Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
mai raba mu dashi sae Allah ko Bukar?" Abba dae bai ce komai ba ya budekofar falon suka shiga, intisaar dama tuni tayi hanyar bedroom tun kan su shigo, inna ta kwado mata kira ta fito da sauri tace "abba sannu da xuwa," inna tace"Aliyu ya yo nan hka?" intisaar ta girgixa kaida sauri tace "aa ban gansa ba," inna kamrtayi kuka ta dage ita fa Aliyu na cikin gidannn bai fita ba, Abba ya sake dialin nmbrsa xae kira, intisaar dama na ganin yana danna waya tasan kiransa xae yi, duk ta rikice ta fara kame- kame"aa,.. Ab.. Abba aibai taho nan ba, emm kila de yana falon Hajiya ne, amma baya nn wajajen," kmr ance ta juya taga wayoyinsa har uku kan kujerar da ya xauna, ta xaro ido a tsorace ga abba ya dage sai neman kiran wayar tasa yake, cikin dubara tayi ta wajen kujerar da wayoyin nasa suke ta xare dankwalin kanta ta jefa kan wayoyin, sae kuma ta xube kan kujerar da karfi, gaba daya suka juya suna kallonta har suna hada baki "lafiya, me ya faru?" ta dafe kanta murya can kasa tace " kai na ke mani ciwo, jiri nake gani," Abba yace"subhanallahi, tun yaushe," ta sake marairaicewa tace "tun daxu," inna tace"bari ina da maganin ibba ki sha nasan shi ne," Abba ya bata dubu biyuta siyo magungunan da take sha ya juya ya fice, inna ta bi sa a baya tana cewa "wae to yanxu ina Aliyu ya shiga jama'ah, Allah yasa dae ba tserewa yyi ba," suna fita tayi ajiyar xuciya ta mike tsaye ta dauki dan kwalinta ta daura tayi hanyar kofar da saurixata rufe, ta kusan cin karo da momy, ta xaro ido cikin tashin hankali tace "mo momy kin dawo," Kallon mamaki Aliyu ya tsaya yi ma Haisam, "ka mareni?" Haisam ya matso gabansa yana kallonsa da kyauyace "an mareka din," inna tuni ta ja intisaar suka shige daki da sauri suna rusan kuka, cikin sanyin murya Aliyu yace masa "xaka gane kuranka," snn ya fice daga falon, hajiya da umma na labe bakin kofa tun bayan ihun inna na farko da ya fargar dasu suna lekan duk abinda ke faruwa, Haisam na fitowa umma ta bi sa da masifa kmr ta rufe sa da duka, "wawa kawae ko ina ruwanka oho," ko kallonta baiyi ba yyi gaba abinsa. Karfe shidda na yamma abba ya dawo gida bayan inna tasa su fadila su kira mata shi ya maxa ya dawo gida ynxun nn, abba ya dafe kansa bayan yagama sauraren surutan inna, gashi sai wani irin ihu take masu a falon , dama da belt din ta shigo falon dan abba ya gani da kyau, "kalle jikina" ta fadi tana nuna ma abba hannayenta da kafafuwanta, sai kuma ta sake fashewa da kuka har da kwantawa inda take tana cewa "wllh yau idan baka dau mataki kan wnn shegen hatsabibin yaro naka ba bar min gidan nn xakuyi daga kai har shi ba mae kwana gidan nn" su xainab sae boye fuska suke suna dariya, intisaar kanta ma dariyar take yi, su hajiya sai faman tabe baki suke suna hararta, momy kam kallon tv kawae take yi a falon, Haisam kuwa na gefen abbansa a xaune, Abba ya jinjina kai cike da takaici ya sake kiran Aliyun da ya kira yafisau goma sae dae yace masa yana xuwa, har ya gama ringin dis tym around ma bai daga ba, abba ya sauke ajiyar xuciya yana kallon innar da ta hade rai, ita kawae jira take taga hukuncin da xai dauka kan dan nasa, ya dubi haisam yace "je ka kace masa ko na xo na samesa ne," haisam ya mike knn xae fita sae ga Aliyun ya shigo da sllmarsa wanda idan ba kunne kasa ba ma baxa ka ji ba, ya nemi gefen khadija ya xauna, yana kallon abbansa fuska a daureyace "gani nn abba," inna tace "to uban waye bai ganka ba, mugu kawae munafuki algungumi, shaidanin mutum kawae, ma dae kam Allah ya isa bamu yafe mka ba" sae kuma ta fashe da kuka ta kwanta kan intisaar tana rerawa, har Haisam sae da ya dan dara a falon, su fadila ma sae yi suke yi, intisaar kadae ce ta hade rai kanta sunkuye, Aliyu yyi ma innar wani irin kallon bnxa ya tabe baki ya maida hnklinsa wajen TV, Abba yyi nisa yana kallonsa rai a bace yace "me intisaar tayi mka ka doketa da belt daxu?" inna ta mike da sauri tana xaro ido tace "kaji wani shirme irin na Bukar, intisaar kadae? Ae ca xakayi me intisaar da inna suka yi maka xaka xanesu da belet daxu, kai jama'ah ni saenaga ma kamr tsoron dan iskan dan nan naka kke yi wllh, idan ba hka ba kai ba ka tashi ka rama min Bukar, dukanmufa ya dinga yi yana kwallo damu kamr wasu 'yan cikinsa, yana xaginmu wae yau sae ya hallaka mu, da kyar Haisam ya kwacemu a hannunsa, duba jikina duk shatan belet ne, hka ma na yarinyar nn" ta gama magana tana huci, abba yyi murmushi yana gyada kai yace, "to miko min belt din baaba," ta mika masa da sauri har tana tuntube, ya mike tsaye ya mika mata belt din kuma yace "gashi nn baaba ki rama bugun da yyi maki, snn ki mika ma fateemah ma ta rama wanda yyi mata," abba ya koma ya xauna, inna tuni hakoranta suko yo waje, intisaar ta rike hannunta murya can kasa tace "inna kawae ki kyalesa don Allah, ki daina biye masa, kawae mu barsa da....." inna ta tureta da sauri rai bace tace " kaji min muguwar yarinya, a kan wani daliin xan kyalesa don uwarki, amma yarinyar nn muguwa ce wllh, ke idan baxa ki iya dukansa ba ma ni xan taya ki wllh" ta mike tsaye tayi wajen Aliyun tana huci, kowa sae hadiya dariyarsa yake a falon yana kallon inna, ita kuwa tsakani daAllah take abunta. "Bukar kace masa ya cire wnn katuwar rigar jikin tasa" abba yace "aa baaba ki rama a hka, shirt ce ai " inna tace "tam," Nan fa inna ta dage da dukka karfinta ta dinga xuba masa belt din tana huci, "mugu... mugu... Axalumi axalumi, mugu axalumi," abunda ta dinga fadi knn tana lafta masa belt din, dariya kam har da na hauka a wajensu fadila da xainab, abba kam murmushi kawae yake, haisam ma kansa dariya yake, hajiya kuwa mikewa tayi ta fice daga falon fuu, umma ma ta bita a baya. Aliyu kam ko gezau, sae dae tuni kamaninsa suka canxa idon nan yayi jajur kamr gauta, sae huci yake yana kallon innar, sae da inna ta gaji snn ta juyo tana huci ta mikawa intisaar belt din "tashi ki rama ke ma," intisaar da tuni ta marairaice fuska tace "ni dae na yafe masa," inna ta xuba mata belt din a kafa tace "to don uwarki ni xan rama maki," ta koma taci gaba da xuba masa belt din tana xaginsa, ta gaji don kanta ta ajiye belt din tana huci kmr warce tayi tseran gudu, Aliyu ya mike yana kallon dukkansu dake falon a xaune ya juya xae fice abban ya daka masa tsawa yace"kuma na bka sati uku ka miko min sadakin 'ya ta." . . Intisaar ta dago kai tana kallonsa ya gallamata harara yace "ba dae ice-cream xaki sha ba,ki shanye su tas ki bani rubbers din ynxun nn," tamarairaice fuska kmr xatayi kuka tace "Allahyaya karya take min ni ban ce...." ya batarankwashi mai xafi cikin tsawa yace "i did nt ask4 ur opinion, i only ask yhu to finish ol nd giveme d bowls," ta jawo roban ice-cream din a hnklita bude ta dauki spoon ta fara sha, ya mike yakoma kujera ya xauna yana kallonta, xainab tunita labe bakin kofa tana lekosu, inna da kursumdae sae kallon intisaar suke tana ta tura ice-cream, ita ga ta ba gwanar son ice- cream ba dontana shan rabi yake gundurarta, ta dago kai dakyar xuciyarta na tashi tace "wllh yaya na koshi,"ya galla mata wani mugun harara yace "xan kofasa maki kai idan baki shanyesu dukka ba," tunihawaye ya cika idonta tana kallon ice- cream din,inna ta fashe da dariya tace "oho dae can tamatse maku, ni ai ba ruwana da lamarinku, kujekuna kunyata ni gaban Bukar," kursum ma dariyatake hka ma xainab shi ko ya hade rai yanakallonta, yunkurin amae ta fara yyi saurinmikewa ya janye ice-creams din a gabanta, ya sakafa yyi ball da ita "don uwarki ciki xakiyi amanda" ta girgixa kai a tsorace tana kallon inna, yadauki rabin da ta rage ya kifa mata a ka, duksuka sauka jikinta, tasa kara don axabar sanyi ,shi ko ya kwashi sauran xae fita inna ta mike dasauri ta jawo robar furar da ke gabanta, yanaganin hka ya fice da sauri ta ko bishi da guduhar tana neman faduwa har waje ta bisa dashi takwara masa amma tuni ya bar wajen don bai mataba shi ba, "gantalallen bnxa kawae mugu," tafadi tana huci ta dawo da robar furarta, kwancetaga xainab da kursum suna dariya kmr wasumahaukata, har ita kanta intisaar din ma dariyartake, xainab tace "ko ba komai dae kinsha ice-cream yarinya, ina ma ni na sami hka," inna nashigowa ta hade rai tana kallonsu tace "kai dukku tashi ku bar mun falona wahalallun bnxakawai tababbun hofi," kursum ta mike tana dariyatace "ni ba sae kin xageni ba ma hajiya inna saeda safe" ta fice, intisaar ta mike da sauri ice-cream na xuba jikinta tayi bathroom din inna donma kar ta koreta don bata san inda xata ba. . ... Tura sa ta shiga yi a tsorace tana nemankwacewa daga rikon da yyi mata amma ta kasa,Aliyu kam bai ma san tana yi ba don idonsa yarufe yyi nisa a abinda yake yi, ganin Aliyu dagaske yake don har ya fara canxa salon abindayake yasa ta shiga dukansa a kirji tana kkrinkwace kanta da duk karfinta "don Allah ka rufamin asiri ya Aliyu kar ka min hka ina rokankaplss" a rude take masa magiyar tana kuka gninabinda yake shirin yi, bata xata ba kawae taji yawanke ta da mari ya shaketa yana numfashi dasauri da sauri, tuni yanayinsa suka canxa,hawaye kawae take hannnunta a baki tanagirgixa masa kai, sun kai minti biyar a tsaye ahkn, har lkcin bae cire hannunsa daga wuyartaba, amma numfashinsa ya dawo nml, ita daesunan Allah kawae take ambato a xuciyarta tanaduk adduar da ya xo bakinta ga wani mugunbugu da xuciyarta ke yi, fixgota yyi ya budebayan motar ya jefata ciki, ya shiga driver sit yaja motar suka bar wajen, wnn karon duk iriingudun da ya dinga yi bata sake gigin cewa komaiba, sae adduar da ta dinga yi kala-kala axuciyarta gabanta naci gaba da buga wa, dae-dae wani katon gida taga yyi park, tsoranta yalinku a kan nada ta toshe bakinta gudun kar tafasa ihu don hkn ba karamin aikinta bne, hawayesosai take yi tana kallon Aliyun, ya bude motarya fita ya kulle, ta bisa da kallon tsoro ganinyanda idonsa ya kada yyi jajur don duk wajenakwae wuta, taga yyi hanyar gate din yana wayaduk da ba jin abinda yake cewa take ba "nashigauku ni fateemah," abinda ta fadi knn a fili tanakuka, taga ko minti biyar ba a yi ba aka budegate din ya shiga. Kuka ta fashe da sosae tanarokan Allah ya kareta daga sharrin Aliyu, a hkabacci yyi gaba da ita cikin motar duk da ba nakwanciyar hankali bne. Karfe biyu saura Aliyu yafito daga gidan, ya bude motar ya shiga, kallodaya yyi mata ya dauke kansa, ya tada motar yashiga driving a hankali, ita ko har lkcn baccitake. Anty nafisa dae kasa daurewa tayi ta kiraxainab don ta san tana da hankali, ringin hudu tadaga cikin muryar bacci tace "Anty Nafisa," antynafisa tace "xainab kiyi hkuri nasan kinyi bacci,kina ina ne," cike da mamaki xainab tace "inafalon inna a kwance, me ya faru anty?" antynafisa tace "intisaar fa?" xainab tace "intisaarkuma, ae ca nake tana gidanki" "nashiga uku niNafisa, xainab don Allah bata dawo ba," tatambayeta a tsorace, xainab ta rude ta mikexaune tace "ta dawo ina?" anty nafisa tace"xainab tun wajen sha biyu saura na hadata daAliyu su taho....." xainab tace "innalillahi antymeyasa baki bar ta ta kwana wajenki ba, kinkirata yanxu?" nafisa a rikice tace "ina fa xainabduk wayoyinsu a kashe yake," xainab ta girgixakai tace "anty wllh ya Aliyu mugu ne, ynxu inaxae kai 'yar mutane cikin daren nn" anty nafisatace "innalillahi wa inna ilaihi raji un, ni kam nagata kaina, ki rufa min asiri xainab kar ki sanar dainna" sae kuma ta kashe wayar, baccin da xainabbata sake komawa ba knn, ita ma duk hankalintaya tashi ta shiga kiran nmbr intisaar din da Aliyuduk switch off, tasan yayanta bai da imani kokadan, to ynxu meye abun yi. To fa, ko ina ogaAliyu xae kara lulawa da matarsa oho.... Tam mudae 'yan look ne. .....A hankali Aliyu yyi parkin dae-dae bakin gate, ya juya for d first tym tunda ya fara drivin yana kallonta, har ynxu bacci take, ya kalle wrist watch dinsa ya ga karfe uku da minti biyar, ya shiga tunanin yanda xae yi, Haisam ya fado masa, sae kuma yyi saurin kauda tunanin, a dalilin tunawa da yyi ae har yau ba sa shiri, ya dae gama tunane tunanen mafita daga karshe ya yanke conclusion kawae ya kira Haisam, ringin biyu ya daga, Aliyu yace "xo ka bude min gate," snn ya katse kiran, bayan kmr minti biyar Haisam ya bude gate din, yyi drivin motar cikin compound din yyi park, ya fito ya kulle motar, haisam yace "daga ina hka" ko kallonsa bae yi ba yace "inda ka aikeni," Haisam ya ja guntun tsaki ya juya xae shiga ciki sae ga Abba ya fito, ya tsaya kallon Aliyun yace "daga ina hka Ali," ya dan shafa kanshi yace "No wani abokina ne ya kirani bai da lfya shine naje," abba yace"ok, ya hanya," yae "lfya" ba tare da ya kallesa ba ya bi bayan haisam da sauri, abba ma ya koma ciki... Haisam yace "wa yasani ma ko wajen shaye shayenka kaje," don bae ga alamar gskya a tare dashi batunda yaki tsayawa abba na masa mgna, Aliyu ya shige gabansa da sauri yana masa wani irin kallo yace "kace me?" Haisam yace abinda kaji snn ya shige bedroom ya kwanta. . Sae kusan asuba intisaar ta farka cikin motar, a hankali ta shiga bn motar da kallo da mmaki tana kokarin tuna abnda ya faru, nn da nn ta tuna, ta jawo wayrta da sauri ta kunna don ta ga karfe nawa, hudu da kusan rabi ta gani, hankalnta ya tashi, to ina Aliyu yaxo yyi parkin dinta ya wuce, ta matso kusa da glass din motar tana leken waje, mamaki ya kamata sosae ganin a cikin gida ne, nn da nn taji ta samu nutsuwa ta shiga hamdala a xuciyarta, wayarta yyi ring ta duba da sauri taga Anty ce, ta daga kan tace komai anty tace "intisaar kina ina ne," a rikice take maganar, intisaar tace "ina cikin motar ya Aliyu..." anty tace "mene? Kina me?" tace "nima ban sani ba anty," anty ta dakamata tsawa tace "don uwarki baxa ki gya min inda ya kai ki ba," ta marairaice kmr xata yi kuka tace "wllh wllh anty kawae yaje yyi parkin dina a wani gida ne, ya shiga ciki ya bar ni cikin motar ban kara ganinsa ba har nayi bacci, ynxun nn na tashi na ganni cikin motar amma a nn gida," anty tace "kin tabbata intisaar, ki gya min gskya donAllah," tace "Allah anty gskya na gya maki" anty nafisa tace "shiknn sae na shigo anjima," snn ta kashe wayar. Karfe biyar saura abba ya fito ya wuce masallaci, Haisam ma ya fito tare da Aliyu suka wuce masallacin, ta bi su da kallo, Aliyu ko kalln motar bae yi ba kmr bae san da mutum a ciki ba yyi gaba, tana nn a hka har su ka dawo daga masallaci har da abba, intisaar taji kmr ta fashe da kuka ganin inda kokallon motar Aliyu baya yi, ta bisu da kallo har suka yi bangarensu da haisam, sae kusan bakwae saura Aliyu ya fito yyi kusa da motar ya bude, abun dariya Aliyu bae bari sun hada ido da intisaar ba ya fixgotaya wurgar waje ya rufe motarsa ya wuce ciki, tayi bangarensu da sauri a tsorace, ta tarda momy na shara ta gaisheta duk da tasan batayi sllh ba don tasan momy xata yi tunanin bangaren inna ta kwana, momy ta amsa ba tare da ta kalleta ba taci gaba da abinda take yi, ta shige bedroom da sauri don ta samu tayi sllh kafin momy ta shigo. . .Karfe takwas anty Nafisa ta shigo gidan yayanta tayi bangaren su Aliyun xuciyarta na tafasa, don tun asuba take kiransa yaki daga wayar, ta kira Haisam tace ya basa yaki karba wai yana busy, direct bedroom dinsa ta shiga yana xaune yana danna laptop Haisam na rubutu a file, cikin bacin rai take magana tana kallonsa "Aliyu nagode da abunda ka min jiya ka kyauta, ni ai ban san kai mahaukaci bne mara tunani sae jiya, wllh kaci sa'ar abu daya yau da sae ka sha mamaki," ita daya ke ta kumfar bakinta, don Aliyu ko dago kai bai yi ba idonsa na kan abinda yake yi a laptop, hkn ya dada tunxurata ta fixge laptop din a fusace ta jefar kan gado tana cewa "don uwarka ba magana nake maka ba xaka maida ni mahaukaciya," ya mike a fusace yana kallonta yace "wllh kika bata min laptop sae kin siya min sabo," anty nafisa ta cakumosa rai bace " iyye! ni ka ke gya ma hka don uwrka, ai Aliyu da mari na kawae kayi ka nuna min kai tatattcan dan iska ne," haisam dae na xaune yana kallonsu bai ce komai ba, nananty nafisa ta dinga masa tijara tana xaxxaga masa rashin mutunci kala kala kmr xata maresa, shi dai ido kawai ya xuba mata yana kallonta sae dae ya tabe baki, sae da ta yi mai isarta bayan tayi ma haisam bayanin abinda ya faru ta fice tana cewa "jahilin bnxa kawae, a hkn xa a dauketa ma a baka idan ba jaraba irin na yaya ba, don inna tuni ta gama sarewa da kai," tana fita Aliyu ya mike ya ja dogon tsaki yce "kawae taxo da sassafe ta cika ma mutane kunne kmr wata sabuwar kamu," Haisam ya girgixa kai yace "kadae bi duniya a hankaliAliyu, indae mutum yyi da kyau...." Aliyu ya shakesa idon nn nasa ya kada yyi jajur yace "kace me dn babanka?" haisam yyi murmushi yanakallonsa kawae bae ce komai ba, hkn yasa ya turasa da karfi yace"don uwarka da ca nayi mka da gudu na bi duniyar," haisam dae bai ce komai ba ya fice ya bar masa dakin, ganin ransa ya bace sosae, don ahka suka taso in dae ran daya ya bace cikinsu daya na kkrin ganin ya fita harkar daya no matter abinda xae masa. Ganin inna da gaske take yasa Anty Nafisa ta fita ta kira abba ta sanar dashi abinda ke faruwa, abba ya rasa ma me xae ce mata don takaici, shi dae har ga Allah uwar nn tasa tana basa matsala tare da daga masa hankali a gidansa, yace ma Nafisar xae kirata snn ya kashe wayar, yana kashewa kuwa kiran inna ya shigo bai daga ba ya kashe wayar ma gaba daya.Ya kira Aliyu ta wayan Alhaji mukhtar yace masa yaje gida yanxun nn ya duba Fateemah bata da lfya, Aliyu ya danyi jim, har sae da Abba yace "kana jina," yace "eh ynxu xan tafi gidan," snn ya kashe wayar. Abba ya tura Alhaji mukhtar yaje gurin inna, bayan yyi masa bayanin da Nafisa tayi masa, Alhaji mukhtar yyi dariya yace "tsufa ne ba wani abu ba ke damun inna," ko rufe baki bai yi ba sae ga kiran innar ya shigo wayarsa, abba yace ya daga, yana daga wa kuwa muryarta kmr speaker cikin tsawa take mgnr "Mukhtar Mukhtar, ina Bukar, kace masa wllh tun kan nasa a kawoni inda yake yaxo ya raba wnn gantalallen auren da ya hada, don wllh baxaku kashe min jika a bnxa ba,kuma bbu shegen da ya isa yyi mata dole " alhaji Muktar ya dinga bata hkuri ya samu ya lallabata yace "gashi nn xuwa," yana kashe wayar yace ma Abba suje can gida abba yace aa shi dae yaje, a hka suka rabu Alhaji mukhtar ya kama hanyar gidan shi daya. Aliyu yyi parkin motarsa a kofar gida amma ya kasa shiga gidan sbda jama'ar da suka cika gidan ta ko ina, ya ciro wayarsa ya kira haisam yarakasa su shiga gidan tare Haisam yace masa yana ciki shimabae dde da shiga ba Anty Nafisa ce ta kirasa, da kyar ya fito daga motar ya shiga gidan yyi bangaren inna ba tare da ya kalli kowa ba duk da tsokanarsa da aka dinga yi, bbu kowa falon inna duk ta koresu ta kunna TV tana kallo fuskar nn tata a tsuke, da yake sun san halin innar kuma da sha'anin tsufa bbu wanda ya kawo komae a ransa sae dariya ma da suka dinga yi suka bar mata falonta, basu san inna da gske take ba, bakin kofa Aliyu yaci karo da Haisam ya fito daga falon ransa abace, Aliyu ya tambayesa me ya faru, yyi tsaki yace ka shiga ka gani, snn yyi gaba, . ya shiga falon yana kare ma ko ina kallo, inna na ganinsa ta dada tsuke fuska tana xare masa ido tace"inji dae da takardar jikata ka shigo" yyi mata wani irin kallo na rashin fahimta, da kmr xae yi magana sae kuma ya fasa yyi hanyar bedroom dinta, ta bi sa da gudu ta shige gabansa tana huci tace "wllh wllh ka ba jikata takardarta kar na tara maka jama'ar kano yau gaba daya,Abin ma dariya ya ba Aliyu, ya tsaya kallon innar yana gyada kai, yace "kan wani dalili xan bata takardar," inna ta gyara tsayuwa tace "sbda saura kiris ta amaye hanjin cikinta yau" dariya Aliyu ya dinga yi har da buga kafa yana kallon innar, inna ta bude baki tana binsa da kallo daga sama xuwa kasa a fusace tace, "ka maida uwarka Aisha mahaukaciya ba ni ba," nan da nn ya hade rai yace"kika ce me?" tace "abinda kunnenka ya jiye mka," bae sake ce mata komae ba ya bi ta gefenta xae shiga dakin ta tare hanyar da sauri tana huci, "nace takardarta kawae xaka bata," wani irin tsawa da ya raxanata ya daka mata, "da'alla ki fice ki ban waje hajiya, naki bada takardar," inna ta fasa ihu mai kara tana kiran jama'ah su xo su taimaketa duniya taxo karshe Aliyu ya bangajeta gefe, abun dariya abun takaici, Anty nafisa dama tuni ta yafa gyalentata bar gidan, momy kuwa can uwar dakanta ta shige, su hajiya da umma kmr suce wayyo Allah don ddi, ga gida cike dam da mutane . Hka inna ta dinga gabxawa da Aliyu kan sae ya ba intisaar takardarta kuma taki barinsa ya fita, dariya kam wasu har da hawaye, intisaar dae duk wnn abun da ake bata sani ba, bacci mai nauyi yyi gaba da ita. Aliyu kam ya kasa ce da inna komai sbda mutanen da ke wajen sae binta yake da ido tana ta xuba masa rashin mutunci, can dae ganin abun nata gaba yake ba baya ba yace "ke wllh baki da maraba da tsofaffin yarbawan lagos, dama can cikinsu kika je kika xauna da yafi maki alkhairi, haba mutum bashi da aiki sae masifa da fadan rashin gskya, wnn wllh duk halin tsofaffin yarbawa ne," nn fa Aliyuya sama ma kansa lfya, don xube wa inna tayi gun ta dinga rusa ihu wae jikanta ya hadata da kafurai yace mata tsohuwar bayerabiya, hehehe gidan Bukar dae ya tashi daga gidan biki ya koma gidan comedy, hmm bari kawae mu tsallake nn wajajen sisters. Karfe takwas aka gama walimar da Anty Nafisa da kawayenta suka shirya don kmr yanda Aliyu yace baya son ko wani irin party, Abba bae bari anyi komai ba duk da Anty Nafisa ta so ko dinner ne ayi, ynxu kam intisaar ta daina kukan da take yi sae dae ta xama kmr wata gunki ga muguwar ramar da tayi duk tayi wani irin sanyi tun bayan nasihar da Alhaji mukhtar yyi mata daxu da wani abokin abba, karfe tara aka fara shirye shiryenwucewa da amarya don abba yace ranar xa a kaita, inna ta shigo dakin rike da kofi tana wangale baki tace "maxa ki shanye wnn jikalleta, shine na karshe," sae ka rantse kace ba innar daxu bace.Anty Nafisa ta dago intisaar tana kallonta tana murmushi bayan matar da ta kawo musamman dongyaranta ta gama tsantsara mata kwalliya na fitan hankali bayan ta gama mata gyaran karshe, lace ne mai laushi da shegen kyau, shi ba milk colour ba, kuma ba light brown ba, da ratsin orange colour a jiki sae daukar ido yake, fuskar nn tata tasha cool make up, ga design din lallenta da yyi ma fara fatar ta kyau sae sheki yake, Anty nafisa ta dago fuskartatana kallon idonta, ta girgixa mata kai hade da bata rai ganin hawaye makale a idonta suna neman xubowa, ta dauki hankerchief ta goge mata hawayen, snn ta dauki babban mayafinta fari ta yafa mata a ka, . ta dauko mata takalminta shi ma farin ta saka, snn ta ja ta tayi bangaren Abba da ita yan rakiyarsu na biye dasu a baya, Nasihar karshe abba xae mata, fuskarta a rufe yake Anty Nafisa tayimata jagora har cikin falon Abba, ta xaunar da ita har lkcn fuskarta a rufe yake tana hawaye duk da Nafisa bata san kuka ma take ba, kamshin turaren Aliyu ta dinga ji a gefenta hkn yasa gabanta ya shiga faduwa, ta juya da kyar ta kalli gefenta taga Aliyu xaune shima kansa a kasa, yana sanye da shadda ruwan kasa yyi masa kyau sosai, cikin dubara ta dan matsa ganin kusa kusa suke,"fateemah" taji abba ya kirata cikin nutsuwa, ta amsa da dashashiyar murya tace "Na'am Abba," abba yyi murmushi yace "kin san abinda nake so dake," ta girgixa kanta ba tare da ta dago ba, nn daeabba ya dinga mata nasiha tun tana daure wa har ta kasa ta fashe da kuka sosai, hkn yasa Abba ya kyaleta ya juyo kan Aliyu, shi ma dae har Abba ya gama bae dago kai ba, sae maganar abba ta karshegareshi ne yasa sa dago kai yana kallon abban,"kuma Ali idan ka cutar min da fateemah bana tunanin xan iya yafe mka," Aliyu yyi wani kasaitattcen murmushi tare da maida kansa kasa, Abba ya sa masu albarka snn yace su tashi suje Allah ya basu xaman lfya, intisaar na gaba yana binta a baya mutanen da suka rakota falon suka rufa masu baya, anty nafisa kuwa ta tsaya don tana son magana da yayan nata kafin ta fita, sae ga inna ta shigo tana murmushi tace "Bukar Bukar, wae da ca nayi don Allah ko xan iya binsu na koma can da xama, don gskya gidan nn naka duk ya fitar min a rae barin da xasu barni ni kadae, dama ga matanka ba gani na da gashi suke ba gaba dayansu, can ko kaga muna tare gaba daya snn suna gani na da mutunci, idan ya so duk bayan wata biyu sae na dinga kawo maka xiyara nn ko

Chapter 11 of 32