Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
dr lawal ke zama kusa dashi.kai mugun maasharranci ne wlh.yace rantse da Allah baka kosaba?ya zura masa ido yana dariya yace yo see! nasan bakada abin cewa nidai ina roqon likita pls nd pls karka manta wa wani almakashi acikin kai.arinqa ajiye sakeena a kofar tiyata.ya bashi hannu suka tafa suna kyayatawa kasamu ni dayawa dr lawal.amma ba komai gidanka naxo.maryam ta fito da tiren kayan abinci ta nufi tebur ta jera musu.sunata yankar dr al'ameen.yazaiyi?sai dariya kawai dan sunfishi baki.shiyasa yace wa dr lawal duk ka bata madam da sharri Allah shiryeku.ahaka suka gama cin abincin takwas da rabi yabar gidan yakoma nasa.can yayi sallar isha'i yayi wa Allah godiya ya rokesa daya nuna masa ranar dazai ganshi da mama a matsayin matarsa.yayi shiru ya rufe idonsa.wayarsa tayi qara ya dauka dadinsa ne.yamayar masa yanda akayi.dadi ya lullubesa.yasa musu albarka tare da fatan Allah nuna musu wannan rana da zata zamar musu abin tarihi a rayuwarsu.bai iya bacci ba dan daya rufe ido mama yake gani tana tura hularsa tana fada masa so much! ranar asabar akan hanyarsu ta zuwa abuja.kaduna suka tsaya makarantar da waleed yake (TURKISH INTERNATIONAL SCHOOL.)inda yake karatunsa makarantar kwana ce ta yaran masu kumbar susa.suna zaune falon karbar baqi aka kawo musu shi.ya rugo ya rungume babansa murna kamar ta kasheshi.mama tayi zuru tana kallonsu tana murmushi daka ganshi kaga al'ameen..ya dago shi suka zurawa juna ido dady yaushe kazo?yace banwani dade ba dama nace kar a gayamaka sai naxo kaganni suprise ko?yace amma kaje kaga waleeda?yace sau daya naje Allah sau daya naje ya tura baki a shagwabe gaskia ba haka akeyi ba .ba haka akeyi ba dady.ya fara dariya ya kama kunnuwansa biyu sorry.i'am very sorry abdul kayi?ya qara rungumeshi i miss u dad.yace nima haka yarona! ya dagoshi ya dubi mama ta zura musu ido tana murmushi.har wasu kwallan da batasan dalilinsuba suka taru.dadi wannan fa?ya dubeshi ya numfasa mominku ce saura sati uku adaura mana aure kana sonta?ya zura mata ido tamkar yadda take kallonsa ina sonta dady wlh tanada kyau kamar balarabiya! suka fashe da dariya mama ta jawoshi jikinta ta rungumeshi.tace nima inasonka kaima kayi kama da larabawan my beloved son.ya kwashe da dariya yace harda waleeda?tace sosaima.131Yace sister nane tana can suleja wajen kakarmu.zakije ki ganta?tace daganan can zamu wuce ya miqa mata yatsansa promise?ta jawo shi ta rungume al'ameen ya sauqe numfashi ya zura musu ido yana murmushi..ta dago ta dubeshi to nagode tunda kana sona kaga zamu zauna cikin farin ciki kenan koh?ya amsa da kai dady kuzo ku dauken ranar daurin auren.yace ai bakuyi hutu ba waleed kasan makaranta bazata bariba.kayi haquri inkunyi hutu kai tsaye zariya zan wuce dakai wajenta.yace waleeda zataje bikin?yace wai meyasa waleeda tazamo kishiyarka?to ita bazata jeba shikenan? gaba dayanku sai anyi hutu inkaiku.yadan saki fuska.mama tadauko wata farar leda ta miqa masa duk wannan naka ne.ya karba ya dudduba.kwalayen biskit da cukulet kala kala wanda yakeso.ya dubeta yana dariya momy na gode!tayi murmushi nima nagode.dr al'ameen yace bari mu wuce koh? muna sauri muje muga waleeda kar dare yayi sai mundawo.sukayi sallama da waleed kamar zaiyi kuka.hakanan suka tafi suka zuciyarsu cike da tausayinsa.shiyasa mama tayi shiru a mota tsawon lokaci sannan ta numfasa waleed kamar kayi kaki dokta!133Yayi dan murmushi Allah ko? tace har muryarku iri daya.ga shagwabar gado.ya kyalkyale da dariya yace.haka kema zaki haifa min ameer da ameera.ta watso masa harara,tace kai ka sansu.yace ashe kingane.kullum na rufe idona su nake gani.suna tumurmusani uhm...mafarkina yakusa zama gaskia.Allah kaban ameer da ameera ta tsatson sakeena wannan shine babban burina.ta zura masa ido harya tsargu yajuyo ya dubeta suka hada ido.yayi murmushi yadauke kai.itama tahauyi cikin ranta tana tayashi addu'ar Allah ya cika masa burinsa.suna tafe suna hira nanda nan suka iso suleja mama tana ganin yanda yadauki babban titi tace ina zamu? yace wajen waleeda mana!tace gaskia inajin kunya dokta.mu wuce kawai watarana na ganta.yace kunya?ina alqawarin dakika dauka wa waleed?tadan runtse ido ya salam.ta dubeshi ta ci gaba sai kuma muje kace musu ni wa?yace mominsu waleed ofcourse!cike da damuwa tace aikaji.sai ace banda kunya harna biyoka ganin yarka.ya karkace kai yace salo!to idan baki biyoni ba waza ki biyo?ta zura masa ido harya gaji yace tsaya kiji karewa cemusu zanyi kece nafara so rashinki yasa na auri ruqayya..tace kaga tun anan ansami matsala kana fadi zanyi baqin jini. Da dai....yanxu zakice bazakije kiga waleeda bako? ta bishi da kallo haka shima yasa mata ido jim! sukayi shiru kafin tace muje dokta amma ka taimakeni dan Allah karka basu labarin daya wuce.yayi dan murmushi yana tada mota fuskarki kamar na mara tsoro can cikin zuciyarki kamar farar kura.ga tsoro ga ban tsoro.tace muje a tsoron aini nasan menakeyi.yace nine bansani ba ko?tace wuuu! banfada ba Allah huci zuciyar mai gida. Da wutsiyar ido ya kalleta in banda abinki gidansu ruqayya ai gidan mune aminin dady fa.yadda yake abbanta nima abba nane tace nima abba nane.har kofar gidan kowa na kokarin kare kansa yayi horn mai gadi yabude suka gaisa ya ajiye motar a wajen ajiye motoci.suna tsaye kofar gidan dr al'ameen yana kwankwasawa yana mata dariya ganin yadda ta tsaya tamkar marar gaskia.jimawa kadan aka bude.ah! oyoyo dadin waleed yana murmushi yace anti niima sauqar yaushe?tace dazu dazu tafe kake da baquwa? yace wlh kuwa wai tanaso tazo taga waleeda.bakinta har kunne tajawo hannunta suka wuce ciki.tana mata sannu da zuwa.har kujera takaita.tace zauna inkira umma.suka zauna dr alameen yace antin ruqayya ce tana aure a kano.tace akwai fara'a sai gasu sundawo.anty ni'ima na riqe da hannun waleeda tana taka qasa dabas dabas.saboda kiba,rugu rugu!da ita.ga gashi kamar buzaye.mama ta zura mata ido ai batasan lokacin data tashi ta runguma yarinyarba saboda sha'awa data bata.bayan angaisa anty ni'ima takawo musu ababen sha.hajiyar ke tambaya hala wannan itace sabuwar mominsu waleeda?Yana yar dariya yace itace hajiya munje makaranta taga waleed shine tace sai na kawota 135-wajen waleeda hajiya tace madalla ya ya kyau Allah ya sanya alkairi yace amin yayin da mama ta kara sunkuyar da kai tanayi wa waleeda wasa ita kuwa tamkar ta taba ganin ta fariya kawai takeyi mata ya sunanta anti ni'ima ta tambaya yace sakeena sunanta tace sakeena ta dan yi shiru ka na ta kara fadin dadin waleeda ko dai sakeenar da marigayiya ta taba ban labari ne duk suka kalli juna sannan ya tambaya ta taba. Baki labarin wata sakeena ce tace ya dade da ta gaya min ka so wata yarinya sakeena amma Allah bai yi auren ba ta auri wani itama iya ce ta bata labarin irin son da kake mata haka ne? Yayi murmushi yace haka ne anti ni'ima ga ta kuma mun sake haduwa hajiya tace haka shirin ubangiji yake matar mutun aka ce kabarinsa ina fatan dai yanzu babu wani sai da na ko sakeena taja mayafi ta rufe fuska suna ta mata dariya kunya ta hana mama sakewa sha biyu rana suka bar gidan da alheri mai yawa da hajiyar taba mama waleeda kuwa harda kukanta da taga sun shige mota sun tafi sun barta, suna tafe suna labarin gidan irin kyakkyawar tarbar da akayi mata abin ya faranta mata rai kwarai da gaske bayan wucewa awa daya. Suka iso maitama gab daza su shiga gidan take cewa kasan wani abu ban fa gaya wa abba komai a kanka ba kamar yaya tace kawai gaya masa nayi zan zo weekend so na ke abba ya sha mamaki yace ai kuwa zai sha mamaki na bazata ma kuwa ba shi kadai ba kowa ma ya ganni zai saki baki yau , kin kyauta da baki fadi yayi horn aka bude musu get suka sulala ciki tace munyi sa'a yaya na gida ga motocinsa nan a jiye yace good al-ameen sa'a ke nan... mu je ciki asa mana rana yarinya balarabiya ta bakin waleed" ta ballo masa harara tace wace ce yarinyar yayi yar dariya ya bude murfin yana fadin Allah na tuba duka kwaya nawa kike ita ma ta fito gara dai da kace Allah ka tuba ta wuce yabi bayanta yana dariya suka tsaya bakin kofa tace ka tsaya anan zan dawo in shigo da kai yace ba laifi ina jira ta shige tana kwarara sallama duk suka amsa mata daga babban falo can ta wuce da sauri suna mata oyayo ta fada jikin abba da murna sanna ta juya. Wajen yayanta da anti amina duk ta gaishesu kana ta mike tsaye tace kun san wani abu duk suka zuba mata ido abba ya bata amsa sai kin fadi mama na tace duk ku rufe idanuwanku akwai abin mamaki dana taho muku da shi yayanta ya aje jarida yace idan kin ka nuna mana shirme sai na balla kafarki tana dariya tace na yarda to kun shirya mun shirya a rufe ido ina zuwa ta fice suna mata dariya abba yace ai sai mu rufe mu bude muga abin mamaki duk suka rufe suna dariya jimawa kadan suka shigo tare da al-ameen ya tsaya saitin daza su ganshi sosai yana ta murmushi tace kuna iya budewa duk suka bude kowa ya yi ido hudu da al-ameen dif yake dauke wuta ya zubo masa ido anti amina ce ta fara magana dokta ko ba shi bane mama tace gashi nan dai abba wanene a tsaye yaya ka gane shi yaya yace al-ameen abba ya miko hannayensa biyu yace zo nan al-ameen zo in taba ka in tabbatar da ba mafarki na ke yi ba ya tako da sauri bakinsa har kunne ya zube,137- gaban abba ya rungume shi yana fadin 鈥渢sarki ya tabbata ga allah ashe zan sake ganinka al- amin?鈥� Ya jima yana rungume da shi.sanna ya dago shi suka duba juna. abba ya numfasa ya sake fadin 鈥渉aba al- amin kuma sai zumunci ya yanke? Babu kai babu labarin dadinka?鈥� Ya-ce 鈥渒a yi hakuri abba. Tunda na ba kasar nan ban dawo ba. Sai da na kusan shekara biyar. Duk abubuwan da suka faru ban dawo ba. Sake haduwarmu da sakeena take gaya min har umma Allah yayi mata rasuwa kai kuma ga lalurar da ta same ka banji dadi ba Abba ubangiji Allah ya jikanta yayi mata rahama hannayensa biyu bisa kafadarsa ya amsa amin summa amin ina fatan su alhaji duk suna nan lafiya ya juya suka gaisa da yaya soja da anti amina yayi masu. Gaisuwar umma nan da nan aka baibayeshi da kayan ciye ciye dana sha kala kala ya jika mako shinsa da ruwan sanyi yace ashe haka al'amura suka faru abba wannan wane irin zaluncine da rashin imani, Abba ya kada kai yace ka bari al-ameen ai munga tashin hankali yarinyar nan ta dawo tamkar mahaukaciya a gari kowa yana ganin kamar rashin biyayya ce ta jawo mata lalacewa da kaskanci ashe ba haka bane ka ganta nan Allah ne yasa tana da sauran shan ruwa a duniya hankalin al-ameen ya kara tashi yace subahanallah Allah karabamu da sharrin shadan suka amsa da amin yace shine wannan zai zama dalilin da* tace ba zatayi aure ba sati uku muna artabu abba da kyar abokin na ya shawi kanta. Inda harna ce na hakura suka zuba mata ido kafin abba yace haka ne kuma nima na kyale ta ta zaba abinda tafiso dan hankalinta ya kwanta sai dai tun lokacin na sani dole wannan kudirin na ta ya tashi domin bani da wani buri da ya wuce in cika maka alkawarin dana daukar maka to Alhamdulilahi,138.tunda itama ta gane gaskia,nakuma tabbatar batada wanda takeso face kai.saboda haka duk lokacin daka shirya kazo adaura auren dafatan bazaka samu matsala da iyalinka dake gidaba.yayi murmushi yace ai babu iyalin abba banganeba.ta rasu abba shekara daya da rabi kenan.yace ayya Allah yamata rahma yasa duk musulmi suna kyakkyawar matsayi.yace amin abba.kowa yayi masa gaisuwa,,,,,suna suka ci gaba da tattaunawa.mama tace abba bakaga yaronsaba.yakusa tsawona.al'amee n yasaki baki yana kallonta,,yayinda abba ke fadin ah lalle ba shakka,su nawa ne?tace su biyu ne,abdulrasheed da ruqayya.sunan mamanta aka samata.abin tausayi abba tana haihuwarta ta rasu.tausayi yakama kowa sunata mata addu'a.al'ameen na amsawa haka suka wuni hira salloli kawai ke tadasu.dare yayi aka kai al'ameen masauqi.farin ciki kamar ya kashesa.shine mutumin dazai iya sharewa mama hawayenta.cikakken labarin abinda yasameta dayaji ya qara masa tsantsar sonta.bashida wani buri daya wuce ya mallaketa ta hanyar sunna.don ya tabbatar mata da cewa Allah baya zalunci kuma bayason mai yinsa.washegari qarfe tara suka bar abuja dauke da albarka mai tarin yawa daga wajen abba.suna shigowa suleja mama ta tunada waleeda.tadan dafa qirji Allah sarki waleeda kamar mu koma mu daukota.yace kinsan rigimar waleeda kuwa? bazaki iyaba nake gayamiki kukanta sai hajiya.139.Tace haka kake gani,badon karatu ba dana daukota.Allah taban sha'awa,jiya saidanayi mafarkinta.kukan da take lokacin dazamu tafi.yace ba waleeda kika gani ba ameera ce.ta ballo masa harara yasan hararar yakesha shiyasa yaqi waigowa ya rinqa yar dariya.ya qirqiro waka.yana rerawa idan da rai da rabo!.......al'ameen zaisamu ameer da ameera! mai harararsa yadena!...takada kai tana dariya Allah ya shiryeka!yace ameen.sannan yace na fahimci kinfison waleeda akan waleed,lalle zakuyi rigima dashi dan kishiyarsa ce.tace naga alama komai saiya tambaya yaji ko anyi mata shi ba a yimasaba? tace ba komai nasan yadda zanbi dasu yace ko? kana shakk ne?uwace fa! yayi murmushi yace uhm....naqosa inganki mama.tace bari gatse dama sunan kenan! yace godiya nake!dai dai lokacin daya dauki hanyar minna.idanuwa waje tace yaya haka?yace haka dinne.dan Allah ina zamu?yace yanda kika nuna ni suprise haka zan nuna ki mamakiyos!ta langume kai amma bakada kirki mesa zakamin haka?yace mesa? tambaya kike?any way....kinma riga kinba kanki amsa tunda kikace banda kirki.rashin kirkin ne yasa zan nunawa kowa cewa alqawarin Allah baya tashi.fuska yamutse tace wayyo Allah na!yace ke yasu!?ta numfasa bata bashi amsaba.yafara mata dariya yana karawa don a gaskia tanajin kunyan su mami balle kuma dady. Ganin abin yadameta sosai yace to miye abun damuwar keda zaku zauna nan bada dadewa ba.kinsan cewa ko bajima ko ba dade zaku zauna tare.tace ai da sai a bari na dolen yazo saboda Allah fa! Yace gaskia bazan iyaba kiyi haquri kawai muje kisha kunyar a yau.kinji ko bebina?tace naji sir! yayi dan murmushi yace thank you mah!suka ci gaba da hira kala kala.har suka isa minna.kai tsaye yadauki hanyar anguwarsu.tace tsaya bansaya wa mami komai ba.gayamin abinda tafi so?yace idan kinaso ki burge mami kisaya mata carrot.cucumba,da kankana.to muje insaya mata.yace karki damu munayin kwanar can akwai masu fruit.yana maganar suna shiga kwanar sai gasu birjik!yayi parking duk suka fito mama ta kwasa kamar banxa gaba daya akace dubu daya.alameen yazaro zai miqa tace anyi ba ayiba kenan.nice zansaya mata bakaiba kokai kace?yakama kunnuwansa tuba nake wannan jan idon?tayi murmushi harmai fruits na tayata.ta zaro dari biyar biyar sabbi dal ta miqa masa akasa a boot.suka wuce alameen na tsokanarta hajiya mama kenan kinfara raina min wayau!tun jiya kike kashe min kudi,karfa ki maidani mijin hajia?tace sai me? yace sai ni baban ameer da ameera.tayi dan tsaki ta kyaleshi yana mata dariya.sunyi fakin harabar ajiye motoci,suka fito shima ya ajeta waje kamar yadda tamasa.yashiga ciki tare da sallama.maminsa na dakin dady.daga can ta amsa sallamarsa.ya qarasa ciki da fara'a maraba da bokan turai!.inji mami yace mamina!ya tsugunna gabanta yadafa guiwowinta.ta dafashi tace ya aiki?yace mungode Allah mamina!141,ya juya kan dady dadina!yace nidai ansaba min son kai.ai de ba haka akeyi ba!yadawo gunsa yana dariya yace dadina albishirinka?yace goro fari yace to duk ku taso muje falo in nuna muku wani abu.meye shi? mami ta tambaya.dady yace miye naki na tambaya taso muje kawai.suka nufi falo.yauwa! to ku rufe idanuwanku!kuma dai?inji mami.kedai rufe dadi yafada suka rufe ido suna dariya.yace minti daya yakoma waje da sauri ya kamo hannunta tana fisgewa yashigo da ita.ya tsaidata gabansu.kunya kamar ta nutse qasa yace kuna iya budewa yanxu..alokaci guda suka bude duk sukayi mutuwar tsaye.dadi yafara fadin sakeena! taja mayafi ta rufe kai.mami kuwa da saurinta ta rungumeta.Allah sarki sakeena! ashe Allah zai hada fuskokinmu?kwalla suka cika idon mami.mama kuwa ta goce da kuka.mami ta dagota hannu biyu menene abin kuka sakeena? don Allah ki dena.wannan ranar farinciki ce.dan na tabbata dan tilon dana zaisamu farinciki data dade dayin qaura daga jikinsa.karki damu da komai kisaki jikinki kamar da kinji ko?ta durqusa qasa baba ina yininku? haryanxu yana mamaki lafiya qalau sakeena.haka shima alameen idanu suka dauki kwalla.yace ashe har umma ta rasu.mami ta kamota sukazauna a 2 sitter,tana rungume da kafadarta tace munji rasuwar ummanki amma rashin jin dadin abinda kikayiwa alameen shiya hanamu zuwa gaisuwa.kuma bamu gaya masaba.karkiga laifinmu sakeena.Allah kadi yasan wahalar da mukasha kafin musamu mu ceto ransa. Allah kadai yasan yan kudaden da muka batar dan neman taimakon addu'ar Allah ya cire mishi sonki.muka samu son yasuma.dan kuwa suma yayi tunda gashi daga ganinki ya farfado.kiyi haquri sakeena wannan al'amari duk cikin rashin sani akayi.ta silale qasa tasake durqusawa wlh babu komai mamii.idan kuwa dame laifi ni yakamata nabada haquri dan angayamin dakanki kikazo rokona.kina bani haquri amma naqi sauraronki nima ku yafemin,,,,,ta jawota ta rungumeta karki damu sakeena.wannan wani qaddararren al'amarine daga Allah.babu mai iya kauda shi.amma dayake bakida hakki gashi ubangiji yabayyana komai....shikuma yaga makomarsa.to Allah ya jiqan hajiya halima.kidage dayi mata addu'a ita kadai ce ribarki gareta.kinji?ta dago tana amsawa dakai tana share kwalla!dady ya numfasa munyi farin ciki da ganin wannan rana.muna masu tsananta godiya ga Allah ta'ala mafificin dukkan komai.saboda haka muke roqonsa ya karemu daga dukkan sharri.yakuma jikan hajia halima ya yafe mata dukkan kurakurenta.143Suka amsa amin summa amin, bayan dadi ya gama addu'oinsa alameen ya dubi mami yace ina iyata?tace suna can bayan gida suna hira.ya miqe yana fadin barin kirasu suga sakeena ta.ta dawo mami tace yakamata.yashige kicin kofar dazata sada shi da waje.mami ta dubi mama tace inaa fata komai ya dai daita?biki kawai zamu shako?ta sunkuyar dakai dadi yace kema kinsan bazata iya fadaba.ki bari ya shigo muji daga bakinsa,,,,sai ga hayaniyarsu dasu iya suka shiga tafa hannu suna sallami lalle matar mutum kabarinsa.suka zauna gefe suka gaisa.iya tace ubangiji yanuna mana ranar auren nan.suka ce amin.al'ameen yazarce da fadin musha rawa ko iyata?baki har kunne tace sosai kuwa dan iya.Allah dai yanuna mana lokacin lafiya.anata raha suka bar falon.ladi ta tafi takawo musu ruwa da abinci.mami ta gyara zama tace yadai? ya ake ciki? nafa kosa..yayi yar dariya yace komai dai dai mami.kinga tun jiya muka baro zariya muka tsaya kaduna makarantar su waleed.mukaje suleja gun waleeda yar rigima.muka wuce abuja gidan abba.bakuga yadda ya karbeni ba murna da farin ciki ba a bayani.ya rungumeni yana kwalla.yanxu maganarku muke jira yace ko yaushe nashirya nazo adaura mana aure ai baza a bata lokaciba ko dady? bakin mami har kunne tana fadin masha Allah! dady yace me za a jira?Mu ai a shirye muke in sha Allahu gobe zan tafi abujar mu sasanta dole in durkusa in nemi afuwa zan karbi lambarsa da adres kafin ku tafi Allah ya shige mana gaba ya kore dukkan fitina suka amsa amin al- ameen ya zarce da fadin amma dadi karya wuce sati uku ayi komai a gama kowa BAKIN CIKI 3******11 kunga kuma zan sami wata shida anan abin zai yi daidai suka yi dariya mami tace gaskiya ne sati uku ai sun wa duk shirin da za'ayi kai Allah ka nuna mana lfy, murna cike da zukatansu bata misaltuwa mami kamar ta hadiye mama ta tasa ta a daki suka ci abanici tare bayan sallar azahar sukayi shirin tafiya haka ta baza mata kaya kala kala tun daga sutura zuwa kayan shafe shafe tace ta zafi duk wadanda ta keso ta cire kunya ta zabi yan tsiraru Al-ameen na taya ta shine ma ya jido mata kayayyaki masu yawa dadi ya kwala wa mami kira ta tashi ta fita mama ta dubi al- ameen tace wai ka manta da tsarabata ne yace ina sane kyale ki naiy in gani komawa zakiyi dasu ta dan shagwabe fuska kai dokta saboda Allaj baka san kunya ba maimakon ka taimake ni, ya zuba mata ido maimakon ka taimakeni ya maimaita a shagwabe tayi yar dariya tace don Allah in ta shigo ka gaya mata gani ma na shigon me za'agaya min mama ta sunkuyar da kai ya fara dariya yana fadin wai tsaraba tayo miki shine ta bari a mota tana jira ni in gaya miki wanda ya siyo abu ba shi yake daukowa ya bada ba? Mami ta dafa ta tace Allah sarki sakeena kyale shi karya gadi din so yake ya manna miki laifi dame dame kika kawo min cike da kunya tace fruit ne kawai mami tace Allah yasa da karot ciki suka kalli juna suna dariya akwai mami ta ce to shine ki ka ki gaya min abinda na ke ta marmari kwana biyu ban ciba ta yunkura da sauri tacr bari a kwaso miki shi ma ya mike yabi bayanta mami ta bisu da kallo tana dan murmushin jin dadi jim kadan suka dawo daddauke da ledojin guda uku manyan gaske mami taji dadi sosai tana sa albarka sannan ta mika wa mama rafar kudi dubu ashirin tace wannan dadinku yace in baki tasa hannu ta karba tana kada kai haka da yawa mami to nagade Allah ya saka da alkairi tace amin sakeena al-ameen yace mun gode mami bari inje wajen dadin mu za mu wuce ya wuce suka zauna jiran fitowarsa basu dade ba suka fito tare mama ta zamo daga kujera ta tsunna tayi godiya yace ba wani abu Allah ya sauke ku lafiya tace amin suka rankayo waje al-ameen ya daga murya yace iya ta na wuce suka fito tare da ladi sukayi masa sallama sannan suka karasa wajen mota sai da suka bar get suka koma cikin gida suna masu addu'ar sauka lafiya ,, lafiyar kuwa suka sauka cikin yarda ubangiji ya sauketa gida ya taimaka kwaso mata kaya zainab ta fito ta tarbe su bakinta har kunne tace ga amarya ga oga shirin yayi yace kin ci ziro zainab kuma baki da sa'a da kin fada daidai Allah kadai ya san yawan ladarki tace sir zan gyara ga amarya ga ango....yace kin makara". Zai wuce ta karbi kayan hannunsa no sir ai ba wani sai ogan mu yana yar dariya yace kinyi gaskiya zainab kina damaki ashirin tace"thank yau sir mama tasa musu baki har wata godiya ki ke yi ki na kware baki kar kiyi karatu yarinya ki jira bonus" ta bude kofa suna dariya dr al-ameen ya ce ina ruwanta zainab ta amsa nima shi na gani ke ko tukuicin baki bani ba amma kina sawa oga ido suna tsaye tsakar daki ya laluba aljihunsa ya zaro dubu biyar ya mika mata karbi wannan ki kyaleta kawai sai mun hadu gobe -tana dan murmushin jin dadi jim kadan suka dawo daddauke da ledojin guda uku manyan gaske mami taji dadi sosai tana sa albarka sannan ta mika wa mama rafar kudi dubu ashirin tace wannan dadinku yace in baki tasa hannu ta karba tana kada kai haka da yawa mami to nagade Allah ya saka da alkairi tace amin sakeena al-ameen yace mun gode mami bari inje wajen dadin mu za mu wuce ya wuce suka zauna jiran fitowarsa basu dade ba suka fito tare mama ta zamo daga kujera ta tsunna tayi godiya yace ba wani abu Allah ya sauke ku lafiya tace amin suka rankayo waje al-ameen ya daga murya yace iya ta na wuce suka fito tare da ladi sukayi masa sallama sannan suka karasa wajen mota sai da suka bar get suka koma cikin gida suna masu addu'ar sauka lafiya ,, lafiyar kuwa suka sauka cikin yarda ubangiji ya sauketa gida ya taimaka kwaso mata kaya zainab ta fito ta tarbe su bakinta har kunne tace ga amarya ga oga shirin yayi yace kin ci ziro zainab kuma baki da sa'a da kin fada daidai Allah kadai ya san yawan ladarki tace sir zan gyara ga amarya ga ango....yace kin makara". Zai wuce ta karbi kayan hannunsa no sir ai ba wani sai ogan mu yana yar dariya yace kinyi gaskiya zainab kina damaki ashirin tace"thank yau sir mama tasa musu baki har wata godiya ki ke yi ki na kware baki kar kiyi karatu yarinya ki jira bonus" ta bude kofa suna dariya dr al-ameen ya ce ina ruwanta zainab ta amsa nima shi na gani ke ko tukuicin baki bani ba amma kina sawa oga ido suna tsaye tsakar daki ya laluba aljihunsa ya zaro dubu biyar ya mika mata karbi wannan ki kyaleta kawai sai mun hadu gobe.............. - Takarba mama na fadin ok mun gane dama da mun ganki da manyan maki mun san na coge ne yace eh ba komai zainab tayi dariya tace na gode sir sai ka fito ta wuce tanayi wa mama dariya yayi mika yana salati sannan ya zauna a kujera ta ware ido tace zama naga kayi kar in zauna tace gida ya kamata kaje yace korata ma kike yi ta kada kai ba haka bane zai fi kyau kowanne mu ya samu yay wanka ya huta kafin magariba ta karasa ya munfasa yace haka ne yi hakuri don Allah sai ina ganin kamar an daura ne unguwa muka je muka dawo ta ware ido iye eh wallahi kiris ya rage in fada katifar nan in kwanta fuska yamutse tace wasa ka ke kin san Allah bada wasa nakeyi ba a dai bar kaza cikin gashinta miko min ruwa in sha in gudu,,Tace sai dai in karbo maka wajen zainab ka sha na firij dina babu sanyi yace to barshi kawai bari in tafi ya zubo mata ido suka kalli juna yai dan murmushi tace mene ne ya mike yana fadin nothing sai munyi waya ko ta kada kai a ranta race dokta ke nan ya wuce tanataka masa tana fadin ina sauraronka tara kashi har mota suka y irin sallamar sa suka saba yaja mota ya wuce ta tako a hankali daki irin son da ala- ameen yake mata shi yasa take jin kanta ita wata ce ta shige wankanta ta fito ta sauya kaya ta kwaso littatafanta ta baye a kasa ta fara karatu tana yi tana zuba hamma barci ne sosai yake son kamata gashi yamma tayi babu kyau yin barci a wannan lokacin don haka ta aje littafinta yunkura zata tashi da nufin fita wajen zainab suyi hira ko barcin ya fita idonta, wani sauti mai dadi ya fito wayarta alamun sakon ya shigo ta dubi wayar kawai ranta ya kwao mata zakin zuciyar tane tasa hannu ta dauko tana dan murmushi ta bude sako amma sai taga sunan yaya ali dake rubuce kamar haka, Assalamu alaiki ya kanwata sai yau nayi saranda na sauke hannayena daga rokon soyayyarki a yau na yarda na amince kin sami gwarzo jarumin da nake da yakinnin zai shaer miki hawaye tamkar yadda nake zaton zan miki shine nake da tabbacin zai rike ki babu gori balle mugun kallo ko zargin kin taba yin wata mummunar rayuwa a. Baya amma ina so ki aje a ranki wallahy wallahi!!! Wallahi!!! Al-ameen bai fini sonkiba sai dai zanyi hakuri ne saboda ke shi kika fi so a gunsa duk farin cikin ki yake to nima ina son farin cikin ki mama shi yasa na ke son abinda kike so ina muku fatan alkari tare da tayaku murnar sake haduwa da juna,,Yanyaki aliyu!! Hawaye kawai taji ya goce mata saboda. Tausayin yaya ali to doka tagumi tana kalubalantar kanta me yasa nake zama butulu akan son da yaya ali ke nuna min laifi na ne meyasa ban yarda. Na aure shi ba tun kafin mu sake haduwa da dokta ta goge kwalla ta kada kai abin ya dame ta kwari

Chapter 26 of 28