Jikin mai daban-daban har karkarwa yake, ya fara yankawa Laraba nama. Ya kalli wani yaronsa ya buga masa tsawa a kan ya karɓi buhun hannun Laraba ya je ya gyara su. Bayan ya miƙa wa Laraba balangun ta ce.
"Na gode sosai masoyina mai daban-daban, yanzu waɗannan zabin idan ka gama gasa su ka ajiye da daddare zan zo na karɓa." Mai daban-daban ya amsa mata yana washe baki. Laraba har ta yi gaba ta waiga ta sake jan kunnensa, a kan kada ya aika zabin gidansu za ta dawo ta karɓa da kanta.
Mahmud bai yi tafiya mai nisa ba, isa bakin wani babban symbol ɗin sabulun wanka da ke gefen titi. Ya ciro waya ya kira abokinsa Muddasir, wanda suka yi da shi za su haɗu a adaidai wurin da ya kwatanto masa. Bugu biyu wayar ta yi ya ɗauka. Daga can ɓangaren ya ce.
"Ga ni nan ina hango ka na kusa ƙarasowa!"
Daga haka Muddasir ya katse. Cikin ƙasa da minti ɗaya mai adaidaita sahu ya sauke shi. Sai da Mudassir ya biya shi kuɗinsa ya ƙarasa wurin motar Mahmud ya ce, "Mutumina ashe ka gane kwatancen!"
Cike da damuwa Mahmud ya ce, "Allah ka yi mana tsari da ƙauye, yanzu saboda Allah a nan za mu yi service?" Mudassir ya yi murmushi yana zama a sit ɗin gaba ya ce.
"Kai kukan daɗi kake yi, da muka samu aka canza mana school zuwa ta garin Gangaren dutse? Da ace an bar mu a garin Rafin gurgu fa? Yanzu ba ga su Haidar can ba suna fama."
Mahmud ya saki guntun tsaki ya ce, "Yanzu ina za mu bi mu ƙarasa garin Gangaren dutsen?"
Mudassir ya nuna masa hanyar shiga garinsu Laraba, gabansa ne ya faɗi amma sai ya basar don ba ya san ya sanar da Mudassir abin da ya faru da shi ya yi masa dariya.
Ganin sun tunkari hanyar garinsu Laraba ya sa Mahmud ya ce, "Wai ina ne garin? Mun kusa zuwa ko da saura. Mudassir ya ce, "Mun kusa zuwa, da ka miƙe za mu bi ta kan doguwar hanyar can har ƙofar gidan mai gari, ka san dole sai mun gabatar da kanmu a wurinsa tun da zama ne ya kawo mu.
A hargitse Mahmud ya taka burki cikinsa yana kaɗawa, Mai garin da ya gama sakawa zawo a wando ne za su je wurinsa su gabatar da kanku?
"Lafiya Mahmud?"
Mahmud da gumi ya gama rufe shi kamar zai yi kuka ya ce.
"Wallahi ba lau ba Mudassir."
Ya ƙarasa maganar yana yin parking ɗin motar a gefen hanya, sai kawai ya kifa kansa a kan sitiyarin motar.
Cike da shauƙi Mai Yasin yake kallon Inno jin amsar da ta ba shi, dangane da sanar da iyalanta a kan maganar aurensu. farinciki fal zuciyarsa ya ce.
"Allah mai haɗa jinin mumini da mumini, Allah kaɗai ya san alkairin da yake ɓoye da silar haɗuwarmu a Saudiyya. Haka kawai na ji kin sake kwanta mini Inno, a gaskiya marigayi ya dace da mace."
Inno ta saki murmushin jin daɗi kanta a ƙasa, ita dai nutsuwar Malam da daɗaɗan kalamansa waɗand ta rasa a baya suna birge ta. Har a cikin zuciyarta tana jin ina ma tun tana budurwa, Allah Ya aiko mata shi cikin rayuwarta, da babu yadda za a yi ta yi rayuwa da tsohon mijinta da ko kaɗan bai iya soyayya da tarairaiyar mace ba. Mai Yasin ya saci kallonta da gefen ido ya ce. "Innota ko ba kya jin daɗin yabon da nake yi miki? Ko da za ki ji babu daɗi sai dai ki ji, amma Allah Ya sani ƙaunarki ta jima da ɗamfaruwa a cikin zuciyata."
Inno ta ɗago ta dube shi ta ce. "Haba Malam, ai duk macen da ta yi dace da kai a matsayi mace ta more a gidan duniya da Lahira."
'An zo wurin, dama nan nake ta jiran mu ƙaraso.'
Malam ya raya a cikin ransa, yana murmushi mai ɗauke da manufa a ransa. Ya ƙanƙance murya cikin yaudara da karuwanci ya ce.
"Wallahi tun da na wayi gari jikin nan yake son dawo mini Inno, ga bakina salam babu daɗi kamar yawun mage. Nace ko zan samu koda kaza ko naman kasuwa?"
Inno ta sauke ajiyar zuciya, tana mamakin yadda Mai Yasin ba ya gajiya da murƙushe cinyoyin kaza, amma da ta tuna a kullum ya ci kazar ya kuma sharɓi romonta ƙara samun lafiya yake sai ta ce.
"To Malam ka ga dai yaran nan ɗazu kusan baram-baram muka rabu da su dutse a hannun riga, kuma dama mai ƙoƙarin sayo maka Iro ne. Yanzu dai ban san cikinsu wa zan tunkara ba, tun da kazar jiya ma shi ya taho da ita."
Mai Yasin yana gama jin haka sai kawai ya fashe da kuka, ya fara jan magina yana matsar ƙwallah. Sororo Inno ta yi jiki a sanyaye ta ce.
"Lafiya malam?"
Mai Yasin ya ja majina ya ce, "Kaico rashin haihuwa, kaicona Allah ka cigaba da ba ni dangana. Da 'ya'yan da na haifa ne ai duk tsiya za su kawo mini duk kuwa yadda muka yi da su, yanzu kamar dai garken wannan yaron Inu har sai na tambaye shi idan na yi niyyar ɗiban kaji ko zabi? Amma tun da ban haifa ba dole na yi haƙuri da rayuwa."
Shiru Inno ta yi tana nazari don ta san mammaƙo irin na Yaya Inu, amma don ta kawar da damuwar Malam sai ta ce.
"Daga yau kada ka sake faɗin yaran nan ba kai ka haife su ba, kai tamkar mahaifinsu ne kuma duk abin da kake muradi, ka yi kanka tsaye ko ka tambaye ni idan kana jin nauyi."
Malam ya hau gyaɗa mata kai, Inno ta miƙe tsaye har ta je bakin ƙofa ta juyo ta ce.
"Kaji kake so ko zabi?"
Malam ya sake narkewa a katifa yana sakin murya a dole shi marar lafiya ya ce, "Idan da so samu ne a samo matasan samarin zakaru masu jini a jika, tun da ai muma a wannan satin ne tariyarmu!" Inno ta saka mayafin ta rufe fuska ta fice tana dariya, tana fita Mai Yasin ya buga tsalle a kan katifa yana rawar oya shake body.
Kai tsaye sashen Yaya Inu Inno ta nufa, a lokacin da ta je ba ya nan sai matansa. Cikin girmamawa suka gaishe ta, bayan ta amsa ta ce su buɗe mata garken awaki da shanunsa. Kusan lokaci ɗaya suka kalli juna, Larai ta yi ƙarfin halin faɗin.
"Inno amma bai ce za ki zo ɗaukar..."
Cikin tsawa Inno ta katse ta.
"Dama ban ce miki na faɗa masa ba, Malam ne ya ce mini yana sha'awar matasan samarin zakaru ni kuma na zo zan bincika masa, idan ya zo ki sanar da shi abin da na sanar da ku." Daga haka Inno ta nufi garken ta hankaɗa ƙofar zagayen da ƙafarta. Safare da Dubu 'ya'yan Yaya Inu ne suka taya Inno ɗiban zakarun guda uku ta fice da su, ta yi wa Malam magana da kansa ya fito zuwa bakin rariya ya yanka su. Inno ta ɗora ruwa ta shiga gyaran kaji, sai ga shi babu jimawa ƙamshin farfesun kaji ya cika gidan, ta zuba a babban food flask wanda ta saba zuba wa Malam ta kai masa. Ta ɗebi ɗan madaidaici ta ragewa Laraba a kai, ƙafa da wuya a cikin tukunya.
Cikin sauri Yaya Inu yake tafe, hannunsa riƙe da baƙar leda wacce take cike da sababbin magunguna da ya taho da su daga bakin kasuwa. Saurin da yake yi La'asar ta ƙarato, ga shi mai maganin sanyin da ya saya ya sanar da shi ba a wuce ƙarfe huɗu na yamma ba tare da an dafa an sha shi ba, saboda ƙa'idarsa kenan. Shi kuma a ranar yake son yin amfani da shi kuma ba ya fatan lokaci ya ƙure, shawo kwanar da zai yi ne ya ci karo da Hajara tsohuwar matarsa wacce ya ji labarin mijin da take aure ya mutu. Dama tun da ya saki Abu zuciyarsa ta shiga wasu-wasi a kan ya dawo da ita.
"Ranki shi daɗe, yau Hajara ce a gari?"
Yaya Inu ya faɗa yana washe baki, Hajara ya ɗan yatsina fuska ta ce.
"Eh ni ce sai aka yi yaya Inusa?"
Yaya Inu ya fara gyara zaman hularsa ta tashi ka fiya naci, ya saka hannu yana gyara wuyan rigarsa yana murmushi ya ce.
"Hajarata tun rannan nake ta so na zo mu gaisa, saboda kin san lamarin duniya komai ɗan haƙuri ne. Wallahi na so na zo na yi miki gaisuwa ma amma Allah bai nufa ba, na ce ƙila ma rabona ne ya yi gaba da marigayi."
Hajara ta ƙanƙance ido cikin masifa ta ce.
"Rabon me? Allah Ya tsare ni da komawa gidanka Inusa, ai ni babbar godiyar da na yi wa Allah da ya sa ban haihu da kai ba. Da zaman yunwa zan ji ko da rashin sutura, kai yanzu ba ka ga yadda na koma ba?"
Yaya Inu ya yi shiru yana bin ta da kallo cike da so, don ta yi shar fatarta har ƙyalli take. Dama ya ji labari an ce a gidan tsohon mijinta ta haɓɓaka uwar gida.
"Ai yanzu wutsiyar raƙumi ta yi nesa da ƙasa na wuce ajinka wallahi Inusa, su dai waɗancan wahalallun matan naka sai su yi ta zama kafin layin saki ya biyo ta kansu."
Tana gama maganar ta yi gaba, ran Yaya Inu ya ɓaci ga rashin samun haɗin kanta da na baƙaƙen maganganun da ta faɗa masa. Ya bi ta da sauri ya ce.
"Banza 'yar wahala an faɗa miki ba zan samu wacce ta fi ki ba, ki zuba ki gani nan da kwanaki kaɗan zan ɓarzo wacce ta fi ki komai." Hajara ba ta kula shi ba ta yi gaba, shi ma Yaya Inu ya ƙarasa gida rai a ɓace.
Tun daga bakin ƙofa ya fara yin ball da kwanika saboda yadda yake a fusace. Hakan ya sa su Larai suka sake shiga taitayinsu, yadda ya ga sun yi tsuru-tsuru ne ya sa ya fahimci abin da ya faru.
"Lafiya kuka yi wani zumu-zumu da idanu kamar an shaƙe zakaru?"
Indo da har lokacin haushinsa take ji, saboda abin da ya yi mata dariya ta kusa ƙwace mata amma sai ta danne ta ce.
"Zakaru kam ai ba shaƙa kaɗai suka sha ba, karo suka yi da wuƙa yanzu ma sun wuce birnin tumbi."
Yaya Inu ya haɗe fuska ya ce, "Abokin wasanki na zama Indo?"
Indo ta fara tafiya irinta ta kai kajiyo, sannan ta sanar da shi abin da Inno ta yi. Jikinsa ne ya shiga karkarwa saboda duk duniya babu abin da yake saurin ɗaga hankalinsa irin a taɓa garkensa. Da sauri ya nufi sashen Inno ya same ta a ɗaki ya ce, "Inno na ji wani zance a kan garkena." Jin haka ya sa Mai Yasin da ya ke zaune a ɗakin Inno ya tauna wani ƙashi wanda ya ja hankali Yaya Inu, wani ƙululun baƙinciki ya tokare maƙoshinsa, ya haɗiyi yawu mai ɗaci yana sauraron Inno.
"Ubanku ne yake marmarin matasan samarin zakaru, shi ne na lalubo 'yan matsakaita uku na yanka masa."
Yaya Inu ya fara huci ya ce, "Amma Inno ko za ki ɗiba ai sai ki sanar da ni."
Mai Yasin ya yi farat ya ce, "Kai Inusa kana neman albarka kuwa? Saboda mahaifiyarka ta ɗebi zakaru uku ka zo za ka yi mana tijara, kai yaro ka shiga hankalinka ka nemi albarkar uwa."
Haushi ya sa yaya Inu ya tunkari Malam yana jin kamar ya murɗe masa wuya, da sauri Inno ta sha gabansa ta ce.
"Ni ka dake ni Inusa ka ji! Ka dake ji na ce."
Shiru Yaya Inu ya yi saboda yadda zuciya ta ciyo shi, sai kawai ya fice daga ɗakin.
Malam ya jima yana zuga Inno ai kuwa ta cika ta yi fam, daga haka ya koma ɗakinsa ya zura doguwar riga ya tafi banɗaki zai yi wanka. Yaya Inu yana daga harabar gidansa ya hango shi, ganin Malam ya shiga wanka ya sa shi faɗawa ɗakinsa da sauri ya ɗauko wani ƙullin yajinsa, ya zura wata doguwar dorina a aljihu ya nufi banɗakin da Malam ya shiga. Sai da ya laɓe ya ji malam ya saɓa sabulu a fuska sannan ya banka banɗakin ya watsa masa yaji a fuska, Malam yana shirin yin magana saboda yadda ya ji an banko ƙofar banɗakin ya ji an zuba masa abu a fuska. Da sauri ya buɗe ido zafin sabulu da na yaji ya haɗe masa a ido lokaci ɗaya, cikin zafin zuciya Yaya Inu ya shiga zabga masa dorina ta ko ina.
07062062624
Ummou Aslam Bint Adam🌚
[14/12/2024, 19:51] Ameera Adam: *GIDAN LIKITOCI*
©®AMEERA ADAM
*FIRST CLASS WRITERS ASSO...*
Tsokaci: Ban amince a sauya mini littafi ta kowacce siga ba tare da izinina ba, yin hakan na iya kai wa ga matakin Hukuma don haka a kiyaye.
*MARUBUCIYAR:*
MARWAN
JARIRI
ASEELA
BAƘAR DAULA
AN YA BAIWA CE?
ƊAN BA ƘARA...
SHU'UMAR MASARAUTA
DUBU JIKAR MAI CARBI
UWANI 'YAR ƘASHIN GWIWA
YAWON SALLAR HAJIYA IYA
ZAUJATU JINNUL-ASHIQ
SANADIN RAGON LAYYA
https://youtube.com/@ameerahaadam9365?si=xyR-pHK5EjkLjQnd
Don Allah duk wanda ya ci karo da wannan page ɗin, ya taimaka ya yi mana Subscribe a youtube channel ɗinmu.👆🏻👆🏻👆🏻
SHAFI NA BAKWAI
Tun da mahaifiyarsa ta kawo shi duniya bai taɓa jin azaba irin wacce yake ji ba, a tsammaninsa aljanu ne suke yi masa wannan izayar don haka Malam ya shiga karanto duk wata addu'a da ta zo bakinsa. Ban da kuka babu abin da yake yi, a zuciye Yaya Inu ya ce masa.
"Wallahi koda wasa idan ka sake cewa za ka ci kaza ko zakaru a gidan nan, sai na yi maka abin da ya fi haka. Munafikin Allah dama ba ka san haushinka nake ji ba, ubanmu ya kwanta dama sama da shekara ashirin Inno ba ta taɓa marmarin aure ba sai a kanka. In sake jin ka saka ta, ta taɓa awakina wallahi sai na lahira ya fi ka jin daɗi."
Daga haka Yaya Inu ya fice daga banɗakin kai tsaye ya wuce ɗakinsa ya sauya kayan jikinsa. Kai tsaye garken awakinsa ya shiga, wani sabon takaici ya mamaye masa zuciya musamman da ya tuna danƙwala-danƙwalan zakarun da Inno ta saka aka yanka.
Tun da ya fara magana cikin gargaɗi Malam ya fahimci Yaya Inu ne, sai da ya ji ya fita daga ɓanɗakin ya yi ƙoƙarin buɗe idonsa ya ji wata azaba ta ratsa shi. Ruwa ya laluba ya shiga kwarawa, ai kuwa ya ji kamar yana zuba wa jikinsa ruwan zafi saboda raɗaɗin da yake ratsa shi. Malam bai wata-wara ba ya fito a guje yana ihu da neman taimako haɗe da faɗin.
"Jama'a taimako, wani marar imanin zai hallaka ni. Jama'a ba kwa ji na ne ku kawo mini ɗauki."
Ihun da Malam yake yi ne ya ja hankulan mutane yara da manya, sai dai manyan da sun yi arba da shi suke komawa a guje. Labaran da Rahina ne suka shigo ba tare da sun san abin da ya faru ba, Rahina da Malam suka yi gware tana yin arba da shi ta kurma ihu suka shige sashensu ita da Labaran a guje. Ɓaɓatun da Malam yake yi ne ya sa Inno ta fito a tsorace ta ce.
"Malam lafiya kuwa?"
Turus Inno ta yi ta zuba hannuwa a ƙirji cikin tashin hankali, shi kuma Malam jin muryar Inno ya sa ya tunkare ta da gudu yana faɗin.
"Inno ki taimaka mini idanuwana za su makance, Innota jikina azaba yake yi mini kamar ana babbake ni."
Inno ta zuba kabbara ta fita da gudu tana faɗin.
"Malam ka yi mini aikin gafara wannan aikin ba nawa ba ne."
Malam Ya rufa mata baya har sashenta yana faɗin.
"Inno a gidan nan ke kaɗai ce kike ƙaunata, ki taimaka mini ki ce iyalina ta gobe."
Inno ta banka ɗaki da yake sashenta shiru yake babu kowa, sai hakan ya sake ɗaga hankalinta ga Malam ya biyo ta a gigice. Ta danna sakatar ɗakin ta ce, "Ka gafarce ni wannan aikin na maza 'yan uwanka ne." Duk bugun da Malam ya yi Inno ba ta buɗe masa ba.
Ana cikin haka Baba Ado ya shiga ya same shi, ko kaɗan bai ji daɗi ba domin tun a ƙofar gida aka fara ba shi labari. Towel ya miƙa masa murya a daƙile ya ce.
"Ka suturce jikinka."
A fusace Malam ya yi warci towel ɗin ya yi wurgi da shi ya ce, "Suturar banza da wofi, kai idan za ka taimaka mini ka ba matsa daga gabana, domin ni kaɗai na san bala'in da nake ciki." Tsaki Yaya Ado ya yi ya ce, "Wallahi idan ba ka ɗaura towel ɗin nan ba, zan tafi na bar ka. Darajar tsufanka na gani shi ya sa na zo taimaka maka, idan ba haka ba wallahi da sai dai ka yi ta zama a haka."
Sanin halin nunkufurcin Yaya Ado ya sa da sauri ya fara lalubar towel ɗin ya ɗauka ya ɗaura a ƙugunsa, kamar ƙaramin yaro haka ya zaunar da shi ya shiga wanke masa fuska da ruwa da sabuli. Zafin ciwukan da dorinar ta ji masa ya sa ya dinga ihu kamar yaro ƙarami, a haka har Yaya Ado ya gama wanke masa sai dai har lokacin wani irin raɗaɗi yake ji. Har ɗaki Yaya Ado ya raka shi ya haye katifa yana rawar ɗari, nan take zazzaɓi ya rufe shi.
Tun lokacin da Bala wanzan ya gama yi wa Ɗan Bishir kaciya ya shiga kiran layin Baba Sale, sai da ya yi ta maza ya ɗauka a nan yake sanar da shi an gana yi masa kaciyar. Jiki a sanyaye ya fita ƙofar gida, yana yin ido huɗu da Ɗan Bishir ya ji wasu zafafan hawaye sun zubo masa.
Da ƙyar ya miƙa hannu ya karɓe shi, har zai shiga gida abokinsa Sani wanzan ya zo wucewa. Ya kalli Baba Saleh sai kawai ya tuntsire da wata irin dariya, wacce shi kaɗai ya san manufar yin ta. Haka kawai gaban Baba Sale ya faɗi, amma sai kawai maze ya wurga masa harara ya shige gida.
Ɗan Bushir ban da yage baki yana kuka babu abin da yake yi. Yana zuwa ya kwantar da shi a kan gado, ya sa gefen rigarsa ya share hawayen ya ce.
"Ɗan Bishiririna! Ɗan Bishiri ka yi haƙuri ban kyauta maka ba ko? Yanzu me kake so na sayo maka?"
Ɗan Bishir ya kalli gabas da yamma, ya kalli mahaifiyarsa da ke gefe a zaune kalli mahaifinsa. Sai ya sake ɓarke baki ya saki kuka.
Ƙirjin Baba Sale ya buga da ƙarfi ya jikinsa yana rawa, ya rungume Ɗan Bishir ya dubi Uwale fuska shaɓe-shaɓe ya ce.
"Uwale tsoro nake ji, wallahi ina cikin tashin hankali."
Uwale ta sauke ajiyar zuciya, saboda ta san za a yi haka ko ma fiye da haka.
"Me ya faru mai gida?"
Baba Sale ya ja gefen ɗan kwalinta ya share hawaye ya ce. "Ina tsoron ko dai an guntule Ɗan Bishir gabaɗaya, Uwale kada fa Bala wanzan ya nakashe mini ɗan ɗaya-ɗayana..."
Kuka ya ci ƙarfinsa.
"Yanzu mai gida duk yaran da ka dinga yi wa shayi, iyayensu ba su ce za ka nakasa musu 'ya'ya ba sai da abin ya zo kanka? Kamar ba ka san yadda Bala yake da ƙware a harkar wanzanci ba? Kar ka manta shi fa ɗan gado ne."
A hassale Baba Sale ya ce.
"Kowa ai nasa ya sani, ni gudan jinina kuma magajina na sani don haka a kansa zan yi magana..."
Ita ma Uwale ta katse shi.
"To ai ɗa na kowa ne, shi ya sa ɗa da dukiya ba a yi musu mugunta. Kuma hausawa suka ka ƙi naka duniya ta so shi, ka kuma so naka duniya ta ƙi shi. Wallahi wannan zazzafar soyayyar da kake yi wa Ɗan Bishir ba za ta kai ka ba. Don ba zan ɓoye maka ba a cikin gidan kowa haushinsa yake ji, ko kaɗan ba shi da farin jini a wurin yara da manya."
Wani irin kallo ya shiga wurga mata, yana jin a ransa yadda ta caɓa wa Ɗan Bishir baƙaƙen maganganu da ace ba a yi masa kaciya ba, babu abin da zai hana bai kora ta gidansu ba. To don dai ya san idan ta tafi babu mai jinyarsa.
"Baaabaaaa!"
Ɗan Bishir ya furta a shagwaɓe, da sauri Baba Sale ya amsa masa sai ya ce.
"Zan ci abincin Rahina, daɗi gare shi. Ni ba zan ci komai ba sai abinci ko shayinta."
Zumbur Baba Sale ya miƙe ya ce, "Ai kuwa yanzu zan karɓo maka, zauna Ɗan Bishiririna ga ni nan zuwa." Ya ƙarasa maganar yana zuwa bakin ƙofa, ya waigo yana jifan Uwale da harara ya ce.
"Shi Ɗan Bishir dai ya zama kabewar kan kabari baƙincikin mai taushe, duk wani mahassadi sai dai ya gan shi ya ƙyale."
Daga haka ya fice daga ɗakin.
Kai tsaye sashen Labaran ya wuce, daga bakin ƙofa ya tsaya yana sallama. A lokacin Rahina ta tsakar gida a zaune tana shan iska, Labaran yana wanka a ta bayan kitchen ɗinsu don ya ce kafin ya samu kuɗin da zai rufa musu banɗakin sashensu, a nan za su dinga wanka saboda abin da ya faru da Rahina.
"Wa alaikassalam."
Rahina ta amsa sallamar tana yunƙurin miƙewa domin ta saka hijabinta, daga can gefe ta ji Labaran ya ce.
"Kada ki sake ki ƙara magana."
Shiru ta yi saboda ta san zafin kishinsa, shi kuma Baba Sale jin an amsa ya saki murya ya ce.
"Amarya mai daɗin tuwo da miya, angon na ki yana ciki?"
Wannan yabon da Labaran ya ji ana yi wa Rahina ya sake ɓata ransa, don haka ya zura gajeren wandonsa ko kunfar jinsa bai wanke ba ya fita fururu ƙofar gida.
"Lafiya Labaran me yake faruwa?" Baba Sale ya furta fuska ɗauke da mamaki.
Labaran ya yarfe kumfar fuskarsa ya ce, "Ita ta kawo haka! Ka san dai abin da ka aikata haramci ne ko? Ka zo ƙofar gida ka zage muryarka kana magana iyalina tana sauraronka, ba ka tsammanin ta ji muryarka ta yi mata daɗi?" Ran Baba Sale ne ya ɓaci, amma da ya tuna Ɗan Bishir ya zo nemarwa abinci sai ya wayance.
"Labaran kenan, yanzu dai duk ba wannan ba. Wallahi Ɗan Bishir ne yake son cin abincin Rahina, saboda zaƙin girkinta kasan na daban ne."
Tun Baba Sale bai gama magana ba Labaran ya hau huci, rai a ɓace ya ce.
"Allah Ya isa, wallahi ba zan yafe maka ba, da wannan yabon. Yanzu saboda Allah abincin Rahina ne wani zindiƙin sankacecen ƙato yake yabawa haka?"
Zuciya ta fara ciwo Baba Sale ya ce, "Kai Labaran kada ka faɗa mini maganar banza da wofi, ban da aska da tasha jinin Ɗan Bishir ka isa na tako wurinka neman abinci ne? Ka faɗa mini ko nawa ne zan biya ka, ka sayar mini abincin nata."
Labaran ya buga tsalle kamar mai shirin tashi sama,
All Chapters
Chapter 1
Chapter 2
Chapter 3
Chapter 4
Chapter 5
Chapter 6
Chapter 7
Chapter 8
Chapter 9
Chapter 10
Chapter 11
Chapter 12
Chapter 13
Chapter 14
Chapter 15
Chapter 16
Chapter 17
Chapter 18
Chapter 19
Chapter 20
Chapter 21
Chapter 22
Chapter 23
Chapter 24
Chapter 25
Chapter 26
Chapter 27
Chapter 28
Chapter 29
Chapter 30
Chapter 31
Chapter 32
Chapter 33
Chapter 34
Chapter 35
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 28 Chapter of 35