Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
gashi duk ta fige ba kyan gani, shi dae bae tanka ma inna ba ya fice, Inteesar dae na kwance falo sae mayar da numfashi take don da kyar ta iya karasowa cikin gidan bayan sun sauka daga mota, kuma da asibiti ne baya barinta ta taka da kanshi yake daukarta su shiga ciki, inna tace "to wae wani irin jarababben cikine wnn dake neman kashe min ke," ta mike xaune tana hararan inna kmr xata yi kuka tace "wae ni nace maki ciki gareni ne," bata jira me inna xata ce ba ta shiga daki tayi kwanciyarta, inna duk ta daga hankalinta ganin irin laulayin da Inteesar take mai tsanani, bbu wanda bae san ciki ne da ita ba a gidan, ko da yaushe cikin amai da kasala take, ko maganan kirki bata son yi sae in Aliyu na yasa ta gaba ko yana tambayarta me take so, duk tausayinta kawae yake, Hajiya da hankalinta yyi mugun tashi bata ga fuskar da xata ma Aliyu magana ba da ya shigo da ya fice daga gidan, tab aiko gwara ta nemo yanda xa ayi da cikin nn, ynxu Aliyu dama sae ya iya kwana daki daya da yarinyar nn duk cika bakinsa, hka aka yi biki hankalin inna rabi na gurin Inteesar rabi na gun bikin, duk aka yi abubuwa masha Allah, amma inteesar na kwance tana fama da kanta, safeena ma ta xo ranar bikin tana daddaga hanci ita matar Aliyu inna ta kunyatata gaban lodin jama'ar biki su kursum dariya kmr xasu shide, ko minti daya bata kara a gidan ba tayi gaba ba shiri jikinta a sanyaye har ga Allah tsoran tsohuwar nn take, ran Hajiya yyi mugun baci amma bbu yanda ta iya da inna, washegarin ranar da aka kai Amarya da daddare Aliyu ya shigo falon inna bae ko kalli innar ba ya durkusa gaban inteesar dake kwance idonta biyu, ya daura hannu a goshinta yace "amma yau bakiyi amai ba ko," a fusace inna tace "kaji gantalalle wani irin bata yi amai ba, ae hanjin cikinta ne kadae bae xaxxago ba yau har tsorata nayi nace to ko su ne ke shirin fitowa" Aliyu yyi mata mugun kallo yace "to ke kuma wa ya somo bakin ki nn, iyayi kawae," sae abun ya ba Inteesar dariya ya dago ta yana kallonta yace "Abba na neman mu, xaki iya ko na daukeki," ta marairaice tace ynxu, ya gyada mata kai, ita mugun kunyan Abba take ji har ma da momynta, duk shigowar da momy take ta gaisheta kar inna ta xaxxageta tace taki xuwa, Inteesar yi take kmr tana bacci, inna ta mike tsaye da sauri tace "bari kawae na kama hannunta mu je," Aliyu ya bude baki yana kallonta yace "wae meyasa kike son shiga tsabgar da ba taki ba ne," bae jira me xata ce ba ya harareta ya sa ma Inteesar hijab dinta ya dauketa suka fice, inna tayi kmr xata yi kuka tace "ni ban san meyasa yaron nn ya rainani da tsufa na da furfurata ba," a hanya ya ajiye ta dalilin rokansa da ta dinga yi ya ajiyeta suka karaso falon yana rike da hannunta, da kyar ta iya bude baki ta gaishe da Abba kanta a kasa, ita kawae kunyarsa take ji, yace "ya jikin fateema," kanta a kasa tace "da sauki Abba," yace "to Allah ya sauwake, kina son komawa dakin ki ne ko xaki xauna nn gun inna sbda condition dinki" ta dago kai a hankali tana kallon Aliyu, shima kansa a kasa yake, tayi shiru ta rasa me xata ce don ita kam bata da burin cikin nn ya kara girma a jikinta, Aliyu yace "Abba da dae na tafi da ita xan fi kula da ita a can kuma ba gida ma nake barinta ba tare da ita nake xuwa clinic, nn ko xae yi min nisa kuma xan takura kaina," Abba xae yi magana inna ta fado falon, ashe tana labe tana jin duk abinda suke cewa tana huci kmr xata yi kuka tace "amma munafurcinka dayawa yake Bukar, hka muka yi da kai? To ni Rahmatu nace bbu inda yarinyar nn xata je aje a kashe min ita da abinda ke cikinta a banxa a hofi a barni da wayyo Allah, don idan an kashe su ma ni nayi hasara ba ku ba". .. Aliyu ya dan yi tsaki ya kauda kai, Abba kam shiru yyi yana ta kallon inna, ita ko ta tsaya masu kmr soja a bakin kofa, can dae Abba yace "to ki hada kayanki sae ki bi su," tayi kwafa tace "ko da naji," snn ta juya ta fice da sauri, Abba ya girgixa kai yace "tashi ka dau matarka ku tafi," Aliyu ya mike yana kallon Inteesar, ita ma ta mike tsaye suka ma Abba sallama snn suka fita, yana rike da hannunta yace "mu je mu gaida momyn ihsaan ne," tayi kmr bata ji sa ba shima bae sake ce mata komai ba har suka fita ya bude mata mota ta shiga shima ya xaga ya shiga suka kama hanyar gida, ko da suka isa tayi bacci ya fito da ita daga motar yana rike da ita kmr bby, safeena na kwance falo ta bi su da kallo ya sakar mata murmushi yace "bbyna," tayi tsaki ta dauke kanta tacigaba da kallonta, sae da ya kai Inteesar sama ya kwantar da ita snn ya sauko ya sameta, ta mike tayitsaki ta haura sama ta bar sa nn ya bita da kallo snn yyi mmrshi yabi bayanta. Washegari sae da safeena ta sa ya makara xuwa office, wanka kawae yyi ya shirya ya dauki makullin motarsa ta rakasa tanai masa shagwaba ya manna mata kiss ya ja motarsa ya bar gidan, ta sauke ajiyar xuciyan jin ddiyau dae ya manta shegiyar gaba daya, ta koma cikin gida murna fal cikinta, tana shiga daki ta fito da kullin maganin da aka basu su sa ma Inteesar a ruwan sha ta tsura ma maganin ido tana murmushi,dukiya fa knn a hannunta, ruwan fridge ta kwashe gaba daya ta bar guda biyu ta xuxxuba maganin cikisnn ta rufe fridge din ta koma sama, ta lura kasa Inteesar ke saukowa shan ruwa bbu ruwa a dakinta kuma bata ga alamar an siyo ba, tana ta kwance a daki tana jiran jin saukowar Inteesar amma shiru, ita ko tana kwance daki ta rasa inda xata sa ranta sae juye juye take ga yunwar da take ji tun safe ta gane Aliyu ya bar gidan hkn yasa ta daure ta mike ta sa ma kofar ta key, kishin ruwa duk yabi ya ishetagashi ba karfin sauka kasa, da kyar ta rarrafa ta shiga bathroom ta bude tap ta sha ruwa ta dawo tayi kwanciyarta kan tiles. Washegari ma abinda ya faru knn Aliyu bae shigo ya ga halin da take ciki ba ya bar gidan da sassafe, duk da jiya don ita ya dawoda wuri amma safeena ta gusar masa da hankalinsa ya manta me ya dawo da shi, ganin yunwa na neman yi mata lahani yasa ta dinga daurewa tana hada tea a nn dakinta da ruwan sanyita sha, shima tana sha ta amayo, duk ta kara xabgewa bata da aiki sae na kuka ita daya a daki, wani lkcn sae taji kmr ta dauki waya ta kira inna kawae sae ta fasa don bata ga amfanin kiran ba don rabuwa kawae take son yi da cikin, ita safeena bbu abinda yafi daga mata hankali irin yanda taga ruwanta na nn ajiye ba a taba ba, hkn yasa da daddare da Aliyu ya dawo ranan tace "anya kuwa kana shiga duba baiwar Allahn nn dear, gashi ita bafitowa take ba, na kan shiga na dubata wllh, amma ba ddewa nake ba kar ace xan yi mata wani abun ne" Aliyu ya mike da sauri kmr an tsikaresa yyi hanyar stairs ta bude fridge ta dauka ruwan da sauri ta bi sa tana cewa "gashi ka kai mata ruwa naga kmr jiya ruwan dakinta ya kare na fanfo take sha, ni kuma kar na kai mata ta xata wani abun ne," ya karba ya haura sama ya bude dakin ya shiga rabon da ya ganta yau kwana uku tun ranar da sukadawo daga gida, ya karaso gabanta ya durkusa yana kallonta a hankali yace "ya jikin fateema, kin daina aman," tayi tsaki ta juya abinta, ya bude fridge dinta ya ajiye mata ruwan yace "me xaki ci," tayi bnxa da shi, yyi shiru yana kallonta, ta juya cikin kuka tana kallonsa tace "wllh tllh idan baka cire min wnn shegen cikin ba...." bae jira ya karasa jin maganarta ba ya xuba mata mari, "don uwarki kika sake min maganar cire ciki sae nayi mugun saba maki kina ma da hankali kuwa, to ki je ki cire tunda ke mahaukaciya ce," ya mike a fusace ya fice daga dakin ta bisa da kallo dafe da kuncinta. Ranar bata yi bacci da daddare ba, kawae Allah Allah take gari ya waye, gari na wayewa ya shigo dakin kafin ya tafi aiki, tea me kauri ya hada mata ya ajiye matagefenta, snn ya dauko goran ruwan da safeena ta basa jiya ya ajiye mata gefenta safeena ta shigo dakin tana murmushi tayi ma Inteesar ya jiki ko kallonta inteesar bata yi ba suka fice tare da mijintata rakasa ya shiga mota ya manna mata kiss snn yaja motar ya bar gidan, safeena ta koma gidan xuciyarta fari tasa ganin goran ruwan da ta ba Aliyukusa da inteesar yau dae xa ayi ta ta kare, ta shige dakinta tana dariya. Inteesar ta mike tsaye ta dauki Hijab dinta ta saka, duk irin wahalan da take sha ko sau daya wanka bae taba wuce ta da safe ba dole sae ta daure ta shiga tayi, ta fito tana ganin jiri mai gadi ya tsaya xae mata maganar bnxa ta fixgo gate din ta fice abinta ta barsa nn tsaye, gidan Aneesah ta shiga, tana xaune tana ba shakur Indomie, tana shigowa ta kwanta kan kujera tana mayar da numfashi, Aneesah tace "lah daga ina hka Inteesar daxun nn nagama xancenki a xuciyata wllh" Inteesar xata yi magana taji yawu bakin ta mike da kyar taje bathroom ta xubar Aneesah tace "A'aah kice oga yyi aiki" . Inteesar ta harare Aneesah snn tayi tsaki tace "ni don Allah taimako naxo kiyi min Aneesah," Aneesah tayi dariya tace "to kawas ina jinki amma cikin nn na baki wahala gskya, kinga yanda kika rame kuwa," Inteesar ta dawo kasa kusa da ita tace "don Allah don Annabi Aneesah kinsan inda ake abortion?" Aneesah tayo waje da ido da mamaki tana kallonta snn tace "kina da hankali kuwa inteesar," inteesar ta jinginar da kanta jikin kujera hawaye ya cika idonta, Aneesah tace "kinyi shiru," inteesar ta share hawayen idonta tace "wllh xubar da cikin nn xanyi kin dae ji na rantse in ma xaki gaya min ki gaya min," Aneesah ta gyada kai tace "to tashi ki fita a gidana, ni bana hulda da maras tsoran Allah," inteesar ta juya tana kallonta tayi shiru snn ta mike tayi hanyar fita daga gidan, Aneesah ta bita da sauri ta kamo hannunta tace "haba inteesar bafa kiyi kama da jahila ba," kuka inteesar ta fashe da tace "baxa ki gane ba Aneesah wllh bana sonsa bana son cikinsa, bae damu dani ba sae wahala nke ta sha," Aneesah ta xaunar da ita tana kallonta da tausayi tace "ni na tabbatar maki kina haife wnn cikin xaki ga tsantsan so gun mijinki, ni banga rashin son da mijinki yake maki ba inteesar nafa ga abinda yyi ma kishiyarki ranar sbda ke, don me xaki walakanta kyautar da Allah ya baki yar uwa," inteesar tayi shiru tana ta sauraran Aneesah tana ta wa'axinta da nasiha, har ta kai Aya snn inteesar ta kirkiro murmushi tace "to ngdd Aneesah, ta dauki shakur tana ta wasa da shi yana mata dariya, tace "amma a gida kika haife yaron nn ko Aneesah," Aneesah tace "me kika gani," inteesar tayi yake tace "aa kawae tambaya ce nayi don ni dae ina tsoran Haihuwa," Aneesah tayi dariya tace "A'a a asibiti na haifesa," inteesar tace "wani asibitn?" Aneesah tace "A'a tender care na haifesa, ai kin san asibitin bbu wani nisa," Inteesar tace "A'a" Aneesah ta gaya mata inda asibitin yake kuma dama abnda kawae take son ji knn, ta mike xuciyarta fal murna ta bar gidan. . Inteesar na fita daga gidan Aneesah ta koma gida cike da jin ddi ta shiga dakinta tana haki kmr warce tayi gudu, ta tabe baki jin wakan da ke tashi dakin safeena, sae da ta huta na kusan minti goma snn ta mike ta dauki purse dinta ta fita daga dakin, dakin Aliyu ta bude a hankali ta shiga ta bude drawer din da taji yace Safeena ta bude ta dauki kudi ranan, taji ta a kulle, tace "na shiga uku," ta mike ta fara kalle kallen cikin dakin kmr xata yi kuka, to ina xata samu kudin xuwa asibitin ynxu, drawers din dakin ta dinga bubbudewa gaba daya ko xata ga kudi amma bbu, duk ta gaji sae haki take, tuni ta fara kuka tana cewa "Allah ka taimakeni in ga kudi" ta bude lst bedside drawer din taga wani babban book an rubuta my diary a gaba, tayi tsaki ta ajiye ta mayar da drawern, ta mike ta isa wardrobe din da yake ajiye kayansa na sawa ta bude ta lumshe idonta sakamakon wani kamshi me ddi da ya bugi hancinta, ta gama bincikenta nn ma ba ta ga kudi ba ta rufe ta xube kasa ta daura hannu a ka tace "wayyoo Abbana wllh ni na gaji," ko ina ta bude daga taga Allura sae taga magunguna da dae kayan asibiti kmr tsiya wnn wace irin jaraba ce, kmr ance ta mike ta daga filo taga dubu daddaya karkashin filon har da Atm dinsa ta wara ido tace "wayyo Allahna," ta kwashi kudin ta shiga kirgasu da sauri hannunta na rawa taga dubu sha biyu ne, ta dan marairaice fuska to xae isheta taje asibitin ma kuwa, tayi tsaki ta bude purse dinta ta xuba kudin snn ta juya xata fita daga dakin taje dakinta ta sha ruwa don mugun kishi take ji don tsabar son taje ta cire cikin ta nemi xaxxabin dake tattare da ita ta rasa sae kasala kawae, har ta isa bakin kofa ta dawo da sauri tuna baxae rasa ruwa a dakinsa ba da tayi ta bude fridge dina ta ko ga ruwa ta dauka ta bude ta sha snn ta rufe fridge din ta dauki sauran ta fita daga dakin, duk wnn abinda take safeena bata sani ba, tana daki kwance tana ta shan kida cike da jin ddi, jiran jin ihun Inteesar kawae take a ko wani lkci, Inteesar kam har ta fita daga gidan rike da purse dinta cikin Hijab, mai gadi dae bae ce mata kala ba ta bude gate ta fice abinta sae da ta isa bakin titi snn ta tsayar da tricycle tayi masa kwatancan asibitin da Aneesah ta gaya mata yace ta bada dari biyu, ta shiga tace mu je. Wasa wasa asibitin shegen nisa ne da shi, yyi parkin dae dae gate din asibitin ya juyo yana kallonta yace "mun kawo Hajiya," ta fito tana kare ma asibitin da ma anguwar kallo, ta bude purse ta ciro dubu daya cikin kudin ta basa kudin ya rage dubu sha daya, ya bata canjinta ta karasa cikin asibitin gabanta na faduwa, wnn dae da ganin asibitin nn ba na talakawa bne, anya kuwa xasuyi mata abortion a dubu sha daya kuwa ta dan karyar da kanta abun tausayi, da Addu'arta ta shiga asibitin, babba ne ssae ta karasa cikin reception ta xauna ganin patients dayawa a xaune, ta shiga kare ma reception din kallo, ta kai kusan minti talatin a xaune ba a xo kanta ba duk ta gaji, taji kwanciya kawae take son yi ga amai dake taso mata, ta daura kanta a cinya taji kmr ta rusa ihu duk ta rasa ina xata sa ranta, wata nurse ce ta dafa ta ta dago da sauri tana kallonta, Nurse din tace "yhur card nmbr Madam," inteesar ta shiga kalle kalle xata yi magana taji yawu ya cika bakinta, nurse din ta lura da hka ta nuna mata bayin dake kasan reception ta karasa ta xubda yawun ta kora ruwa snn ta dawo, nurse din ta debo vitamin c ta mika mata ta sa a baki tayi mata gdya ta karba, tana kallon Nurse din tace "i dnt have a card in here," Nurse din tace "to dole sae kin yanki kati," Inteesar tayi shiru snn tace "nawa ake yankan katin," nurse din tace "family card dubu biyar, na mutum daya dubu 2 da dari 5," inteesar tayo waje da ido tana kallonta, ganin xata bata ma nurse din lkci ga kuma patients dayawa suna jira yasa tace "to ki yankar min na mutum daya," nurse din tace "ok" snn tayi gaba, a hankali inteesar tace "na shiga uku, to ai kudin ya kare," ba ajima ba nurse din ta fito daga wani dan daki ta mika mata katin snn wata nurse ta daddubata ta duba har da weight dinta tayi rubutu a file tasa nurse ta rakata bayi aka xuba mata ruwa a kanta don temperature dinta yyi sama, ita dae binsu kawae take, a xuciyarta tace ko da yake basu san me ya kawota ba shiyasa suke bata lkcnsu, ita dae ynxu likita kawae take son gani, wata nurse ce ta gwada mata office din doctor din da xata shiga a sama, tana rike da file dinta ta haura sama da kyar ta karasa office din tayi knock. A hankali Inteesar ta tura kofar bayan an mata ixinin shigowa office din, cak ta tsaya daga bakin kofa tana kallon likitar, doctor din ma ta mike tsaye tana kallon Inteesar da mamaki tace "fateema," inteesar ta kirkiro murmushi gabanta na faduwa ta karaso office din a sanyaye, ta nuna mata kujera ta xauna, doctor din tace "daga ina kike hka fateema, me ya kawo ki nn," ta rasa karyan da xata mata, da kyar bakinta na rawa ta ce"banda lfya ne," doctor din ta hade rae tace "shi Aliyun fa," inteesar ta rasa me xata ce ga xuciyarta sae tashi yake, likitan ta dawo kusa da ita tana kallonta ta dago kanta tana kallon cikin idonta tace "ciki gare ki fateema," inteesar tayi shiru bata ce komai ba, doctor din ta ciro wayarta ranta a bace ta shiga neman layin Aliyu, da sauri inteesar ta dakatar da ita gabanta na faduwa tace "A'a don Allah doctor kar ki kirasa wllh ya sani kuma yana dubani nice dai bana son shi ya duba ni, Allah yana kula dani doctor kawae ni ce bana so, idan yaji na xo nn xae bata min rae don bae sani ba," doctor din tace "haba fateema, to ma don me xaki fita ba tare da ixinin mijinki ba, kuma meyasa baki son ya duba ki," inteesar ta fashe da kuka tace "wllh ni bana sonsa doctor," doctor din ta tsaya da mamaki tana kallonta snn tace "sbda me fateema, gashi har rabo ya shigo kice baki son mijinki," Inteesar ta sunkuyar da kai tana hawaye, doctor din tayi shiru tana kallonta, can ta koma sit dinta ta xauna ta shiga yi mata nasiha kan cewar ta rungumi mijinta ta cire duk wani rashin sonsa a ranta, ita dae bata ce komai ba sae kukan da take a hankali, Doctor din tace "yyi maki scan ne?" inteesar ta girgixa kanta tace "A'a nace masa bana so," doctor din ta harareta tace "to karki sake yi ma mijinki musu baki san aljanarki na karkashin kafarsa ba," inteesar ta dan tabe baki kanta a kasa ba tare da ta bari doctor din ta lura ba, doctor din ta yagi wani takarda ta danyi rubuce rubuce snn ta danna bell wata nurse ta xo da sauri, ta mika mata takardar tace "scan xa ayi yi mata sisterna ce," doctor din ta kalli Inteesar tace "tashi ki bita," inteesar ta mike a sanyaye ta bi bayan nurse din har sun kai bakin kofa ta juya tana kallon doctor Maryam tace "don Allah doctor kar ki kirasa wlh xae bata min rae,"doctorn tayi murmushi tace "baxan kirasa ba ki kwantar da hankalinki" bayan kusan awa daya inteesar da nurse din suka shigo da sakamakon a hannun nurse din, ta mika ma doctor maryam ta fita, doctorn ta bude takardar tana dubawa, inteesar dae kallonta kawae take ranta a hade, ba shiri taga doctor maryam ta mike tsaye da sauri tace "waw Ahmdllh, twins 4 Aliyu, Allahu akbar," ta rungume inteesar tace "Allah ya raba lfya kanwata, kinga ma yan biyu ne" inteesar ta sunkuyar da kanta da sauri hawaye ya cika idonta, hka doctorn ta dinga mata surutu cike da murna kmr ita xata haifa ma cikin, ita dae bata ce mata komai ba daga karshe ta hada mata magunguna, da allurori a office dinta ta xuba mata su a leda da takardar scan din tace "to maxa tashi ki koma gida sae ki kai masa takardar scan din, sae ya fada maki yanda xaki sha magungunan yyi maki alluran," Inteesar ta mike da sauri kmr jira take tace "ngdd ssae doctor," har gate doctorn ta rakota snn tayi mata sallama bayan ta kara jaddada mata ta hakura ta xauna da mijinta, ita dae inteesar sae gdya take mata har ta koma ciki snn ta kama hanyar titi inda xata samu tricycle, a cikin wani flower ta watsar da magungun da injectns din dake cikin ledar dake hannunta ta bar takardar scan din kawae, ta isa titi xuciyarta na suya, ta tsayar da tricycle tace "malam don Allah idan kasan ko wani asibiti a nn wajajen ka kai ni," yace "to shigo muje akwae wani can gaba," ta shiga da sauri ya ja machine din suka kama hanyar asibitin, ae ko yan goma ne a cikinta ba yan biyu ba sae ta xubar da su yau wllh . Wani babban Asibitin aka kuma kawota, ta fito tana kare ma asibitin kallo snn tace "nawa xan baka," yace "ki bada ko nawa ne," ta ciro dari biyu ta mika masa tayi hanyar gate din shiga asibitin, gabanta ya shiga faduwa ganin asibitin bana wasa bane don har yafi wanda taje da xu, tana isa reception bata tarar da patients da yawa ba aka xo kanta, nurse din tace "yhur card nmbr madam," Inteesar tace "i dnt have a card in here, nawa ne katin," nurse din tace "family card dubu biyar, na mutum daya dubu uku, na Anti natal, dubu biyu," Inteesar ta ciro dubu uku ta mika mata, matar tace "sunanki fa," inteesar tace "Fateema Aliyu," matar tace Address fa? Da date of birth, Inteesar ta bata fake address da date of birth dinta, matar ta juya ta wuce, ba ajima ba ta dawo ta mika mata katinta snn aka dubata wata nurse ta rakata da file dinta a hannunta xuwa office din doctor, yana xaune yana ta rubuce rubuce farin glass a idonsa, sae da gabanta yyi mugun faduwa don sae taga kmr ya Aliyu barin yanda ya hade rae da tsukekken bakinsa, shima kyau kam ba a magana, ta karasa office din xuciyarta na ci gaba da bugawa ta ajiye masa file din a gabansa ta xauna kan kujera a sanyaye tana kallonsa, yana ta rubuce rubucensa har lkcn bae dago ba, hkn yasa ta dan marairaice a hankali kmr me shirin kuka tace "doctor," sae a snn ya dago yana kallonta yace "srry ina dan abu ne," ya jawo file dinta gabansa ya bude, tana kallonsa a sanyaye tace "don Allah don annabi taimako naxo ka min doctor," ya dago yana kallonta yace "taimakon me fa," nn da nn hawaye ya cika idonta ta rasa me xata ce, yace "tok 2 me mana yan mata, taimakon me kike nema, baki da kudine kika xo a dubaki," ta girgixa kai ta fashe masa da kuka tace "A'a," ya kauda kansa yace "ni karkiyi min kuka a nn, ki fadi abinda ya kawo ki, mijin ki fa?" a hankali muryarta na rawa tace "ni banda miji," ya wara ido yana kallonta yace "wat? Amma kin san kina dauke da juna biyu kuwa," ta fashe da matsanancin kuka tace "ka taimaka min ka tausaya min ka cire min don Allah abinda ya kawo ni knn," yace "kina da hankali kuwa ca aka maki ana xubar da ciki a nn," cikin kuka tace "nasan ka iya doctor, ni taimakona nake son kayi don Allah," ya girgixa kai yace "me ya aike ki kanwata, meyasa kika xabi ki..." da sauri ta katsesa tace "rapin dina aka yi, kuma har yau ba a sani ba a gida," yace "innalillahi wa inna'ilaihi raji'un, to don me baki fada ba a gida" tana kuka tace "ba yrda dani xasu yi ba wlh," yace "to waye yyi maki," tayi shiru kmr me tunanin abinda xata ce nn kuma amai ne ke taso mata, ta daure tace "saurayina ne," yyi shiru yana kallonta, mikewa yaga tayi da sauri shima ya mike, yaga ta toshe bakinta ya bude mata bayi da sauri ta shiga ta fara kwarara amai, yana tsaye gefenta tausayinta ya rufesa ganin yanda take aman kmr xata shide amma bae taba ta ba har tagama ya bata ruwa ta wanke bakinta ta xuba ruwa a wajen ta fito da kyar ta xauna kan kujeran ta kifa kantakan table dinsa abun tausayi, yace "to sae mu ce ma Allah me, wllh ban taba xubar ma mace ciki ba kanwata," ta dago tana hawaye tace "plss ka taimakeni kuma ka fadi nawa xan baka ko ba yau ba xan biyaka don kudin hannuna ya kare," shi dae yyi shiru bae ce komai ba, har dae daga karshe ya mike ya fito gabanta yana kallonta yace "takardar meye a hannunki," ta kalli takardar snn tace "na scan da nayi ne," ya karba yanadubawa snn yace "Mrs Aliyu kuma aka sa," kmr xata yi kuka tace "kunya nake ji, ace bani da miji kuma gani da ciki," bae ce komai ba ya maida idonsa kan takardar yace "ya salam, yan biyu ne ae," ta gyada masa kai tana hawaye, ya koma ya xauna ya dafe kansa, yace "anya kuwa xan iya taimakon nn kanwata, rae biyu fa kuma har kusan 2mnth," ta fashe masa da wani sabon kukan tace "don Allah ka rufa min asiri," ya mike shima da ganin sa kasan jikinsa yyi sanyi, ya bude wani show glass din magunguna ya shiga xaban wasu magani har kala uku, snn ya dawo yana kallonta rike da maganin yace "amma xan maki allura a nn," kai kawae ta gyada masa tana kallonsa ya hada alluran ya juyo yana kallonta tace "ni ba kai xaka min ba ka ba nurse su min," yana kallonta yace "ok ni xan rufa maki asiri, ke kuma ki tona min nawa ko," da sauri tace "A'a wllh," ta bude cinyarta yyi mata snn ya dauko magungunan ya bata ya gwada mata yanda xata sha, tayi ta masa gdya har da kuka, nn dae yyi mata nasiha ssae akan matsalar da ta tsinci kanta a ciki, ya nuna mata ita ce me babban laifi, ita dae hawaye kawae take har yyi

Chapter 22 of 32