Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
ga BAKIN CIKI Ba tamkar yadda muka ganshi kiri kiri.amma bamuda maganinsa.kisani duk abubuwan da kika lissafa babu wanda bamu kwatanta akankiba.sai dai abin ya faskara.saboda anriga an mallaki zuciyarki mama.karki danganta laifin akan kowa.don babu wanda yasan gaibu sai Allah.shidin kuwa mukayi ta roko ya warware mana abunda ke boye.agame da lamarinki.ina ganin yakamata ki kalli uzirinmu.kiganecewar munyi iya kokarinmu. Hargashi Allah ya shige mana gaba ya kwato mana ke.ayanzu mukeda damar nunawa danliti cewar lalle ya debo ruwan dafa kansa.dazai kaisa har lahira.ki kuma sa ido kigani. Da sauri tadawo wajensa shima ta rungumeshi murya na rawa take cewa karka barshi da rai yaya!kasa a masa azaba mafi radadi harya mutu.ya lafe kanta a kirjinsa zuciyar maxa ta motsa.idanuwa suka qara jirkita.kawai gani sukayi yasaketa ya miqe cikin hanxari zaiyi waje,,,abba yayi azama yace ku riqo minshi don Allah!su alh basiru suka cafke hannayensa.dawo ciki ka zauna ya qame a tsaye suna ganin yanda jikinsa ke rawa.namansa na girgiza saboda fishi.alh adamu yace alh ne zaiyi magana dakai..abba ya daga murya yace abduqadeer dawonan ka zauna!a hankali fishin yarinqa sauqa sannan su alh basiru suka dawo dashi ya zauna.yayinda mama tasake baro jikin abba tadawo gunsa ta zauna. Abba ya numfasa dukkanmu musulmai ne,,kuma munyi imani!da ko waccw qaddara ce.ina ganin fushin farko banamu bane.kar zuciya tasa mu aikata aikin nadama.yaya soja ya kasheshi babu nadama dan an harbe azzalumi macuci.irin danliti.karka manta muya fesa mana gubar mutuwa.mun shaqa harta shige mana da ginshikin gidan nan abba,!bazamu yafewa danliti ba abba.koza a kasheni saina harbeashi.abba yace kenan bamu godewa ubangiji ba daya nuna mana wannan ranar?wanda yace muyi afuwa a tsakaninmu.domin shi yanason masu yafiya.ko bamuyi fansa a gun danliti ba.nayi rantsuwa Allah bai gama walaqanta shiba.tunda ya walaqanta ayoyin alqur'an.inaso mugane wannan.ba haqqin mama kadai ke wuyansaba. Banajin akwai hukuncin dazamu yankemasa face mu qyaleshi da wanda yabasa ikon aikata wannan aiki akan mama.na tabbata bazai qyaleshiba yaci bulus!ba.ina roqonku da muyi haquri.mu sadauqar da yafiyarmu a matsayin godiya ga Allah daya musanya mana bakin ciki da farin ciki.ina fatan yaya soja zaibi umarni na? jikinsa yayi sanyi yadan kada kai..yace ya wuce abba yayi dan murmushi. Yace nagode! mama zonan...!ta rarrafo ta dawo jikinsa ya jawota. Yace ki nitsu nasan kinrasa komai na tsarin rayuwarki yanda kika shirya....saidai inaso ki gane cewar shirin Allah shine gaba da komai...saboda haka ki rokesa sabon rayuwa mai albarka.muma zamu tayaki zakiga kamar wannan abun bai faruda rayuwarki ba.ki sani har ummanki ta rasu bata taba yi miki baki ba.kullum addu'arta Allah shiyaki.idan zatasa albarka tare takesa muku da sauran yayunki.don haka tsakaninku adda'a ne kawai. Na tabbata hasken addu'arki zaije gareta.harta gane cewa lallai albarkar ta na tare dake kinji mama?ta dubeshi kwalla na zuba tace naji abba.don Allah kayafemin ya goge mata hawaye yace baki min komaiba mamana.ayau nagane baki da laifi ko kankani saboda haka ki saki jikinki.tace nagode abba intambayeka abba?yace tambayeni mamana.ta karya wuya gefe tace al'ameen fa?ya kada kai yace allahu akbar!alkairi Allah yakai mas duk inda yake.haqiqa bantaba ganin tashin hankaliba irin wanda nagani a fuskar al'ameen..saboda rashinki mama kiris yarage ya zautu amma qarfin adda'a ya miqar da imaninsa zuciyarsa ta daidaitu bisa shirin ubangiji.ya rungumi qaddara yawuce da ita rasha.gaskia bansake jin duriyarsa ba haryau din nan danake magana dake...kuma hulda ta yanke tsakaninmu.ni kaina bansan daliliba.watakila iyayensa sun nisancemu don qara nesanta rayuwar dansu ga tinaninki.hasashe nayi amma bansan musabbabinba. BAKIN CIKI 3***7 Tacire kai ta dubesa kwalla na zuba tace tabbas zai iya zama hakan abba!nima nayi alqawarin zanyi masa addu'a Allah qara nesantamu.ya mance ya taba sanina a duniya..ko a hanya kar Allah ya qara hadamu.abba yashafa kanta Allah ya shige miki gaba.yayi miki jagora a sabuwar rayuwar dazaki fuskanta nan gaba.kowa yace ameen yace muyi addu'a.sun raba dare a falo suna hirarrakin duniya abba yace aje a kwanta a huta.mama ta turashi a kekensa zuwa dakinsa wanda tuni anty amina ta dade da gyarawa.suka kamasa yakwanta a gado.sannan sukayi sallama takoma dakin umma!inda anty amina da baraka suke. Kowa ya kwanta barci ya kwasheshi.amma mama ta kasa.kawai tunanin yanda tayi cudanya da danliti take.nan da nan ta ji kyaman kanta ta kamata.tafara sunsuna jikinta.hankalinta tashe batasan lokacin data diro tashige bayiba.ruwan sanyi ne a bokiti da anty amina ta dibo.mama ta duba ba soso ba sabulu.haka nan tahau kwara ruwan sanyi ajikinta.tana dirjewa da hannu hawaye na xuba.ruwan ya qare ta dauki bokoti ta kwarara sauran. Tadauki bokitin takwara sauran ruwan gaba daya.haushin qarewar ruwan yakamata.tasanya kayanta ta figi bokitin da nufin taje tsakar gida ta debo a rijiya.su anty amina da baraka tagani cirko cirko abakin bayin.tawuce abinta ta doshi kofar.yayinda anty ameena kefadin haba mama! ashe bakiyi bacciba?yakamata kimanta komai karki zautu a banxa da wofi.ta zuba mata ido kwalla na xuba wari nake anty ku bakuji?babu wani warin da kike mama!tunaninki yagaya miki qarya.yakamata kisamu bacci ko kwakwalwarki zata huta.ta dubi baraka taga hawaye itama take,,,tace saboda Allah baraka bakiji warin danake ba?sunsuna fa kiji....takara mata hannu a hanci baraka ta goce da kuka ganin haka jikin mama yayi sanyi ta zube qasa dabas takama kai.wayyo Allah na!suka kamota sukayi ta rarrashinta.tadan nutsu.amma barcin da basu komaba kenan gabadayansu Washegari kowa ya hallara da iyalansa.ya abdulkareem da anty rabi kamar su hadiye mama sukeji.sun xubda hawaye saboda murna.ta dubi girman ameer da ameera kawai sai ta kada kai.tana tuna al'ameen shikansa docta yazama saurayi.ta zura masa ido,,,hannayenta bisa kafadunsa ta matse ido.hawaye suka kwararo..jitayiyana share mata hawayen tayi wuf! ta bishi da kallo.bakinta na rawa tace al'ameen momy nagayama inasonka?? ta taba gayamaka? ya juya ya kalli mominsa.yamaidoda kansa gareta ya girgiza kai.bata gaya maka ba?amma momy bata kyautaba.tasanfa yadda nake sonka Allah tasani boyema tayi togayamin kana sona? yadaga kai alamar eh.ta rungumeshi tana fadin nima inasonka dokta. Anty rabi ta taso ta dafata.ta dago kai ta dubeta kwalla na xuba mama!ki kwantar da hankalinki na tabbata Allah baxai barki hakaba.zai musanya miki mafi alheri wata qilama fiye da al'ameen.tayadd a rayuwarki zata daidaita tamkar da. Ta miqe a hankali ta fuskanceta tace hakane.nasan babu abunda zai gagari Allah.amma dokto shine farko shine qarshe.ta wuce ta murda kofar dakinta.ta qare masa kallo inba qarya idonta ke gayamata ba.kamar ta taba ganin al'ameen tsugunne a wajen data qurawa ido.dukda takasa tuna kalaman dayake fadi.idanuwantana nuna mata zubar kwallansa.tayi wuf!ta cafke yatsunta ta runtse su tamau.tana tambayar kanta ina zobe na?ina na ajeshi?ta wuce a hankali bakin gado ta zauna tayi shiru tana tuna kalaman dayake fadi idanunta na zubda hawaye.kai al'amarin mama qara sukurkucewa yake dalilin dayasa abba yace subar garin wataqila tafi samun nutsuwa.nanda nan suka fara shiri.kafin wani lokaci kowa ya kimtsa abba ya sallami en uwa da abokan arziki.su hajiya hajo sunata neman gafara wajen abba da mama.motoci suka kwashesu kowa da iyalansa suka miqe hanya.suka bar danliti hannun hukuma.duk abinda yakamata su masa A kagara suka sauqe baraka tukuna suka dau hanya.minna suka yada zango gidan ya abdulkareem.ko anan dinma al'amarin bai sauyaba.haka suka kwana ba barci a idon mama.washegari suka kimtsa masu tafiya abuja suka dau hanya.ya abdulrahman yayi kaduna da iyalansa da malami.shikuwa abdulkareem jirgin shabiyu sukabi zuwa legos.yan abuja suna dira gida wanka mama tafarayi.wannan wanka yafara damun yan uwanta.su wanka ma kawai suke gani basusan yanda taga dare haka take ganin ranaba!akwai fargaban rashin bacci zai mata illa.idan ba'ayi gaggawar daukan matakiba.towayasani bare ayi mata magani? shiyasa kafin sati ta birkice gaba daya.ga zama shiru ga sunsune sunsunen jikinta.wanka kuwa ba'a maganarsa.saidai in danliti bai fado mataba.nan da nan tafara mura zazzabi mai zafi ya rufeta.hankalinanty amina yatashi.data shigo dakin tasameta nade cikin bargo sanyi na kadata.cikin sassarfa tasamu abba.ta durqusa a hankali tace abba idan ba'a dau matakiba mama zata kashe kanta da yawan wankan nan. Mama zata kashe kanta da yawan wankan nan.gatacan jikn kamar wuta sai rawar sanyi take.yakamata asan abinyi cikin gaggawa.nanda nan ya latsa control din kekensa yawuce ya nufi dakin yana fadin kira yayanta a waya.kuma fa yau dinnan naji yana fadin sun gama magana da yan uwansa egypt zasu wuce da ita asibitin dana kwanta. Su duba lafiyarta! tace nima yagayamin amma duk da haka yakamata afara kaita nan tafara samun taimakon farko.yana kutsa kai dakin yana fadin gaskia ne.kirashi din ki kara gaya masa.ta juya shiya shige dakin yasamu mama sai kyarma take cikin bargo.kwananta biyu a asibiti basu gane ainihin matsalartaba.amma taimakon dasuke bata yataimaka kwarai wajen sanyata bacci.tana samun hutu.duk takardar tafiyarsu masar sun kammala itada yayanta wato soja.a ranar basu kwana ko inaba sai egypt .acan bincike ya tsananta.don babu irin gwaje gwajen da bata samuba.hoton kwakwalwa hiv aids,,ciwon sanyi da sauran ciwuka dakan kama mutum sakamakon shiga wahala mai tsanani.Ba a sameta da wata matsalaba sai hawanjini da rashin bacci.kamar dai yadda likitotin nigeria suka ce amma su abba basu yaddaba dan gani suke kamar hauka mama keda niyyan yi.sai dai Allah da ikonsa likitotin masar suna kokarin shawo kan matsalarta.da magunguna da shawarwari.don cire mata damuwa wanda gabadaya ita ummul aba isin komai.to muma bari mubarta ta huta. A lokacin da mama ke kwasar hutu damagunguna akasar masar.shi danliti yashe yake aofishin yan sanda.yanata hauhawa kamarfarashi.gaba daya fuskarsa ta aune ta kumburasundum.sukansu yan sanda sun gaji da saya masagarin rogo yanasha..babu mai belinsa.tsawon kwana biyar dama ayuba ne yake zaton ziyi belinsa to shimatunda yaga ayar Allah ta sauqa.don haka yayi wakansa alqawarin tuba daga nasa laifukan zinacezinace dayake aikatawa.babbar mota yabi sai indamai yaqare.wajen neman halal.to Allah ya karbitubansa.shikuwa dan goga yarasa tudun dafawa ga ciwo ga masifar yansanda.ranar daya cika kwanashida.sukace zasu sakeshi yatafi yanemilafiyarsa.idan yaga dama ya gyara halayensa ko yacigaba da lalacewarsa..shidai yana kuka yana roqonsusu barshi dare yayi su sakeshi saboda kunya kunjidan iska ashe yanada kunyan?kuma da tsoron kar jama'a suganshi su sake rufar masa da duka,Yansanda suka amince hakan amma baxasu bashiabinciba.h aka yazauna da yunwa har qarfe gomandare.suka tarkata shi suka tura waje.a hankaliyasamu ya sulale yakoma gidansa ya kwana.yanatunan in mafita da da hali gidansa zai sayar a darannan yahada kudinsa yatafi neman magani.sai dai kash takardun sun kone a shago lokacin gobara.meyeabunyi yanxu?bai runtsa ba kamar sauran dararendasika shude.yana wahala da ransa.sai dole yakaudakunya ya nemi wasu takardun yasaida gidan danbashida wata mafita data wuce wannan.idan yanasoya tsira da sauran mutuncinsa duk inda zashi..haka kuwa akayi da sassafe ya lallaba gidan maianguwa.baiko dawo masallaci ba.ya zauna yajirashi.ya gurfana gabansa yayita roqon gafara.sannanya miqa masa kukansa.mai anguwa bai bata lokacibaya amince domin shima zaiyi farin ciki idan danlitiyabar garin fandogari.saboda haka nantake yakawo takarda da biro suka rubuta wani takadda.dakansayanemo shaidu uku sukasa hannu.kuma yasa akanemo dillalai sukayi wa gidan kudi yace shi zai Saya,Gaba daya dubu dari biyu cinikin ya kaya.danliti yasallama ya karbi kudinsa a hannu.kafin qarfe goma nasafiya ya tattara yabar gari.gashi nan gashinan harwani kauye da ke tsakanin zariya zuwa kura jaharkano.da la'asar sakaliya.kofar gidan daya dosa cikeyafe fal!da jama'a anata alwala.a raunane yayi musu sallama.suka amsa ya tambaya..ko lafiya kofar gidanmalam?daya daga ciki yabashi amsa ai malam wa'adiyayi.shirin yimasa sutura ake.danliti ya dora hannuaka yace ciwo yayi? yace to ciwon ajali ne.kwanansabiyu kacal a kwance.ya nemi waje a qasa ya zaunahankalinsa ya qara tashi..wanda ke bashi amsa yamiko masa buta yana fadin hala kaima cikinalmajiransane?yace aytoo harda neman taimakoma.Allah sarki malam Allah jiqansa.yace amin yialwala yanxu za'a fito dashi.jiki babu kwari yafaraalwala.ya na kammalawa ana fito dashi.daganan sukadiba zuwa makabarta..ga kabarin malam an haqa duk abunda ake anyi akasakasa a kabari aka maida qasaakarufe iyalansa nata kuka harda danliti,Daga nan aka dan jira ayi masa addu'a kawai ganingawar malam akayi ta bulloqo waje,subhanallah! mekefaruwa ne? tashin farko jama'ar wajen suka watse.kafainbak iyi kibani waje musamman danliti.daya riga kowaficewa daga wajen.daga bisani liman yasa aka tattaromasa mutane suka dawo.danliti nacan baya yana rarraba idanu.liman yadaga murya yace innalillahiwainna ilaihi rajiun.! jama'a wannan al'amari fa banagudu bane.! wata ayace dake bukatar bincike.matsayin malam agarin nan wannan zai iya zama abin kuka agaremu.domin mu a zahiri munsan malam mai iliminaddini ne,,wanda ya koyar da almajire da yawa.wanda yake wakilta na lokutan danake da uzuri.sai dai ahalin yanxu wannan abun yanuna mana akwaiboyayyen laifi agareshi!ina rokonku dan girman Allahku tsaya muyi masa addu'a.mu roqa masa rahamarubangiji.alfarmar annabi muhammad (s.a.w) Yayi kabbara sau uku jama'a na amsawa.iyalanmalam kuka da firgici yaci qarfinsu labari kuwa tuniyabaza kauye.har wadanda wani uxiri yahanasu xuwasun sheqo aguje.shiyasa makabarta taqara cikamakil.liman ya jagoranci addu'a mai tsawo.sannanaka qara haqa kabari aka sakasa.shikansa liman kuka yake da hawayensa saboda ganin wannantashin hankalin.bayan anmaida qasa an rufe .sukasake tsugunnawa dan nema masa gafara.ai sai gagawa tayo waje.ana salatin annabi da tasbihi daistigifari akasake mai dashi.amma ba'a gama maidaqasar ba gawa tasake bullowa waje.liman ya dubi babban dan malam.ya tambaya!meka sani agame damalam wanda mu bamu sani ba? gashi ubangiji yananuna ishara gamasu yi su tuba su daina.ya gogekwalla yace wlh bansan komaiba,,,bantaba lura dawani aiki na assha atare dashiba.dana sani wlh danafadi sai dai ko aje atambayi mata a gida, LLiman ya numfasa duk guri yayi tsit!kawai sai ganindanliti akayi a gaban liman ya tsugunna Allah gafartamalam ni nasani.na kasance ina daya daga cikinmasu zuwa gun malam.neman taimako akanabubuwan dasuka damemu ko ince nemanduniya.bansan irin shirin dayake wa sauranba amma nida kaina. Nasha kawo ruwan..........ruwan maniyyinayana rubuta ayoyin Allah dashi.yana hadaminmagunguna danake buqata.ina bashi maqudankudade.tahanyar malam mun cutar da bayi Allahwadanda basujiba basu ganiba.ba malam kadai kebuqatar addu'a ba harda ni.Allah gafartawa malam.wuri ya kaure da sallami.wasu sukafarazungurar dan liti suna la'antarsa.liman yatsawatar.yace a saurara.tsarki ya tabbata ga ubangijindukkan halittu.jama'a kunji wannan mummunan tashinhankali?toga aya ta tabbata.ina ganin ta ishemutsoron Allah.ta ishemu mu gane komai ka boye wa mutane bazaka boye wa Allah ba..kuma ko ba dadekoba jima zaka koma gareshi.bamu da abinyi a halinyanxu dan hukunci yakoma gunsa. Ya daga hannunsa sama yaci gaba da fadin yaubangiji muna tawassali da sunayenka guda casa'inda tara,,,ka taimakemu ka amshi wannan bawa nakadan kar warin gawansa yazama guba ga bayinkasalahai!ya Allah ka sauqar da rahamarka cikinkabarinsa badon halinsaba.badon halinmuba.badon ayyukanmu ba sai don monxon mu annabimohammad (s.a.w)suka qarasa tare da muryoyinmutane dake cike maqil.kai tsaye liman yace akamaa maidashi.kankace kwabo ansakasa a rami anrufeakayi zuru! ana jiran ikon Allah.amma tsawon mintocishabiyar. Babu abunda yafaru.aka soma qabbara.liman kuwa fadi yake jama'a muji tsoronAllah.muji tsoron Allah ya al'umman musulmai.kodada nliti yaga haka saiya fakaici idon mutane tuni yasulale ya tsere kar yasha dukan banxa gun wadannanyan kauyen.A gigice yashiga kano cikin dare da kullin kudinsayanufi inda yasaba sauqa,,,,,zuwa safiya yayi amfanida kudinsa danyin wata sana'ar don riqekansa.washegari yashiga kasuwa yin sari wani mutumya bangajeshi ya wuce.saida aka hada masa kayandubu dari da hamsin.ya laluba kudi sukace daukarmu inda ka ajiyemu..nanda nan ya firgice.ya tubekayansa tsundur yana dube dube....ina kudin suke?anan fa na ajiyesu...masu shago sukayi zuru sunakallonsa.am ma dasukaga abin nasa babu hankali aciki sai suka turasa waje.ga ganin wannan mugun nufine yakawo sa Allah yakamashi.yakama haukan qarya.haka masu shagon da jama'ar wajen ketafadi.danliti kuwa ya rinqa bi kwararo kwararo akasuwayanata surutai.fadi yake...wannan bala'in yayiyawa..wata tsiyar ma sai anmutu.lalle lahira dakallo.toni wama zan kalla?aini ne zanxama abinkallo.da dama idan sukaji dariya suke.wasu kuma al'amarin yabasu tausayi.ga mutum har mutum daganiya aje iyali amma ba saiti,Bayan watanni hudu har mutan fandogari sunfaramantawa da abin mamakin daya faru...wanda ya ajetarihi musamman ga yan jarida ta yadda..suka rinqawatsa labaru.cikin shafukansu.na abin al'ajabindayafaru a kauyen dunduta.ba xato ba tsammanikawai sukaga danliti ya keto titi a kafa da rana face face.yayi bakikirin.gashi n kansa cunkus hade daqasumba.harda furfura.dafarko basu shaida shibasaida yayi sawu uku.nanda nan labari yayi tambari harkunnen su abba cewa danliti ya HAUKACE.Allah daikonsa,tunda ya iso fandogari bai qara gaba ba.nanyaketa bilayinsa.qafafu duk sun kumbura.wani lokacinma kasa tafiya yakeyi.kaganshi kwance cikinrana quda na binsa.idanyaji yinwa yayi tabin gungunmutane yana bara.asiya masa abinci.kai jama'a muceALLAHU AKBAR! **A watannan hudu,,ita mama sauyi sosaitasamu.domin tasamu matuqar kulawa a sati ukundatayi a masar.tacci gaba da samun kulawar yanuwanta.suna nuna mata gata fiyeda wanda tasamuada.tadawo sakeenarta.sai dai dan qara manyanta dafuskarta tayi.ayau suke sa ran dawowarta daga umara!inda tasami sati biyu a saudiyya tana ziyararka'aba.tana samun nutsuwa tare da miqa addu'ol daneman buqatu na alheri.sai dai bata sauqa abuja ba alegos ta yada zango.anty rabi dasu ameera sukadaukota a filin jirgi tayi bulbul. Abinta gwaninsha'awa.dokta yafi kowa tsaraba masu tsada.bayan taci abinci ta huta ta kira wayan abba.ya dauka tayimasa sallama kafin yace haba mama na! watau dagaske kike a legos din kika sauqa? tayi murmushitace yi haquri abba.ai bazan dadeba zandawo kwanauku kawai zanyi,Yace sunyi yawa mamana!kiyi kwana biyu na tabbatasun isheki warware gajiya.akwai magana muhimmiyadanake so muyi.tace shikenan abba Insha Allah jibinzanbiyo jirgi inade ya soja baiyi fishiba?yace yayiamma ya huce tunda yayan legos din yabada haquriinkindawo jibin kinqara wanke kanki.ta qara murmusawa tace nima na qosa in ganka abba dukkewarka tadamen.yayi yar dariya,,,mamana kenan tomuna sauraronki jibin.sai munsake waya tace toyanxuma zankira any amina mu gaisa. Toyayikyau.ace ina gaida halima.zangayamata.sukayisallama takashe wayan tasake kiran yayanta.sannan ta kira anty amina duk suka gaisa.tagaya musu inshaAllah jibi zasu iso abuja.daganan kaduna ta bugasuma suka gaisa.bayan tagama wayan duk indatakeson kira ta dubi dokto.dake liqe jikinta.kanatakallona na fiye surutu koh?yayi yar dariya yace nibanceba anty.taja habarsa tace ai nasan bazaka ceba.kai din waya kaika surutu?yaware ido kamarnata yace ni anty?ko a skul gentle man antynmu kecemen saboda banda surutu da yawa.Ta zura masa ido fuskarta cike da murmushi taceuhm.....yabon kai adai rage dokto saboda gobe yacemai zan rage?tace qarya!yadan cunno bakin takamatana dariya.toyi haquri gettlemen ai nima nasan kaigentle ne.akwai wasu cakulate a jakata miqominnaqara maka sunfi ta dazu dadi.yamiqe da gudu yadauko mata bisa madubi.ta bude ta kwasomasa.tadauki daya ta bare tace bude bakin insanyamaka...kunya takamasa.ya tsaya yana kallonta yanamurmushi.lah!kunya?dan kyauye bude mana.yakasabudewa sai rufe fuska yake ba zato tafara fadin bahaka akeyiba...gaskia ba haka akeyiba dokto!ka bude bakin insaka maka.anty rabi ta kyalkyale dadariya.sannan mama tagane tashigo dakin.tadubeta afirgigi.lah anty labe kike mana?ni yasu mezanyi walabe a sha'anin uwada danta?akwai dai son kai danbashi kadai bane dan.amma ankilliceshi shikadaianabasa gara.adai rinqa adalci...... Tayi dariya sosai tace kaji hassada,,bude bakinkamubasu haushi.ya bude tasanya masachocolate.suna ta masa dariya.ta jawosa jikinta tarungume..anty rabi tazauna gefen gadon sukaci gabada hira.da daddare ma bayan cin abinci haka sukataru.a falo suna kallo suna hira.da yayanta.washegari bayan cin abincin rana.suna kebe cikin daki da antyrabi..suna hira.mama tace anty nikuwa tuntuni nakeson tambayanki wani abu amma inajin nauyi.tazubamata ido menene shi? tace don Allah ko kinadatsofaffin hutunan su ameera da al'ameen?tayimurmushi mama kenan!inbanda abinki waya isa yarabaki da al'ameen balle yahanaki ganin hotonsaharda zaki rinqa jin nauyin tambaya?ni wlh bakiji dadindanake jiba innaga yanda kike hira da al'ameen dankisai inrinqa ganin kaman a'ameen dinkine.yanzu zanbinciko miki nasan dai suna nesa cikin tsofaffinalbum. Tayi murmushi to nagode!tamiqe tayita sauqe kaya tazakulo album din tadawo dashi inda mama kezaune.ta miqa mata tace gashi duba,,tafara budewatana kallon tsofaffin hotunansu harta kawo wandaal'ameen yadauka dasu ameera.yana tsakiyarsu duksuna dauke da wadataccen murmushi!gabanta yafadi ta bude ledar ta dauko hoton tazuba masa ido.dagacan tajiyo muryar anty rabi na fadin nidai mamatsorona daya kar ganin hoton nan yasake jefaki waniyanayin da bama fata.kinsan abba bazaiji dadiba.tanumfasa ta dubeta anty rabi nayi rashi tace nasani!nakuma tabbata shima bazai taba mantawa dakeba.tace zai manta idan haryasamu labarin mummunan halindanake ciki......takada kai nikuwa banjin wannanaraina saboda shine mutum na farko dayaqi yardacewar akan ra'ayinki kika canxa.kullum fadi yakeyasan kina sonsa..lalle akwai rashin sani a waniwaje.kowa yayi biris!da zancensa.dan anaganin zautuwar sanki ne.ta gigitashi.kinga kuwa banjinakwai wani abu dazai goge sonki aransa. Ta goge kwallan daya zuba mata.anty rabi tacekingani koh?gaskia bazan baki hoton nanba.kisa inyilaifi gurin kowa.tagoge da sauri tace bawani abu antyrabi kinsan Allah?zuciyata adake take kanal'ameen.kuma nasan narasa sa har abada.kuma nikaina bana fatan mu hadu.ina mai tabbatar miki a gaban ka'aba nayi wannan rokon wajen Allah.fatanaya amshi rokona.saboda haka kar hankalinkiyatashi.donkinga ina hawaye bazan iya hanasuzubowa bane..tunda sun taho sanadin farin ciki.tacegaskia ne.to Allah zaba mafi alheri.taceameen.intambayeki mana...waiya kikaji da akace miki danliti ya haukace?tayi murmushi ta kada kai tacemaizanji kuwa anty?ai qarshen alawa qasa kuma dukwanda yataba qur'ani.bazai shaba anty.Allah yayigaskia dayace qurani nashi ne kuma shi zai bashikariya! kinga kuwa danliti yadebota da zafi.wata qilada haqqina kadai yadauka abin yazo masa da sauqi.Allah ya shiryi zukatanmu baki daya.ta amsa daameen tana mata kallon tausayi,80..... .jirgin safe tabi xuwa abuja tana zaunecikin jirgi tunanin maganan anty rabi kawaitake.tabude jaka ta zaro hoton ta zura masaido,,,salon soyayyar dayake mata take karantowa.tasauqe numfashi cikin ranta tace inasonka al'ameenamma bana fatan sake haduwarmu dakai.tamaida hoton cikin jaka takoma ta jingina da kujera.taci gabadayiwa Allah tasbihi har suka iso abuja.tana fitowaharabar taran fasinjoji ta hangi anty amina a tsaye.Suka rungume juna zuwa inda tayi parking.suka shigemota anty amina tajasu zuwa gida.a guje tashigegidan cikin falo ta iske abba zaune kan kekensa ta zube jikinsa cike da murna..abba nah!mamana kenan! andawo lafiya? ta dago kai tadubeshi lafiya lau.yacenayarda saudi ta amsheki kinga kumatunki kuwa? tayidariya kai abba harda zolaya? yace aiba zolayabacekowa yaganki zai shaida hakan.anty amina tace nimadai haka nagani.tace to ai hakan akeso ko? yace kwarai kuwa bakiji dadin danajiba.toya mutan legos?tace qalau suke suna gaidaku.ina amsawa.anty aminatace nizan haura sama.Anty amina tace ni zan haura sama..duk abindakikeso naci akwai a kicin.tace to anty sai na hayosaman.tajuya ta haye saman tabasu gu su gana.abbayace kije kisamu abunda zakici..tace aibanjin yunwaabba karfe 12 ne yanxu akwai sauran lokaci.yacekodan ruwa mamana.?tayi murmushi ta miqe barin dauko abba..ta ajiye mayafinta tawuce kicin ta zuboabinci filet tanaci suna yan hiransu.tana bashi labarinumara har aka kira azahar.takaishi dakinsa yayisallah.itama taje tayi tasawo tasamesa yana cinabincinsa gefensa ta zauna ta qara yawan abincinsunaci tare abba kace zamuyi magana..amma bakace min komaiba?yace ina sane inasone ki qaranitsuwa.tace a nitse nake abba...kagayamin nimainada nawa maganan.yace toki saurarenidakyau.bayan tafiyarki umara kawunki alh basiru yabugamin waya wai mutane sunata zuwa nemanaurenki... ..aurena?yace wlh kuwa kuma abin mamaki duk yan fandogari ne..bangama nazarin maganarba..saiga wata wayar tasameni aranar dakika sauqalegos,,,ake gayamin ko yar gida zamuyi, Domin yayanki ali yadawo da maganarku tabaya.nace duk sumin uxiri kidawo muji tabakinki..nanda nan fuskarta ta sauya tashin hankaliyabayyana a fuskarta..abba ya zura mata ido kafinyace..yanaga hankalinki yatashi?hawaye suka gocemata tace dole hankalina yatashi abba nah!don ka kawo min maganar dana jingineta a babinrayuwata.....kamar ya mamana? aini addu'ata kenanAllah fidda miki miji nagari kuyi aurenku.hankalinkowa yakwanta..kuma Allah ya amsa ganin gamanema Allah ya turasu..ko baki zabi kowaba inakyautata zaton bazaki qi zaben dan uwankiba.domin aliyu yacika dan halas kuma masoyi na haqiqa. aliyuna daya daga cikin mutanen da bazanmantaba.saboda shine mutum na biyu daya roqe ninayi afuwa a gareki duk ranar da kika dawo gidalokacin dakika bi danliti kuka gudu.al'ameen shine nafarko sai ali.haka bana manta ranar daya kamo hannunki yakawo minke.ya durqusa yanema miki,Kuma ya hana mu daga miki murya saboda baqi cikingidan.aliyu ya jima yana zubda hawayensa akanBAKIN CIKIN Qaddarar data sameki.ba qaramin maisonki bane zai nuna maka irin wannan yardabamamana.a yanxu kinga zahiri ali mai qaunar ki ne.donAllah mamana kar kice bazakiyi aureba! saboda wani dalili nikam ayanxu banida wani buri face nagankidakin mijinki.ta kada kai tana share hawaye wannanbashi ne burinka akaina ba abba,,,tun banda wayaukagayamin burinka akaina amma yarinta yasanamaka musu.na sauya maka tunani.akan dolekadauki zabina.bansani ba wataqila musun dana maka ne yazamemin matsala.abba yanxu nayihankali burinka shine nawa,,,yadda kake sha'awar yamace likita insha Allahu Allah zai nuna maka ni amatsayin likita.kamar yadda kake burin hakan tunasali.da wannan tunanin nadawo umara.kuma itacemaganar danace zamuyi.don Allah abba kagoyamin baya akan rayuwar danake ganin itace zaman lafiyada kwanciyar hankalina,Kuka sosai takeyi hankalin abba yayi mugun tashiyace saurara mamana sanin kanki ne idan na goyamiki baya kikaqi aure,,haqiqa nabi son raina.ni aganina ai auran bazai hanaki karatu ba.idan banmantaba hakan kuka shirya da al'ameen.Allah ne bainufaba inkuwa hakane mezaisa ki fasa mamana?tace abba a fuska faram faram,amma zuciya saiAllah.inada abin gori ajikina wanda yazame mini adolena nesanta kaina da kowa.don tsira damutumcina.abba na tabbata ka gane nufina.dangirman Allah kaban izini nakama karatu.ya kada kaicikin damuwa.mamana ko wani zai miki gori kamar yadda kike hasashe na tabbata aliyu dan uwankibazai miki gori ba.ki sadauqar masa da kanki kamaryadda ya miki halacci lokacin da kowa yakyamaceki.tace zan iya yiwa ya ali komai muddin inadashi har qarshen rayuwata amma bazan iyaaurensaba.tu nda yanada mata.kubashi haquri yaci gaba da juriya da kulawa da iyalinsa yadda yadace.tayunqura ta tashi tayi waje.abba yabita da kallo yanasoyakirata amma ya kasa saboda tausayinta. ana fitowa ta hadu da yayanta yana shigowa.ta rugata rungume shi yace menene? takasabashi amsa yajata suka koma dakin abban yanazaune shiru yana juyayi,,abba meya faru ne? sukazauna kusa da abban yace ba'ayi komaiba akan maganar nan ne dana gaya maka masu sonta daaure.shine tace karatu zatayi amma ban yarda dahujjojintaba.ina ganin aurenta zai zamo mata garkuwaaduk inda zata neman ilimin.yaya soja yace gaskia nesai dai inbata aminceba akwai matsala dan ita bayarinya bace.tasan abinda take hangowa kanta,,,so pls abba..idan bazaka damuba a madadin sauran yanuwana muna roqonka kabar autanmu ta nemiilimi.ahankali zata gane aurenma yanadamuhimmanci.dakanta zata kawo maganar cikin gidannan so please abba!please!!ya tallafe goshi shiru jim!Ya dubesu yace.shikenan Allah yasa hakan shine mafi alheri matsalata kawai bansan mezan cewa aliba.inajin nauyin yaron nan.farin ciki ya mamaye matazuciya.yayin da ya soja ke fadin yayi haquri.Ai ali ya girma babu wannan haukan yarinta a taredashi kamar da.kekuma dole kiyi taka tsan tsan andaishaki kin warke.rayuwa ta zarce duk yadda kikezatonta saboda haka ki kiyaye.tayi murmushin farinciki ta matsa kusa da abba nagode abba,,kuma dayardar Allah zan kiyaye.yadafa kanta yace Allah yayi miki albarka tace amin.yaya nagode.yace inatsarabata?kinje kin rabeta a legos ko?kin kai wa lazydokto.ta rufe baki hannu biyu lah yaya me kake nufi?ya damki bayan wuyanta yace are u askin me? aiangayamin kayan al'ameen yafi tsada da yawa.taceok nasan magulmaciyar ameera ce babbar kwabo batada abokin kishi sai al'ameen.sukayi dariya abbayace umman takice mai gulma?lalle ya ta riqa.tacigaba da dariya tana cewa ni ummata bata kishi dakowa.Allah ya jiqanta amin.anty amina tayi sallama tashigo ta zauna cikinsu abba yace mutuniyarki taqiyarda.yayanta kuma yace abarta tayi karatu.tayi murmushi kayi haquri akan hakan abba Allah saalherine.yace amin haka nake fata.hira ta tsunke ananya soja yaci abinci. BAKIN CIKI 3***8 Ai ali ya girma babu wannan haukan yarinta a taredashi kamar da.kekuma dole kiyi taka tsan tsan andaishaki kin warke.rayuwa ta zarce duk yadda kikezatonta saboda haka ki kiyaye.tayi murmushin farinciki ta matsa kusa da abba nagode abba,,kuma dayardar Allah zan kiyaye.yadafa kanta yace Allah yayi miki albarka tace amin.yaya nagode.yace inatsarabata?kinje kin rabeta a legos ko?kin kai wa lazydokto.ta rufe baki hannu biyu lah yaya me kake nufi?ya damki bayan wuyanta yace are u askin me? aiangayamin kayan al'ameen yafi tsada da yawa.taceok nasan magulmaciyar ameera ce babbar kwabo batada abokin kishi sai al'ameen.sukayi dariya abbayace umman takice mai gulma?lalle ya ta riqa.tacigaba da dariya tana cewa ni ummata bata kishi dakowa.Allah ya jiqanta amin.anty amina tayi sallama tashigo ta zauna cikinsu abba yace mutuniyarki taqiyarda.yayanta kuma yace abarta tayi karatu.tayi murmushi kayi haquri akan hakan abba Allah saalherine.yace amin haka nake fata.hira ta tsunke ananya soja yaci abinci.Basu tashiba sai la'asar kowa yaje sallah.bayan taidar da sallah ta haye gado tasaka (ear piece)tanasauraren karatun qur'ani.wucewar minti talatin tanasaurare dadinsa na ratsata.tashi guda karatun yayanke adalilin kiran daya shigo.ta duba allon wayandan ganin waye sunan ya ali ya bayyana.gabanta yafadi amma ta daure ta danna ok' ta dauka kawaitaci gaba da saurare.da sallama ta fara.ya amsadawata muryar dabata saba jiba.tace yaya ali dangirman Allah......ya katseta da sauri yace karki hadanida Allah ki cuceni mama!meyasa baki tausayina newai?ta numfasa idanu suka kawo kwalla.tace bazaka fahimceni bane ya ali .....yace babu abinda zanfahimta mama,,,ai dama kin dade kina azabtardani.axatona yanxu tunda babu al'ameen zaki iyamaye gurbinsa dani.ashe bazaki iyaba? wannan yanatabbatar min ko alama can zuciyarki bata sonamama.mesa?ta kada kai tace yaya ali ba haka bane nasan ada al'ameen kadai naso amma ayanxu hardakai kashiga raina.saboda halaccin dakamin.wlh dazaniya aure kai zan aura Sai dai bazan iyaba don girman Allah kayi haquri..yayiajiyar zuciya yace mesa mama? kinkuwa san yandatausayinki ya ke bin jinin jikina?bani da wani buri dayawuce kizama matata mama don inshare mikihawaye.kimanta rayuwar wahalar dakika sha canbaya.kiyi tunani zanbaki lokaci karatu kuwa na miki alqawarin ko ina kikeso zakije indai kinxama mataagareni.kai tsaye tace bana buqatar lokaci yaya ali.ainagama yankewa kaina hukunci..kariqe matarka zaifima kyau yaya ali..idan kuwa qari kake sha'awakanemi maras tabo ka aura.tabo? ban fahimceki bamama.tace bazan jure goriba.ka kuwa san yauda gobe sai Allah.ba daga gareka nakejiba ina nufinkishiya da kaidinta.zan iya mutuwa saboda BAKINCIKI.Duk ranar da matarka ta gorantamin.wani abudaga rayuwata.kasani ba ruwan kishiya da asiri idantaso musguna maka zata iya maka sharri zata iyarufe komai ta musguna maka da gangan.Yaja dogon tsaki wannan ne hujjarki mama?ni bankarbetaba dan nasan amina bazatayi mikihakaba.idan kuwa harta kuskura zan nuna matabayan tsananin sonda nake miki zan nuna mata keyar uwata ce ta jini.saboda haka bake zatayi wagoriba ni zatayiwa.tace nagode Allah da bakinka

Chapter 23 of 28