Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
yayi Cikin Falon Har Gaban Alhaji Tsoho ya Duka ya gayamai Shuru Alhaji Tsoho yayi yana Nanata Sunan kwamishina Kafin ya kada kai yace yamai Jagora ya Shigo,yana Fita Alhaji Tsoho ya yi gyaran Murya yana kallon ya"yansa Lokaci Daya yana Fadin"Ku Saurara..Yanzu Abubakar yazo ya gayamin ina da Bako awaje..Kwamishinan kudi na Jahar kano.." Gabadayansu Da mamaki a Fuskarsu Suke kallon Mahaifin Nasu kai ya Jinjina musu yana Fadin"nace amai iso...Ku Mata ku Tashi ku Shiga ciki har muji damai yazo.."Ba gaddama suka mimmike zuwa Cikin Falon Hajiya Mama,Suna Shiga ba Dadewa Sai ga Sadiq ya Shigo da Sallama Bayansa Kwamishina Alhaji Gaddafi Sheerif ne Yaci Riga da wando na Shadda Harda Babban Riga Bayansa kuma Hajiya Batula ne Cikin Shigar alfarma sai Excort Dinsa wanda Kwamishina yabama Izinin Komawa waje Gabadaya su Abba mikewa sukayi na alamun Girmamawa Kafin suma gama mamaki sai ga Zakiya ta sawo kanta Falon Dina na Binta Abaya Cikin Shigar Abaya ta Nannade mayafin Bisa kanta. Gabadaya kallo kallo kawai ake ma Juna Alhaji Tsoho ya yanke Shurun da yima Kwamishina Maraba Har gabansa ya karisa ya mikama sa Hannu sukayi musabaha Lokaci Daya da gaisaawa Gefensa nan kasa Kwamishina ya zauna ayayinda Hajiya Batula dasu Zakiya suka yada Zamansu kan Kujerun Dake Falon suna kallon Ko"ina suma su Abba komawa sukayi suka zauna Sadiq ma bai Fita Shima ya samu Waje ya zauna. Alhaji Tsoho ne ya kalli Kwamishina yana Fadin'Naji mamaki da aka sanar dani Kai ne Bako ne..Ina Fatan lafiya.? Kwamishina ya gyara zama yana Fadin"Eh Toh Lafiya ba lafiya ba..Kamar yadda ka sani Sunana Alhaji Gaddafi Sheerif Wannan kuma Matata ce Hajiya Batula sai Yata Dina da kawarta Zakiya.."Yafada Yana nuna Kowa da Hannunsa Alhaji Tsoho Dasu Abba suma suka Bisu da kallo. Gyada kai Alhaji Tsoho yayi yana Fadin"Masha Allah...Sannunku da zuwa.."Hajiya Batula ce kadai ta amsa Dina da Zakiya kansu suka maida kasa,kara gaisuwa akayi Suma su Abba Suka yi Hannu Da Kwamishina aka gaisa Cikin Girmamawa. Alhaji Tsoho ya Kalli Sadiq yana Fadin"Abubakar Shiga ciki kace Tabawa Ta kawo kayan Motsa Baki da Ruwa.."Da Sauri kwamishina yace"A"a Akoshe miki Mungode.."Alhaji Tsoho yace"Ayi haka..? Annabi ya koyamana Girmama Bakon mu..". Kwamishina yace"Hakane..Ammh kafin nan bari mu fara gabatar da Abunda keTafe Damu..Dina Dago kanki.."Yafada yana kallon Dina Wacce kanta ke kasa da Sauri ta Dago Kanta Tana Fadin"Na"am Daddy..."Kai Tsaye ya kalli Alhaji Tsoho yana Fadin"Ka ganeta..? Alhaji Tsoho ya kalli Dina da Zakiya Sosai Gashi yana so kamar ya ganesu ammh kuma sai ya rasa ina ya sansu Su Abba ma kallonsu suke sudai Tabbas sun Shaidasu,Alhaji Tsoho ya Juya yana kallon Kwamishina Lokaci Daya yana Fadin"Kayi Hakuri..Kasan Jikin Tsufa Kila ko na Taba ganinsu yanzu na mantasu gaskiya.." Kafin kwamishina yace Wani Abu Baban Kaduna ya kalli Alhaji Tsoho yana Fadin"Alhaji Tsoho Ka manta ne,Sune wadanda suka zo gaida kai Lokacin da ka kwanta asibiti,Har Haddir yake Fada maka Ita wannan Din Tana aiki a asibitinmu Dayan kuma Kawarta ce..." Ya karishe Fada yana Nuna su Mirmishi Alhaji Tsoho yayi yana Fadin"Anyi Haka kuwa...Na Sha"afa kwarai har ma suka Fadamin Sunayensu,Gashi Har sunayen nasu ma ya Shigemun.."Yafada yana Yar Dariya Kwamishina ya Kalleshi yana Fadin"Wannan ce Yar Tawa Sunanta Dina...Sai kawarta Zakiya..' Alhaji Tsoho yace"Ba Shakka Sun Fadamin Sunayensu..Masha Allah Sannunku da zuwa..."Suka amsa da yauwa kafin Alhaji Tsoho ya maida Hankalinsa kan Kwamishina wanda ya gyara zama yana Fadin"Dama Abunda ke Tafe dani Abu ne mai muhimmanci Ganin Dukkanmu ba yara bane Naga kafin Komai ya Biyo baya yakamata nazo na sameku mu Tattauna na Sanar Daku Abunda Dan'ku ya aikata ma yata in ma kunsani Toh ku kara sani in ma baku sani ba Na sanar daku..! Yafada yana kallon Fuskokin su Abba da su Baban Kaduna,Suma Kallonsa suke Cikin Rashin Fahimta Baban Kaduna ne ya Bude baki yana Fadin"Wani irin Abunda Dan'mu ya aikata..? Wani.." "Bashir..."Yaji Alhaji Tsoho ya Kira sunansa ya Dago yana kallonsa Cikin Umarni yace"Karka kara mgana sai na baka Umarni.."Kai ya Jinjina yana Fadin"Shikenan.! Juyawa Alhaji Tsoho yayi ga kwamishina yana Fadin"Ina Jinka..Wani aiki Daya Daga Cikin ya"yan nawa suka aikata maka..? Kwamishina ya karkace ya saka Hannu a aljihu ya zaro Takardu guda Biyu,Daya sakamakon Cikin da Dr Bala ya basu ne Daya kuma wanda Dr.Imran ya basu Zakiya ne ya Mikama Alhaji Tsoho Karba yayi Yana kallonsa Cike da karin Bayani bai samu zarafin mgana ba Kwamishina yace"Daya Daga Cikin Ya"yanka ko Jikan kane yayi ma Yata Ciki gata nan Zaune..! Da sauri Zakiya tace"Jikansa ne ba Dan"sa ba Daddy..!. Kwamishina ya gyada kai yana Fadin"Duka dai zakiya Daya ne..! Dam...Dam! Haka gaban su Abba ya Fadi Alhaji Tsoho kuwa Gilashin Idanuwansa ya gyara yana kallon Kwamishina Lokaci Daya kuma ya maida Hankalinsa kan Takardun Dake Hannunsa yana Nazarinsu Daddyn Abuja ne ya Mike afusace yana Fadin"Ji wata mganar Banza..? Wani irin Ciki kuma sai kace wasan yara Haka kurum kazo da wata mganar ai Daga Ahalinmu anyi ma yarka ciki yar naka Yar Tsana ce da za"aJata amata ciki..! Ya karishe Fada Cikin Kumfar Baki Zakiya da Dina suka kalli Juna Hajiya Batula kuwa acikin Ranta tace"Kuma kwa gani.."Alhaji Tsoho ne ya Dagama Daddyn Abuja Hannun yana Fadin'"Koma ka Zauna Aliyu.." Ba musu ya koma ya zauna Shuru Falon ya Dauka na wani Lokaci Kafin Alhaji Tsoho ya Dago Daga Nazarin Dayake ma Takardun Hannunshi Lokaci Daya yana Fadin'Wanne Daga Cikin Jikokin nawa..!? Kasan suna da yawa..? Kai Tsaye Kwamishina Ya kalli Dina yana Fadin"Ke Gaya mishi Sunanshi.."Dina ta Dago kanta Lokaci Daya tana kallonsu Fuskar su Abba wanda suka Hade Fuska Tamau suna kallonta kafin ta Dirr kan na Alhaji Tsoho wanda Ba"a gane yanayin Dayake Ciki. Cikin Sanyin Murya Ta maida kanta Kasa Tana Fadin"Dr.Z...Zain ne..! Dum! Dum gaban Abba Usman ya Fadi Hakama na Baban Kaduna Tare Dana Daddyn Abuja,Tare kuma da Bugawar Zuciyar Alhaji Tsoho Daidai Kuma da Bugawan Zuciyoyinsu Umma domin Tun Lokacin da Daddyn Abuja ya tashi ya Fada fada sukaji Hayaniya suka Firfito suka Tsaya Daga Bakin Falon Hajiya Mama,Dukkansu Ido Suka zaro waje Cikin mamakin Abunda suke ji yana Shirin Faruwa. Nene ce ta Fizgo kanta Ta Fito Daga Cikin Falon Tana Fadin"Karya ne..Wannan Sharri ne ake so ayi ma Yarona..Zainullahi bazai taba iya ma Wata ciki ba karya ne.." Baban Kaduna ma ya mike Cikim Bacin Rai yana Fadin"Wannan ai ma wata mganar Banza ce wacce Hankali bazai Dauka ba.."Alhaji Tsoho Dai na kallonsu yama Kasa mgana Kwamishina ne yayi Mirmishi yana Fadin"Meyasa kuke gaddama..?ga Shaida nan kuma ku kira yaron naku mana sai ya karya ta gashi gamu da Dinar ko..? Dadyn Abuja ne ya mike yana Fadin"Ba wani mu Kira Dan"mu...Mu mun Riga munsan irin Tarbiyan da muka bama ya"yanmu bama Ya"yanmu bs,Wlh ko Karen gidan nan baazai Taba aikata irin wannan aikin ba..! Hajiya mama kuwa kuka ta Fashe Dashi Tana Fadin"mun shiga uku..? Me Jikana ya Tsare musu suka Biyoshi da wannan Sharrin..? Su Mama Safiya Mom Iklima tuni sun Fada Falon suna Fadin Karya ne wannan mganar ba Abun yarda bane  Barin ma Inna Hannatu da take Fada Tsaye tayi gaban Alhaji Tsoho Tana Fadin''Kwamishan me Alhaji Tsoho..? Mu za" a nuna ma Siyasa me ake jira da ba'a Fattake su ba Har ma sai azauna ana Jinsu suna Fadin karya da Abunda Tunda muke bamu Tabagani cikin Zuru"an mu..! Sadiq ma Ransa ya baci Huci kawai yake yana Fadin"Wannan ai bata suna ne..,Wlh zan iya Rantsuwa Ya zain bazai Taba aikata haka ba.."Umma kuwa da Zaneera da Hamdiya suna Kofar Falon Sun kasa gaba sun kasa Baya Umma wani Jiri Taji yana Dibanta Zareena kuwa sai da Ta Dafa bango TanaJin wani Sabon Tashin Hankali Ita Da Hamdiya haka suka Damke Hannun Juna Suna Sallalami. Hayaniya ta kaure afalon Irin su Inna Hannatu da Baban kaduna Masu Zuciya Kokarin cewa Suke Su Dina su Tashi su bar musu gids ko su kira musu Hukuma Ganin Haka yasa Alhaji Tsoho da Miyan bakinsa ya kafe yayi gyaran Murya yana Fadin"Bashir...Hannatu,Aliyu..Da kowa ma kowa ya samu waje ya zauna..! Jin Haka yasa suka kalleshi da Mamaki kai ya gyada musu Yana Fadin"Eh ku samu waje ku zauna...Mganar da suka zo da ita akwai kamshin Gaskiya aciki..'jin haka yasa Zuciyoyi Da Dama suka Buga Gabbai ya sanyaya sai ki ka ga Daya bayan Daya Suna Zama Umma dai sai da Hamdiya ta Rikota Ta iya zama Nene kuwa da Hajiya kuka suke suna Fadin Sharri ne karya ne. Mirmishin Karfin Hali kwamishina yayi yana Fadin"Ni da fari Yadda kukayi haka nayi..Sai da"a ace ban Nemo Hankalina ba Da Tuni nakai mganar gaban Hukuma ammh Sai Banyi haka ba nacegwara na Fara zuwa na sameku Na sanar daku Kila kuma baku da Masaniyar komai.." Kai Alhaji Tsoho ya Jinjina yana Fadin"Hakane..Kwarai kuma kayi Hikima da Baka sako Hukuma Cikin Lamarin ba Hakan yasa na kara ganin Kimarka Sosai.."Yafada yana Kokarin Boye Halin Dayake Ciki Kafin ya Dago yana kallon Baban Kaduna Ido Cikin Ido yace. "kiramin Zainullahi a wayarka Bashir...! *Janafty...* *ZAINAZAIN..!* _(Is a love Story and Betrayal)_ *Wattpad:Jamilaumar351* *Mallakar:Janaftyshakira*❤️ *BOOK 1*            1️⃣7️⃣ "Gabadayansu ido suka sakarma Alhaji Tsoho Suna kallonsa cike da mamaki Baban Kaduna ne ya kalli Alhaji Tsoho yana Fadin"Nakira Zain fa kace Alhaji Tsoho..? Gyada mai kai Alhaji Tsoho yayi yana gyara Siririn Gilashin Dake Idanuwansa yace"Eh haka nace ka Kiramin Zainullahi awaya yanzu..Ka sanar dashi Duk inda yake yazo ina son ganinshi.."Yafada Cikin Dattako da kamala Dina da Zakiya suka Rike Hannun Juna alamun Nasara. Daddyn Abuja ne ya Mike yana Fadin"Haba Alhaji Tsoho..Ai bai ma Kamata ka Biye ma wannan Shirmanmiyar mganar ba wacce bata da Tushe ballatana makama ba.Miye Abun Kiran Yaronnmu Mu Tsitsiyeshi kan Abunda zan Iya Rantsuwa bai aikata ba wanman karya ce Tsagwaronta da Bita da kulli kawai ake so azomana Dashi Cikin Zuru"a Domin abata mana Suna.." Yafada yana Kumfar baki Cike da Bacin Rai Baban kaduna da su Inna Hannatu kuwa Jinjina kai Suke alamun Gamsuwa da Zencen Daddyn Abuja,Abba kuwa Zaune yake kawai kansa na kasa yana Kiran Sunan Allah yama Rasa wani Tunani zai yi ko kuma ya Zai Dora Abun akan Mizani. Alhaji Tsoho ya Dade yana kallon Daddyn Abuja kafin ya Saki Mirmishinsu na Manya kawai ya Juya yana kallon Baban Kaduna yana Fadin"Bashir kiramin Zainullahi nace ko..? Umarni nake baka ba Shawaranka nake nema ba..". Yafada cikin Kakkausan Murya Inna Rukkaya Ta Bude baki zatayi mgana ya Daga mata Hannu yana Fadin"In har na isa Daku kada wanda ya kara mgana..Bana so ku zage da yawa Daga baya kuzo kusha Kunya..,Daga yar wajensa Har Zainullahin Duka namu ne Domin Da na kowa ne Mugu sai Mai Shi..Kuma In ba Rami me zai kawo maganar Rami..?bawai Ina da yakinin Gaskiyan Abunda suka Fada bane ammh In babu Gaskiya meyasa sai nan Gidan zasu zo..? Bauchi Tana da Fadi da sai su nemi Gidan Daya fi Namu suna da Asali,ammh kuma Kai Tsayen nan suka zo..Kuma karku manta yarinyar tana aiki Tare dasu Zainullahi a asibiti baku Hango Wani Abu Acikin Wannan Zencen..? Ya karishe Fada yana Binsu Da kallo Daya Bayan Daya,Yana karantar yanayin Fuskokinsu Sai kuma daya Fada sai kowa Jikinsa yayi sanyi,Daddyn Abuja ya koma ya zauna kaawai yana Salati acikin Ransa,Hajiya Batula na gefe Tana kallon Komai Su kuwa Dina da Zakiya Farinciki ya cika Ransu kwamishina kuwa Nadama ce Mai Tsanani ta Shigeshi na yarda ya sake ma Rayuwarsa Da yawa haka in ba Domin haka mai zai kawosa nan da Kimarsa yana Fadar mgana ana karyatasa Kwarai yana Cikin Nadama mai Tsanani. Baban Kaduna ya Fito da waya ya Nemo Lambar Zain ya Kira sai kuma,sai tayi kamar zata Shiga sai ta Dauke Cikin Tararradi Ya Dago yana Fadin"Alhaji Tsoho Layin Zain baya Tafi fa.."Kai tsaye yace"Kira na Hadiru kaji..ko basa Tare shi ya Nema mana shi..' Ba musu ya juya akalan Kiran Zuwa ga Haddir wanda ana Kira wayar ta Shiga ammh har ta katse bai Daga ba Baban kaduna ya Dago yana kallon Alhaji Tsoho yana Fadin,"Na Kirasa bai Daga ba.."Nan ma kai Tsayen yace"Sake Kiranshi Bashir..Insha Allahu zai Daga Jin Haka yasa ya sake Kiranshi Haddir kuwa Lokacin da Kiran Baban Kaduna na Farko ya Shiga wayarsa yana kan Mashin Ya Shigo garin Bauchi Suna Tafiya Sun Fita Bauchi kenan sun Dau Hanyar kano Wani karfe na Jikin Taya ya Fita Daga Motarsu. Hankalinsu ya Tashi gashi ba Garejin Akusa sai ya bar Zain nan Wajen Motan ya Samu wani mai Mashin Ya Daukosa zuwa Cikin Gari ya Sauka adaidai Garejin da yake kawo Motarsa gyara,Ya Dauko Walet dinsa yabama mai mashin Din kudinsa kenan ya sallameshi Sai yaji Wayarsa na Ringing yana Daukota Sai da Gabansa ya Fadi Daya ga Sunan Baban Kaduna Cikin Girmamawa ya Daga Kiran. Sallama yayi Baban Kaduna ya amsa yana Fadin"Ina ka shiga ne in kiranka baka Daga ba..?cikin Girmamawa Haddir yace"Wayar tana Aljihu ne ban ji kiran Ba Baba.." Baban Kaduna ya Numfasa yana Fadin"Kuna Tare da Zain ne..? Na kira wayarsa bata Shiga..? Wani Rugurugu Haddir yaji Dakyar ya Fizgi mganar yana Fadin"Ehm...Ehm..Muna Tare munzo Cikin gari Daurin Aure...!ya karishe Fada yana Goge wani Zufa Dake ketomai Duk da Iskan Dake kadawa awajen Kai Tsaye Baban Kaduna yace'"Ok Toh kuyi maza ku Dawo Gida yanzu yanzu..Alhaji Tsoho keson  ganinku.."Yafada Daidai Lokacin Da Haddir yaji Muryan Alhaji Tsohon yana kara Jadadda suyi Sauri fa ai Haddir Bai san sadda ya samu Jikin Garu ya Lafe ba yana maida Numfashi Baya Duba ammh Tabbas Ranar Daya ke ta Gujema Zain ce Tazo baya Raba Dayan Biyu Dina ta Fallasa mganar Cikin ga Alhalinsu. Har Baban Kaduna ya gama Hello Hello Dinsa yaji Shuru ya katse Kiran Haddir bai sani ba Zufa kawai ke ketomai Tuni yaji na Maransa ya Daure maimaita Salati kawai yake acikin Ransa yasan kuma ba wata Dubara sai ta Allah Dakyar ya iya Karisawa Cikin Garejin sukayi magana da Mai Garejin Dayake sun saba Yana kawo gyara wajen bayan ya gayamai Matsalan Nan ya bashi Cikin Yaransa guda biyu Daya yana Da Mashin ya Dauki Haddir su biyun suka koma Wajen Motar. Suna zuwa Haddir ya kalli Zain wanda ke jingine Jikin motan Kallo Daya zakamai ka Fahimci baya Cikin Natsuwarsa,Cikin Tsausayawa yace"Bakaniken nan zamu bari anan..Zan bashi Key din Motar in ya gama gyaran motar zai Tukata zuwa Garejinsu Daga baya zan zo na karba.."Cikin Rashin Fahimta Zain yace"Bangane ba..?motar haya zamu samu Zuwa kanon..? Bazai iya kallonsa ba Shiyasa ya Juya baya yana Fadin"Gida zamu koma..Na samu wayar Baban Kaduna kan cewa Alhaji Tsoho na neman mu dagaggawa.."Gum Zain yaji kamar an Bugamai Guduma asaman kansa Cikin Rashin Fahimta ya isa ga Haddir ya Juyo Da Fuskansa yana Fadin"Me kake son Fada Haddir..? Cikin karaya Haddir yace"Banda...Tabbas ammh ina Bakincikin Sanar dakai Dina ta Rigamu...Ina Zargin mganar Cikin nan takai ga iyayenmu..! Girgiza kai Zain ya Farayi kamar wani Zararre yana Fadin"Kai ina..? Karya ne Wlh bata isa ba...Kila dai Kiran na Taron nan ne,kasan Alhaji Tsoho ya matsa fa.."Yafada Cike da kwarin Gwiwa,Cikin son yarda da Mganarsa Haddir ya Gyada kai yana Fadin"Allah yasa hakan.."Zain cikin karaya da Rauni yace'Ameen Daga haka Haddir ya Fara Taran musu Mota sai dai basu samu ba Wajen Minti goma sai bakaniken yace su Jira gyaran bai da yawa yanzu zai gama,sai gashi Cikin Ikon Allah ko Minti Talatin baiyi ba ya gama gyaran Haddir ya Hau ya Bata wuta yaga Komai Daidai 5k ya bashi yace yakai ma ogansu su kuma ya basu 2k,Daganan suka Hau Mashin dinsu Su kuma su Haddir suka Hau tasu Motar suka Juya zuwa Gida Zuciyoyinsu Kowanne yana Saka Abubuwa Dadama. Gudu Haddir yayi sosai Cikin Lokaci sai gasu sun iso Haraban Gidan Alhaji Tsoho Suna Fitowa Daga Motan su da Jeep din da su Kwamishina suka zo da ita suka ci karo Sai kuma Excort dinshi Guda Daya da Mamaki Haddir da Zain suka kalli Juna cikin alamun Tambaya,ganin basu da masaniya Dukkansu yasa suka Nufi Hanyar da zata Sadasu da Babban Falon Gidan na Alhaji Tsoho. Haddir ne agaban Gaba Zain na Biye Dashi abaya cike da karfin Gwiwa koda suka ga Takalma akofar Falon Basu Tsinke ba sanin Duka iyayensu yau suna gidan na Alhaji Tsoho Shiyasa suka Shiga da karfin Gwiwansu Musamman ma Zain,gwara ma Haddir Tsoro ya Shiga Zuciyarsa. Akusan Tare suka yi sallama akuma Tare Duka Jama"ar Falon suka Daga suna kallonsu Lokaci Daya suna Amsa Sallaman nasu Atare yadda Duka iyayen nasu suka Zuba musu ido ne yasa Jikin Haddir kawai yayi sanyi sai kaawai ya samu kansa da kwarema yan Falon kallo Daya bayan Daya zuciyarsa ta Tsaya Cak ne sanda yaci karo da kwamishina da Hajiya batula bai gama Mamaki ba sai da ya sauke ganinsa kan Dina da kawarta Zakiya suna kallonsa Cikin Wani yanayi ai sai Haddir yaji kamar an Dasashi lokaci Daya kuma Yaji kansa ya Sara wanda yasa ya Dafe kansa Lokaci Daya yana Kiran sunan Allah Cikin Rawan Zuciya da Rawan kafa Zain kuwa Da zuciya Daya bai Fahimci Halin da Haddir ya Shiga Ko domin Shima bashi da Natsuwar ne,Wucesa yayi ganin ya Tsaya bai ma Lura da Su Dina ba Idanuwansa kawai iyayensa kadai suke nunamai acikin Falon kai Tsaye Alhaji Tsoho ya Nufa yana zuwa ya Zauna agefensa yana Fadin"Kai Tsohon Likitan nan ka cika Takura Miye kake ta kiranmu baka ya"......! Sauran Kalaman Bakin nashi Sun makale ne sanda ya Dago zai Nuna su Baban kaduna kawai karaf Suka Hada ido Hudu Da Dina Wacce Daman Tunda ya Shigo Take nacin kallonsa Taga in ya ganta ya zaiyi aikuwa yana ganinta sai ya Fara Tunanin Gizon ta ne ya gane da Fari kafeta da ido yayi yana kallonta Cikin Bushewar Miyan Baki kafin ya waiga yana kallon Alhaji Tsoho irin kana kallon Abunda nake gani Sai dai kuma..? Kawarta Zakiya Dake gefenta Dukkamsu suna Jifansa da wani manufukin Mirmishi Kamar wani wanda Wutar Lamtarki taja Haka ya Mike Jikinsa Ko"ina ba inda baya Rawa Idanuwansa ya Rufe Cikin Nuna ta yatsa yake Fadin"Dina..! Kallonsa Tayi Ido Cikin Ido Kafin Tace"Na"am Zain..."Tafada tana wani karkatamai kai Idanuwansa gabadaya sun Rufe ya manta da Wadanda ke Falon ya fara Taku zuwa Gareta Kowani Taku kuma Kirjinsa na wani lugude kamar amafarki Yaji Muryan Alhaji Tsoho yana Fadin"Kai Zainullahi ina zaka..? Maza dawo nan ka zauna..! Yafada Cikin Kakkausan Murya,Cak ya Tsaya sai Lokacin kuma Ya Fara dawowa Cikin Hayyacinsa ya Lumshe Idanuwansa ya kara Budewa yana Bin Kowa Dake falon da kallo So yake ya Gani Da gaske ne Dina ya gani ko Gizon ta ne..? Yakuwa kara ganin Gaskiyan Harda karin Kwamishina da Hajiya Batula,Gabadaya Falon Shi aka zuba ido ana kallonsa Idanuwansa ya Sauke kan Dina kyam kamar an Dasashi Wani Irin Hajijiya ce da wani Taurin Abu yake taso mai kamar zai kadashi Rufe ido yayi ya sake Budewa Still Dai gaskiya ne Tuni yaji Numfashinsa ya Tsaya Cak ya Daina aiki. Cikin Bacin Rai Alhaji Tsoho ya kalli Zain yana Fada'Ko baka jina ne..? Cewa nayi ka Dawo nan ka zauna.."zuwa Lokacin Tuni Jikin Su Umma ya gama yin Sanyi da Abunda zain yayi wannan ya nuna akwai wata akasa atsakaninsa,,Nene kuwa kai kawai ta Sadda Tana jin Duk Wata gabarta na Saki Haddir ne Daya ga Ran Alhaji Tsoho ya baci ga Zain kamar baya Cikin Hayyacinsa yasa ya Daga kafarsa Da yayi masa Nauyi ya isa ga Zain din ya Rikosa yana Fadin"Muje Alhaji Tsoho na Kira..! Kamar wani karamin yaro ya Juya yana kallon Haddir lokaci Daya Yana Fadin"Kaga Abunda Idanuwana suke ganemin kuwa afalon nan Haddir..? Cikin Wani irin kunya da Nadama Hade Tsausayi Haddir ya gyada mai kai yana Fadin"Eh nagani Zain..Yanzu ba Lokacin mgana bane muje ka amsa Kiran Alhaji Tsoho.." Karyansa kuma ta karse yau..Haka Zain yake Fadi acikin Ransa Har suka isa Gaban Alhaji Tsoho wanda ke Binsu da kallo Cike da Nazari Cikin Dakiya Haddir ya Zaunar da Zain Kusa da kafafun Alhaji Tsoho Shima ya koma ya zauna Gefensa kansu suka maida kasa Haddir Nata Kiran Sunayen Allah ayayinda Zuciyar Zain Tana Daina ma Bugawa bakinsa kuwa Motsi yake ammh kuma baisan me yake Fada ba. Gyaran Murya Alhaji Tsoho yayi kafin ya Daga Dayan Takardan Dake Hannunsa yana Fadin"Wani Likita ne ya baku wannan Shedar acikin asibitin Saulawa Spealist..?ya fada yana Kallon Dina Wacce Cikin Ladabi ba alamun Damuwa tace"Dr.Imran ne Ranka ya Dade.."Atare gaban Haddir da zain ya kara Bugawa kuma atare suka Dago suna bin Takardan Dake Hannun Alhaji Taoho Da kallo Sai dai Daga nan Basa Fahimtar komai Zain Dai kafe Dina kawai yayi da ido yana kallonta da Tambayar ni zaki ma Haka Don Kutumar Ubanki..? Kai Tsaye Alhaji Tsoho ya kalli Haddir yana Fadin"Kai Hadiru kasan wani Dr.Imran a asibitinku..? Cikin Sanyin murya ya Daga kai ba mgana Alhaji Tsoho yace"Toh Tashi..Kayi maza ka Dauki Mota kaje asibitin ka Taho min Dashi nan yanzu.."Daga shi Har zain sai da suka kara kallon Alhaji Tsoho aammh ganin yanayinsa yasa Basu kara marmarin kallonsa ba Da Sauri Haddir ya mike yana Fadin"Toh Insha Allahu. ! Da Hanzari ya Fice Daga Falon Har yana Hada Hanya yana Fita Baban kaduna ya Kalli Alhaji Tsoho yana Fadin"Alhaji Tsoho zaman me meke haka ne..? In zain ne gashi ya iso ka Tambayeshi ya gayamaka gaskiyan mgana Atashi wannan Taron mara amfani kowa ya kama gabashi.."Wani Mirmishi Takaichi kawai Alhaji Tsoho yayi kafin yace"Yaro Yaro ne...Yaro man kaza ne.." Yana Fadin Haka ya koma ya Gintse Ransa kawai yana Bin Zain da kallo Cikin Takaichi Da Bakinciki Wanda ke Fitowa Daga kasan Ransa Duk da bai da Wani Sheda kan Zain bai aikata wannan Fasadin ba ammh kuma alamun Rashin Gaskiya da Kamshin Gaskiya sun bayyana Garesa sai dai kuma Koda Hakan ta kasance yayi alkawarin kamanta gaskiya ga Duka Shashen Insha Allahu. Har Haddir yaje asibiti ya Dauko Dr Imran Alhaji Tsoho bai kara mgana su Inna Rukayya ne ma ke Cecekuce,Dina kuwa da Zakiya Zukatansu kamar Farar takarda Saboda Fari,Zaim kuwa Tunda Haddir ya Tafi yana nan zaune inda yake Motsi mai karfi ma Bayayi kansa na kasa Baya ma Marmarin Dagowa saboda yadda Kowa na Falon ke jifansa da Wani irin kallo wanda ke kara Tsinkamai ya"yan Hanji. Shigowar Haddir da Dr.Imran ne yasa Falon ya Dau Shuru gaban Alhaji Tsoho Suka Rusuna Dr Imran ya gaisheshi ya amsa Cikin kulawa kafin Dr.Imran yace"Ina cikin Office Dina Sai ga Dr.Haddir yazo ya sameni da cewa Ka umarceshi Dayazo ya Daukoni kana Nemana..Allah yasa Lafiya Ranka ya Dade..? Alhaji Tsoho Ya muskuta yana Fadin"Eh hakane...Karbi nan.'ya fada yana Mikamai Takardan Dake Hannunsa wanda keda Tambarin asibitinsu wanda kuma Dr Imran din ya basu Sakamakon Cikin Dina ajiki Da Sauri ya Gani na wasu sakwanni kafin ya Dago yana kallon Alhaji Tsoho bai samu Zarafin mgana Alhaji Tsoho ya katseshi da Cewa"Ka gane wannan Takardan..?. Dr Imran Dagowa yayi yana Bin Mutanen Falon da kallo sai alokacin Yaga Dina da Zakiya Cikin mamaki ya ke kallonsu da Neman karin Bayani Ido Kawai zakiya Ta kadamai Cikin Takaichi Inna Hannatu tayi Tsulum Tace"Kai Shashasha...Tambyarka akayi bawai an ce ka juya kana kallon wasu ba..! Tafada Cike da Takaichi Cikin Wayancewa ya waiwayo yana kallon Alhaji Tsoho Lokaci Daya ya gyada kai yana Fadin"Eh Tabbas..Ni da kaina na bada ta  ta Shekaranjiya da yammah..' Alhaji Tsoho yace"Kai kayi Test din..? Nan ma kai ya Girgiza yana Fadin"A"a Bani keda alhakin wannan ba nidai Dina da kawarta Zakiya  gasunan sunzo sun Sameni kan Dina Bata da lafiya na Duba Toh Bisa Tambayoyin da nayi mata ne sai na Fahinci kamar Gwajin Ciki ne ya Dace da ita nan kuma take na Dibi Jininta na kai Lap dinmu na Basu suka Gwada kuma suka Fitar da wannan sakamakon.." Yafada Cikin Fargaba da kuma Tunanin meyake faruwa..? Kowa yaji Abunda ya Fada Cikin Hikima Alhaji Tsoho yace"Ka Tabbata wannan sakamakon na gaskiya ne..? Kai Tsaye Dr.Imran yace"Wlh Allah kenan..Wannan Sakamakon Gaskiya ne..In ma baku yarda ba sai akoma asibitin akara gwadawa a gani"Alhaji Tsoho ya Dagamai Hannu yana Fadin"A'a Ba Bukata ai ka Rantse..In ma karya ka Fada kai da Allah..Mungode..Kai Hadiru bama Abubakar Key din Motarka ya maidashi..' Ajiyar rai ya Sauke yana Fadin"Nagode Ranka ya Dade.."Daga haka ya mike yana Tafiya yana waiwayansu su Dina kamar zai Fadi Dina kai t kauda zakiya kuma Fari kawai ta mai ido alamun zamu gamu,Yana Fita Sadiq Daya karbi Key din Mota hannun Hadir yabi bayansa Ya Daukesa ya maidasa Har suka isa Dr.Imran kansa na

Chapter 18 of 32