Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
Fadin"Haba..? Wane Imran yace Baya Maraba da zuwan Baki kamar Dina da kawarta...U are Higly Wlcm..."Ya karishe Fada yana wani Shafa gemunsa na yan Duniya wani kayattacen Mirmishi Dina tayi kafin Tace"Zuwa nayi yau ka dubani Dr Imran..! Tafada Cikin Son Tabbatar da Abunda Ta Fada kura mata ido yayi yana Fadin"Topha..Meke damunki kuma.? Don naga alaman Idanuwanki sun Fada Sosai..! Yafada yana Jifanta da wani kallo kafin Dina ta samu Zarafin Mgana Zakiya ta Rigata da Cewa"Zazzabi take Fama dashi da Ciwon kai ga kasala da Mutuwar Jiki Amai da Rashin Dadin Baki,mutuwar Jiki da tsinkewar yawun Baki.."Ta karishe Fada tana kallonsa kafin ta maida kallonta kan Dina Wacce ta zaro ido Tana kallonta kai ta gyada mata alamun karta Damu. Maida Hankalinta Tayi kan Dr.Imran wanda ya zura ma Dina Ido kawai yana karantar wani Abu Daga bayanan Zakiya kawarta Kafin ya samu Bakin Mgana Zakiya tace"Wani gwaji kake ganin ya kamata kayi mata Dr Imran..? Sai da ya wani Gyara zama kafin yace"Pregancy Test ya Dace da ita..Domin ina da Tabbacin Dina ciki gareki.."Yafada yana so yaga wani Reaction zata nuna sai yaga bata damu ba illah Zakiya Data kura ma ido Ita kuma kawai sai ta kada kai Tana Fadin"Zamu jira ka yanzu ka bamu Tabbaci..! Tafada tana wani Laso Harshenta Waje,Mirmishi Dr.Imran yayi kafin ya Jawo Wata Takarda yayi Rubutu asamanta Lokaci Daya ya Mike yana Fadin"Ku jira bari naje na kira Wata Nurse ta Debi Jininta..! Da Hannu Zakiya ta Dakatar Dashi Tana Fadin"A"a bama bukatar wani cikin wannan aikin.Kai zaka Dibi Jininta kuma Muna bukatar a Sirrinta Sirrinmu Saboda gudun ajikama aikinmu.."Tafada tana kada mai Hannunta wanda yaji jan Lalle. Kai Tsaye yake kallonta kafin yace'"Na yarda zan Sirrinta Abun.Ammh ni miye Tukwaicina akan Hakan..? Kai Tsaye Zakiya tamike Tsaye ta Fara Taku zuwa gaban Dr.Imran batare da Tunanin komai ba ta Saka Hannu ta Shafa gemunsa zuwa Fuskarsa Tana Fadin'"In komai ya Tafi Daidai..Nice Tukwaicinka Tun Daga Farkon Dare Har karshensa naka ne.."Tafada tana wani kashe mai ido Wata Dariyan yan Bariki ya saki kafin ya kada kai yana Fadin"An gama." Daga Haka ya fice Daga Office Din Jikinsa na Rawa da Sauri Dina Ta Mike tana Fadin"What me kikayi haka Zakiya..?. Hannu Zakiya ta Daga mata Kafin Tace"Shiii..Ba yanzu zaki Tambayeni ba..Ki bari sai mun Fita..'Dole Dina ta koma ta zauna tana maida Numfashi Itama zakiyan zaman tayi,Cikin Lokaci sai ga Dr.Imran ya Dawo Da Sirinji da Allura a Hannunsa nan Take ya Dauki jinin Dina ya sake Fita Shudewar Mintina Hamsin Biyar suna zaman jiransa sai gashi ya Dawo Da Farar Takarda ya mikama Zakiya yana Fadin"Ga Tabbaci nan Saura nawa Tukwaicin yaushe zan karba...? Karba zakiya tayi ta Bude Ta karanta ta gani Mirmishi ta saki ganin Sunan Dina maimakon Dina Gaddafi Sheerif sai aka Saka Dina G Sheerif kuma Sakamakon Iri Daya ne Dana Dr Yusuf Cikin Sati5 da kwana Biyu,Dagowa tayi Tana kallon Dr.Imran kafin ta mikama Dina Takardan Tana Fadin"Sai nan da kwana Biyar ko Shida zan nemeka da kaina..! Zai yi mgana ta Dakatar Dashi Lokaci Daya da mikamai wayarta Tana Fadin"Sakamin Lambarka In baka sabamana alkawari ba nima bazan saba maka ba.."Karba yayi ya saka mata lambarsa ya mikamata yana Kallon Dina a karkace bata Bashi Fuska ba ta Mike kawai Tayi gaba Zakiya tabi bayanta tana kada ma Dr.Imran Yatsunta Har suka Fice yana Binsu da Kallo,komawa yayi ya zauna yana wani Tunanin ya sani ba Tun yau ba Dina na Harka da maza ammh bai zata Haka ta zama wawiya da wayanta da Iliminta Itafa Likita ce Taya zata zauna ta bari Har tayi Ciki..? Ya fara Tunanin anya ba wata aksa ganin Daga ita har kawar tata basu nuna wani Damuwa ba kamar ma sun san da Ciki ya Dade yana Saka Abubuwa ganin bai gano komai ba yasa ya watsar da komai Murnansa Daya zai More da zakiya Gefe Daya na zuciyarsa na kara kwaidaita masa Dina Domin Har ga Allah yana Sha"awarta kuma yana da Burun ya kauda wannan Sha"awar koda na Dare Daya ne. Zakiya bata ma Dina mgana ba sai da Takaita Kofar gidanta kana ta Dauki Result din Da Dr.Yusuf ya basu ta mikama Dina Tana Fadin"Wannan zaki nuna ma Zain bayan kin kirashi yazo kin gayamai kina Dauke da Cikinsa..! Dina Ta kalleta Tana Fadin"Miye Manufar hakan.? Zakiya tace"Manufofi da yawa ne Dina..Yanzu ki Sauka kije gida kiyi wanka ki Sauya kaya Sai Ki kira Zain kice yazo Kina son mgana Dashi Da Daddare in ya nuna Bazai zo ba ki Turamai Sakon ko yazo ko kuma ke ki biyoshi Gidansa na Tabbata Dayaji Haka zai zo,Sai ki nuna mai wannan sakamakon Zai Firgita kuma zai yi Challaging dinki kan kin Shirya wani Abu ke kuma sai ki nuna mai baki Shirya komai ba in ya gama Rudewansa zai nemi ki yarda azubar da Cikin,karki gaddama Ki yarda da cewa zaki Zubar da Cikin.! Dina Tace"Na yarda fa kika ce..? Kai ta kada mata Tana Fadin"Eh ki yarda mana..Ammh na iya baki bai kai Zucci ba.Nasan zai ce ki bari da safe zai koma gida yana Tunanin mafita kuma Tabbas da Safe zai dawo yace ku Tafi wani asibiti azubar da Cikin.."Ta Dakata Tana kallon Dina kafin Ta Cigaba"Kafin yazo mu kuma mun Tsufa a kano zaki kashe Duka wayoyinki yadda bazai Taba samumki ba..Ke kuma Yau Da kinga Zain ya Shigo Gidanki ki Kirani awaya ni kuma zanyi Sauri na Daga Wayar na sakata cikin Recording Zan ji Abunda yake Fada Gefe Daya kuma ina Nadanshi a matsayin Hujja kin gane..? Kai Dina Ta Jinjina Tana Fadin"nagane ammh baki Tunani  yaji wayata akashe bazai yi wani Tunani ba..? Zakiya tace"Zai yi mana Lokacin yana Rudene..zai yi Tunanin wani Abu ammh kafin Tunaninsa yaje mai kan plan dinmu komai ya kamallah Sai dai kawai Bom din ya Fashe Bumm...! Tafada tana Dariya Dinar na Tayata sun Dade Tana kara Fada mata mganganun da sata gayama Zain indan yazo kafin su Rabu Ta sauka ta Bude Gidanta ta Shige ita kuma ta Sakar ma Motanta Wuta ta Fice Daga Wajen da Gudu. ****** Zaune yake akan kujera mai zaman Mutum Biyu,Zaina kwance Gefensa Tayi Matashi da Cinyarsa Tana sanye Cikin Wasu Riga da wando na Barci Masu Taushi Sun lafe ajikinta,shi kuma Dagashi Sai Boxers wasa yake da gashin kanta Suna Hira Cikin so da kauna. Lokacin Dare ne Domin Wajen 9 pm na Dare ne har ma ta wuce,Bai Dade Da dawowa Daga asibiti ba yayi wanka sukaci Abinci kana suka yada Zango a Falo suna Hiran Ma"aurata mai Dadi. Juyo da kanta yayi Yana kallonta Ido Cikin ido yace"Firstlove kin kara Haske fa..? Mirmishi Tayi Tana Fadin"Haka kowa ke Fadi...Umma Dazu haka tacemin Dana Biya bayan na Dawo makaranta.."Kumatunta Yaja yana Fadin"Har da kiba ma kin kara kalli kumatunki kin zama Zaina bombom yanzu fa..'. Yafada yana Dariya Itama Dariyan Take Tana Fadin"Haka Ukti tace Jiya da mukayi VD call da ita.."Kiss ya sakarmata agoshi yana Fadin"Naji Dadi..Abba Da su Umma zasu gane yanzu nafisu iya kiwo Tunda Gashi kinyi kiba.."Yar Dariya Tayi Tana Damke Hannunshi Cikin Kura mai Ido Tace"Firstlove..! Asama yaji Sunan ya kalleta yana Fadin"Umh menene Zainazain.."Ajiyar rai ta Sauke kafin tace"Kwanakin nan ina yawan Fama da Faduwan gaba..Sai ina ji ajikina kamar zan Rasa wani Abu Daya zama mai matukar amfani agareni.! Ido kawai ya sakarmata yana kallonta har tagama mgana kafin ya Saka Hannu ya Tadata ita Kan Cinyarsa ya Sauketa Lokaci Daya ya saka Hannuwansa ya Zagaye Kugunta Dashi yana Fadin"wa zaki Rasa Firstlove..?Nine nafi komai Muhimmanci gareki kuma Bazan Taba barinki ba Har Abada..". Tana kallon kwanyan Idanuwansa Tace"Mutuwa fa..In mutuwa ce fa ya zakayi..? Fadin Haka yasa sai Jikinsa ya mutu,Kawai sai ya lafe Ajikinta yana Fadin"Ki daina wannan mganar Firstlove ko mutuwa ce Insha Allahu Tare zataDaukemu Wani baazai mutu ya bar wani Cikin Tashin Hankali ba Kinji ko..? In kin kara Jin Faduwar ba kiyi ta Maimaita Hasbunallahu Wani'imal wakil.."Tana Daga Jikinsa ta gyada mai kai Tana Fadin"To Firstlove na Daina kuma zan Dinga yi insha Allahu..! Matseta yayi yana Fadin"Nagode My Wife...Allah ya barni Dake har Mudin Rai ta amsa da Ameen,Sun Dade ahaka kafin Ringing din wayarsa ta katsesu,Saussauta Rumgumar da yayi mata yayi Lokaci Daya yana jawo wayarsa Dake gefensa Sunan Dina Daya gani Tana Kira sai da gabansa ya Fadi Sororo yayi kawai ya kasa Daga Kiran ganin haka yasa Zaina ta waigo Tana Fadin"Ba kiranka ake ba..? Yake yayi yana Fadin"Sharesu Daga asibiti ne..' Da Sauri tace"A"a bazai ayi haka ba in wani Abun gaggawa ne fa..?ka Daga ni bari naje Kitchen nayi kaye kaye na Dawo.." Tana gama Fadar haka tatashi Daga kan Jikinsa ta wuce Kitchen sai da yaga ta Shige kana ya Tashi da Sauri Dauke da wayarsa ya Shige Bedroom dinsu ya Turo Kofa yana Kokarin Kiran Dinar sai gata ta sake Kira da Hanzari ya Daga yana Fadin"Why Dina..? Baki san ina gida bane so kike Firstlove ta Zargi wani Abu..? Dagachan Bangaran Dina Tace"Kiran yana da Muhimmanci ne...Ina son ganinka ne yanzu yanzu..! Cikim mamaki yace"Yanzu yanzu kuma..? Kan wani Dalili Kuma kinsan na dawo Gida.."Yafada yana waige waige na Marasa gaskiya. Dina tace"Eh mgana nake so muyi mai muhimmanci..."Kai tsaye yace mata,"Ki Barta sai gobe da Safe..Gaskiya yanzu ba zan iya Fitowa ba Basan wani karya zan yi ma Firstlove ba gaskiya.." Mirmishi Dina Tayi Tana Fadin"Allah ko..? To ka zauna ni sai na Taho gidanka yanzu na Sameka.." ido ya zaro Waje kamar yana ganinta yace"What.? Kizo ina..?Kai tsaye Tace"Gidanka mana in yaso sai kama Firstlove din Taka bayanin in Taganni adaidai wannan Lokacin.."Da Sauri yace"baki da Hankali ne..? Dina tace"Ina dashi..Kazo gida ka sameni yanzu ko kuma Wlh ni nataho yanzu.." Jin Haka yasa yace mata"Is Ok karki zo ganinan zuwa.."Mirmishi Ta saki kafin tace"Gud.."Daga haka ta katse Kiran Tana Dariyan Mugunta Zain kuwa Zufa ce ta Shiga ketomai Ya Fara safa da marwa Cikin Bedroom din ya Rasa mafita kawai sai ya hau Saka kaya Wata Milk din Jallabiya kawai ya saka ya Dau key Din Mota ya Fito yana Fito suka Hade Da Zaina ganinsa a gaggauce yasa Taja ta Tsaya Tana kallonsa Cikin mamaki tace"Lafiya..? Karamin Tsaki yaja yana Fadin"Baza abar mutum ya Huta ba Dai...Bana ce bazan Daga wayata ba..Kikace na Daga Kira ne Daga asibiti An kawo Emegency wata mata ce zata Haihu sai Bleeding take.."Ya karishe Fada yana Kauda kai Domin yana Jin kunyar karyan Daya Shararamata ita kuwa Cikin Tsausayawa tace"Wayyo Allah sarki har na Tsausayamata..Bakomai Firstlove kaje zan Jiraka Ina Alfahari dakai..' Rumgumeta yayi tare da mata Kiss a goshi ya wuce tana Binsa da addu"an dawowa lafiya baya Cikin Natsuwarsa yana Fita ya Rika kwalama Tanimu maigadi Kira cikin Tsawa yace ya Bude mai Get Tanimu jiki na Rawa ganin Dakta Rai bace ya Budemai get din ya Fice da Gudu kamar zai Tashi sama Kai Tanimu ya girgiza yana Fadin"Allah Huci Zuciyar Gwarzom maza.." Lokaci Daya yana Maida get din Ya Rufe ya koma kan kujeransa ya zauna ya Dauki Radionsa ya kara Sauti Abunsa Ransa fes babu Abunda ya Dameshi. Shi ko Zain yana Fita ya Dinga Tsula Gudu Bisa Titi kamar zai Tashi Sama,Cikin Lokaci kadan sai gashi kofar apartment din Dina Ita kuwa Dama Tana Jirace Dashi Tana Jin Dirin Mota ta leka ta Window falo Tana ganin Shine ta Dauki Waya da Sauri ta Kira Zakiya,Tana Dauka Ta gayamata isowarsa ita kuma tace Ta bar waya akunne,Saman Center Table din Dake Tsakiyar Dakin ta ijiye wayar Da Sauri Ta Shiga Cikin Bedroom Dinta ta Dauko Result din Da Zakiya ta bata tazo ta ijiyeshi Saman Kujera,Daidai Lokacin Taji Zain na Knooking din Kofar nata Bedroom din ta ta koma ta Samu Robe ta shafa kasan Idanuwanta nan da nan Hawaye suka Fara zubo mata ba kama Hannun yaro Idanuwan kuma suka kumbura luhu luhu kamar wacce Tasha kuka gashi Sun sauya Launi. Jin yana ta knookig ne yasa ta Fito Da Sauri Zuwa Falon ta isa ga Kofar ta Budemai Suka kalli juna Cikin mamaki yake kallonta ganin yadda Hawayen Idanuwanta suka Kasa Tsayuwa Cikin Mamaki yake Fadin"Lafiya kuwa..? Hannu Dina ta saka Tana Sharban Hawaye batare da Tayi mgana ba ta Juya kawai zuwa Cikin Falon Ganin haka yasa ya Rufa mata baya,bayan ya saka Hannu ya maida Kofar ya kulle Zama Tayi kan Daya Daga Cikin Kujerun Falon tana matsar kwallah karya kamar yadda Zakiya ta Tsara mata,Cikin Fargaba Zain Dake tsaye kanta ya kalleta ya sake Fadin"Wai lafiyarki..? Nazo kuma kin Tasani kina kuka..? Kara Fashewa da kuka Dina Tayi kamar wata karamar yarinya Cikin Faduwar gaba da Ta samu Zain Lokaci Daya ya zauna Kusa da ita yana Fadin"Look Dina...Ki Saussauta kukan nan ki Fadamin Abunda ya Faru plz..,? Batare da Ta Dago ba ta Mika Hannu Ta Dauko Takardan Dake saman Center Table din Ta mika mai kin karba yayi iillah Zura mata ido Da yayi Lokaci Daya yana Fadin"Wannan fa..? Takardan menene..? Cikin Shakewar Murya Dina Tace"Taka ce..Ka duba ka gani.."Baiyi gaddama ba ya karba ya Bude ya Fara karantawa Tunda Abunda Takardan Ta kunsa Zain ya Fara Jin Wani irin Jiri jiri da kuma kafewar Miyan baki bai ji Tashin Hankali Wanda Tunda yazo Duniya bai Taba samun kansa Ciki ba sai da yagama Fahimtar Takardan da Abunda ta Kunsa Cikin Wani irin Sauri da Firgita Hade da Rawan Jiki ya Mike yana Rike da Takardan Gabadaya Idanuwansa suna Waje Hannunsa da Jikinsa da Bakinsa suna Rawa Lokaci Daya Dakyar ya iya Fizgo kalmar "Innalillahi Wa'inna Illaihiraju"u....Hasbunallahi Wani"imal wakil kalu inna lillahi Wa"inna Illaihirraju"un...Haka Zain ke ta maimaitawa bakinsa da Ko"ina na Jikinsa yana Ta bari kamar wanda Wutar lantarki ke ja Dina Dake zaune gefe Tana kallonsa ta Wutsiyar ido Kamar ta saki Dariya ganin Irin Tashin Hankalin da Zain ya Shiga. Cikin Fitan Hayyaci ya Zube kan Dina yana Fadin"D...Ddina Ban gane ba..? Me wannan Takardan Take Nufi..? Cikin kukan makirci Dina Tace'Nima haka na Shiga wannan Tashin Hankali Zain...Dama ai jiya ka barni bana Jin Dadi Toh Shine Zuwa yammah na Rarrafa na Tafi Asibiti ana gwadani aka bani wannan sakamakon.." Cikin wani karaji ya Rike Kafafun Dina yana Fadin"Wani Sakamako..? Ki fadamin da bakin ki Domin ina Tunanin idona ne bai gani Daidai ba..? Cikin karfin Hali tace"Ina da Ci..Ciki na sati Biyar da kwana..."Bata gama Rufe baki Ba kamar kiftawan Abu Taga Zain ya Mike ya Cafki Wuyanta ya Shake da Hannu Daya ya Dagata sama kafafunta na Wutsul Wutsil Daga sama Cikin Lokaci Daya ya Makata Jikin Bango ya Shake mata Wuya Sosai Idanuwan Dina suka Firfito Ta fara kakarin Mutuwa Lokaci Daya tana Saka Duka Hannayenta Jikin Na Zain tana neman kwatan kanta. Cikin Wani irin Murya mai Cike da Amon Tashin Hankali da Firgici Yace"Me kike Shiryawa Dina..? Meyasa zaki min Haka..? Na Taba gayamiki a Tarayyah na Dake babu Ciki kika kuma amince meyasa sai yanzu zaki Saba alkawari kizomin da Abunda zai zama Baraza gareni Ehe..? Yafada ya Zaro mata Jajayen Idanuwansa yayinda Da Jijiyoyin kansa suka mike Radau Cikin Son kwatan kanta Dina ke Fadin"Sakeni Zain..Zaka kasheni Ka sakeni nayi maka bayani..' Ganin Tana neman Suma ne yasa ya watsar da ita gefe ya koma ya Zube saman kujera yana maida Numfashi Dina kuwa Data samu ya saketa Gefe Taja Tana Tattaba Wuyanta inda ya Shaketa Cikin Kakkausar murya taji ya kara Fadin"Me kike Shiryawa Dina..? Bana gargadeki kada ki kuskura ki Sako Ahalina awannan Mganar tamu ba..? Meyasa zakimin Haka ehe..? Ya karishe Fada Cikin Tsawa da Sauri Tace"Nima bansani ba..kuma Babu Abunda nake Shiryawa ka yarda dani..".. Ido ya sakarmata yana kallonta Cike da wani Tashin Hankali kafin yace"Karya kike kin Sani..Ina Alluran Da kike saboda haka..?Da Sauri tace"Allah ina nayi yanzu hakama nayi na Wata 6 bansan ya akayi haka ba Ka yarda dani.."Tafada tana Fashewa da Kukan makirci Kai kawai Zain ya Dafe yana Fadin"Kin kashe ni Dina..Kim kasheni yanzu ya kike so nyi..? Cikin Shege fa..Cikin Shege Fa Ni Zain da wani Ido zan kalli Mutane in mganar nan ta Fasu..? Da sauri Dina Ta kallesa Tana Fadin"Ba wanda zai ji wannan mganar..Mganar Ciki kuma muyi Abortion dinsa in ka yarda.."Kamar an Tsaida shi haka ya kafeta da ido kafin ya Mike Zumbur ya Rarumi Sakamakon yana kara Dubawa kafin ya kalleta yana Fadin"Kin Tabbatar wannan asibitin kadai kika je aka Dubaki..? Kai ta gyada mai Tana kallonshi Baki ya Cije kawai Taga ya saka Hannu ya yayyaga Takardan yayi mata Gutu Gutu ya watsar da ita anan Tsakar dakin Yana Fadin"Hakane mganarki Dole ne zamu san hanyar da zamu bi mu Zubar da Cikin nan Dina Dole ne Shine kadai Rufin Asirina..! Jinjina kai Dina Tayi Tana Fadin"In har ka amince nima na yarda da Hakan wani asibiti zamu a zubar da Cikin..? Shuru yayi yana wani Tunani gabadaya kansa ya kulle sai Zufa yake yi kafin yace"Ba anan garin za"ayi aikin ba..Saboda Sunana ya Fita In Mukaje Watarana mgana zata Fasu zamu nesa da Garin nan Muje Gombe ko Kaduna Cikin Biyu Zamu Zabi gari Daya Inda zai sama Sirri garemu har muje azubar da Cikin mu Dawo ba wanda ya sani...Yes Haka ma za"ayi Gombe zamu Tafi Gobe da Sassafe saboda bamu da Lokaci.." Cike da mamaki Dina Take kallon Zain Kafin tace"Gobe kuma..? Cikin sakarmata Jajayen Idanuwansa yace"Eh gobe goben nan ba Lokaci Dina..Ya zama Dole a zubar da Cikin nan gobe Bana so ya kara kwana kada ya zamemin mtsala sannan ina Fata baki sanar da kowa Zencen Cikin nan ba sai Ni..? Gyada kai tayi tana Fadin"Ban Sanar da kowa ba..! Da Sauri yace"Gud...yanzu Abunda za"ayi Gobe ki Shiya da Wuri ki Dauki kayanki kamar Set uku haka Zan dauki Hutu a asibiti agida kuma zance Wata Tafiya ce ta kamani zuwa Gombe,Ki Jira anan Karfe 7am na Safe zan zo na Daukeki mu Tafi Ina so in muka je chan zamu Sauya Sunayenmu Saboda koda Watarana kin gane..? Ita dai kai kawai take gyada mai Gefe Daya na Ranta na Jinjina Son kai irin na ZAIN gefe Daya kuma na Zuciyarta na Fadin sai Kafi haka Razana Lokacin da mganar takai kunnin Iyayenka Zain Lokacin zaka Shiga kugin Nadama. Bai wani Jima ba ya Fice da Sassafar bayan ya gama Jadaddamata yadda ya Tsara komai,Yana Tafiya ta Tashi da Sauri ta Dauki wayarta Dake kan Layi har yanzu Tana Fadin"Zakiya na Shiga uku..? Zain ya kusa Kasheni fa yau..? Zakiya Dagachan Bangaran ta Saki Wata Dariya kafin tace"Daman ai nasan haka zai Faru..Saboda Abun bai zata bane ya Faru...Karki Damu Normal ne Tsarin na Tafiya Dai Dai yadda muka Tsara.."Dina Tana Sauke Numfashi Tana Fadin"Kinji Abunda yace..Ya zamu yi namu Tsarin Goben..? Zakiya tace"Karfe 7am na Safe yace...Mu kuma zamu Tafi karfe 6am ne na safe in Juransa Sammako mu Atafe muka kwana..Karki manta ki zama Cikin Shirin In kika batamana Lokaci zai iya Riskanmu kuma kinga Faruwar hakan kamar Batamana Shirin mu ne.."Da Sauri Dina Tace"Karki Damu zan yi kamar yadda kika ce..! Daga haka suka yanke Kiran Dariya kawai Zakiya ke kwasa Lokacin Data ke maimaita Mgangamun Zain Data gama Nada cikin wayarta Cikin Kada kafa ta Furta"Waya gaya Maka Borno Gabas Take Zain...Wlh sai na Tabbata kaji kunyar Duniya gaban Duka Ahalinka Sakarai kawai.." ****** Zain Allah ne kadai yakai Shi Gida Lafiya Domin yana Cikin Tashin Hankali da Dimuwa da Firgita Haka yaje gida ba Cikin Natsuwarasa ba Da Zaina ta ganshi ahaka sai da ta Tsorata Ta Fara Tambayanshi Lafiya yama kasa mata mgana ganin Hankalinta ya tashi ne yasa yamata karyan cewa Sun Rasa Patient din Dayaje Dubawa ne Allah Sarki Baiwar Allah harda kukanta Shi kuwa Zain Abunda ke Damunsa Dabam yana Tunanin yadda komai zai Tafi ne Batare da wani matsala ba. Tun adaran ya Fadama Zaina tafiya ta kamashi Zuwa Gombe kuma zata Dauki Tsawon kwana Uku zuwa Hudu bata kawo komai acikin Ranta ba tamai Addu"an Fatan alheri Harda Hadamai kayan Tafiya Shi kuwa yana zaune ya Zafga Tagumi kawai yana Ta Zufa,Natsuwa kwata kwata bai da ita Duk zaina ta Damu ganinsa Cikin wannan Halin,Ammh sAbun da ya bata mamaki ansha Samun irin wannan Case din a asibiti bata taba ganin Firstlove ya Shiga irin wannan Halin ba sai yau ammh sai ta Danganta da kila yau Matar ta bashi Tsausayi ne Haka Dai Ta gama Hadamai kayan Dakyar ta lallasheshi ya Shiga wamka ita kuma Barci yaci Idonta koda ya Fito Tayi Barci sai yaji Dadin haka,Zama Dirshan Zain yayi barci ko Barawo ya kasa Saceshi Zaina kawai yake kallo yana jin kwallah na Cika kwarmin Idanuwansa lokaci Daya yana mai Kaico da Rayuwarsa daya Kasa Barin Abunda Allah ya Haneshi gashi yau Dalilin Bijirema Allah ya saka kanshi Cikin Wani Bala"i wanda Fitar dashi sai Allah Da Zaina taso ta Farka sai ya kwanta ya Rufe ido kamar yana Barci,sai kuma yaga ta koma Farkawanta na uku ne ta tashi ta Bude ido ganin Wuta kau ga kuma Shi Zain din ya kwanta Ko Towel din daya fito wanka Dashi bai Cire ba saboda Zullumi da Fargaba,Ganin haka yasa ta Sauko Daga kan gadom tana Fadin"Allah Sarki Fistlove Daga gani ya gaji..Ji ko Towel bai Cire ballatana ya saka kayan Barci.." Wardrope ta Bude ta Daukomai Boxers dinsa tazo a Hankali ta Warware Towel din ta Zuramai wando Tana yi tana Lura kada ta Tadashi,Har tagama sakamai ta gyaramai kwanciya ta Rufeshi da Blanket ta sakarmai Kiss a goshi Lokaci Daya tana Shafa Fuskarsa kafin ta Dauki Towel din ta Bude Tiolet ta Shiga Idanuwansa da suka Kala sukayi ja ya Bude ya bita da kallo Sai ya kara jin Nadamar Abubuwan da yayi ta aikatawa Tun Suna London sai kuma yau ya kara yarda Da kalaman Haddir ya kuma yarda Masoyinshi ne Ace bai yi ma Matarsa ta Sunna Ciki ba sai karuwa..? Dama haka Allah ke lamarinsa Kodomin yanu mana mana Ishara mu Bayinsa,Yana Jin Motsin zata Fito ya sake lambo kamar mai barci yana Jinta ta kashe Wutar dakin ta kunna Dumlight,Ta hayo Gadon kan Kirjinsa ta yada Zango Ta Ja bargo Ta Rufesu Gabadaya Shi kuwa Zain kasa Rungumeta yayi Domin haka kurum yau yaji yana jin kunyar Tabata Haka kurum zuciyarsa ke wani Rawa ga Zunubun aikata Zina ga kuma Girman Zunubin Kashe Rai Lalle yana Cikin Bala'i Yadda yaga Safe haka yaga Dare,Sai gabda Asuba ne barci ya Kwaaheshi,Sai dai yaji ana sallame Salla Ita kanta Zainar ta makara Haka ya tashi Jikinsa Duk ya Mutu,Agurguje yayi wanka yayi sallah kana ya Shirya yana yi yana Duba agogo Fatan Dake Hannunsa Zaina na Kitchen Tana Hadamai Breakfast ya Bitachan yace mata zai Wuce Duk iya Kokarinta na Ya tsaya ya karya kasawa yayi ganin 7 din Daya ce ta Kusa haka ta Rakashi har Bakin Mota Har Motarsa Ta gama Ficewa Daga gidan Tana Tsaye Tana kallonsa Haka kurum Take jin wani Sanyi Jiki da Faduwar gaba haka kuma Take ganin yau kamar Firstlove din nata baya cikin Natsuwarsa Haka dai ta koma Cikin Gida Sukuku ta karisa aikinta ta Fada wanka Domin itama tana Da Shiga Sch 8am na safe. Koda zain ya fita Daga Gida kai Tsaye Gidan Dina ya tsaya Ammh Abun mamaki har ya kusa Mintina goma yana Mata Knooking Shuru bata zo ta Budemai ba ganin haka yasa ya koma Mota ya Dauko wayarsa ya Shiga Kiranta Abun Da yakara saka Zuciyarsa Bugawa Fat Fat Shine wayarnata Tana Kasheni,kamar zararrare haka ya Fito Daga Mota ya koma Jikin Kofar yana Bugawa Lokaci Daya da Kiran sunan Dina yayinda kuma Hannu Daya yake ta Gwada Layinta. Neagbours dinta ne wani Namiji Dama Gidajen irin ajere suke Kamar Estate ne yaji Bugun kofan yayi yawa ya Fito yana Tambayan Zain ko lafiya Shine ya karisa suka gaisa yana Tambayarsa Dina Shi kuma ya bashi amsa da Bata nan Domin yana Dawowa Daga sallar Asuba Yaci karo da ita ta Fito Daga gidanta da akwati a Hannunta wata Mota ta Dauketa Sun Fita da Gudu,kafin ma ya gama Zain bayani Numfashinsa ya tsaya Cak kamar wanda aka Dauke ma ji da gani Shidai yana gama gayamai ya wuce ya koma cikin Gidansa ya maida kofa. Zain kuwa wani Irin Juyawa ce ta Daukesa sai gashi a kasa yana Haki,Idanuwansa sum koma Jajir cikin wani yanayi yake Tunanin toh ina Dina Taje..? Wata zuciyar tace gidanku

Chapter 15 of 32