Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
ta sanar da Laila cewa wayar Zainar tana Cikin Jakarta sakamakon bata Da lafiya Shiyasa ba wanda yabi ta kan wayar,Dakin zainar ta Nuna mata tace ta Shiga tana Ciki. Cikin alhini da Tsausayin Halin Da zaina ke Ciki ta taka Zuwa Cikin Dakin acikin Ranta Dama Tana Tunanin wannan Abunda ya Faru sai ya Taba Rayuwar Halima Fiye data kowa acikin lamarin. *Janafty..* *ZAINAZAIN..!* _(Is a love Story and Betrayal)_ *Wattpad:Jamilaumar351* *Mallakar:Janaftyshakira*❤️ *BOOK 1*             2️⃣5️⃣ "Koda Laila ta shiga Dakin Bata iske Zaina a ciki ba Ammh Taji kamar Motsi Daga kofar Toilet sai Aranta Tayi Tunanin ta Shiga Tiolet ne. Gefen Gado ta samu Waje ta zauna Tana Bin Dakin da kallo bata jima ba sai ga Zaina ta Bude kofar Tiolet ta Fito Daure da Towel,Ido Hudu suka Hada da Laila Dake zaune Tana kallon Kofar Toilet Gaban Laila ne ya Fadi Ta zaro Ido Tana kallon Zaina ganin yadda tayi Uban Rama Idanu Duk sun Zurma sai karan Hanci gashi Tayi wani Fayau da ita kamar mara jini ajiki. Cikin Mamaki da Al"ajabi Tare da Tsausayi Laila Ta bude baki tace"Halima...!!! Ta karishe Fada Cikin Muryan Amoh da Sauti. Mirmishin Dayafi kuka Ciwo Zaina ta saki kafin ta Fara Takowa Zuwa Cikin Dakin Wardrope ta Bude ta Dauko Wata Doguwar Riga Baka Cikin kayan Zainab ne Domin Kayanta Duk Suna Lowcost Umma tace zata aika Zainab ta kwaso mata kila Ta manta ne koda yake Zainab din bata zama Saboda makaranta. Juyowa Tayi Dauke da Rigan a Hannunta Ta kalli Laila Dake Binta Da kallo Ido Cikin Ido Tace"Na"am Laila...! Karo na Farko da Zaina Tayi mgana da wani ba Cikin kuka ba Tun bayan Faruwar al"amarin. Laila Tayi Tsuru kawai Tana kallonta Imani da Tsron Rayuwa ya kara kamata Har zaina ta koma Tiolet Ta Zura Doguwar Rigar Data Shiga Dashi ajikinta sai da ma ta Fito Laila Ta kara ganin Ramarta Zaina Tana Bula Bula Cikin Bakar Doguwar Riga Kirar Armani Sai da Taje gaban Madubi Ta Dauko Man Vaseline kana Ta zo Ta zauna Kusa da Laila Tana kallonta Lokaci Daya Tana Fadin"Yanzu kike Tafe Laila..? Laila Ta saki Gauron Numfashi kafin tace"Halima Ciwon da kikayi Mai Tsawo ne da kika koma Haka..? Kinga yadda kika Rame kika Lalace kamar ba ke ba..? Mirmishin Dayafi kuka Ciwo Zaina Tayi kanta na kasa Tana Shafa ma kafafunta mai tace"Eh nayi Cuta mana Laila...Cutar Gubar Da Namiji ne ta maidani Haka wacce kikayi ta Nuna min Illar Shanta nakiji sai da nashata Tamin yawa Gashi yanzu Tana min Illah Laila..! Ta karishe Fada kwallah Suna Cika mata kwarmin Ido Har sun Fara Zuba Cikin sanyi Jiki Laila Ta Dafa Kafadarta Tana Fadin"Na sani Halima ammh ai hakuri ma Mgani ne..? Tunda Abun nan ya Riga ya Faru bai kamata ki zauna kina Kokarin kashe kanki ba Tun Ranar da na muka Rabu ban samu Natsuwa ba Halima Tsausayinki ya Cikamin Zuciyata Tuna irin Rauniki game da Mijinki Ina ta addu"a Afili a Boye Allah ya baki Hakuri Da Dangana kada wannan Lamarin ya Shafi Rayuwarka Nayi ta kiran Wayarki Baki Dagawa Daga Karshe kuma Tana kashe,Naso nazo Sai kuma nake jin nauyi kada ace Jin Kwakwaf ya kara kawoni Halima ammh kina Raina Gashi Mun Fara Test Tun Last week Dakyar na samu nayi Miki Guda 2 sauran kuma ban samu Dama ba Shine Daman nazo naji lafiya..?na kuma gaya miki ya kamata ki koma makaranta Kada ki Rasa Semester Halima.." Kafin Ta gama Gaban Rigar Zaina ya Jike da Ruwam Hawaye Cikin karaya Ta Dago Idanuwanta Cike Tab da kwallah Tace"Laila ki gayamin Inda ake saida mganin Hakuri zan siya nasha Domin Zuciyata ta Daina Zugi..! Taya kike tsamanin ki ganni..? Ina Farinciki ko walwala Da Har wata Waya zata zauna ahannuna Tun Ranar da kika barni ban kara bi ta wani kawan Duniya ba Laila ina nan Inda kika Tarar dani ina Fama da Kuncin Zuciya Wlh Laila ina Ji Dama na Mutu na Huta da wannan Bakinciki Dake Cushemin Zuciya.." Tafada Tana Fasheewa da kuka Cikin Sigan Lallashi Laila tace"Nasan Abun akwai ciwo  Ammh ki Daure ki kuma Cirema Ranki ki Dage da addu"a haka ba Karshen Rayuwarki bane Halima..'Cikin wani irin Yanayi Zaina tace"Karshen Rayuwata ce Tazo mana..Domin ni ba zan iya zama Gida da Matar da Firstlove yagama Bata Dukkan Rayuwarsa Harda Tsaraban Ciki ba Tun waje zuciyata zata iya Bugawa Laila ba Zan iya Jurewa ba.." Jawota kanta Laila Tayi kan Cinyarta Ta Dora Tana aikin Lallashinta da bata baki Har sai da Taga ta Tsagaita da kukan kana ta Dago Tana Fadin"Ki koma makaranta Don Allah Halima..Bana so ki Rasa wannan Damar.."Da Sauri Zaina tace"Kina Tunanin akwai Abunda zan iya ganewa yanzu..? A"a laila karatu na irin ku ne masu kwanciyar Hankali Wanda wani Tabo bai taba Gifta ma Rayuwarku ba,kila Haka Allah yaso ya ganni Shiyasa ya Jarrrabaceni da wannan Jarabawar mai Wuyar Sha"ani.."Da Sauri Laila tace"A"a fa Halima kema baki da wani Tabo ai bake kika aikata Laifin ba Mijin ki ne.." Zaina Tace"Ni kuwa keda Babban Tabo akwai Abunda Tabo yafi Mijinka wanda kafi yarda Dashi kake matukar Sonsa da kaunarsa Tun tasowarka ace yau Ya Fifita wata karuwa Daga waje akanki yana Raba muku Rayuwarsa Tare Daga karshe Harda Tsaraban Ciki kuma tazo ta Raineshi acikin Gidan ta Haihu kuma Daga karshe ta Aure miki Miji akwai Abunda yafi wannan Babbam Tabo.." Cikin Karaya Laaila Tace"Hakane ammh...! Mganarta Ta makale ne da Shigowar Umma Dakin Dauke da Breakfast din Zaina Tana ganin Tana kuka ta bata rai da Sauri Zainar ta Share Hawayenta Gudun kada Umma sai dai bata san ta Riga Ta gani ba Cikin Damuwa Ta kalli Laila wacce ke mata sannu da aiki Ta amsa Tana Fadin"Ya haka Laila..?ya naga Tana kuka kuma..? Laila Tace"Wlh Umma Takan na mata mganar komawa makaranta Shine tace bazata koma Ba take wanman kukan.."Karamin Tsaki Umma Taja kafin tace"Kyaleta Laila...Mganar bazata koma makaranta Bai taso ba..Zata koma Dolenta in ta kara Warwarewa Karki Damu kinji ko.."Cikim Wani ganin Girman Umma Laila tace"Shikenan Umma Allah ya Rufamana asiri.." Umma ta amsa da Ameen Tana Kallon Zaina wacce ta Dukar da kai Tana Sharan kwallah Tana Shirin Barin Dakin Tace" Ba za ki bar wannan koken banza ba ko..? Inaga kin ga ban taba Dukanki bane Shiyasa...Laila ga kayan karyawanan ku karya"Cikin Ladabi Laila tace"Toh Umma sannu da aiki Umma na Fita Zaina ta Fito da Kukanta Sarari Laila sai ta Bita da kallon Tsausayi dakyar ta matsa mata Suka karya Shima Din Tea kadai tasha ta koma ta zauna Tana maida Numfashi Laila Kafin ta Tafi sai da tayi ta kokarin ganin Zaina taCire dmuwa kuma tace zata koma makaranta ammh har ta bar Gidan Zaina bata kara mata wata mgana ta dai tafi ne da ganin Umma ta Tabbatar mata da zata koma Har takai gida Tana Cikin wannan alhinin Abunda ya Faru da Halima yasa ta karajin duk wani Namiji ya Fita kanta Domin Tunda Firstlove ya iya aikata ma Halima irin wannan Katon Cin Amana koma waye zai iya aikata Haka sai dai Tana Fatan kada saboda haka zaina ta kuntata Rayuwarta har wani abu mara Dadi ya sameta. Laila tazo da safe zuwa yammah kuma sai ga Zafeera kamar an Koreto ajaran majaran Domin Inna Rukayyah Ta gayamata komai Tun Sadda Ta koma Hakika Zafeera ta Shiga Tashin Hankali Nan da Takaichi da Tsanar yayanta ya kamata Gefe Daya ga Tsausayin Zafeera wacce suka taso kamar ta gwaye tafi kowa sanin wacece Zaina ta kuma sani Tana Rauni indai akan Ya Dakta ne,Labari yakai kunnun kowa Domin Har Faruq sai da ya kirata sukayi mgana yace yana ta Kiran Layin zaina Tana Shiga Ba"a Dagawa sun dai yi mgana da Umma sau Daya Shi kanshi ya Shiga Damuwa Sosai Shi ya ma Karfafa Zafeera Gwiwan Taje Taga Halin Data ke ciki Domin sunyi mgana da Ya Sadiq yace ko da ya koma Zaria ya barta Daga ita Har Ya Dakta sunam kwamce ba Lafiya ita bata Damu dashi ba Domin Shine Silam komai Tafi Damuwa da Ukti dinta Tun a satin taso Zuwa sai kuma suna Test Dalilin Haka ne yasa tace Bari ta bari zuwa Weekend Tazo Taga Halin da Ukti Take Ciki. Tana Zuwa Dama da karamar Jaka tazo Tunda Ga Falo ta watsar da ita Cikin Luhu Luhun Ido Ta kalli Umma Dake Falo Tana Fadin"Umma ina Ukti..? Umma batayi mgana ba illah Dakin Data nuna mata ai Zafeera bama Jira cewarta ba ta afka Dakin Tana Kiran"Ukti...! Zaune Kwance ta Tsira ma Ceeling Ido Kamar amafarki Taji Muryan Zafeera Tana Kiranta da Sauri Ta mike sai ko ga Zafeera ta Fado Dakin Ido Ta zaro kafin tace"Ukti..! Cikin Rauni Murya kamar wacce Taga Wata Uwa ko kuma wata Shakiyar yar"uwa haka ta Sauko Daga kan gado ta Zura da Gudu Zuwa ga Zafeeran itama da Gudun Ta Tarbeta suka Rumgume juna Kamkameta Zaina Tayi kawai ta sakar mata wani marayan kuka itama Zafeeran kukan take kamar Wasu yara tun sunayi Daga Tsaye har suka Sulale suka zauna Suka Dungule waje Daya Suna kuka im kaga yadda suke kukan sai sun baka wani Irin Tsausayi kuma Lokaci Daya zaka Fahimci akwai tsantaan kaunar Juna da Shakuwa Sosai a tsakaninsu kuka suke bilhaqqi da Gaskiya acikinsu bamai iya Lallashin Juna. Umma ce ta Shigo ta same su ahaka Baki ta Rike Tana kallonsu kafin Tace"Ko kuma Lafiyanku kuwa..,? Miye haka ..? Hala gidan mutuwa ne nan da kuka wani Hada kai kuna ta ma Mutane wani koken Banza.."Tafada Tana Hararansu Dukkansu Da Sauri Zafeera ta Dago Tana kallon Umma kafin Tace"Haba Umma ba Dole nayi kuka ba..Kalli yadda Ukti ta koma kamar wacce ta Shekara Tana Ciwo..Tsakani ga Allah Ya Dakta bai kyauta ma kansa ba kuma ya Cutar da Zuciyar Ukti yayi Sanadiyar saka mata wani katon Tabo acikin Rayuwarta Wanda bazata manta Dashi ba Umma Tun ina kano da Inna Rukayyah Tagayamin Abunda ya Faru Kukana ya kasa Tsayawa ba kukan Tsausayin Kowa bane sai na Ukti Umma nafi Kowa sanin Rauninta kan Abunda ya Shafi Ya Dakta..! Tafada Hawaye suna kara Bulbulowa Daga Idanuwanta Umma Ta Kada kai Tana Fadin"Ba Dole ta Rame ba Zafeera Ta saka Damuwa acikin Ranta bata cin Abinci bata barci Sai kuka..Kuka Dai Dole kiga Ta koma Haka Ni kaina nagaji da wannan Ramar nata tun ina Lallashinta na Fara Biyo mata ta Bayan Gida..Gwara da kika zo ke kya gayamata Taji Ki gayamata Abunda ya Dace da ita Gwara Tun Wuri ta kama Jikinta in ba Haka ba ta zauna Takaichin Namiji ya kasheta Namijin ma wanda ya nuna ma Duniya baki da wani amfani yana Chan yana Shashancinsa da wata wannan bai Ishesa bama Harda Tukwaicin Ciki..! Zaina dai na jin Umma tama kasa Dagowa Domin bata da ta cewa Taya zata ma Umma bayanin ba ita keda alhalin Daina wannan kukan ba Abun Fitowa yake Daga Karkashin Zuciyarta Zafeera ta Sharbe Majina Tana Fadin"Danaji wannan Labarin Umma Yaya Dakta ya gama Bani kunya naci Sauran Maza sun Fita Daga kaina...Wlh bai kyauta ma Ukti ba sam Dame ta Rageshi..? Tunda muka Taso Tare nice Shaida bata san Soyayyar kowa ba sai Tashi Shi ya kasa ya tsare ya nuna mata Shine garkuwanta awannan Duniyar ammh Daga karshe sakamakonsa kenan..? Naji Bana son ma na ganshi Umma.." Tafada Cikin Tabbatar da mganarta Da Sauri Zaina Ta Dago Tana kallonta Cikin mamakinta Ammh ita Zafeera ba ita Take Kallo ba Umma Take kallo wacce tace"Hmmm...Ni abu Daya yafi Bakantamin arai wannan Lamarin ya gama Jajibo Abun kunyarsa maimakon Abun Duk ya tsaya kansa A"a hardamu ya Shafa Abun Bakinciki wai Dadiron nashi nan Cikin Gidan Zata Renon Dan Shegen Ta Haifa mana Duk agabanmu Don Allah Miya fi wannan Bakinciki da Takaichi.." Da Sauri Zafeera Ta Dafe Kirji Lokaci Daya Tana Fadin"Mun Shiga uku Umma injiwa yace Haka..? Umma tace"Inji Alhaji Tsoho mana.."Lokaci Daya Tana Cigaba da gayamata komai Zafeera Ta mike Daga Durkusan Datayi Tana Fadin"Gaskiya wannan Rashin adalci ne...Taya Abba zai ji da wannan Bakinciki..?gaskiya da sake bamai Haifama Dan Shege ko Shegiya acikin Gida Umma ta Zauna Chan Gidan Ubanta Shima ta Haifamai itama ai yar Barikin ce,Domin Ba"a Shege sai an yi Shegiya Umma" Zaina Ta kura ma Zafeera ido Ganin Ta Dauki Zafi acikin Lamarin Bata dai yi mgana ba Umma Ta Jinjina kai Tana Fadin"Ahto Nima Abunda nagani kenan..Kinsan Alhaji Tsoho mgana Daya yake baya Sauyata...Ammh Duk da wannan Bakinciki Daya kunsa mata Kin ganta nan Har yanzu bata Daina Sonshi ba Tana kuka wai Tana Fadin Bata jin Dadin yadda Abba ke Cewa bazai yafe ma Zain ba,kuma ya Hanashi Shigowa Gidanan In dai kinga ya Shigo Toh sai dai in baya Gidane wai ahakan ma Tsausayinsa Take bansani ba ko Matakin Dana Daukan kan bazata koma Gidansa bane yasa ta kasa Daina kuka..." Zafeera Ta waigo Tana kallon Zaina Cikin Takaicinta Tana Fadin"Ita nan har yanzu Sonshi Take Umma Duk da wannan Katotin Cin Amanar Daya aikata mata..? Tabe baki Umma Tayi Tana Fadin"Kema kya gani..Tambayanta kila Ta gaya miki..Bari naje na Duba Girki na Dawo ."Cikin gyada kai Zafeera Tace"Tom Umma..! Umma na Fita Zafeera Ta kalli Zaina Tana Fadin"Don Allah wai ke nan yanzu kukan Son yaya Dakta kike ko kuwa kukan Cin Amanar da yayi miki .? Zaina ta Dago Fuskata ido Jajir Tana kallon Zafeera kafin Tace"Ba kukan Soyayyarsa nake ba Ukti..Ina Tsausayama kaina ina Tsausayama Firstlove..Saboda ni Abba ya kasa yafemai ya hanashi Shigowa gidanan Umma bata mai mgana ko Gaisheta yayi bata amsawa Duk Saboda ni Ukti yaya zan Ji da wannan Abun..?ta dalilina Uba zai yi Fushi da Dan"sa hakama Uwa zata Juyama Danta Baya Abun na Damuna na rasa yadda zanyi.." Ta karishe Fada Cikin Raunin Murya kafin Zafeera Ta saki Wani Dogon Tsaki Tana Fadin"Aikin Banza..Har shi wani Abun ki tsaya kina Tsausayi ne..? Hala Shi ya Tsausaya ma kansa ne ballatana ke..? Kuma Da kike mganar ta Dalilinki Abba na Fushi Dashi Haka baki bashi Hakkinsa na Aure ne Daya sa yaje yana Iskanci da karuwa...? Cikin Kuka Zaina Tace"A"a Wlh Ina bashi Dukka hakkinsa..Bana taba nuna mai gajiyata ban Taba Juyama Bukatarsa baya ba Ukti Koda Ina cikin Jinin Haila ne Ina Kokarin wajen Kwantar da Hankalinsa Ban sani ba..Ban san Ta ina na Rageshi ba Ukti.."Zafeera Tace"Toh kin gani..Kenan babu Ruwanki bakuma saka hannunki wajen Zuwa yayi Iskancinsa Har yayi mata Wata ciki..Banga laifin Abba da Umma ba Ko ni nan Dayake Dan'uwana na jini naji ya Fita kaina naji kuma Wlh Duk Labarin kukan da Kwanciya Rashin Lafiyar da akace yayi bai bani Tsausayi ba Kece ma kika Fi bani Takaichi..." Zaina Ta Rausayar dakai Tana Fadin"Inda alkawari Ruwa ba zai Dafa Kifi ba Zafeera..Na yarda Yaci amanata kuma bai min adalci ba ammh kuma Sai nayi Duba da wani Abu ni wacece da Haka bazai Faru dani ba..? Kinga yadda Firstlove ya koma Ukti ya rame ya lalace Wlh Tallahi Ina Matukar Tsausayinsa acikin Raina.." Baki Sake Zafeera Take kallon Zaina kafin ta Kada kai Tana Fadin"Alkawarin yaci Ubansa..Wlh in Kikaga Ruwan bai Dafa Kifin ba Don Ubansa sai dai in ba"a sakoshi Cikin Ruwa ba..Kuma Tunda kina so ki Koma Wajensa Koma Ukti Ammh ki sani Babu Ruwana In Kika Kirani Watarana Kina kukan Bakinciki zai kasheki Kina ji kina gani zai Auri Abokiyar watsewar tashi akoma ana Miki ganin Daya bayan Daya Gefe Daya kuma Dan gaba da fatihq na Gifta muku acikin Gida.." Runtse Ido Zaina Tayi Tana Fadin"Haba Ukti..Kidaina aibata shi Haka karki manta Dan"uwanki ne fa.."Saboda Haushi Ko mgana Zafeera Bata mata ba ta Fice Daga Dakin Ta bar Zaina na Kiran Sunanta Kitchen Taje wajen Umma Ta kama mata aikin Abinci Sunayi suna Hira kan al"amarin Dayake Umma,Bata da wasu abokam Shawara sai ya"yanta Musamman ma Zafeera Tunda ita macece mai manyance da kuma Dattako kamar wata Tsohuwa. Tare suka gama Girki kana Umma ta wuce Dakinta Domin Domin Tayi wanka Itama Zafeera sai ta koma Dakin Domin ta Dauro alwala Kai Hade da Gwiwa ta iske zaina kan Sallaya bayan Ta Idar da sallah kai kawai ta Jinjina Batayi matamgana ba ta Shige Tiolet ta Dauro alwala tazo Tayi sallah bayan ta Idar ne Umma ta kawo musu Abinci ta kuma sanar da Zafeera cewa Abba ya Shigo Daman yaje gaida Alhaji Tsoho ne Tace bari Tagama taje ta Gaisheshi Ganin Daga Umman Har Zafeera sun yi baanza da ita yasa ta sauko Ta Fara Tura abincin ko Rabi bata Ci ba Tatashi Zuwa Tiolet sai amai sai ta gama ta Fito ta Fada kan Gado Tana maida Numfashi Suka Bita da kallo kafin Zafeera tace"Anya Umma Ukti ba Ciiki gareta ba..? Da Sauri Umma tace"Bar mata Fata Zafeera..Ni da nake so arabu Salin alim.."Kai Zafeera Ta gyada Tana Fadin"Kuma fa Hakane Umma...Zamansu ma ai ya Haramta Saboda zata cigaba da zarginsa Tana ganin sa da Abun gwara kowa ya nemi Daidai Dashi.."Umma tace"Shi nagani..."Zaina Tana Jinsu Lokacin da Zafeera tace ko Ciki gareta..? Sai da gabanta ya amsa ta Fara Tunanin wajen wata na Uku kenan bata ga Al"adanta ba Da kuma yanayin Data samu kanta akwanakin nan Zuciyarta ce takara Tsinkewa Domin bako Tamtama Mganar Zafeera zata iya Tabbata Kunshe Bakinta Tayi kada Umma Taji kukanta kuma Ta Tabbatar ma kanta Umma Taasan Da Cikin nan da gaske sai ta kaita an Zubar mata Dashi Ita kuma bazata bari ba Domin Tana Son Cikinta kuma Tana Son Uban Cikin Tafi kowa sanin babban Burin firstlove aduniya Shine Yaga ta Haihu Bazata bari wannan Burin nashu ya tafi abanza ba Wata Zuciyarta tace mata Kin makara Domin Wata ta Rigaki Daukan kwayan Hallitan Haihuwansa a mahaifanta Tuna Haka yasa Duk wani Farincikinta ya gushe Kishi ya Rufe mata Ido sai kuka ammh kukan Zucci Sanin Daga Umma Har Zafeera Suna Jami"iya Daya ne kamata Tana kuka Dukkansu bada Sauki zasu mata ba. Zafeera Taje ta gaida Abba ya Dinga Mata Fadan me ya Dawo Da ita suna Shirin Fara Jarabawa Tace gobe da safe zata koma kana ya kyaleta,Zain kuma Har kofar gidan yazo sai dai Megadi ya Tabbatar mai da Abba yana Gida Shi ya Hanashi Shiga ya Juya kan Motarsa Zuwa Gida wanda yayi mai Fadi babu Firstlove acikinsa Ba Laifi ya Rage damuwa saboda Asibiti Duba Marasa lafiya ma na Dauke mai Hankali ammh Tabbas ya gama Ramewa ya Fige da alamu dai yana Jin Ciwo ammh Bayaso ya kwanta ya Cigaba da Tsayuwa kan kafafunsa Domin in ya nuna Rauninsa Babu abunda zai Sauya. ****** Har suka kwana suka Tashi Daki Daya Zafeera bata sakar ma Zaina Fuska Duk da Tana Tsausayinta ammh kuma Ta bata Haushi yadda ta kasa mantawa da Ya Dakta da wani Abunda ya aikata gareta. Bayan sun karya Zafeera ta Fara Shirin Tafiya ganin hakane yasa Zaina ta Fara kuka wannan Dalilin yasa Zafeera ta watsar da komai ta isa gareta ta Rumgumeta Tana ta lallashinta Da bata baki kan ta Cire Damuwa aranta ganin Zafeeran ta Sauko ne yasa tayi mata alkawarin zatayi Hakan Insha Allahu Zafeera taji Dadi ta Dinga Share mata Hawaye Cikin Shakuwa. Abba kuma yana Gida bai Fita ba yau weekend Misalin 11am na Safe sai ga Kiran Alhaji Tsoho Bayan sun gaisa ne yake Shaidamai Tun safe sukayi waya da Kwamishina Baban Dina kan Yau Ita kanwar Mahaifiyar yarinyar Datazo Daga Sudan da mai Dakinsa zasu kawo ita Dinar kamar yadda ya Tsara saboda haka sun Taso Suna Hanya agayara mata masaukin da zata zauna Har Zuwa Lokacin da zata Haihu Adaura musu Aure tatare Gidan Mijinta Shikenan.. Abba yaji Kamar yayi kuka ammh kuma bai da yarda zai yi Tunda tun yana yaronsa baya Jayayyah da Alhaji Tsoho ballatana yanzu da Girma ya kamashi Waya ya Dauka ya Kira Nene da Umma Dukkansu yace su Zo Dakinsa su sameshi Kusan Tare suka Shigo kowacce Cikin mamakin wannan Kiran gaggawan sanin ma basu Dade da Fitowa Daga Dakin ba Umma kuma Dama nan ta kwana. Cikin Kallonsu Dukkansu ya Isar musu da Sakon Alhaji Tsoho Dukkansu sun Ji wani Irin Barin ma Umma Nene ce ta Sauke Numfashi Tana Fadin"Umm..Sai dai Dakinsu da Halima ke Ciki yafi Girma,Dayan karami Kuma nan Zareena ke sauka In Tazo,Kaga kuma Sauran Dakunan na Sadiq ne da Faruq kaga ai bama Sauketa Dakunaansu ba Duk basa nan,Suna Zuwa mana Hutu kwatsam ne.." Cikin Nazarin Mganarta Abba ya Sauke Numfashi Takaichi kafin yace"Shikenan agyara Dakin su Sa"adiya sai ta sauka aciki.."Cikin mamaki Umma tace"Ita kuma yar tawa taje ina..? Karfa ku manta Dakinsu ne Tun suna yaransu har girmansu kawai rana tsaka sai asaka wata Najasa aciki kuma alhalin Zaina Tana zaune acikin Dakin..? Umma Ta Fada Cikin Takaichi Nene ta kada kai Tana Fadin'Haba Umma ya kamata ki Daima aibata Wannan al"amarin da wani muguwar kalma Ko muna so ko bama so Cikin Jikinta Jinimu ne Tunda Danmu ya Digashi Kinga kuwa ya Kamata mu Cire komai mu Rumgume wannan kaddaran Tamu Hannu Biyu ammh naga ke kina Fifita Abunda kika Haifa kan Abunda Bake kika Haifa ba Umma.! Ta fada Tana kallonta Cikin Hawaye Mirmishi Takaichi Umma Tayi Tana Fadin"Halima yata ce Halak Makak..Kamar uwa nake gareta ke nice ma Uwartata kuma Ubanta ban damu da me zaki ce ba ammh ina so Ki sani ni ba irin Matan da Domin Nasu yayi Laifi su kare su ki Nuna yayi Laifin Saboda Don yana nasu ako"ina ina Bayan gaskiya..Na Riga nagama mganata Anemar mata wajen zama ammh ba Dakin Ya"yana ba wlh..! Tana Gama Fadin Haka ta Fice su Abba suka Bita da Kallo,Kallonsa Nene Tayi zatayi mgana ya Rigata da Fadin"Har kin Manta Fatima..? ki naka kenan ka so na wani..Tayi gaakiya uwar Sa"adiya take gareta Har Abada..Bari na Kira Alhaji Tsoho na gayamai.."Nene na Tsaye ya kira Alhaji Tsoho ya gayamai Abunda Umma tace Cikin Muryann Dattako yace"Me Halimar take Acikin Dakin Usmanu.. ? Kace ma Fatima nace Injini Ta maida Halima Dakin Miijinta ita kuma Yarinyar ku sauketa nan Usmanu hakkinka ne ka kula da ita kaida Matanka Laifin wani baya Shafar wani mene ne laifin Abunda ke Cikinta..?babu Laifinsa na Iyayensa saboda haka kada ya karbi Hukuncin da ba nashi ba..! Abba dai Toh kawai yace batare da ya kara yin wata mgana ba Nene  ma bai kara mata mgana Bayan Alhaji Yace In sun Kariso Hajiya mama zata kariso Dasu nan Gidan Damuwarsa yake so ya Boye Shiyasa ya Nufi Hanyar Tiolet yana Fadin"Kije ki saka ko Zainab ta gyara dakin nasu Sa"adiya Alhaji Tsoho ya bada Umarnin a sauketa anan.."Daga Haka ya Tura Kofar Tiolet din ya Shige ya maida Kofa ya Rufe. Nene Fita Tayi zuwa Falo Ta samu Umma zaune Tana kallon Sunna Tv Ana Wa"azi ammh a zahirin gaskiya ba wa"azin Take kallo ba Hankalinta da Tunaninta na kan yadda Zuciyarta zata Juru zama da Dina acikin Gidanan da Suna wacce ke Dauke da Cikin Dan'ta kuma ba na Sunna ba Bakincikinta zai karu Kila har itama asameta da Hawan jini Daga sama kawai Taji Nene na Fadamata Umarnin Alhaji Tsoho na asauke Dina Dakin Su Zaina Umma ta Dago Tana kallonta Kafin tace"Toh in ko Hakane sai dai Zaina ta Dawo Dakina..Ban yarda Ta Hada wajen zama da Wannan Yarinyar ba Bazata ma sabu ba.." Nene dai bata kara mgana ba ta Wuce zuwa Dakin nasu Zaina ta Iskesu Zainab da Zafeera ke Hiran karati zaina na Gefe Tana kallonsu bata dai mgana Ammh kuma Daga Dukkan alamu Hiran na Debe musu kewa Cikin Dakewa Nene ta Kalli Zainab Tana Fadin"Zainab ki gyara Dakin nan ki Share ko'ina ga Baki nam Daga kano..! Zafeera ce tace"Baki kuma..!? Ko Inna Rukkaya ce Nene..? Kafin Nene Tayi mgana Umma ta Fado Dakin Tana Fadin"Ba Rukayyah bace...Yarinyar da Alhaji Tsoho yace zata Dawo nan ne suke Tafe yau..Kuma nan Dakin yace asauketa.."Dam!gaban Zaina ya Buga Har sai da ta mike zaune Dakyau Cikin yamutsa Fuska Zafeera tace"Dakin mu kuma Umma..? Ukti kuma ta koma ina .? Umma tace"Tashi ki Hada mata kayanta dana amfaninta..Dakina zata koma Kema in kinzo Hutu chan zaki Dinga Sauka Daga yau.."Tafada Fuska ba walwala,Zafeera ta Sauke Numfashi Tana Fadin"To Umma.."Daga haka Umma Ta Juya ta Fice Nenema tabi Bayanta Suna Fita Zainab tace"Har ga Allah bana son Dawowar yarinyar nan Gidanan..." Zafeera Ta mike Tana kallon Zaina wacce

Chapter 26 of 32