bamai Biye mata ballatana ya san da zamanta Itama Dinar bata Fitowa kullum Tana Daki Taci mai kyau tasha mai kyau sai Abunda ta Zaba shi Take ci Nene ta Daure mata Gindi Bangaran Umma kuwa basu kara ma Haduwa ba kuma kafarta bai Taka Dakin ba ballatana Abba Da bama yasan ganinta Ballatana mganarta Ragamarta komai yana Hannun Nene ne Shi Kanshi Uban gayyah bai Tana Zuwa Inda Take ba,itama Dinar bata Damu ba Saboda Zakiya tace ta bashi Lokaci Zai Dawo gareta.
Dina Tana waya da Daddyta da Kuma Hajiya Maimu wacce ta koma Sudan kuma Tayi ma mahaifiyarsu bayanin komai har mgana sunyi da Dinar ta waya ta kara yi mata Fada da Nasiha Wanda bai wai Domin Dina ta Jita bane Yadai Shiga kawai ya Fita,Hajiya Batula kuwa bata Taba Kiranta ba itana ba Damuwa Tayi da ita ba Wayarta Daga Daddy sai Hajiya Maimun sai Zakiya take Doguwar mgana Dasu bayan su Bata da wannan kwaramiyan sai dai Shiga Kafafen yada Labarai Tana Chart dinta Hankalinta kwance Babu Abunda ya Shalleta Nene Bata Taba ganin inda Dan Shege ke zama ado ba sai Wajen Dina Alfahari Take da wannan Cikin Jikin nata wanda Allah ya Taimaketa Bai sakata Laulayi Sosai yanzu Damuwar Dina Daya Rashin sanin makomar Auran Zaina da zain kuma gashi bata ma Jin Motsinta acikin Gidan Fargavanta Daya kada ace Ta koma Gidan Zain dinta wanda bata Fatan haka Zakiya ce ta Lallashe da cewa ta bi komai a Hankali kuskuran kadan Zatayi zata Lalata Duka plan dinsu ta bari zata samu Lokaci Tazo koma miye Sai ta ganoshi kafin Tatafi da wannan mganar ta Saurara da har taso Ta Tambayi Nene Kan Zaina sai kuma Ta Fasa Tunda Zakiya ta kwabeta.
Bangaran Zain kuwa Yasha Zuwa gidan in ya Daidaici Abba ya Tafi office Umma kuma Tana Daki ko Tana Kitchen sai ya Rutsa Zaina yayi ta mata magiya yana kwakwumarta,Nene dai ta sani kuma batayi wani abu ba Dagani Tana so ayi ma Ummi Shigo Shigo ba Zurfi ne bata Sani ba Haka zai zo yagama Nacinsa in bai ci Sa"a ba Ranar zaina ko mgana Batamai sai dai ma Ta Hadashi da kokenta,Duk da Haka bai Hakura ba sai ya latsata Don ya nuna mata bazai yarda arabasu ba Wajen kwana Hudu yana yin haka Ranar na Biyar Dubunsa ya Cika Umma Na Kitchen zaina na Dakinta Ta Fito Zata koma Daki Suka ci karo ya Riko Hannun Zaina zai Kaita Dakin Nene Daman nan ne Deport dinsa Daya ga Umma sai ya Dake ammh Zaina kamar tayi Fitsari saboda Tsoro wani mugun kallo Take watsamai Kafin ta Saka Hannunta Ta Fizge Hannun Zaina Ta Bishi Da katon Dundu Sai da Nene Ta Shiga Tsakani Haka Umma ke Fada ta Inda Take Shiga bata nan take Fita ba aka bar Nene da ban Hakuri
Zaina kuwa Hannunta ta Fincika Zuwa Daki Cikin Tuhuma Ta kalleta Tana Fadin"Tun yaushe ya Fara zuwa yana Janki aboye ban sani ba..? Cikin Inda inda da Tsoro Zaina Tace"Tun...Tun..Ranar ne Wlh Umma bana so.ya.."Bata gama Rufe baki Umma ta make bakin Tana Fadin"Rufemin baki in baki so zai miki Dole ne..? Daukan ki yayi..? Wato kema munafuka ce bansani ba ko..? In gaskiya ne meyasa baki Taba gayamin ba..?
Zaina na Hawaye Ta Bude baki Zatayi mgana Umma ta Sakarmata Dundunaye har guda uku agadon Bayanta Tana Fadin"In kuna Takaman ku yaran Zanani ne nima Uwar zamani ce..Bazan barki ya kara Cutanki ba Tunda ke kam baki da wayau Shashasha mara Tunani kawai.."Daga haka ta Fice ta barta Tana kokenta.
Umma Taki barin mgana Ranta ya Baci Har Abba sai da ta gayamawa Tace yajama D'ansa kunni ya daina zuwa ya Horema yarta kunne agabanta ya Daga waya ya kira zain wanda Tun bayan Faruwan lamarin Abba bai Taba Kiransa ba Jiki na rawa ya Dauka ko amsa gaisuwansa Abba bai yi ba ya Sauke mai nashi Jidalin da Fadan Yace ya Daina Zuwar mai Gida ashe bai ji ba..?hala da kudinsa ya Gida gidan..? Daga Karshe yajamai kunni kada ya kara Zuwa gidan Ballatana Har yazo kusa da Zaina Daya na sonta da bai aikata wannan Shanshancin ba ya Dai Jira in wannan Cutar da yayi ma Mutane ta Haihu aka musu Aure ya Dauketa zuwa Gidansa Su Huta.."
Ranar Zain yaga Fada iri iri Umma Tayi nata Abba ma Haka Numfashi kawai yake ta Saukewa washegari daya bama Haddir Labari sai da ya kwanta Saboda Dariya Shi kuma bai ga Abun Dariya ba wannan Abun a Tsausayamai ne gashi Firsrlove ya kasa gane kanta ya bata Hakuri kamar ya kwanta mata ammh Daga Dukkan alamu Tana son Goyon Bayan mamarta ne Shi kuma bazai bari haka ta Faru ba,yaji Fadan Abba ya Dauke kafa na kwana Biyu.
*******
Yau da Bikin Hamdiya ya Rage saura kwana Biyar Dukkan wasu Shirye Shirye sun kamkama,Tuni an kawo Lefe nan Abuja Dangin Mama Safiya suka je suka karba Achan,Sai Zuwa Gobe zasu iso Yan Chan Abujan Dukkansu Inna Hannatu dai ta iso Da nata gayyar Inna Rukayyah kuma sai Gobe Zafeera ma ta Dawo Duk Yau din Gidan Alhaji Tsoho Suka Tafi Harda Umma da su Saudart Zainab ma bata Shiga makaranta ba Tare suka Tafi.
Nene ce kadai agidan sai Zaina wacce Take cikin Damuwa Dazu sunyi mgana Da goggo Halima ta wayar Umma tace tana ta Kiran wayarta bata samu Ta Kira Zain Shine yace Tana Gida Wajen Umma,Shine ta Kira Toh itama Umman ahaka ta bari a Zaina bata da Lafiya Domin bazata ce komai ba yanzu Ta Kira sun gaisa da Zaina kana suka Cigaba da mgana da Umma Har take gayamata Bikin Hamdiya Tace zata zo Insha Allahu Daganan ta Duba Halimar Shine zaina ta Damu bata so Umma Ta tari Goggonta da wannan mganar ko bakomai Ita Mai Rufama Firstlove Sirrinsa ne ba kuma Tasan ya Goggon zata Dauki Lamarin ba Gefe Daya ga Laila Data Dameta Da zuwa kan Ta koma makaranta Ta Fadamata Ta Hakura da Karatu har Abada Tundai Gashi zata Rasa Firstlove.
Tana Cikin Dakin Umma Kishin Ruwa ya Fito Da ita Har ta Shiga Kitchen din ta Dauko Ta Fito Tayi Mugun gani Dina ce ta Fito Falo Ta Rako Zakiya zata Tafi Daman dazu Taji Nene na Fadin Wannan kawar Dinar tazo Wajenta,Dina sanye Take da Wando Plazo sai wata karamar Riga Kallo Daya Zaka mata ko ba"a Fada maka kasan tana da Ciki Saboda yadda ya Budeta ba kamar Zaina da Cikin Jikinta ya saka Rama ba sai Laulayi don ma yanzu Yayi sauki ko aman ba sosai take yinshi ba Bata kara yarda ta kwanta bata lahiya ba saboda Umma kada ta Mtsa sai sunje asibiti asirinta ya Tonu wanda kuma Bata Fatan hakan
Ruwa Take Sha alokacin da suka Hadu Sai da ta Dawo da Ruwa ta kware ta Fara Tari Dina ta kalleta sama da kasa Hakama Zakiya kafin su saka Dariya su Tafa Cikin Shakiyanci Zakiya tace"Topha ita wannan Daman Ta na gida nan..?na Zata ganin Matar so ta bayyana Tuni An koma Kauyen Tsoho da Tsohuwa..?
Tafada Cikin wani Wulakantattacen kallo Datake Bin Zaina Dashi Wacce Taji har ta Fara Hawaye ga kuma wani Mugun kallo da suka Jefanta Dashi cikin Kishi Dina tace"Kema kya Fada Ba Zuciya Namiji ya gama nuna maka baka da wani amfani awajensa ammh ka manne..! Duk kukan Banza ne bata iya Rabuwa Dashi Tunda gashi Ta kasa ta Dawo Gidansu Ta Tare kamar gidan Ubanta.."
Zakiya tace"Ayya yi mata Uzuri Matar Zain..Kinsan ba"a saba zaman kauye ba..Kuma da kike Fadin Ta Rabu dashi Toh in ta barshi wa zata kama..? Daman ai Taimakonta yayi ya aureta ammh Ita kanta taasan Wutsiyar Rakumi Tayi nesa da kasa..Kuma mganar gida kamar Gidan Ubanta Haka take gani mana kin manta nan Tsohouwa Tayi aikatau Tsoho ma yayi gadi Kinsan Dattakon iyayanmu na Baya Rikon Dan wani ba wani Abu bane..Kema ki barta Ta Raba agidanku ko yayane ta Rika Cin Jan miyar kar Abun yayi mata yawa ga Rabuwa da Zankadaden Miji ga kuma Komawa Kauye zaman Zawarci."
Cikin Shakiyanci Dina tace"Allah ko Tawan..?
Zakiya tace"Keda kikasan komai kuma..adai Daga mata kafa.."Dariya suka Sheke Dashi Harda Tafawa Lokaci Daya Dina na Fadin"An barta Tawan.."Zaina Da gabadaya kalamansu Zakiya yasa ta Jike da Hawayen Bakinciki da Takaichi Mganganunsu sun sakata ta Tuna Abunda ta manta,Kuka take so ta Fashe dashi ammh sai ta Danne Bata kara kallonsu ba ta Juya zuwa Dakin Umma Ko gani batayi suka Bita Da Dariyan Shakiyanci.
Ko gani Batayi ta karisa Dakin Bata ma kai ga Haawa gadon ba ta Sulale nan ta Saki wani marayan kuka ita kuwa Dina sun Dade da Xakiya nan Suna Ta Mganganunsu sai ga Nene ta Fito ganinta ne ma yasa Sukayi sallama da Juna zakiya ta Juya ta Fice tana ma Nene sallama Ita kuma Dina ta Koma Cikin Dakin Nene ta Bita da kallo acikin Ranta Tana Fadin"Allah ya Shirya.."!
*Janafty...*
*ZAINAZAIN..!*
_(Is a love Story and Betrayal)_
*Wattpad:Jamilaumar351*
*Mallakar:Janaftyshakira*❤️
*BOOK 1*
2️⃣8️⃣
"Kuka kawai Zaina Take kuka mai Cike da Bakinciki Da Takaichi Gefe Daya Mganganun su Dina na kara mata amsa kuwwa acikin kunnuwanta,Dafe kanta kawai Tayi Tana jin yana Sara mata kamar zai Tsage gida Biyu.
Hawayenta kuma Suna ta Zuba Suna Diga saman Cinyarta.
Hakikanin gaskiya Su Dina gaskiya suka Fada mata Ita wacece..? Ba kowan kowa bace Eh gaskiya suka Fada ita din Diyar maryama Wacce tayi aikatau ne anan gidan kuma Diyar Abdullahi wanda ya zauna matsayin Megadi Kuma Ita Jika ce ga Mallam Umar gada Wanda Shima Gadin ne Sana"arsa,Itama Kakar nata Atine itama kamar mahaifiyar nata aikatau tayi sai dai me..? Sun yi Dacen Iyayen Gida irin Iyalan Alhaji Tsoho Tunda Gashi Basu Hada komai da ita ba Suka Dauketa suka maida Tamkar yarsu suka Kula da Rayuwarta suka bata Ingantattacen Ilimin zamani Dana addini Daga Karshe suka aura mata D'ansu mafi Soyuwa garesu Ita kuwa me zata ce ga wadanan Bayin Allah..? Dame zata saka musu..?
Wani kukan Ta kara sakawa Tana Tuna kalaman Dina akanta na Cewa bazata iya Rabuwa da Firstlove bane ammh yaci ace Bayan haka yasa Ta gane cewa ita din ba kowan kowa Bace Tabbas mganrta na kan Hanya Inda Baya sonta bazai Fara Mu"amala da ita ba Har yayi mata Ciki ba me hakan ke Nufi..? Tayi kuskuran Yarda da Duka kalaman Bakin Firstlove Domin Duka ba gaskiya bane,ammh ba Laifinta bane Laifin Zuciyarta ne Data ke matukar Kaunarsa kuma ta Soshi da Zuciya Daya Kodomin Mganar Dina bazata yarda ta watsa ma Umma kasa a ido ba zata Nuna mata ko Babu Shi zata iya Rayuwarta..!
Wata Zuciyar ta Tambayeta Zaki iya Zaman jura wannan Zaina..? Koda Tana Tunanin bazata Jure ba ya zama mata Dole Ta Jura hakan kuma Lokaci yayi da Zata Sam me take ciki nan fa ba Gidansu ba Tasan ina ne Tushenta Gada Ammh kuma Taya Tun abaya bata koma Musu ba sai yanzu da komai ya kare zata koma musu Babu Auran Tare da ita kuma Harda Tsaraban Ciki Domin in Ta Jure Rabuwa da Firstlove bazata iya Juran Rabuwa da Abunda ke Cikinta ba.
Ta Dade Tana kuka Tana kuma Saka da warwaran makomar Rayuwarta kafin ta tashi Ta Fada Tiolet Tayi wanka Ta Dauro alwala jin ana kiran sallar La"asar yasa Ta Tada Sallar Ta idar kenan Sai ga Nene ta Leko Cikin Shirin Fita Tana Fadin"Diyar Umma na Shirya Zan wuce gidan Alhaji Tsoho..ki Shiyar Ummanki ta barmin Sallahun na Taho Dake chan.."
Cikin Sanyin Murya Zaina tace"Bazan samu zuwa ba Nene sai gobe kaina ke dan Damuna.."
Cikin Tsausayawa Nene ke Fadin"Ayyah sannu kinsha mgani..?kai ta gyada mata alaman Eh Nene tace"Shikenan Allah kara sauki ni na wuce..Keda Dina ne agidan ki kula kinji ko..? In Abban ku ya Shigo Abincinsa na Kitchen ki mikamai.."
Cikin Ladabi tace"To Nene adawo Lafiya.."Daga Haka ta Fice Kafin Nene ta wuce sai da Ta Shiga Dakin Dina ta Isketa kwance kamar kullun Tana cin popcorn Tana ganin Nene ta gyara Zama Tana kallonta kafin ma Tayi mgana Ta Riga ta da Fadin"Zan Fita....Bakowa agidan Sai Halima zani gidan Alhaji Tsoho Saboda Sha"anin nan Daya Karato.."
Cikin Mamaki Dina Tace"Sha"ani..? Nene tace"Eh...Daya Daga cikin Jikokin Gidan ne zata yi aure kanwar Haddir ne yar wajen Daddynsu na Abuja Shine Zasu zo nan ayi Bikin Daganan za"a wuce da Amarya Gidanta Dake kaduna.."Kai kai kawai Dina Tayi Kafin Tace"wai ni Nene haka zan Ta zama ba Fita..! Ina som komawa wajen aikina fa.."
Nene taJuya Tana Fadin"Ina zaki da wannan Abun kunyar kuma..?koda yake ke ado ma kike da Ita ai ko cewa akayi ki Fita zaki ce bazaki Fita ba saboda kaucema Idanuwan Mutane gashinan Cikin ki har ya Fara Bayyana ko bama Haka ba Duk wanda ya kalleki yaga mai Juna Biyu.."Baki Dina ta Tura kawai Kafin Tace"Ai Duka Da Haihuwa ce..Kuma Yana da Uwa Da Ubansa.."
Nene na gyada kai tace"hakane ba Shakka..Kinga Tafiyata.."Daga Haka ta Fice Dina Ta rakata da Harara,Nene bata ma Jira Direba ba Tunda yana Office Tare da Abba Da kafarta Ta taka Zuwa Gidan Alhaji Koda Taje duk an Hadu Falon Hajiya Mama ana ta Kira Hira Itama ta Shige Cikinsu Ganinta ita kadai yasa Umma ta Tace ina zaina Nene tace Tana Gida tace bata jin Dadi Umma Tayi Shuru tana wani Tunani Har ma Inna Hannatu ta kada baki Tana Fadi su daina barinta Tana zama ita kadai Ta Riga zama cikim Mutane ko Abun zai saketa,Hajiya mama ta kada baki Tace Tunda Uwarta Ta na Kokarin Raba auranta ai Damuwa yanzu suka kulla Inna Hannatu na jin haka tace Wlh itama Tana Bayan Umma abar Zain din ya zauna da Dina Tunda ita ya zaba nan fa Nene ta saka baki Tana kare zain kan yayi Nadama don Allah su karbi Tubansa Inna Hannatu tace har ga Allah komai ya wuce ammh fa Tana Bayan Umma yarinya karama Bakincikin yayi mata yawa ko ita Babba wannan Abun ya Faru da ita ya zatayi ganin sun Dake ne yasa Nene ta sakarmusu ammh fa tace su bazasu saki ba Sai dai ayi wacce za"ayi.
Umma dai Zainab ta Nema kan Ta koma Gida ta zauna da Zaina Tsoronta Kada wani mgana ya Shiga Tsakaninta da Dina kana kuma Bata son yaudaranta Da Zain yake yi yana Zuwa yana Hore mata kunni,Dole Zainab Ta Shirya ta koma Gida koda Taje ta Iske ma Har Abba ya Dawo Zaina ta kawo Abinci nan Falo Ya zaunar da ita yana kara bata Hakuri da kuma yi mata Nasiham Hakuri da Takwalli Dawowar zainab din yasa ya barta suka koma Daki Tare Dina kuma na cikin Dakinta ko Motsinta ba"a ji.
Sai Umma sai Dare suka Dawo Umma dai Haddir ya Dawo da Ita da su Zareenaa dasu Saudarta Nene kuma Zain ya Daukota Tunda Bayan ya Tashi Daga asibitin chan ya wuce,Inna Hannatu ta Kebe dashi Ta karamai Fada sosai da Nasihan Gudun Duniya ya Tabbatar mata Daya Tuba kuma yayi Nadama,Ammh yana Rokonta Ta saka baki Umma ta maidamai da Matarsa yayi ma Alhaji Tsoho mgana Shi kuma yaki Cewa komai,Inna Hannatu tace Itama Tana Goyon Bayan Umma wannan Shi ya sagar mai da Gwiwa har suka Iso Nene baki Take bashi kan kar ya Damu Umma Fade kawai Take,Bai Shiga Gidan ba yana Sauketa ya juya zuwa Gida Tunda Abba na Gida,Haddir ne ya Shiga Har suna Hira da Zareena sai chan dare ya koma Gida.
*****
Washegari Bakin Yan Abuja Suka iso Mama Safiya da Hamdiya da kawayen Hamdiya Guda Biyu sai wata yayar Mama safiyar Amina,Daman Mama Safiyar yar Kano ce,Sauran Dangin suna Tafe gobe,Chan kuma sai ga Inna Rukayyah da Zafeera da Maryam yar wajen Inna Hannatu Daman Taje kanon Hutu sai Shema"u sun Dira Su Asma"u sai zuwa Gobe Gidan Alhaji Tsoho ya Cika ba Matsaka Tsinke Chan zuwa yammah kuma sai ga Mom Iklima ita da Takwanran Hajiya Mama Wacce suke kira da Hajiya Harda Amin aka zo Duk da basu samu Hutun makaranta ba Baban kaduna yace azo Dasu Saboda Yan"uwa kowa zai Hadu su ga yan"uwa da abokan arziki Mazan dai basu Riga sun iso ba sai Ranar jumma"a Duka zasu Hallara Harda Tawagan Angwaye.
Su Zafeera suna Zuwa Gida Suka Wuce ita da Shema Harda kayansu,Nene da Umma daman tun safe suka Tafi Harda Zareena Zainab ce agidan sai Zaina sai Kuma Dina Hakima Zaina Tayi Murna da ganin Zafeera suka Rumgume juna Daman Umma tace Zafeera Karta bar Zaina agida Ta matsa mata su Taho Tare Sai da sukayi sallar suka ci Abinci suka sake wanka kana sukayi Shirin komawa Gidan Alhaji Tsoho Zafeera kuma ta matsa ma Zaina ta Shirya su Tafi da ta Fara Nokewa kan bata da kayan sawa tafarayi Zafeera ta Bata nata tace sai ta saka Dole Kanwar naki ta Shirya Ta saka kayan Zafeera Doguwar Riga Duk da Daman Zafeera Tafita Jiki ammh abaya Kayanta na yi mata Saboda ita tayi Cikar aure ammh yanzu Rigan Tayi mata wani Burum sai Dan Wuya,Zafeera ta Daukota mata mayafin kayan ta Bata Da Farko tace bazata saka ba Zafeera Ta Rantse mata sai ta Saka Dole ta saka Sun Fito Falo zasu Tafi sai ga Shigowar zakiya Wacce Dina ta Kirata kan tazo Ta Tayata zama Duka gidan sun Tafi sun barta ita kadai kallon kallo Sukayi ma Juna Daman Daga Zafeera har Shema yan Bana bakwai ne suma awulakance suka kalleta suka Dauke kai zaina dai Tana Rike da hannun Zainab Jikinta na Rawa Ita kuwa Zakiya mamakin yaran Take Shema cikin Kallon Tara Saura kwata tace'Wannan itace uwar Shegen..? Wacce tazo Goyon Ciki Gidan iyayen abokin Farkan nata..?
Da Sauri Zafeera Tace"A"a ba ita bace..Abokiyar Shanshancin nata ne.."Shema Tace"Ko Daga gani Daman ba kima.Mudai an Hadamu da Bakin Gaddara.."Zainab tace"Wlh kuwa.."Kafin Zafeera ta Ja Hannun Shema da Zaina Tana Fadin"Let go.."Suka wuce Zakiya Data kame Tana Binsu da kallon Mamaki har suka fice Daga Falon.
Kada kai Zakiya Tayi ta karisa Dakin Dina ta sameta Ade ade kan gado Tana Dannan waya Cikin wani irin Isgilanci Zakiya tace"Wasu Kwalayen yan iska kuma kuka samu agidan..? Nagansu tare da Kodaddiyar Kishiyarki Wacce Duk ta Rame ta Kode kamar Kudin Guzuri...!
Dina Tace"Hmm Waya sani..Kila yan Biki ne nidai ina ta jin Hayaniyarsu.."Zakiya na zama Gefen gadon Lokaci Daya Tana Fadin"Lalle..Kam...Naji sunata mganganu ni Dariya ma suka Bani Dukkansu kananan yan Iska ne basu san me ake Kira Bariki ba Ballatana Iskaci.."Dina Tace"Nidai bar wannan mgana Cikin nan ya Fara isata na kosa na Haifeshi yamin Katanga da Abun kaunata Tunda fa nazo Gidanan ko Inda nake Zain bai Taba kallah ba ballatana na saka Ran wani kyakyawan kallo Daga Barayinsa.."
Zakiya Tace"Karki damu...Sauran wata Biyar ki Haife Abunda ke Cikin ki Daga Lokacin kuma ai bashi da yarda zai yi zai saba mganar kakansa ne bayan Tarin Laifukansa Kisha Kurumin ki kin Riga kin zama Matar zain Ta har Abada.."
Dina Ta washe baki Tana Sakin Dariya,Zakiya kuma Tana mata Mirmishi Cikin Tsausayamata yadda Ta Kwallafara akan Zain Wanda ita bata Fatan hakan ya Faru da ita,tafi son Rayuwar yanci Da kuma Sakewa nan Ta gyara zama suna ta Hira da Dina Rabi Duk Labarin Shanshancisu ne Da kuma Mafarkin Dina na Auran Zain.
****
Umma Taji Dadin ganin Zafeera Ta Taho da Zaina Kowa ya ganta sai ya koka Ramarta Inna Rukayyah da Mom Iklima sai da sukayi mganan kan Ramar Zaina suka kuma yi mata Fadan Ta Cire damuwa aranta Ta kuma Dinga cin Abinci Tace Toh,Sai Ranar Alhaji Tsoho Ya ga Zaina Tun bayan Faruwar Lamarin Alhaji Tsoho Shi kanshi Yaga Ramarta Sosai ammh sai bai yi mata mganar ba Ya dai mata wasan Dayake mata Tunda yaga bata wani maida kai ba yasan Har yanzu Abun bai saketa ba,Daganan sai yan matan suka kebe kansu Dakin Hajiya mama Harda Hamdiya da kawayenta,Duk da Sauran kawayen suna Tafe gobe,Duka suna Tare ana ta Hira Zaina na gefe sai dai in Su Zafeera Sun sakota ta Dan Murmusa nan suka kai Dare sai Wajen 9pm na Dare suka koma Gida Taga dai Haddir ammh Bata ga Zain ba,wanda kuma ya ZO gidan Bai Kawo Cewa Zaina Tazo ba kuma yayi Tunanin Binta Gida sai yaga pass 6 Abba ya koma Gida sai ya Fasa Bayason Ran Abba na Baci saboda shi!
Sai washegari alhamis ya ganta Dayake sunyi Sister Day nan Filin Gidan Alhaji Tsoho akayi komai bayan anyi Hayan Konofi da kujeru Baki na Nesa Dna kusa sun kariso Dangin Mama Safiya Mota Biyu suka yo Daga kano Banda na Sauran garuruwa,Wasu ma suna Hanya basu kariso ba manyan ya"yan Inna Hannatu dana Inna Rukayyah duk sun kariso Da nasu Tawagan,Daddyn Abuja ma ya Iso aranar Baban kaduna ne sai Zuwa Gobe Suma Daga Barayinsu sunyi gayyah Sosai,Domim Katin ma Guda100 Suka Bugo wanda Abba ya Daukin Nauyin buga katin Gayyata Daga Gidan Saulawa Harta da chan katsina yan"uwan da suka Rage duk Hajiya mama ta Kirasu awaya ta sanar dasu Ganin gidan ya Cika ne yasa Haddir ya Tattara Inashi Inashi zuwa Lowcost wajen Zain wanda yaji Dadin haka Sosai,Yan matan kuma Ranar ma Gidan Abba suka yada Zango chan ya Cika da Iyayensu.
Kowa ya maida komai bakomai ba an manta da Abunda ya Faru..Zaina ce dai suke Tsausayamawa Kowa yana nan nan da ita Bangaran Dina ba wanda ya Damu da Tambayarta ma Domin kowa haushinta yake ji Gwara ma Inna Rukayyah Tayi mganarta Tace chan gida suke Barinta Don karta Fito Labari ya Yada gari,Nene tace Tana Gida Ko Su Shema da suke kwana agidan ba ganinta suke ba,Tana Dakinta Bata Fitowa komai sai dai ayi mata Tana Daga Cikin Daki Nene ce ke wannan Wahalar Suna Gidan suna Sha"aninsu basu ma Damu da ita ba Itama bata Damu dasu ba Sai dai in Zakiya Tatashi aiki Sai ta Kirata tazo Ta Tayata zama,Su Wuni suna Shakiyansu wani Lokacin sai su Umma sun Dawo Take Tafiya.
Ranar Daya ganta ana Tsaka da Sister Day din ne Sun yi Shigar Jallabiya baka,Wanda Zaina bata ma san Umma ta Siya mata Har taso ta Zuke zuwan Taga Umma ta Dauko mata Dole ta saka Zafeera Tayi mata Rolling Da Vail Din Harda Shafa mata Hoda da Man baki sai gashi Ta Fito kamar ba ita ba sai dai Rigar Ta bayyana Ramarta Sosai ,Abunda yasa ya ganta Daddyn Abuja ne ya aike su Shida Haddir suka je gidan Buredi suka Siyo Buredi mai yawa Cikin Booth Daga asibiti suka Biya suka Siya sai Suka Wuto Dashi Gida suna zuwa suka Iske ana Taron,Ganin mata sun yawa bai ma Tsaya gane kowa ba sai Haddir ne ya Tabashi Yana nuna mai Zaina wacce ke zaune kusa da Zafeera Ido ya kura mata Yana kallonta Cikin wani yanayin Ganin yadda Rigar Tayi mata kyau ne Sosai Tabbas ya sani Firstlove ta Rame sosai ko kula da matan Dayake wajen bai bi yi ba ya isa inda Suke zaune Tun kafin ma yayi mgana Umma Tazo Taja Hannun Zaina ta maidata Kusa Da ita Tana Hararan Zain wanda yayi kasake kawai yana kallon Umma Inna Rukayyah ce matayi ma Umma mgana kan ta Sausasauta ammh Taki mgana sai ma Hade rai Datayi ita kuwa Zaina Tama ji Dadin haka Domin bata kaunar Kara Haduwa ko Kebencewa da Zain.
Jiki ba kwari ya Juya ya Tafi Ko Cikin Gidan Bai Shiga ba Haddir ne ya Shiga Ciki Buredin kuma yara suka kwashe Zuwa Ciki,Har suka Tafi Umma na makale da Zaina Bata matsa ma,sai Gabda Mangariba aka gama Sister Day din Aka koma Cikin Gida Ba Wuta katon Genenrator Din Gidan Alhaji Tsoho aka kunna Haske ya Gauraye ko"ina Dama su Zafeera da Shema da Zaina da maryama Haraban Gidan suka Shimfida Darduma katuwa Tun bayan da aka kwashe Kujerun,nan sukayi Sallar Mgariban kana suka Nufi Cikin Gidan Inda Hamdiya Take da Bakin kawayenta Yan wajen aikinsu da abokan karatunta da suka Sauka Dazu Da Rana.
Koda suka Shiga Falon sun Tarar da Duka iyayen nasu suna Falo Inna Rukayyah,Inna Hannatu,Mama Safiya da yan"uwanta Mom iklima Umma,Nene da Sauransu sai Hira ake ana Dariya sai gasu Zafeera sun Shigo sannu da gida suka yi musu kafin su Wuce Zuwa Dakin Hajiya Mama Mom Ikilima ce ta Kura ma
All Chapters
Chapter 1
Chapter 2
Chapter 3
Chapter 4
Chapter 5
Chapter 6
Chapter 7
Chapter 8
Chapter 9
Chapter 10
Chapter 11
Chapter 12
Chapter 13
Chapter 14
Chapter 15
Chapter 16
Chapter 17
Chapter 18
Chapter 19
Chapter 20
Chapter 21
Chapter 22
Chapter 23
Chapter 24
Chapter 25
Chapter 26
Chapter 27
Chapter 28
Chapter 29
Chapter 30
Chapter 31
Chapter 32
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 29 Chapter of 32