Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
Biyun ya aura bai yi gaddama ba ya amince Dr.Saulawa ya Aura masa Fatima da Aisha Arana Daya Bashir kuma sai bayan Shakara Daya da wani Abu da Auran Usman kana yayi Auransa Tunda Daman Shi Duk yafi su akidan Boko ita kanta Ikliman yar Boko ce Tunda itama ma"ikaciyar gwamnatice. Usman yana Zaune nan GRA inda ya Gina Gidansa kusa da iyayensa Tunda Shi kadai ne ke Zaune garin Bauchi sai yaga gwara ya zauna kusa da iyayensa Tunda Shi kanshi babu wasu Dangi Duk Sun kare ammh Har yau bai manta da garin katsina ba yana zuwa kuma Hannunsa na kaiwa nan yake Zaune Shi da Matansa Tamkar Tagwaye Wato Fatima da Aisha. Ayayinda Bashir ke garim kaduna Shima ya mallaki gidan Kansa da Motar Hawa haka ma Matarsa nada Motarta Sai Aliyu Barrister kenan yana Zaune agarin Abuja Shida matarsa Safiya Suna Zaune a Maitama Abuja Shima Din ya mallaki gidan kanshi Da Motar Hawa Rayuwa Dai ta inga Su Rukayyah kuwa da Hannatu kowacce Tana Gidan Mijinta ta Haiyayyafa Suna kuma Cikin Jin Dadi sai wanda ya gani. Dr.Abubakar Saulawa ya Samu Duka Cikar Burinsa Shiyasa Shekara na Zagayowa ya Tattara Duka iyalansa da matansu sukaje kasa mai Tsarki suka Sauke Farali,Shi dai Dr Saulawa da Hajiya mama Gida suka Dawo Ammh Su Bashir Kowanne kasar Dayake Muradi ya Wuce Shi da iyalansa Haka ma Su Rukayyah kowacce da Mijinta da ya"yanta Tun a Saudiya sukayi sallama da Junansu kowanne ya yada Zango a Inda ya Tsara zashi Su dai su Rukayyah da Hannatu da Mazajensu sun koma Gida da Wuri ammh Su Usman kam sai da Dr.Saulawa ya Dinga Musu waya yana Fadin Sun bar ayyukansu sun je wani kasa Sun Tare,Maza su Tarkato su Dawo wannan Dalilin yasa suka Tattaro Suka Dawo Kasar su ta Haihuwa kowanne na amsa Sunan Alhaji matansu ma na amsa Sunan Hajiya. Duk acikinsu Matan Usman ne suka Fara samun Ciki Wato Fatima da Aisha kuma duk atare,Murnan wajen wannan Ahali ba"a mgana barin ma Dr.Saulawa Farinciki ya Cikashi zai Fara samun Jikoki,samuwar Cikinsu da Wata Biyar sai ga Wani albishir din Safiya ma Matar Barrister Aliyu itama ta Harbu Sai Farincikin ya ninku,Bashir dai Shuru Dama Shi yace Tsarin iyali zasu yi ba yanzu zasu Fara Haihuwa ba sai zuwa gaba koma sun Fara 3 Childeeen ya Ishesu. Samuwar Cikin Fatima da Aisha Sai kuma Lalura ta karu gasu dama su kadai agidan ba yar aiki Tunda Tun Farko sun Nuna basu bukatar Wata yar aiki su Zasu Dinga aikinsu da kansu,sai kuma ga Samuwar Cikinsu Lokaci Daya kuma Dukkansu Suna Fama da lailayi sai Hankali Alhaji Usman ya Tashi kwarai yaje ma da Hajiya mama da Batun Samun mai Taimaka ma su Fatima kafin komai ya Daidaita ita kuma sai ta gayama Dr.Saulawa Batun Shi kuma sai yace Abun bana gaggawa bane gwara a tsaya a samu mai amana Tunda zata zauna da iyalansa ne. Da wannan Mganar Alhaji Usman ya bar komai a Hannun Dr.Saulawa Da Hajiya Mama kwatsam Atine taji Hajiya Maman na Zencen sai tayi karaf tace In suna so ga Matar Dansu Abdullahi wanda yayi Aure Shekaru Uku da suka gabata ya Gaba Karatun allo ya koma Gada ya Fara Sa"anan sai da kayan Dinki Wanda Dr.Saulawan ne ya Tankamai Jali Tunda yaki Karatu kuma Har yau har gobe akwai amana Tsakaninsa da Mallam Umar da iyalansa Atine kuma ta zama kamar yar gida. Wannan Mganar ta Atine Hajiya Mama ta kaima Dr.Saulawa Shi kuma yayi Na"am acewar Iyalan Mallam Umar Abun so ne Takalawa ne masu Wadatar Zucci da Dr.Saulawa ya Tuntubi Mallam Umar gada da mganar sai yaso yamusa saboda yace Kada Maryama Tayi Nesa da Mijinta Jin haka yasa Dr.Saulawa yace kada ya Damu Duka da Maryama da Abdullahin Zasu dawo nan gidan Usman da zama kamar yadda shi da atine suke zaume agidansa Dama yaji Usman Din na neman mai kula mai da Kifayen Dayake Kiwo Faduwa tazo Daidai da zama Mallam Umar Bai iya mgana ba,sai Godiya kamar yayi kuka na Karamcin Dr.Saulawa agaresu. Koda Dr.Saulawa ya Tuntubi Usman da mganar bai yi gaddama ba Saboda Baba Atine kamar Wata Babba yaya Suka Dauketa Shi kanshi Mallam Umar ba"a Matsayin Megadi suke kallonsa ba Suna Kallonsa ne Kamar kanin Mahaifinsu Baba Umaru ma Suke Kiranshi Batare da bata Lokaci ba Dr Saulawa ya Saka Mallam Umar ya Kiramai Abdullahi sukayi mgana Dayaji labari murna ta Cikashi Dama Tun bayan da yagama Almajirancinsa ya Dawo Bayan yayi Sauka ya Dinga Nadamar kin karatun Boko da yayi Tunda ya Fahimci yanzu Rayuwat bata Tafiya sai da Duka Fuka fukan Biyu gashi kuma Lokaci ya kuremai Dole dai Kanwar naki ya zauna chan Babban Gidansu a Gada ya Auri Wata yar"uwansa Maryama Bayan Dr.Saulawa ya Tankamai Jali ya Fara Sana"an kayan Miyan Jin wannan Rokon alfarman ta Dr Saulawa Sai Abdullahi yaji kamar an sakashi a aljannah ko kwana Uku basu yi ba ya Tattaro maryama Zuwa Bauchi bayan yayi sallama da Yan"uwansa ita kuma maryama Tayi sallama da yar"uwanta kwara Daya Tal aduniya wato Halima wacce ke Aure a nan garin Gada. Direct Gidan Alhaji Usman aka yi musu masauki,awani Shashe Dake gefe wanda bama Boysquaters bane Flat mai kyau aka kuma ingantasu da komai na More Rayuwa,Babu Abunda zasu iya cema Iyalan Dr.Saulawa sai Fatan gamawa da Duniya Lafiya,Cikin ikon Allah Maryama ta zama mai Taimakama Fatima da Aisha Duk da kasancewarta yarinya Domin Lokacin bata wuce Shekara 19 ba ammh akwai kwazo na matan kauye da kuma Biyayyah gata Shuru Shuru ba Ruwanta ga kwaici ga kunya,Anty Fatima Anty Aisha Sama Shi kuma Alhaji Usman Daga ita Har Abdullahi Yaya Suke Kiranshi yayinda Suke Kiran Dr Saulawa da Alhaji Dr. Ayayinda Gefe Daya kuma Abdullahi na Cigaba da kula da Kifayen da Alhaji Usman ke kiwo aikinsa kenan,Gidan Dr.Saulawa kuwa kowani Lokaci Suna Zuwa Shida Maryama Domin ganawa da iyayensa Danginsu na chan gada kan kawo musu Ziyara Lokaci Bayan Lokaci Ita ma Maryama Yayarta Halima tazo Taga inda take ta Dinga murna da Fatan alheri Ganin Maryama ta samu iyayen Daki na Gari Tunda Daga Fatima Har Aisha Suna matukar Tsausayin Fatima Shiyasa komai suka samu itace Shi kanshi Alhaji Usman din kallonta yake kamar Hannatu ko Rukayyah Shiyasa suka Rikesu Hannun Bibbiyu tun Bale ma Dr.Saulawa wanda akullun Usman yaje gaisheshi sai yayi Fadan Kula da Hakkokin mutanen Dake kansa Tunda Tamkar Amanace gareshi. Sannu Sannu Bata Hana zuwa sai dai Adade ba"a je ba Cikin Hajiya Fatima da Hajiya Aisha na kara Girma suna kuma samun Dukkan kulawa Domin Likita guda Dr.Saulawa Ya samu Daga asibitinsa tana Zuwa Duk bayan 4 weekes Tana Dubasu Tana musu awo Hankalinsu kwance Har Cikinsu ya Shiga Watan Haihuwa Wata Ranar Jumma"a Babba Rana Allah ya Saukeki Hajiya Fatima Lafiya inda ta Haifi santalelen Danta mai kama da Dr Saulawa,ko Mintuna Talatin ba"ayi ba itama yar"uwanta Hajiya Aisha ta Haifi Santaleliyar yarta mace mai kama da Alhaji Usman acikin asibitin Daya ke mallakin Surukinsu Wato Saulawa Speacialist Hosp Bauchi. Dama Hajiya Fatima na Fara mukurkusun naguda Abu kamar wasa Maryama ta Kira Hajiya mama ta gayamata Tunda Alhaji Usman baya Gida Ita tazo Da Direba ita da Atine Bayan ta Kira Dr.Saulawa yace ta kawosu nan asibitin yanzu,kamar wasa fa Harda Hajiya Aishan da Maryama Suka Shiga Motar zuwa asibiti sai dai kafin su kai asibitin Itama Hajiya Aishan Ta Fara Nagudan maimakon Hajiya Fatima Sai Dr Saulawa yaga Duka Surukan nashi ne ke kan gwiwa ganin haka yasa aka Shiga Dasu Bangaransu masu Haihuwa Domin basu Taimakon gaggawa. Haihuwan batayi Tambari ba Sai da aka gama Shirya masu Jego da yaran kana Hajiya mama ta Shiga kiran Waya tana Fadan Haihuwa murna ba"a mgana Alhaji Usman haka yazo asibitin kamar bakinsa zai Yage saboda Murna Maryama ita ke Tare da masu jegon a Dakin Hutu kuma Duka Jariran na Hannunta itama bakinta yaki Rufuwa iyayen Dakinta sun Haihu... Atare da Dr.Saulawa da D'ansa Alhaji Usman Suka Shigo Dakin na musamman da aka Kai su Hajiya Fatima,Hajiya mama da Atine na Binsu abaya suna Shiga bayan sannu da Barka daya Biyo baya sai Dr.Saulawa ya kalli Maryama yana Fadin"Maryama Mikominsu nan naji Dumin Jikokina..Allah yakai Raina.! Tana Mirmishintaa na kunya ta Tashi Ta mikamai Su Duka ya Hada ya Dauka Har Hajiya Mama namai Tsiyan bai bari Uban Yara ya Dauka ba yayi mirmishi yana Fadin"Nima Uba nake garesu Amina..Ko ba Haka ba Usman Bin Fodiyo..? Dariya yayi yana Fadin"Kwarai Abba..Tabbatas kai Uba kake garesu kai zaka musu Hudubu yanzu yanzu ka Sa ka musu Sunan da kaga yayi maka..Ai Dani da Matana Da ya"yan Dana Haifa duk ikon ka ne..! Kowa Mirmishi yake adakin Dr.Saulawa ya kalleshi yana Fadin"Allah yayi maka albarka kaida Matanka Usman Fodiyo..! Duka suka amsa da Ameen kujera Usman ya bashi ya Zauna ya Fara Daga macen ya mata Huduba aduka kunnuwanta kana ya Matsamata Dabino a baki kana ya mikama Usman yana Fadin"Allah ya Raya ZAREENA USMAN ABUBAKAR SAULAWA..! Ya karbeta yana Fadin"Masha Allah Ameen Ameen Abba.."Namijin ya Daga Shima yayi mai Huduba kuma ya Bashi Dabino Shi harda Ruwan zamzam ya mikama Alhaji Usman yana Fadin"Wannan yaron Magaji na ne..Tun a Suna na sakamai DR.ZAINULLAHI USMAN ABUBAKAR SAULAWA..Allah ya Rayamana Shi.." Gabadayansu suka amsa da Ameen kafin ya mike Alhaji Usman ya mikama Hajiya mama Jaririan ta Dauka kana ta mikama Atine itama ta Dauka ta saka Albarka kana ta mikama Maryama su Wanda Ta Nufi Hajiya Fatima Ta mika mata Zainullahi sai taki karba sai kawai ta saka Hannu Ta karbi Zareena Tana Fadin"Nifa ga yata nan..Mikama Aisha yaronta..! Kowa sai ya saki baki yana kallonta Jin Haka yasa Hajiya Aisha Tace"Naji bakomai..Maryama Mikomin Da'na..Dama mun Riga mun gama mgana nayi miki alkawarin in mace na Haifa taki ce Har Abada ke kuma in kika Haifi Namiji nawa ne Har Abada..Allah ya cikamana Burinmu sai dai muyi Fatan Allah ya tayamu Tarbiya..! Maryama Tana Mirmishi Tace"Nice Shaida..Ni kuma nayi alkawarin Tayaku kula dasu Tankamar ya"yan da zan Haifa da Cikina..! Gabadaya Dakin suka amsa da Ameen Mirmishin Farinciki da kuma Annushuwa ya wanzu a zuciyar Dr.Saulawa hakama Hajiya Mama da Atine Shi kuwa Alhaji Usman mamaki ya kamashi na yarda har suka Tsaida wannan alkawarin bai sani Hadin kan matanshi na Burgeshi kuma yana jin Duk Duniya ba wanda yakai shi Dace.. *Comments* *Share and vote* *Shakira...* *Intelligent writer"s asso...* *ZAINAZAIN..!* _(Is a love Story and Betrayal)_ *Wattpad:Jamilaumar351* *Mallakar:Janaftyshakira*❤️ *BOOK 1*             0️⃣5️⃣ "Dr.Abubakar Saulawa yafi kowa Murna da wannan Sabon Hadin kai Tare da alkawarin Dake Tsakanin Hajiya Fatima da Hajiya Aisha,sai dai kuma ya katse musu Hanzari Wajen basu Umarnin kowacce ta Shayar da Abunda ta Haifa da kanta Ammh alkawarinsu na nan bai Tashi ba Da Suka nemi sanin Dalili sai yace musu Saboda Halin Rayuwa Ko bakomai Tunda Dukkansu Suna Raye ya Zama Dole kowacce ta Shayar da Abunda ta Haifa da wannan matsayar aka Tsaya Inda aka Mikama Fatima Zainullahi ta Shayar dashi Ita kuma Aisha aka Mika mata Zareena ta bata Nono kuma Dukkansu suka kama Bayan Sun gama ba Jaririnansu Nono ne bayan sun Samu Natsuwa aka Sallamesu suka Dunguma Zuwa Gida Cikin Tsantsan Farincikin da baki bazai iya Furta shi ba. Kafin kace kwabo Haihuwan Tagama Karade Dangi kafin Suna ta Zagayo yan"uwa na Nesa Dana Kusa Sun iso kamar su Hannatu da Rukayyah Bashir da iyalansa Hakama Aliyu Shima Da nashi Iyalin Wacce Itama Cikinta Dan Kimanin Wata Shida ya bayyyana Dukkansu Sun Taru Domin Taya Dan"uwansu Murna samun karuwar ya"ya a karo na Biyu bayan Matansa Daya Aura Rana Daya. Ranar suna ansha Shagali Abunda sai wanda ya gani bayan Raguna Harda sa Dr.Saulawa ya sa aka Kada Saboda Haihuwan Jikokinsa aka Rabama Takalawa kowa fa ya Shaida wannan Haihun matuka kuma kowa ya Fahimci yadda Dr Saulawa ya Dauki Haihuwan da matukar Muhimmanci Shi da Hajiya Mama. Bayan Suna Baki da yan'uwa kowa ya koma Gidajensa aka bar masu Jego Maryama na Tare Dasu na Kula da yara Sai kuma Atine Dake zuwa Tana yima Su Hajiya Fatima wankan Tare da Umarnin Hajiya Mama ganin Maryam bawata Babbace bace Sai aka bar mata kula da yaran Wanda ko yake Kiransu da yan Biyu ganin Rana Daya suka Zo Duniya Kuma Duk da kowa Uwarsa ke Shayar dashi Ammh Da Zarar Kowacce ta gama Shayar da nata Hajiya Fatima Zata Karbe Zareena Itama Hajiya Aisha Zata karbi Zainullahi Har suna Rige Rige Wani Lokacin Maryama Ke ganin Dirarmar nasu Tayi ta bama Alhaji Usman in ya Dawo Labari Shi kuwa yana Jin Labari Nishadi da kaunar matan nashi na Kara Wutar Ruruwa acikin Ranshi... Wata Hudu da Haihuwan su Zareena Safiya Matar Aliyu ta Sauka achan Abuja Ta Haifi Santalelen Danta Jajir mai kama da Ubansa Wannan karon ma Dr.Saulawa ya Saka mai Suna Wato HADDIR ALIYU ABUBAKAR SAULAWA..! Tun Daga sannan kuma Babu Wata karuwa da aka Kara samu Sai Duka Suka maida Hankulansu Wajen kula da yaran da Allah ya basu,Bangaran su Zareena da Zainullahi kuwa Maryama ce keda alhakin kula dasu Har ma Sun Saba da ita,domin itace komai nasu Wankansu Saka musu kaya kula da Cin Abincinsu da kuma Cire Musu pampers in sun bata Duka itace Lokaci kadan Yaran suka Shaku da ita Bama Ita kadai Harda Abdullahi mijinta Sun Shaku Dashi Domin In Tagama aikinta Sassan su Hajiya Fatima kwasan Yaran take su koma Barayinsu Su tayi ta kula Dasu Ita da Abdullahi Tunda Shima ba wani aikin yake ba kula da Kifaye ne,da basu abinci Safe da Yammah Da ka gansu zaka Fahimci Suna Cikin Farinciki da Jin Dadin Rayuwa. Bashir Bai Haihu ba Sai da su Zareeena Suka Shekara Biyar a Duniya Yayinda Haddir keda Hudu da wani Abun Sun Girma Babu Inda kafarsu bata takawa Har an sakasu a Makaranta,Lokacin da Iklima ta Haihu Tasha Wuya Sai kuma Jaririn ya Fito bashi da lafiya haka akayi Suna yaro yaci Sunan Dr Saulawa Wato Abubakar bai kai Wata Biyar ba Allah yamai Rasuwa Tun kuma Daga Lokacin sai ya koma in ta Samu Ciki Sai ta Dinga Barinsa Ko kuma Sai yakai Wata bakwai ta Haifeshi Ba Rai,Sakamakon Ita Ikliman Binciken Likitoci Sun gano Tana da Raunin Mahaifa Sosai Gashi kuma ta Fara Palanning kafin Ta Haihu Shi ya jawo mata matsalan Bashir ya Damu Sosai Domin a Lokacin yana Bukatar Haihuwar ammh kuma Sai Allah ya Nuna ikonsa Dole babu yadda Suka iya suka koma Suka Rungumi Junansu Tunda bai isa ya Gujema Ikliman ba Koma meya Faru Shine Silan komai. Su Zareena Da Zain nada Shekara Bakwai Aduniya Zain kamar yadda Zareena Take Kiranshi Tunda bakinta bai iya furta Zainullahi din Sosai ba,sai Sunan Gabadaya yabi bakin iyayen nasu kowa da Zain yake Kiransa Ita kuma Hajiya Aisha Zain ne Tunda ya Fara koyon mgana ya Fara Kiranta da NENE shikenan kuma Sunan ya Bita ayayinda Zareena ke kiran Hajiya Fatima da UMMAN ZAREENA,saboda yadda Duk Duniya Hajiya Fatima Bata da Abun kauna da Tattali Irin Zareena Shiyasa Dr Salauwa Ya sakamata Umman Zareena sai kuma ya Bita har ya"yan suka kama Maryama kuma Mama maryama Abdullahi kuma Suna Kiranshi da Baba ne ayayinda Suke Kiran Alhaji Usman da Abba Tun Suna yara. Duk da kowa ya Fahimci mahaifiyarsa ammh yarintarsu bai Hana Sun Fahimci inda suka Fi Samun kulawa ba,Kowanne sai ya fi Nuna Doki ga inda akafi Jansa ajiki,Zain yafi Son Nene Saboda itace komai nashi Sai ko Mama Maryama Umma Zareena kuwa komai ta samu yarta ce Zareena Ko ta kan Zain bata Bi Tana mai alkunyar dan Fari da kuma Kawaicin Nuna ita Zareena ce yarta Da Farko Zain Din ya Fara nuna Damuwarsa Sai kuma Daga Baya da Nene itama Ta Tare komai nashi Sai Shima ya koma Tamkar itace ta Haifesa ba Umma ba. Mama maryama kuwa Tamkar Uwa Haka Suka Dauketa Domin Itace Komai nasu Sun Taso Sun ganta ne Ita da Baba Abdullahi sai suke kallonsu kamar wasu iyayensu kuma na Dabam Tunda Watarana ma nan Shashen Maryama Suke kwana In Tatashi aikinta Daga Cikin Gidansu zata Shashenta sai su makale mata Sai Sun Bita su kuma iyayen suce Tatafi Dasu Haka zasu Bita suje chan suyi ta Kirniya Abdullahi na Biye Musu Har barci ya Daukesu Maryama ta kwashesu zuwa kan gado ta kwantar Dasu bayan tayi musu addu"an Barci Cikin so da kulawa. Gidan Dr Saulawa kuwa Suna yawan Zuwa Musu Weekend ko Hutu Duk su nasu baya Wani Dadewa Suna kusa da gidan iyayensu Haddir ne kulafunci Zuwa Hutu Bauchi Saboda Su Zain Wadanda Tun Suna Yara mafarin Abotansu ta Fara Su ukun Haka mafarin Rayuwarsu Ta Fara Da Shakuwa da kaunar Juna Barin Ma Zain da Zareena Tamkar yan Biyu haka suke wanu bai isa ya Taba Wani ba acikinsu Hakama Haddir sunfi Shakuwa da Zain sosai kan Zareena,ita Suna yawan Fada Tunda Tana ganin yana so ya nuna yafita son zain sai suyi ta Fada Sai Maryama ta Raba Fadan ko kuma Chan Gidan Hajiya Mama ko Atine su Raba Tsiyan Da karfi da yaji Haddir ya Dawo Bauchi yaki Abuja Dr.Saulawa yace su kyaleshi cikin yan"uwansa Dole suka barshi Alhaji Usman ya Dauki Haddir ya sakashi makarantar da  su zain suke zuwa mai Suna International School Bauchi,Iyayensa basu wani Damu ba Tunda Lokacin Safiya Tana Goyon yarta mace Da Ta sake Haihuwa mai Suna Hamdiya. Kwatsam Megadin Gidan Alhaji Usman yazo ya sameshi kan Zai ijiye aikinsa yana so ya koma Garinsu Mahaifinsa bai da lafiya karfi ya karemai zai koma yayi Jinyarsa Hakika Alhaji Usman Yaji ba Dadi Saboda Sun Saba Da Yusha"u megadi ammh Uba ya wuce wasa Hakanan yayi mishi Fatan samun Lafiya ga Mahaifinsa kuma ya Hadamai Sha Tara na arziki Suka Rabu Faruwar haka sai Alhaji Usman ya Fara Tunanin Samun wani Megadin Jin haka yasa Maryama ta Shawarci Mijinta kan me zai Hana Shi ya karbi Gadin Yayi Tunda dai ba wani aiki yake yi ba karamcin Su Alhaji Garesu yasa Ya amince mata kuma ya samu Alhaji Usman din da mganar da Farko yaso yaki Tunda ya Nuna Tamkar kani ya Dauke Abdullahi Shi kuma ya Dake sai yayi mgana dai Har ta kai ga Dr.Saulawa Da Mallam Umar Shi Mallam Umar shi ya kashe mganar inda yace Sai dai In Usman bai yarda da Abdullahi ba Ammh in ya yarda Dashi ya barshi yayi mai gadin Tunda Ba wani Abu yake ba Dole Alhaji Usman ya Amince ammh Har Cikin Zuciyarsa baya Kallon Abdullahi Da maryama wasu Bare yana kallonsu nr amatsayin Wasu Shakikan yan"uwansa.. Faruwar  Haka da wasu Wattani Ciwon Daji mai Tsanani ya kwantar da Mallan Umar da Farko Abun kamar Ba Ciwon Daji ba Sai da Dr.Saulawa yayi ta Shige Da Fice dashi a asibiti kana aka Fahinci Ciwon nashi Duk da kokarin da Dr Saulawa ya Dinga yi Bai Hana Mallam Umar Rokon alfarman Su barshi ya koma ga Ahalinsa yayi Jinyar achan ba,Yana Tunanin Ciwonsa bana Tashi bane Da Farko yaki Sauraransa ammh ganin yadda ya dinga Rokonsa sai bai ki ba Lokacin da Mallam Umar da Atine zasu koma Gada da Zama Gabadaya Ahalin Dr.Saulawa Sun Girgiza Sakamakon Sabo Ammh ba yadda zasu yi Tunda Mallam Umar ya nuna musu ko basu ga Abdullahi da Maryama nan Tare dasu kuma in da Rai ba"a Rabu ba. Suna ji suna gani Haka zamansu ya yanke a garin Bauchi Ashe kuma ta Har Abada ne,Da komawarsu Garin Gada da Rasuwar mallam Umar Kwana Ashirin ne yace ga garinku ne hakika ba Yan"uwan Mallam Umar kadai sukai Rashi ba Hadda Dr.Saulawa da Duka iyalansa,domin dasu akayi zaman gaisuwar har akayi bakwai Saboda Atine wacce Tunda Taji Mutuwar Mijinta ta yanke jiki ta Fadi ko da ta Farfado ba Baki Ance Jininta ne yayi bala"in Hawa. Bayan addu"ar Bakwai su Hajiya Mama suka Dawo Bauchi Harda Abdullahi da Maryama Saboda Yara,Wanda Suna Gida Tare da iyayensu sai dai suna Ta Kuka da kiran sunan maryama din Da Abdullahi,Allah mai Gagara Misali Rasuwar mallam Umar da Wata Biyu itama Atine ta Bisa kuma ta Rasu ne Akarkashin Kulawan Likitocin asibitin na Dr Saulawa Tunda yaje garin yaga Halin Datake Ciki ya Daukota ashe bazatayi Tsawon Rai ba Duka Duka kwanta Biyu a asibitin tace ga garinsu nan. Duka Chan suka Tafi Gada Tunda Dangin nata sun Nuna Chan suke so ayi mata Sutura Hakika Hajiya mama tafi kowa jin Mutuwar Atine awannan karon sai kuwa Abdullahi Daya Dawo Maraya Sadakar uku kawai Sukayi suka Dawo ammh Sun bar Abdullahi da Maryama achan sai da akayi bakwai suka koma Cike da alhinin Rasa Iyayen nasu Domin Ita kanta Maryama Bayan yayarta Halima bata da kowa sai iyayen Mijinta Abdullahi. Bayan Dawowarsu ne kuma Umma Zareena ta Fara Laulayin Ciki wannan karon ita kadai ce Sai kuma Matar Bashir itama Iklima da ta Fara Nata laulayin Cikin,Kwanci Tashi ba wuya a wajen Allah Umman Zareena ta Haihu Da kwana Uku iklima ta Haihu kuma Duka maza Suka Samu Bashir sai ya maida ma Dansa Sunan Dansa na Farko Daya Rasu Abubakar hakama Abba Usman Shima Abubakar din ya saka ma nashi Suna Kiranshi Sadiiq Babba Yaron Wajen iklima kuma Suna Kiranshi Sadiq karami. Wannan karon ma Nene tayi Ruwa Tayi Tsaki kan Abata Sadiq Babba Har Dr.Saulawa da Jikokinsa ke kira Alhaji Tsoho yayi mata Lakabi da Nene Uwar Maza Domin Allah ya Doramata Son Haihuwan ya"ya Maza Sai dai kuma Allah bai bata ba Shiyasa,Zain da Sadiq babba Suka koma Tamkar sune ya"yanta Ita kuma Umman Zareena Dama Uwar matace Domin Itama Tafi son ya"ya mata Sai aka Raba kowa yaja Nashi Cikin zaman lafiya da kwanciyar Hankali. Sadiq Babba nada Shekara Daya da wani Abu Ciki ya Bulla ajikin Maryama Murna Wajen Nene da Umman Zareena Ba"a mgana kamar su Za"ayi ma Haihuwan,Ita kanta Maryaman Tana Farinciki Domin Sosai Take son ganin kwan ta adunya koda Kwara Daya ne,Duk da Su Zareena Sun Debe mata wannan kewan komai Mama Maryama kinga Haddir ko.? Mama maryama Kinga Zain ko..? Mama maryama kin ga Xareena ko..? Aikinta kenan Cikin Rabon Fada da alkalanci. Tunda Cikinta ya Fito yaran suka Fahimci Tana da Ciki suka kama Murna Kada ma zain yaji labari Domin Tun Sanda yaga Cikin Mama maryama yayi Girma ya Tambayeta ya yaga Cikinta yayi kato ko Bata da lafiya ne..? Lokacin Tana Shashen Su Umman zareena ne Nene ce Ta bashi amsa da Cewa kani za"ayi musu ko kanwa Yana jin Haka ya Bata Rai yace Shi Gaskiya Mata yake so Mama maryama ta Haifamai Kowa sai da yayi mamakin kalaman yaro Dan Shekara Takwas da Wani Abu sai dai Ba Abun mamaki bane sanin Halin manyance irin ta Zain kamar wani Babba Kowa ya Bude Baki Yana kallonsa Sai Mama Maryama Taja Jikinta Tana Fadin"Karka Damu D'ana zain...Nayi maka alkawarin in mace na Haifa Na baka Ita matsayin mata Ko da bana Raye in kuma Namiji ne zan baka shi a matsayin Karamin kani Wanda zai iya ma Yayansa Biyayyah Har karshen Nunfashimsa..! Kowa ya Dauka kalaman Maryama da Zain amatsayin Wasa ne Har da Alhaji Usman ya Dawo Matansa ke gayamai yana ta Dariya,Ashe a Bangaran Maryama Da Zain ba Haka bane Shi da Gaske yake Cikin yarinta ita kuma Da gaske take Cikin Son Cikamai alkawarin Tana jin Babu Abunda zata mallaka wanda ba zata iya mallaka ma Iyalan Dr.Abubakar Saulawa ba. Tunda ga Lokacin Komai Zain ya samu sai yace na Matar sane wanda Mama Maryama Zata Haifamai ko makaranta yaje baya kashe kudi wai yana Tarawa zai Siyama Matarsa Babyn Wasa,Komai dai ya Samu ko naci ne sai ya Tsakura yace na Matarsa Wacce Mama maryama Zata Haifamai ne,Tun ana Daukan Abun Wasa Har dai aka Fahimci Zain Da gaske yake Labarin kuma yakai ma Kowa,kowa kuma sai Dariyan Kuruciyar Zain yake da Shirmensa Lokacin da Cikin Maryama ke Wata na Shida Umman Zareena itama ta samu Ciki kuma kusan Lokaci Daya Suka Fara laulayi da Nene Wannan karon ma. Cikin kwanciyar Hankali Duka Suka Cigaba da Rainon Cikinsu Har Cikin maryama ya Shiga Watan Haihuwarta sai Yayarta Halima tazo akan Tana son Tafiya Da maryama Chan Gida taje ta Haihu ammh Sai Alhaji Usman ya Hana yace Maryama Tamkar kanwa take garesa Saboda Haka anan zata Haihu Karamci Irin nasu yasa Halima Batayi Gaddama ba Ta Tsaya ta kwana Biyu Ranar

Chapter 5 of 32