun ina ganin Mutumcinki kafin Sauran Mutumcinki Dake Idona su Zube..Wlh zan saka ayi Miki Wulakancin da in har kika bar cikin asibitinan bazaki so ki Dawo ba Ki Fita nace..! Yafada Cikin Bayyana Bacin Ransa Lokaci Daya Jijiyoyin kansa na Mikewa Ganin haka yasa Dina Ta Mike tana Kallonsa Gefe Daya kuma tana Kokarin maida Hawayen Idanuwanta kafin tayi wani Mirmishi kawai ta Juya da Sassarfa ta Fice da wani katon Tsaki ya Rakata yana Fadin"Shedaniya kawai..Allah yamin Tsari Daga Shedancinki.."! Batulatanan Dake Tsaye ta amsa da Ameen Ameen Saboda ita kanta Dinar bata mata kalan Mata masu kima ba,Komawa yayi ya zauna yana Dafe kanshi kafin yace"Zauna Hajiya..!kai tsaye yana Janyo Fayel Dinta Zama tayi Shi kuma Cikin Zafin Numfashi yace"Meke damunki.? Bayani ta Faramai Shi kuma yana Rubutawa Lokaci Daya yana Jifanta da Wasu Tambayoyi Tana Bashi amsa. Dr.Dina kuwa na Fita Daga Office Din Zain Hanyar barin Cikin aaibitin Ta Nufa Tana Tafe Tana Sharban Hawayen da ta kaasa Hanasu Zubowa,Allah ya Taimaketa bata Hadu da wani Likita ba sai dai Nurses da Metro wadanda ke mata kallon Ko lafiya wasu kuma suka Fara Gulman cewa Dama ai ita ke Bin Dr zain ammh Shi kallo bata Isheshi ba,Ahaka dai ta kai kanta Haraban Ajiyan Motoci Ta Bude Motarta ta Shiga Tayi mata Key idanuwanta Har Rufewa suka Farayi saboda kuka da Bacin Rai Da gudu ta yi Riverse ta Saki Hon aka Wangalemata Get tafice da Gudu Daga Cikin asibitin kamar azata Tashi sama Kai Tsaye Hanyar kano ta Dauka Domin Haka Kurum taji Tana Bukatar Zuwa Gida ko Zataji Sanyi Ko taje wajen zakiya mganar Duk Dayane Wlh zain yana so yayi mata Wulakanci kuma Wlh karyansa,Tana Tsausayamai bataso komai ya kwacemai ammh zai Fusata tayi Abunda batayi Niyyah ba,Haka tayi ta Sharara gudu kamar zata tashi sama. ***** Yau da Halima Tatashi Daga School Sun gama Lecture da Wuri Wajen 12pm ta Fito Daga Cikim makaranta Sai da ta Shiga Motarta ta Kira Zain Bayan ya Dauka sun yi gaisuwan da suka saba da Tambayan lafiya juna ta tambayeshi Tana so Taje Gidansu Laila Ta Duba Mamarta Bata da lafiya Dazu sukayi mgana da Lailar ganin batazo School ba yasa ta Kirata nan take Shaida mata Mamarta bata ji Dadi ba Batare da wani Tunani ba Zain yace Taje ammh Ta Tuka kanta a Hankali ta kuma kula da Kanta ta kuma Dawo da Wuri Domin Shima Bayan Sallar Jumma"a zai Dawo Gida Da Haka suka Rabu. Laila Suna zaune a anguwan yakubu Wanka ne,Koda Taje Jikim Mamar na Laila da Sauki Tunda Har an Cire mata karin Ruwan Da aka saka mata nan Halima Ta gaisheta da Jiki ta amsa Cikin Sakin Fuska Tana Tambayanta megidanta Daganan Dakin Laila suka Shigo Suna Hira Halima na Fadama Laila Karatun da sukayi a makaranta yau bata wani Jima ba ta mata Sallama ta Tafi da alkawarin gobe zata Dawo ganin yau din Bata Riko ma Mamar Lailan komai ba. Har Wajen Mota Laila ta Rakata Sukayi sallama Daganan Gida ta Koma Tayi wanka ta Shiga Kitchen Tayi Tuwon Shinkafa Miyar agun da Tok Fish Saboda Alhaji Tsoho da Kuma Abba ta Riga ta saba Tunda sukayi Aure Da Zain Duk Jumma"a bata Fashi Sai tayi musu wannan Tuwon Takai musu,Tana kamallahwa ta Saka a kololi guda Biyu Daya na Gidan Alhaji Tsoho Daya na Gida ne,na Abba kenan Sauran kuma ta Zuba ma Tanimu megadi nashi Sauran kuma ta Saka Cikin Wata karamar kula nata Dana Zain kenan Dama Tun Da Tadawo Zobo Ta Fara Hadawa ta saka a Fridge saboda yayi sanyi. Sai dai ta Gyara Kitchen din kana ta Koma Cikin Bedroom Ta Shiga Dama bayan ta Dawo Sai Taga Jinin al"ada yazo mata Tana Cikin Toilet tana Wanka Zain ya Shigo Gidan Bayan ya Shigo Dakin Jinta Tana wanka yasa Shima ya kwabe yabi ta Chan Bayi sai ta ganshi kawai ya Shigo Bata damu ba sanin Dama Yawanci Tare suke wanka nan suka Hadu sukayi wanka bayan an Sha Shafe Shafen Juna kafin su Fito Tare suka Shirya kansu Ita Shigar abaya Tayi Domin Halima Tana son Abaya Sosai Shiyasa Zain ya Cikamata Wardrope dinta dasu Shi kuma wani yadi ya saka mai Santsi Falo Suka Fita suka baje sukayi Dinner kana sukayi Shirin Fita Zain shi ya Dauki Duka Kololin Tuwon Ita kuma ta Dauko na Miya Sai Wani katon Jug da Zobo na Abba ne Alhaji Tsoho baya Chan Zobo,sai da suka kai komai Cikin Booth din Motar Halimar kana ta Koma ta Daukoma Tanimu megadi nashi haka ya Duka Har kasa yana mata Godiya da Kirarin Gimbiya agidan Dakta. Shidai Zain gabam Motar ya kame Saboda yace mata a Motarta Zasu Fita ita zata Tukasu ganin ta Biyema Surutun Tanimu ne yasa ya Fara latsa mata Hon da Sauri ta Sallameshi bayan tace ya Bude mata get da Gudu ya wuce Yana Fadin"Angama Uwargidan Dakta..Amaryama kuma Insha Allahu Daga ke ba kari gimbiya agidan Dakta..! Yafada yana yar Dariya Mirmishi kawai ta saki ta Juya ta Shiga Motar kallonta ZAIN yayi yana Fadin"Meyasa kike Biyema Shirmen Tanimu ne..? Shifa baya gajiya ko kwana zaku yi kuna Mgana..! Mirmishi ta Saki Lokaci Daya Tana ma Motar key Ta tasheta tayi Kwana ta Saki Hon kafin ta Sulala ta Fice Daga Gidan Tanimu na Faman Daga mushi Hannu Shi kuwa Fadi yake"Kai Tirr...Ga Gimbiyar Dakta..Tana Tuka Daktan da kanshi Allah bar kauna Kaji..! Sai da ta Daidata Tafiya kan Titi kana ta Saki yar Dariya Tana Fadin"Allah Tanimu na Tuna min da wani Idi akusa da gidan Goggo Halima Dake gada..Surutunsu da komai nasu Iri Daya ne.."Zain na Latsa wayarsa yace"Kidaina dai Biyemai Zainata..Karki manta ke Matar Dr.Zain ce..! Mirmishi Ta Saki kafin tace"Insha Allahi Zain Dina..! Hannunta Datake Driving yakai ma Kiss Yana Fadin"Nagode zainata..! Hira suka Fara sama sama Cikin Hiran ne Halima ta Kalli Zain Tana Fadin"Firstlove wai yaushe Zamu je Gada ne..? Ina son ganin Goggo Halima bansani ba ko lafiya kwana Biyu ina ta Kiran Layinta bana samu..! Kansa ya Shafa yana Fadin"Ki bari ku samu Hutu mana..Nima Kinga bani da Lokaci ko Weekend ne ina Shiga asibiti.." bata som mai musu yasa Tace"Shikenan Allah ya kaimu.." shi kuma ganin kamar ta Damu yasa yace"Karki damu ba komai..Tunda baki sameta ba ki kira Layin Isuhu mana kiji ko Lafiya..? Da Sauri tace"Kash nako manta da Kiran Ya Isuhu bari mu Daawo zan Kirasa naji ko lafiya..? Kai kawai ya gyada mata yana Cigaba da Latsa wayarsa ahaka har suka kai Gra Gidan Abba suka Fara Zuwa Sun ci sa"a kuma yana Gida Tana Shigowa da Kololi Bayanta kuma zain ne da kulan miya da Jug Din Zobo Nene Tace"Mungode Allah Da zuwanki Halima Domin ga Abbanki nan Duk Abincin da muka gama Jeramai yaki Taba komai yana Jiran Tuwonki..! Zain da Halima suka saki Mirmishi Abba kuwa yana Zaune kan Daya Cikin Kujerun Falon ya Sauko kasa yana Fadin"Allah yayi miki Albarka Diyata..Bani nan Kigani Hannuna Dama Tun dazu na wankeshi ke nake jira..'Gabadaya suka sakamai Dariya Har Umma data Fito Daga Kitchen nan Halima ta Baje komai Bayan Taje Kitchen ta Dauko Filet da Cokali ta Zubama Abba Kin karban Cokalin yayi yana Fadin"Bar ni na saka Hannuna Dashi Annabin Rahma ke Cin Abinci..! Umma na Gefe Tace"Ba Tayi ne Abba..? Kai ya girgiza mata yana kai Lomar Tuwo yana Fadin"A"a fa kuci Abincin ku yau na yafe..Wannan Tuwon Har Dumamen Gobe..'" Su zain Suna ta Dariya nan aka zauna ana ta Hira Halima ta Tambayi su Saudarta Nene tace suna gidan Alhaji Tsoho. Basu bar Gidan ba sai Bayan Sallar La"asar suka isa Gidan Alhaji Tsoho Shima chan Hajiya Mama Nata Fama Dashi yakin Cin komai yana Jiran Tuwon Halima Suna zuwa Hajiya mama tace"Nikam Halima wani Boka kika kai Sunan Mijina ya kamashi haka..? Aka saka Dariya Alhaji Tsoho nacin Tuwonsa yana Fadin"Ba Boka ba Mallam..Yin Allah ne Ko Hali Dubu..? Halima ta Daga kai Tana Fadin"Gayamata dai Tsoho..Kyaleta Kishi Take dani..! Hajiya Mama tace"Nima ai na Rama Domin Zainullahi yanzu Nawa ne.."Halima na Dariya Tace"Wane ke..?Mata ma Dadama sun gwada sun kasa ai Ba wacce ta Isa ne Ni da Firatlove Takalmin kaza kenan.."Zain yace"Kin Fadi gaskiya Zainata.." hararansa Hajiya Mama Tayi Tana Fadin"Au bayanta kabi.." yana Dariya Yace"Toh yana iya Hajja mama..? Ki dau na Annabawa kawai..! Gabadayansu Dariya suka saka Nan suka kai Dare har sallar mangariba nan sukayi suna Shirin Tafiya ne sai ga Haddir da kaya yayo parking din kayansa ya dawo gidan Alhaji Tsoho Zain sai Dariya yakai mai yana Fadin"Wanda Yaja da Likitan kwakwalwa zai ga ba Daidai ba..! Alhaji Tsoho na Zaune yana Sakacen Hakorinsa Daya gama Cin Nama yana Fadin"Kwarai Matukar ina Raye Idanuwana na kan Jikokina Musamman ma Kai da Hadiru...'Haddir bai Tankashi ba Fuskarsa ba Walwala ganin Haka yasa Hajiya Mama da Tabawa suka Rika Tayashi kwasan kayansa Zuwa Bedroom Din Dake kusa dana Alhaji Tsoho Tana Fadin ta Sauya Miji ga Hadiru Yaro Sammari ga kyau ga Kudi me zatayi Da Ragowan Halima. Sai Dariya ake Zuwan Haddir yasa suka Kara Shantakewa sai Wajen karfe 9pm suka koma Gida,Zain yana Cike da Bukatarta Ganin Tana Fashin Sallah yasa ta Lallabashi ta mai Dubarin Datake mai in Tana Cikin Jinin Al"ada har ya samu ya gamsu suka kamkame juna Har Barci mai Nauyi mai Dadi ya kwashesu. *Shakira..* *ZAINAZAIN..!* _(Is a love Story and Betrayal)_ *Wattpad:Jamilaumar351* *Mallakar:Janaftyshakira*❤️ *BOOK 1*             1️⃣0️⃣ *KANO...* _Area:Sabuwar kofa..!_    "Kwance Take Kan mamaken Royal Bed wanda yaji Shinfudun Alfarman,Misalin karfe 10:46am na safe na Ranar Lahadin karshen mako. Motsawa Tayi Ta leko Da kanta cikin katon bargon Datake ciki Lokacin Da Taji Karar Wayarta Dake saman Side Drower din Gadon,Hannu ta zira tana wani yamutsa Fuska Lokaci Daya Ta Jawo Wayar nata ganin Sunan Zakiya Ya bayyana baro baro saman Sreen Din Wayar nata yasa Ta Daga Cikim kasala Tana Fadin "Zakiya yane...! Dagachan Bangaran Zakiya Tace"Kina ina ne nazo naga gidanki a kulle..? Ko kina Cikin asibitin ne..? Wani Hamma Dina Ta tattaro ta sakarma Zakiya Tana gyara zaman Blanket din Data Rufu Dashi Take Fadin"Ina anguwar Sabuwar Kofa...! Cikin Mamaki Zakiya Tace"Kano..? Dakai Dina Ta mata amfani Wajen bata amsa Kafin Tace"Eh ina Kano..Tun Ranar Friday na Taho.." Zakiya Ta gyara Tsayuwarta Jikin Bakar Motar kirar prado Tace"Ke kuwa me kika je yi kano Haka da gaggawa ba Labari..? Karamin Tsaki Dina Taja Lokaci Daya Tana yamutsa Fuska Kafin ta Yunkura ta Mike zaune ta Jinkina Bayanta da Jikin Gadon Lokaci Daya Tana Fadin"Hmm Bari kawai Zakiya Wai ni Zain ya kora Daga Office Dinsa..." Cikin Zaro Ido Zakiya Tace"Kora kuma..? cikin Takaichi Dina Tace"Wlh Korar kare yayi min Ranar friday Dana Shiga Cikin Asibiti,Abunda ya bani Tsoro Shine wani kallon Tsana Danaga Yana Bina Dashi Abun ya bani Tsoro Sosai...! Zakiya Ta saki Tsaki Tana Fadin"Hmm lalle..Ai Indai baki kama kanki ba kina Tare da Wahala Dina...Karki manta Boka Yace Sihirin Dayayi masa fa na Dan anace ne Ko Baki Bishi ba zai Biki Dolensa ammh sai kiyi ta Binsa yana Miki Wulakanci Kuma ahaka ke ki kiran kanki mai aji Mtswwss Wlh,Wannan dai Abunda kike yi Shine Rashin aji mu kuma Abunda muke yi kina ganin Rashin Aji ne Shine ajin Tunda ko Yayane Namiji bai isa ya Wulakantani ba Sai na Juya akalata Tunda bashi kadai bane Namiji agidan Duniya ba.." Cikin Zafi da Takaichin Kalaman Zakiya Dina Tace"Zakiya kin fa sani Ba iya Sha"awar Zain kadai nake ba Ina Tsananin Sonsa Wanda bana iya Jure Rashinsa,Ina so Koda Yaushe ya kasance yana Tare Dani Nima ina Tare Dashi Ina so Na zama wata Bangaran Rayuwarshi Gabadaya zakiya ya zanyi..? Wlh ina Son Zain So kuma mai Tsanani Wanda Domin Son na mallakeshi ban Damu da kowa waye zai Rasa Kimarsa ba, indai Zain zai zama Nawa na har Abada.." Tafada Cikin Fidda Wasu Zafafan Siraran Hawayen Da suka Cika mata Idanuwanta gyara Tsayuwa Zakiya Tayi Tana Fadin"Shawarata kawai zaki Dauka Dina Cikin kankani Lokaci Burinki zai Cika zaki mallaki Zain Insha Allahu..."Kai Dina Ta gyada tana Share Hawayenta Take Fadin"Shikenan Hakan za"ayi Na yarda mu Sare macijin Da Kansa Lokaci Daya Tunda bayajin Roko ballatana ban baki..Zan Dawo Gobe in Allah ya kaimu Asibiti sun Kirani.." Zakiya ta Kada kai Tana Fadin"Ok..Sai mun sake mgana.."Daga haka suka yanke Kiran Dagachan Bangaran kuma Zakiya ta Shige Motarta Ta bata Wuta ta bar Kofar Gidan Dina Ranta Cike da Sake Sake da kuma Hanyar da zasu bi komai ya Daidaita Ita kuwa Bangaran Dina Ture Bargon Tayi ta Sauko

Chapter 10 of 32