Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
dauke kanta da sauri tayi hanyar stairs yana yatsina fuska yace "wa yace kiyi girki da kifi a gidan nn, kinga ina son jin warin kifi?" tayi masa wani mugun kallo ta haura sama ta bar sa nn tsaye, ko da ta koma ta tarar inna na shafa'i da wutr, ta shiga bayi ta wanke baki snn ta fito ta xauna gaban madubi tayi shafe shafenta ta saka kayan barcinta ta kwanta don tayi isha, inna na idarwa tace "to ynxu dae tunda dare yyi, sae mu bari gobe da sassafe mu bar gidan nn, shi kuma wnn yaro dama baya dawowa gida ne naji shiru har ynxu, ko dama ke daya ke rayuwa cikin gidan," Inteesar bata tanka ta ba tana ta game da wayar Aliyu, inna ta tabe baki tace "to Allah shi kyauta, ynxu dae kije ki hado min tea don idan ban sha ba bana jin ddi" Inteesar tace "kai inna duk tuwon da kika ci," inna tace "naga dae ba ke ke siyowa ba jikana ke siyowa," inteesar ta harareta ta mike tayi hanyar fita xata je hado mata tean, tana bude kofar ta kusan cin karo da Aliyu dake labe jikin kofar, shi ma xuwansa knn, suka xaro ido a tare xata fasa ihu don ba karamin tsorata tayi ba kuma bata yi xaton ganinsa gurin ba yyi saurin fixgota ya rufe kofar . . Inteesar ta turasa xata koma cikin dakin ya rikota da sauri ya toshe bakinta ya ja ta suka shiga bedroom dinsa ya tura kofan ya jingina jikin kofar yana mata wani irin kallo, tace "meye hka ni ka bude min kofa na fita," yace "hakkina nake so ki bani yau," ta xaro ido gabanta na faduwa tace "meye hakkinka kuma," yace "bari na nuna maki, yyi kanta ta koma baya da sauri tana cewa "wllh xan maka ihu idan baka bude min kofa ba," a tsorace tayi maganar ya galla mata harara yace "kiyi mana," ta girgixa masa kai kamr xata yi kuka tace "don Allah kayi hkuri tea fa xanje na hada ma inna,"yyi murmushi yana kare mata kallo, rigar bacci ne sky blue mara nauyi iya gwiwa a jikinta mai hannun singlet, ta saka gashinta cikin net, ya lumshe ido yace "bani hakkina tukun sae kije ki hada mata kitchen din gaba daya ma," xata yi magana ya daga ta sama kamr wata yar bby sae kan gado, ba karamin tsorata tayi ba cikin muryar kuka tace "ya Aliyu don Allah ka bari ni ban san me kke nufi ba," ya cire jallabiyar jikinsa yana kallonta ya ajiye yace "xan gwada maki abinda nake nufi," xata sauko daga kan gadon ya danneta tace "wayyo na shiga uku," kissin dinta ya shiga yi yana rungume da ita, duk ta gigice ta shiga turasa amma yaki sakinta ya shiga romance dinta, kuka ssae ta shiga yi ganin abun nasa ba na wasa bne, suka ji inna ta bude kofar dakin Inteesar din ta fito tana cewa "yau naga rayuwa daga xuwa a hado min tea shiru har ynxu," inna ta rike haba tace "lau ko dae shafe shafen nn da naga tana yi daxu gun mijinta xata" sae kuma ta fita ta samu mai gadi tana kallonsa tace "kai mara mutunci mai gidan ya dawo ne," da kmr baxae kulata ba sae kuma yace "ehh" tace "amma yarinyar nn anyi yar bnxa gun mijinta ta tafi ta barni," ta koma ciki ta hada tean da kanta ta koma daki tace "ikon Allah, amma wnn anyi munafuka" Inteesar na jindawowanta cikin kuka tace "kayi ma Allah ka kyaleni na kai mata abinda ta aikeni," Aliyu bae ma san tana yi ba lkci daya yanayinsa ya canxa ya xaman mata kmr wani xautattce, duk ita ma ya bi ya kashe mata jiki ganin ya soma rabata da kayanta yasa ta kankamesa jikinta na rawa tace "don Allah ka bari ya Aliyu ka tausaya min wllh tsoro nake ji," ya girgixa kai da kyar yace "plss fateema ni ma ki tausaya min," cikin kuka tace "wllh baxan iya ba," murya can kasa yace "don Allah fa nace maki," ta shiga turasa jikinta na rawa tana kuka tace "wayyoo tsoro nake ji don Allah kajitausayina wllh bna so," ya fada gefentayana mayar da numfashi, ganin tana nemansauka daga kan gadon yasa ya fixgota ya rungumeta, cikin shessheka tace "don Allah kaji tausayina ka bari," da kyar yace "bbuabinda xan maki," duk da hkn bata kwantar da hankalinta ba sae kuka take, shi dae yana rungume da ita idonsa a lumshe, hkn yasa tayi shiru sae ajiyar xuciyar da take,suna nn a hka har bacci ya dauketa, ya kwantar da ita ya lulluba mata bargo ya koma dayan side din jikinsa a mace ya kwanta, hka ya kwanta ranan a wahale da ciwon ciki, ita ko tana ta bacci abunta, cancikin dare ganin bacci ya gagaresa yasa ya mike ya koma falo ya sami lime ya sha ya kwanta, da asuba ruwan sanyi gora guda ya tashe sa . Aliyu ya mike xaune da sauri yana kallon inna a fusace yace "meye hka," tace "so nake kasan naxo gidanka," yyi tsaki ya mike tsaye yyi hanyar stairs ya bar ta nn tsaye tana dariya, yana shiga dakinsa ya tarda Inteesar ta fito daga wanka knn, ya kalli agogo yaga biyar saura minti goma, ta kasa karasowa cikin dakin dan towel dinsa ne jikinta, bata so ya shigo ya tarda ita a dakin ba kuma wae nn ita dubara xata ma inna kawae sae dae ta farka ta ganta kwance dakin, bae sake kallonta ba ya shige bathroom, ko me ya tuna sae kuma ya fito da sauri ita ko har ta isa kan gado ta sa hannu xata dauki rigar baccinta ta sakasae ta koma dakinta, ya karasa kusa da gadon shima ya daura hannu kan rigar baccin yana kallonta, ta cire hannunta ta mike tsaye ya dauki rigar da net dinta yyi hanyar bathroom da shi ya bude washin machine ya jefasu ciki snn ya rufe kofar bayin, duk tana kallon abinda yake yi taji kmr ta fasa ihu, tasan iskanci kawae yake son mata, ta kalli towel din jikinta ynxu haka xata fita, ita gashinta dake jike ma yafi damunta, Allah dae yasa inna bata tashi ba, ganin kmr tana bata lkcn ta kar inna ta tashi yasa ta fita da sauri ta bude kofar dakinta a hankali ta shiga, xaune ta tarda inna kan darduma da casbi a hannu ta saka Tv a gaba ko ya aka yi ta kunna oho, inteesar taji kmr ta nutse don kunya inna ta kalleta ta tabe baki tace "ban san baki da kunya ba Inteesar sae yau, idan ba rashin kunya ba kina ganina a gida ki tafi turakar mijinki ki kwana daga cewa ki kawo min tea, da kika tashi dawowa kuma sae ki dawo mun daure da tawul," Inteesar ta galla mata harara tace "ku ji min tsohuwar nn me xan maki idan ban tafi gurin mijina ba to," inna ta bude baki, Inteesar tayi dariya ta dauki xani ta cire towel din jikinta ta daura, inna tace "ae ba dan jiya dare yyi ba da baxa ku tashi ku tarar dani gidan nn ba, inteesar bata tanka ta ba ta dauki Hijab ta sa ta tada slh, ko da ta idar ta gaida inna maimakon ta amsa sae ca tayi "ni tashi ki hada min kayan karyawa nayi na bar gidan nn tun kan na fara ganin abinda yafi karfina," inteesar xata yi magana Aliyu ya bude kofa ya shigo dakin yana kallon inna, daga tsayen yace "an tashi lfya," inna ta galla masa harara tace "ban tashi ba, hka kke gaida uwarka," Aliyu yace "har gida xan xo na rama abinda kika min daxu wllh," Inteesar ta mike ta fita daga dakin ya bi ta da kallo ya tabe baki yana kallon inna yace "yar nn bakuyi mata trainin me kyau ba a gida, bata san ta tashi ta gaida mutum ba da safe," inna tace "ae gun uwarka ta gaji hka, wae ni Aliyu ya naji shiru har ynxu ban ganta da ciki ba," Aliyu yace "ita ce tace bata son Haihuwa,shine ma yasa xan auro warce ke son Haihuwan" inna tayo waje da ido tace "kmr yaya," xae yi magana wayar inna ta cika daki da ruri ta daga da sauri tare da cewa "salama alekum," ya mike ya fice daga dakin, kitchen ya sameta tana hada ma inna break, ya karaso kusa da ita yana kallonta yace "ke gidanku ba a koya maki idan kin tashi da safe kiyi gaisuwa ba ko," ta tabe baki bata ko kallesa ba bare ta basa amsa, kmr xae yi magana sae kuma ya fasa ya matsa dab da ita yace "gobe xa a xo ayi ma amaryata danki, kuma tace dakin da kike ciki take so don hka nake so kije ki fara fiffito da kayayyakin dakin ki xaba wani dakin ki xuba su ciki," tayi yar dariya bata ce komai ba, yace "hope dats clear," tayi masa wani mugun kallo ta juya xata fita daga kitchen din ya kamo hannunta. Inna na xaune a daki tana kallo bayan ta ci tayi kat, inteesar kuwa na wanke Bathroom Aliyu ya shigo yana kallon inna yace "inna xo mu je indan xaga dake gari mana tunda ina gida yau," inna na kallonsa da mamaki don daxun nn suka gama fada tace "kai da gske? Amma fa ba tukin nan taka ta ganganci xaka yi dani ba fa," yace "wllh a nutse xan tuka ki," ta mike da sauri tana gyara daurin dankwalinta tace "to ita Inteesar ita kadae xa mu bari gida, wae ma to wa xae je ya kwaso min kayana ne," yace "ehh xan kira Zainab ta kwaso maki, inna tace "Inteesar ke baxa ki je bane, Aliyu yace "ki dae gaya mata me xata girka maki kafin mu dawo," inna tace "to kiyi min tuwan semo da miyar kubewa," inteesar ta fito tana kallonsu, ko kallonta inna bata yi ba tace "sae mun dawo," ta fice Aliyu ya juya ya galla mata harara snn ya fice shima, mai gadi na bude masu gate tace "yauwa Aliyu wnn ba mutumin arxiki bne jiya kokuwa ya dinga yi dani ka koresa," yace "to inna," suna ta tafiya suna hira inna sae kyalkyale dariya take duk da Aliyu bae ga abun dariya ba don hiran ma ba ganewa yake ba, tafiyar kusan minti talatin suka yi snn yyi parkin yana kallon inna yace "to fito in siya maki nama," inna ta fito da sauri tace "yauwa dan albarka" tana kare ma inda suke kallo bakinta a wangale, can sae fara'ar dake fuskarta ya bace tace "nn ae anguwansu farida ne Aliyu," yace "yauwa ashe kin gane, kuma nasan xaki iya gane gida daga nn kina shan kwana xa ki ga gate, in kin koma sae kice da Haisam ya siya maki naman don ban fito da kudi ba" yana kai wa nn ya shige motarsa yyi gaba inna ta fasa ihu tana salati, mutanen dake gun suka taho da sauri suna tambayar lfya. Inteesar na kwance da daddare ya shigo gidan ita dae tasan bbu maganar dawowan inna gidan, tana ji ya bude dakinsa ya shiga, ta mike xaune ta rafka tagumi tana naxarin abinda yace mata daxu da safe ita har lkcn ta kasa gaskata wae Aliyu aure xae yi nn da kwana hudu, tunanin hkn yasa hawaye ya cika idonta, tana nn xaune har kusan karfe daya ganin bacci ya kaurace mata yasa ta mike a sanyaye ta shiga bathroom ta dauro alwala ta fito ta fara sllhn dare. Da safe tana gaban madubi tana gyara fuskarta ya shigo dakin, 1st tym in history Aliyu ya shigo mata daki da sallama ta amsa ba tare da ta kallesa ba yana kallonta bbu yabo bbu fallasa yace "kina jina, ki kama kanki safeenah xa su xo gidan nn anjima don nasan baki da kunya, infact bance ki fita ba ma," tace "akan me baxan fita ba? Wllh bbu abinda xae hanani fita," yace "shknn, ni kuma xan ce mata duk abinda kika yi mata tayi min maganinki" ya juya ya fice daga dakin bayan kmr minti goma ya dawo yana kallonta yace "kinga dakina yyi kama da dakin kaya, c'mon kin wuce kin dauke min kayanki da kika ajiye min a ciki ko sae na bata maki rae," xata ce wani kaya sae ta tuna kayan baccinta dake dakinsa ta mike fuskarta daure ta fita tayi hanyar dakin ya bita a baya tana shiga dakinsa ya jawo kofan yasa key, ta juya da sauri tana kallon kofar ta shiga bugawa tana cewa "meye hka," yace "hka xaki tsaya har sae na dawo," ya rufe nata dakin ma da key snn ya fice ya bar gidan, kuka ta fashe da ta durkushe tana kare ma dakin kallo, sae a snn ta lura da kayan tea da cakes din da ya ajiye mata kan fridge sae plantain chips, karfe sha biyu taji ana shigowa gidan da motoci ta mike da sauri don bayan ta gama cin kukanta ta gaji kwanciya tayi, ta karasa jikin window taga manyan motoci shake da kaya har kusan guda uku, wasu lafiyayyun motoci suka shigo gidan, manyan mata kusan su goma suka fito suna daddaga hanci, sae ga wata motar ma ta shigo safeena da kawayenta suka fito daga cikin motar tana gwada masu ta inda xa su bi su shiga gidan, tuni aka fara sassauke lafiyayyun funitures din da aka shigo da, Inteesar ta sake labulan a sanyaye ta koma kan gado tayi kwanciyarta tare da lumshe idonta da taji na neman kawo kwalla, duk suka cika gidan da hayaniya wasu na sakin magana, ana ta shigo da kaya. Ko minti sha biyar ba ayi da shigowarsu ba Anty Nafeesa da Zainab suka shigo gidan, suna shiga falo duk aka juya ana kallonsu, batare da Anty Nafeesa ta kallesu ba tace Sannunku fa, Zainab kuwa dama ko kallonsu bata yi ba, Safeena dake kwance kan kujera da kawayenta suna ta hira da shewa ta bi su da wani irin kallon raini hka ma iyayen nata, cikin daga murya Anty Nafeesa tace "to ina uwar gida sarautan mata kuma ran gida take ne," Zainab tace "ina xata iya da wnn hayaniyar Anty, kila tana can cikin daki," . Safeenah da 'yan uwanta suka bi su da kallo har suka haura sama Anty Nafeesah na cewa "gskya kam ina xata iya da wnn hayaniyar," wayar Zainab yyi ring ta duba ta ga ya Aliyu, tace "ashe dae ya Aliyu na da nmbrna," ta daga yace "ki fito waje ki karbar maku makulli," tace "na me," yace "ban sani ba snn ya katse kiran" ta kalli Anty Nafeesa dake buga kofar inteesar tana kiranta tace "wae yaya naje na karba makulli a waje," Anty Nafeesa tace "na me, ko tare suka fita da Inteesar din ne," Zainab tace "kila, ina xuwa na karbo keyn," ta fice da sauri, yana cikin mota yana jiranta ta karasa ya mika mata keyn dakinsa da na Inteesar, tace "to ina inteesar din," yace "in kun bude xa ku gani," ya ja motarsa yyi gaba, ta tabe baki ta koma cikin gidan, dakin Inteesar suka fara budewa bbu kowa ciki, snn suka bude nasa, tana xaune ta hade kai da gwiwa, suka karaso cikin dakin Anty Nafeesah tace "amma Aliyu dan rainin wayo ne kulle ki yyi a daki don ya isa," Zainab ta dago kanta tana kallonta, kuka take, Anty Nafeesa ta galla mata harara tace "ban san shashanci kukan lfya" ita dae bata ce komai ba ta gaida Anty Nafeesa, Zainab tace "meye na kuka Inteesar" Anty Nafeesah tace maxa tashi kije ki gyara fuskarki kiyi kwalliya kar na bata maki rae ke dae baki gajiya da wnn shegen kukan naki komai kuka komai kuka, ita dai bata ce komai ba suka bar dakin Aliyu Zainab ta kulle suka koma nata dakin, sae da ta sake wanka snn Anty Nafeesa ta sa ta gaba ta tsantsara kwalliyanta snn ta fito mata da wata shaddarta dogon riga maroon colour ta saka Nafeesa tayi mata dauri mai kyau, Zainab tace"waw yan matan yayanmu kin ga yanda kika xama kmr wata balarabiya," inteesar ta galla mata hara, ba karamin kyau tayi ba duk da ta rame ssae, Anty Nafeesa tace "to akwae abinci ne a gidan? Don ni yunwa nake ji," Inteesar tace "sae da na girka maku," Anty Nafeesah tace "to da dae yafi," ta ce "toAnty suna falo kuma," Anty nafeesa tace "to ina ruwanki da su ae don su ganki da kyau nake son kije kiyi mana girkin," ta mike ta dauko mata takalmikalan shaddar ta ajiye mata snn ta feshe ta da turare tace "maxa sa ki tafi indomie kawae xaki girka mana," Zainab tayi dariya tana kallon Anty Nafeesa, Inteesar kam murmushi tayi ta sa takalmin gabanta na faduwa ta fita xuwa kitchen, duk suna xaune falon har da safeena kusan su goma banda wa inda ke ta jere a daki, Inteesar bata ko kalle inda suke ba a nutse cikin takunta mai jan hankali ta nufi kitchen ta bude kofar kitchen din tana yatsine fuska don duk sun dauki cups sun sha lemo da shi, ta dan tabe baki ta shiga kitchen din, duk kawayen safeena suka juya suna kallon safeena da yanayinta ya sauya lkci daya xuwa bacin rai tana kallon kofar kitchen din, inteesar ta kunna gas ta daura ruwa snn ta fito falon ta shiga kwala ma Zainab kira cikin wani irin tsiga, da sauri Zainab ta sauko tana cewa "na'am yan matan yayanmu wnn kira hka," inteesar ta galla mata harara da wasa tace "ban fa son iskanci indomie nawa kike ga xae isheku," Zainab tace " wani irin tonan asiri ne wnn, ko ma dae duka nace ae gidan yayana ne nn bbu uban da ya isa ya hana," Inteesar tayi dariya ssae tace "ikon Allah to shigo ki girka maku kinsan dae ni ba daga nn ba ban gaji rowa ba kuma duk yanda nace hka xa ayi a gidan nn bare kice kina tsoran wataran ki xo...," a fusace safeena ta mike tana nuna Inteesar da yatsa tace "ke ki kama kanki kar ki kaini bango don dukan tsiya xan maki wllh wllh kuma sae dae mijikinki ya gode min idan ya dawo," Zainab ta yo waje da ido tace "wa xa a duka ni Zainb" Inteesar tayi dariya tace"tambayan min ita don ni kaina ban gane inda ta dosa ba," Safeena ta ciro wayarta da sauri ta shiga kiran Aliyu, "Aliyu Aliyu ka ja ma ballagaxar da ka ajiye a gida kunni wllh ta fita harkata idan ba hka bakafin na bar gidan nn yau sae na yi mata kaca kaca, kuma wnn shegiyar kanwartaka ita ma kaja mata kunne," Zainab tace "wllh ni ba shegiya bace sae dae kece shegiya," Inteesar ta ja ta suka shiga kitchen suna dariya, safeena tayi shiru tana sauraran abinda Aliyu ke ce mata tana bubbuga kafa, sun gama dafa indomien knn xasu wuce samaAliyu ya shigo gidan, ba karamin tsorata inteesar tayi ba tayi hanyar stairs ba tare da ta kallesa ba, Zainab tace "ke kar ki bada kanki mana ki tsaya ae Anty nafeesa na nn," Aliyu na kallonta yace "ke xo nn," ta galla masa harara tace "nayi maka me," karasowa kusa da ita yyi ta dake xuciyarta na bugawa, duk yan falon suka xuba masu na mujiya, ita kanta Zainab karfin hali tayi ta tsaya, Safeena kosae taunar cingam take tana jujjuya ido xuciyarta fal murna ita nn kawayenta suka yanda ta isa da Aliyu, yana isa kusa da inteesar ya kama hannunta ta fixge tace "da'alla malam kyaleni," ya tsaya kallonta da mamaki bae ce komai ba,ya juya yana kallon Zainab yace "je dauko mata mayafinta ko ki bata naki," Zanab ta cire mayafinta ta mika ma Inteesar taki karba, shi ya karba snn ya sureta kmr wata bby suka fita daga gida . Inteesar ta tsorata ssae murya can kasa tace "don Allah kayi hakuri ka saukeni wllh ita ce ta fara,"Safeena kam binsu tayi da kallo da mugun mamaki don tsabar mamaki kasa rufe bakinta dake bude tayi, ita nn jira take taga ya rufe ta da duka, Zainab kuwa dariya tayi tace "kai irin wnn soyayya hka, ko me Inteesar ke ma yayana hka oho," ta haura sama tana ci gaba da dariya, bayan mota ya jefata snn ya xaga ya shiga motar ya ja ta, ita ko kallonsa kawae take gabanta na faduwa ko ina xae kai ta, sun yitafiya ssae snn taga yyi horn aka bude gate ya shiga yyi parkin, ya bude mata kofa yace "fito kar na mareki," ta fito tana kare ma wajen kalloduk da tasan inda ya kawota don ta taba xuwa, lallai ma Aliyu asibiti ya kawota, yyi gaba tana biye da shi a baya kmr xata yi kuka, nurses duksuka kama kansu ganinsa, suka bi inteesar da kallo suna masu sannu da xuwa, bae ko kallesuba sae ita ce ta gaishesu ganin yanda suke kallonta, can last flour office dinsa yake kusa dana aminin dad dinsa don shine mai asibitin wato dad din Sadeeq, ya bude office dinsa ya shiga, ganin taki shigowa yasa ya fixgota, ta shiga karema office din nasa kallo, ba karamin haduwa yyi ba kmr ba office ba ita fa bata taba gskata Aliyuna aiki ba duk da tasan da sassafe yake barin gida ya dawo late, ya shiga dakin da ke cikin office din ita dae tana nn tsaye har ya fito bayan kmr minti goma sanye da kayan surgery, green colour yana kkrin sa hand gloves alamar theatre xae shiga, ya galla mata harara yace "kada Allah yasa ki xauna kuma idan lkcn sllh yyi kar kiyi," snn ya fice, tayi tsaki kmr xata yi kuka ta xauna kan kujera tana kare ma office din kallo, ko minti goma ba ayi ba da fitarsa wata nurse ta shigo rike da abinci a rufe da lemo ta ajiye mata tace "sannu madam," snn ta fita. Hka inteesar ta yi ta xama kamar gantalalliya a office kmr tayi kuka, abincin da aka kawo mata ma kin ci tayi, ta gaji da xama ta kwanta kan gadon da ake duba pregnant women tayi kwanciyarta sae bacci, ko da ta farka taga biyar ya kusa ita da ta kwanta tun kusan daya da rabi, bata damu ba don dama bata sllh, ta bude abinci daxu ta yatsine fuska ta rufe, aka bude kofa wasu nurse biyu suka shigo da jarirae har biyu suka yi ma inteesar sannu, snn suka daura su kan gadon yara dake office din daya ta kunna wani wuta mai haske dae dae fuskarsu snn suka fita, inteesar ta wara ido tana kallon yaran kyawawa dasu, ta karasa kusa dasu da mamaki tana kallonsu tace "yan biyu," a hankali dayan ya shiga kuka yana tsotsan hannunsa dayan ma ya karbe taji kmr ta daukesu don tana bala'in son yara, ta rasa yanda xata yi dukta rude ganinsu tayi can tayi nn, aka bude kofar dakin Aliyu ya shigo ta juya da sauri tace "ya Aliyu yan biyu ne?" ya cire abun bakinsa yace "ehh" ba tare da tasani ba tace "waw a ina kukasamo su" ya karaso kusa da gadon yana kallonsu yace "daxun aka cirosu daga cikin mamansu, bata farfado ba har ynxu ma" inteesar ta juya da sauri tana kallonsa kmr xata yi kuka tace "theatre aka mata," xae yi magana daya yaron ya tsala ihu tace "wayyo ya Aliyu in daukeshi," ya harareta yace "basu da lafiyasuma," tayi shiru tana kallonsu kmr xata yi kuka.Ya dauki dayan a hankali ya mika mata yana kallonta. . A hankali Inteesar ta sa hannu ta karbi bbyn da yake mika mata tana murmushi, tace "ya Aliyu ni ina son twins ssae" yana kallonta yace "kina sonki haifi twins knn," da sauri tana kallonsa tace "eh mana ina so," ganin irin kallon da yake mata yana murmushi yasa taji kunya ta kauda kanta da sauri, wae Aliyu take ma wnn maganar? Ita bata ma sani ba, ya matso dab da ita ya tsaya har tana iya jiyo numfashinsa a bayanta ya rike kugunta yace "wnn waist din naki xae iya daukar twins?," ta bar wajen da sauri nn da nn ta tsorata xae yi magana ta riga sa da sauri tace "Yaya yunwa fa suke ji ko," bae ce komai ba sae kallonta da yake, ta daga bbyn xata yi kiss dinsa ya dakatar da ita da sauri, snn ya karbe shi ya kwantar gefen dan uwansa, tace "yaya baxa a basu abinci ba," yace "sae xuwa karfe sha biyu na dare," ta wara ido tace "sbda me yunwa fa suke ji," yace "eh xa ayi ta basu ruwa" kmr xata yi kuka tace "to waye xae dinga basu kace mamarsu bata farfado ba," ya daka mata tsawa "ke da'alla kar ki dame ni" yyi tsaki ya shiga daki, ta bisa da kallo snn ta tabe baki ta koma kujera ta xauna, wata nurse ta shigo rike da mug a rufe tana kallon Inteesar tace "doctor fa? Ya shigo?" a dari dari take tambayar, Inteesar ta gyada mata kai, nurse din ta ci gaba da tsayuwa har ya fito sanye da kananan kaya, yana kallonta yace "wathappen" tace "coffee sir," ya daka mata tsawa "to kaina xaki daura ko me," ta karasa kusa da table ta ajiye ta fita sum sum. Ya bude abincin da aka kawo ma inteesar yana kallonta yace "meyasa baki ci ba," tayi kamr bata ji sa ba, ya rufe ya koma kan table dinsa ya xauna kan kujera ya bude coffeen ya shiga sha, hka yaran suka dinga kuka Inteesar taji kmr ita ma tayi kukan, ta kasa jure kukan nasu tace "yaya kuka fa suke," ya kalleta yace "cnt yhu see they re under medication," bata sake cewa komai ba bayan kmr minti sha biyar ya kira nurses su kashe wutan su fita da su, inteesar ta bi su da kallo kmr xata bi su suna fita ta bata rae ta juya tana kallon Aliyu taga kallonta yake yana murmushi, ta dauke kanta da sauri, karfe takwas da rabi suka bar asibitin bayan ya kaita ta kara ganin yan biyun da mamarsu, ya biya ta eatry ya siya masu abinci snn suka kama hanyar gida, gidan ba kowa duk sun watse sae kamshin turaren wuta ke tashi, ta haura sama ta bar sa nn falo shima ya bi ta a baya, spare key Aliyu ya dauko ya bata na dakinta don su Anty Nafeesa sun tafi da shi, dakin safeena ma a kulle yake ta tabe baki, ta bude kofar dakinta, ba shiri ta koma baya da sauri tana kallon dakin da mamaki kadda cikin dakinta aka yi ma safeena jere, ta juya tana kallon Aliyu da ya fito daga dakinsa yana kallota yace "Abba ne ya ba kansa wahala ya bata kudinsa shi me 'ya," ya sauka kasa ya barta nn, sababbin funitures masu rae da lfya wanda suka fi na da ne a dakin nata, ashe su Anty Nafisa abinda suka xo yi knn, ta karasa cikin dakin a sanyaye, bbu abinda ba a canxa ba a dakin. Tanaxaune gefen gadonta bayan ta fito daga wanka ta sa kayan bacci tayi jigum ta ma rasa abinda

Chapter 17 of 32