Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
wani gun da dakin ki amma ba nn ba, don dis is myn, kuma kika sake ce min jahila wllh sae na kusan illataki kmr yanda mijinki ya gaya maki daxu, don wnn karan ba sae ya dukan min ke ba, ni da kaina xan nakade ki, ki san cewa ni ba sa'ar uwarki bace bare......" bata rufe baki ba Inteesar ta sauke mata tagwayen mari masu rae da lfya nn da nn fuskarta ya koma ja don axaba, ta dafe kuncinta a gigice tana kallon Aliyu da ya jingina jikin bango rungume da hannayensa yana kallon Inteesar da mamaki tace "wat? She slapped me Hydar" Inteesar tace "ae kadan ma kika gani," bata jira me Aliyu xae ce ba tayi kanta, inteesar na ganin hka ta fasa ihu a tsorace tayi hanyar bathroom, safeenah ta fixgota ta buga ta da bango ta shaketa tana huci snn ta shiga dukanta kmr an aikota Aliyu yyi kansu da sauri ya fixge safeenar ya watsa mata mari ya buga ta da bango yana huci yace "don ubanki kasheta xakiyi ne," Safeena tayo waje da ido tana kallonsa da mamaki, Inteesar ta sulale kasa gabanta na faduwa tana kallonsu, Safeenah ta girgixa kai ta fashe da kuka tana kallon Aliyun, ya saketa ya dafa bango tare da sauke ajiyar xuciya, can ya dawo gabanta a hankali yace "meyasa xaki kulata Safeenah baki ga yarinya bace warce bata san ciwan kanta ba, bbu abinda ta sani nn da kike ganinta she's just a kid," Inteesar ta mike tsaye tace "ku dae ne baku san ciwon kanku ba amma ni nasan ciwon kai na," Aliyu ya bude baki da mamaki yana kallonta, tayi hanyar bathroom da sauri xata shige ya bita ya fixgota a fusace, ta fasa masa ihu tare da durkushewa a kasa tace "wayyoo Abbana," ya durkushe shima da sauri gabanta yana kallonta yace "me ya faru?" ta dago tana kallonsa kmr xata yi kuka tace "to ba kai bne xa ka doke ni . Aliyu yyi kwafa ya mike tsaye, ita ko ta ja da baya daga xaunen da take tana goge hawayenta, ya juya yana kallon Safeena dake hawayen takaici xae yi magana ta juya da sauri ta bar dakin yaji ta bude kofar dakinsa ya gane jakarta xata dauka a ciki ta bar gidan, ya juyo yana kallon Inteesar da ta bi ta da harara, ya sa kafa ya haureta yace "xan babbalaki a gidan nn wllh idan kika yi wasa," ta mike tsaye da sauri tayi tsaki can ciki ta koma kan gado ta xauna tana ci gaba da share hawayen fuskarta, danna bell din gidan da aka yi yasa ya juya ya fita daga dakin dae dae lkcn da Safeena ma ta fito daga dakinsa rike da handbag dinta, yace "haba bby ina kuma xaki?," ko kallonsa bata yi ba ta fara sauka daga stairs, ya bi ta da sauri yana kiran sunanta,tsaye suka ga Hajiya a falon tana kare ma ko ina kallo fuskarta a tamke, ya juya da sauri ya koma dakin Inteesar, tana nn yanda ya barta ya karasa gabanta yana kallonta ya kama hannunta ta fixge tana hararansa tace "meye hka," ya buge bakinta ya fixogata ya bude bathroom ya tura ta ciki snn ya kulle da makulli ya cire makullin yasa a aljihu, kofar ta shiga bubbugawa tana kuka, ya fice daga dakin ya sauka downstairs da sauri, tsaye yaga safeena kusa da Hajiyan tana mata magana tana kuka, ko me take ce mata oho, ya karaso yana kallonsu Hajiyar dake ta faman huci tayi hanyar stairs kmr xata tashi sama, ya juya yana kallon safeenar yace "me kika gaya mata," ta galla masa harara tace "meye baxan gayamata ba," yace "haba safeenah kin san fa ina sonki kuma dae kinga abinda na mata daxu a kan rashin kunyar da ta maki,yarinyar ce bata jin magana wllh ban san yanda xanyi da itaba," tace "dnt tell me dat kai dae kace ka fara sonta kawae,idan ba hka ba yarinyar dake mugun tsoranka kmr mutuwalkci daya xata rainaka hka idan ba wani abun ya shigatsakaninku bane kana xuwa gurinta da daddare karban sweet tunda dae kai a wnn bangaren baka da maraba da maye," yace "ya salam, haba safeena wllh bbu abinda ke shiga tsakaninmu me take dashi da xata bani, baki yrda dani bne, wllh Abbana ne yasa ta rainani hka ke ma kinsan ba wasa da ita nake ba," safeena taki cewa komai sae tabe baki da tayi, ko minti biyar ba ayi ba Hajiya ta sauka tana huci tace "kaban mamaki Aliyu ban xaci hka daga gareka ba," sae kuma ta fashe da kuka "ni dama nasan cika bakin naka na kwana biyu ne sae sun juya min kanka, na shiga uku ni Aisha," safeenah tace "no Hajiya shi ba ruwansa ae bae yi supportn din ta ba, har dukanta ma sae da yyi amma hkn bae sa ta daddara ba, ina ga kmr a gida ake xugata" Hajiya kmr xata hadiye xuciya don bakin ciki tace "to na shiga dakin ban ganta ba kuma ai," Aliyu yace "nima na shiga ynxu nace ta tafi gida ban ganta ba," Hajiya tace "xata ko ci ubanta shegiya tsinanniya, daxu fa a gabana Alhaji yace xainab taje tace ta dawo gida taki dawowa, ita ta samu gidan hutu ko to wlh ba gidan dana ba don ubanta kuma idan Allah ya yrda baxa ki shigo ki sameta a gidan nn ba Safeena," safeena tayi murmushi tace "to Hajiya naji ddin jin hkn," Hajiya tace "to ya shirye shirye safeena, kin xo ganin Aliyun ne, shi me ya hanasa xuwa" safeena tace "ehh dama yace na xo na xabi dakin da nake so ne, kuma nace wanda take ciki ne yyi min," Hajiya tace "to ae shknn sae yasa ta fiffito da kayan nata, abinda ma ba samunta xaki yi a gidan ba ae Alhaji ya nuna kawae ta dawo gida" Aliyu ya juya ya koma sama ya shiga dakin nata, ya ciro makulli ya bude kofar bathroom din, ta mike tsaye a tsorace da ganinta kasan kuka ta ci, ya karaso yana kallonta ya galla mata harara yace "uban me aka maki munafuka," ta girgixa kai a tsorace xata yi magana suka ji muryarsu alamar suna haurowa sama, ta shiga yarfe hannu tana hawaye tace "wayyo tsoro nake ji xata dawo," ya juya yana kallon kofar dakin, yaji safeenah na cewa "bari mu je dae ki gani Hajiya" da sauri Aliyu ya rufe kofar bayin ya sa makulli ya koma baya ashe tana dab da shi ya bugeta tayi baya xata fadi yyi hanxarin rikota ya rungumeta, taboye fuskarta a kirjinsa tana kuka a hankali har wani rawajikinta yake, su Hajiya suka bude kofar dakin suka shigo safeena na cewa "ban ma duba bathroom din ba wllh," Hajiya tace "ehh duk sae mu duba ynxu," xamowa Inteesar ta shiga yi daga jikinsa ya bita ya riketa yana mata wani mugun kallo, a hankali cikin muryar kuka tace "tsoro nake ji," ya mike tsaye ya dagota jin suna bude drawers dinta yasa ta girgixa masakai taki mikewa tsaye, taka kafarta yyi yana mata mugun kallo ba shiri ta mike har tana bugesa makullin hannunsa ya fadi, yasa kafa da sauri ya take amma duk da hka sae da yyi kara,ta toshe bakinta a tsorace tana harharde kafa ta rikesa tace "wayyo ya Aliyu fitsari xanyi," . Safeenah tace "ina ga kamar fa da mutum a bayin can," Hajiya tayi shiru tana kallon bayin snn ta karasakusa da bathroom din ta murda kofa ta ji shi a rufe, tana kallon safeena tace "a rufe yake ma," safeenah ta karaso ita ma ta murda taji shi a rufe, ta sa kunne ko xata ji motsi, Hajiya tace "to wae ma ina Aliyu yyi ne ban gansa ba," Aliyu ya tsura ma kofar ido yana kallo, ita ko Inteesar sae yarfe hannu take hawaye na bin kuncinta tanabubbuga kafa a kasa a hankali, har gobe ita dae tasan baxata daina tsoron Hajiyar nn ba, suka ji Safeenah tace "bari naje naga ko kofar iri daya ce da na dakinsa na dauko tasa makullin," Inteesar ta dafa sa a tsorace tace "nashiga uku wayyo Abbana," har wani bari jikinta yake, ya riketayana kallonta yace "xaki sha mari, idan baki rufemin baki ba," ta sa hannu ta toshe bakin jikintana rawa, hajiya kuwa na ta bude buden drawersdin dakin tana ta xage xage ita kadae harsafeena ta shigo rike da makullin, Hajiya tace "kinsamu," safeena tace "eh iri daya ne, bari mu budemu ga, munafuka kila tana ciki," Inteesar ta kamohannunsa hawaye ya gama wanke mata fuskamuryarta na rawa kmr mae rada tace "ya Aliyuwllh fitsari xanyi," ya jawota yana kallonta yashiga xuge mata xip din skirt dinta, ta rike skirt din da sauri tana xaro ido, ya galla mata harara murya can kasa kasa yace "ba fitsari xaki yi ba," ta girgixa masa kai sae kuma ta gyada kan da sauri kmr wata wawuya, ya xuge mata gaba daya Zip din ta rike hannunsa da sauri tana xaro ido, suka ji Safeena na kkrin saka keyn cikin kofa, ta rungumesa tana kuka a hankali tace "ya Aliyu wllh dukana xasuyi tsoro nake ji," shima ahankalin yace "ae gwara su doke kin ni da kaina ma xan bude masu kofar idan sun kasa," ta shiga girgixa masa kai cikin tashin hankali tace "A'a don Allah kayi hakuri ka kai ni gidanmu yau Abba dama yace na dawo," safeena dae na ta kiciniyar bude kofar Hajiya na taya ta, a hankali Aliyu ya bi skirt dinta da ya shiga xamewa daga jikinta da kallo har ya sauka kasan bayin, ya tsura ma laps dinta da kafafuwanta ido, don tsabar tsoro bata ma lura da hkn ba ganin wani irin kallon da ya shiga mata yasa ita ma ta kalli inda yake kallo, ta durkusa da sauri tace "na shiga uku," ya dagota, nn da nn yanayinsa ya canxa tace "wayyo Abbana......" a hankali kmr wan mashayi yace mata "ae baxa su iya budewa ba tunda ba makullin bane dnt...." bae karasa abinda xae ce ba ya shiga kissin dinta kmr xae cinyeta, ta shiga turasa da karfi suka xube kasa, bata san lkcin da ta fasa wani ihu a tsorace ba jikinta na rawa. Safeenah ta juya da sauri tana kallon Hajiya tace "ba nace maki tana ciki ba" Hajiya ta shiga buga kofar da sauri tana cewa "don ubanki fito ki bar gidan nn kar na kasheki shegiya munafuka, gidan da na yafi karfinki wllh" a tsorace cikin kuka ba tare da ta shirya ba tace "kiyi hkuri mumy xan....." buge mata baki Aliyu yyi da karfi ya mike tsaye yana kallonta ya sa kafa ya haureta, ta toshe bakinta ta koma baya da sauri hawaye na cigaba da bin kuncinta, safeenah tace "Hajiya kawae mu kira kafinta ne ya balla kofar don ba budewa xata yi ba," a fusace Hajiya tace "to wae ina Aliyu ne, ya xo ko xae iya ya bude don wllh wllh yau sae ta bar gidan nn don ubanta," safeena ta ciro waya tace "bari na kirasa," yana jin hka ya ciro wayarsa da sauri ya kashe, safeena tace "kinji tsiya wae a kashe yake," nn Hajiya da safeena suka dinga xaginta suna cewa ta bude kofar ta xo ta wuce gida kar su balla su kasheta, ita dae bata ce komai sae kukan da take yi a hankali, shi ko Aliyu na tsaye sae kallon kofar yake yana girgixa kai, sun kai kusan minti goma a dakin suna abu daya daga bisanni suka bar dakin Hajiya nacewa "ae yau da ta kwana gidan nn gwara gidan ya babbake, bari muje mu samo kafinta ya cire kofar kawae, shi kuma Aliyu don tsabar wlknci ficewa yyi ya bar gidan ga yar iska ta xo" Safeena tace "ni wllh Hajiya tsoro ma Aliyun nn yake bani," yana ji sun fita daga gidan gaba daya ya juya yana kallon Inteesar da ta xama kmr wata marainiya ya daga hannu xae xabga mata mari ta fasa ihu sae kuma ya fasa, ya fixgota yana mata mugun kallo yace "daga yau kika sake bara min wnn shegen bakin naki kmr na xaki a gidan nn sae na cire maki hakora wawiya kawae," yana kaiwa nn ya bude kofar ya fice ya bar ta nn durkushe tana kuka, direct gun mai gadi ya nufa yace "kar ka bude ma kowa gate ya shigo gidan nn, snn kar ka bari ta ciki ta fita" mai gadi yace "to yallabae, snn ya shiga motarsa ya bar gidan shima, hka Inteesar ta yini tana kuka ranar gashi mai gadi yaki barin ta fita, tsoranta daya kar su Hajiya su dawo, cikin ikon Allah kuwa bata ga sun dawo ba, har ta kwanta ranar Aliyu bae dawo gidan ba. Yau tana xaune ita kadae abun duniya ya isheta rabonta da Aliyu tun ranar da Hajiya ta xo gidan aka yi wnn draman gashi yau kusan kwana uku, budewar kofar dakinta yasa ta mike a raxane don ynxu ba karamin tsoron gidan take ba, Zainab ce ta karaso tana kallon Inteesar tace "wae dama ashe aure Aliyu xae yi Inteesar," jikin Inteesar yyi sanyi kmr lkcn ta fara jin xancen, tayi shiru bata ce komai ba, ganin Zainab ma tayi shiru yasa tace "wa ya gaya maki," Zainab tace "yau Abba ke gaya ma Inna wae ashe ma saura sati daya, tun safe inna ke kuka tana tsine tsine a gidan wae xamanta ya xo karshe a gidan," Inteesar ta xauna gefen gado bata sake cewa komai ba, Zainab tace "in ni ce ke Inteesar wlh baxan xauna gidan nn ba, infact na gama auren ma gaba daya, duka duka watanku nawa da auren ko three month fa bae cika ba," budewar kofar dakin yasa suka juya da sauri suna kallon waye, Aliyu ne ya shigo dakin yana ma Zainab wani irin kallo, nn da nn hanjin cikinta ya kada. . Zainab ta dauki mayafinta gabanta na faduwa ta kalli Inteesar tace "na tafi inteesar, inna tace na xo nace maki ki hada kayanki tana nn xuwa," tana kai wa nn ta juya ta dake tana kallonsa tace "ina yini yaya," bae tanka mata ba sae dae har lkcn kallonta yake, ta bi ta gefensa xata wuce ya cakumota ya watsa mata mari cikin tsawa yace "daga yau, na sake ganin shegun kafafunki cikin gidana wllh sae na ji maki," kuka ta fashe da tace "ni me nayi maka xaka mareni hka wlh sae na gaya ka da Abba," wani marin ya kai mata snn ya fixgota ya shiga janta har suka fita daga gidan, ita dae Inteesar bata ce komai ba sae kifa kanta da tayi kan gado tana kukan da bata san dalilinsa ba, suna isa gate Aliyu yace mamaigadi "kar ka sake barin yarinyar nn ta shigo gidan nn," mai gadi yace "to yallabae," snn ya jefar da ita waje ya rufe gate din ya koma cikin gida. Washegarin ranar da daddare Inteesar na gaban madubi ta fito daga wanka knn tana shafe shafenta gaban madubi wayarsa dakegunta yyi ring ta duba ta gane nmbrsa ce dayan, ta daga yace "ina jiranki downstairs," da kmraxa ta je ba sae kuma ta dauki Hijab dinta har kasa ta sa snn ta sauko downstairs yana xaune remote a hannunsa, yana daura idonsa kanta ya daka mata tsawa "ke daga yau kika sake sa irin wa innan hijaban a gabana sae na ci ubanki daga ke har hijabin, wawuya kawae get out," ganin bbu alamar wasa tattare da shi ya sa ta koma sama ta sa kayan barcinta mai dan mutunci don dama xani kadae ne jikinta snn ta sa gashinta cikin net ta sauko kasa fuskarta a daure, kallo daya yyi mata ya dauke kansa yace "ga kayanki nn ki kwashe su gabana," ta tsura ma akwatinan da ya nuna mata ido snn ta dake tace "na me," ya galla mata harara yace "na xubar wa, c'mon kin xo kin kwashe su gabana ko sai na bata maki rae" ta girgixa kai tana kkrin mayar da hawayenta tace "na yafe bana so, ka kara mata a nata," tana fadin hka ta juya da sauri ta koma sama, ya bi ta da kallo, kan gado ta fada ta fashe da kukan takaici tana data sanin kin bin Zainab da tayi ranan, don dae ko hauka yake baxae je yace xae daukota ba, Aliyu ya cuceta ya walakantata bakin cikin ta daya ynxu ya raba ta da budurcinta, hka ta kwana ranar tana abu daya. Washegari da safe ya shigo dakin yana kallonta bbu yabo bbu fallasa yace "ki shirya anjima xa a raka ki registration na Jamb," yana kai wa nn ya juya xae fita ta mike da sauri tace "bbu inda xa ni wllh," ya juya yana mata wani mugun kallo yace "to sae me, me xa a fasa mutuwan ko hisabi, kar Allah yasa kije din jaka kawae" ta fashe da kuka tace "ni a jaka bace wllh, ka jira jaka na nn shigowa nnba da ddewa ba," ya karaso cikin dakin ya kwashe ta da mari ta fasa ihu tana kiran Abbatace "Allah ya isana ban yafe maka ba wlh mugu kawae," juyawa yyi ya fice daga dakin da sauri ta mike jikinta na rawa ta shige bathroom ta rufe da key. Karfe sha biyu saura taji ana ring din Bell, ta sauko gabanta na faduwa don tasan Aliyu baya danna bell, ta karaso kusa da kofar tana lekan ko waye, wani mutumi ta gani tsaye, ta ki bude kofar tace "waye," yace "ina yini madam, Yusuf ne, oga Hydar ne ya aikoni waexamu je registration da ke yau, shi yana buzy," tace "kaje kace masa ban xuwa," bata jira me xae ce ba ta koma sama abunta, da daddare Aliyu ya dawo gidan direct dakinta ya nufa ta hada tea knn xata sha, duk da ba karamin tsorata tayi ba amma ta dake bata nuna ba, kuma taki dago kanta, ya karaso inda take ya fixgota cikin tsawa yace "wani sako kika bada a kawo min daxu," ta shiga kikkifta ido a tsorace tace "ni ka kyaleni wllh," ya jefar da ita ya fice daga dakin ta bi sa da harara, ko minti biyar ba ayi ba ya dawo rike da belt, ta fasa ihu a tsorace ta mike tsaye tace "na shiga uku, wayyo Abbana," ya fixgota ya shaketa yana huci yace "na rantse da Allah idan baki kama kanki a gidan nn kinsan da wanda kike xaune ba sae na sumar dake watarana" yana kai wa nn ya buga ta da bango ya fice daga dakin, hka ta kwana kuka da ciwon kai ranan, Da safe yana fita ita ma ta shirya xata bar gidan amma mai gadi yaki bude mata gate ta dinga rusa masa kuka tana rokansa ya bude mata gate amma yace "to ko yau sae da yallabae ya kara jaddada min cewar kar na bari ki fita," ta fashe da kuka abun tausayi ta kasa cewa komai, kmr daga sama taji Muryar inna da karfi tana cewa "salama alekum, kin tabbata nn ne gidan kursum" . Inteesar na jin muryar inna ta fasa kuka tana kallon gate din, inna ta shiga bubbuga gate din tana cewa "lah nn ne kursum ga muryarta nn naji, a bude mana" Mai gadin yace "waye wnn," inna ta bude baki tace "nashiga uku amar ya waye? Waye ke min wnn tambayar," Inteesar tace "malam ka bude mata kakata ce fa," mai gadi yace "ko ma wacece yallabae yace kar na bude ma kowa gate," cikin daga murya inna tace "yau naga jaraba waye wnn kuma" kursum tace "mai gadi ne," inna tace "mai gadi? To ya ci ubansa ba a gaya masa ko ni wacece bane ni da gidan jikokina xae hana ni shiga," kursum ta fashe da dariya inna tace "ke ban san shashanci fa," sae kuma ta shiga kiran Inteesar," cikin kuka inteesar tace "Na'am inna yaki bude gate din," a fusace inna tace "yau ni naga jarababben dan iska gate din ta ubanka ce ko ko, kaji min mutum," dariya ma abun yaba mai gadin inna tace "shi Aliyun yana ina," Inteesar tace "oho nima ban sani ba," inna ta shiga buga gatedin da karfi tana duddura ma mai gadi xagi,shi dae yana xaune sae shan rakensa yake inteesar tace "wae kai wani irin mutum ne baka jin ka bude mata gate ne ka maida mutane mahaukata," inna tace "ki rabu da shege, kursum maxa kira min Bukar," kursum ta karbi wayar ta kira Abba ta mika mata tace "Bukar Bukar gani gidan Aliyu wani kato yahanani shiga, na kai awa biyu tsaye cikin rana Bukar," Abba yyi murmushi yace "to ae umarnin da aka basa knn baaba ku koma gida kawae," cikin kuka inna tace "kambu, Al'quran bbu inda xani sae ya bude min gate don uwarsa," nn ta shiga jijjiga gate din kmr xata cire tana tsine ma mai gadi, maigadi yyi tsaki ya ciro dan wayansa ya kira Aliyu "oga ga wata tsohuwa nn ta xo ta cika anguwa wae sae an bude mata gate," Aliyu yyi dariya yace "karka kuskura," snn ya katse kiran mai gadi ya mike yana fito ya shige dakinsa. Inteesar taji kmr ta shakesa ta karasa kusa da gate din tace "inna Aliyun ne fa yace kar ya bude maku wlh, ku tafi gida kawae ba budewa ae yi ba," inna ta yo waje da ido tace "me? To wllh bbu inda xani ina nn har sae an bude min gate din," cikin kuka take maganar, kursum kuwa sae dariya take har da faduwa,inna ta nemi dakali ta xauna tana sharbe majina, tace "ae yau bbu abinda xae hanani shiga gidan nn wllh sae na shiga" Inteesar ta gaji da tsayuwa ta shiga, ciki lkci lkci ta kan fito ta tarar suna nn, sae tausayin innan ya cika ta taji kmr ta dinga ihu don takaici lallai Aliyu ya cika mara mutunci, duk irin yanda ta lallaba inna ta tafi kin wucewa inna tayi, har aka kira azahar inna na nn xaune kursum ta gaji ta kama hanyar gida inna ta rakata da xagi, shegiya kawae ni ba mutum bace kuma ban san ciwon jikina ba sae ke ko, ganin har kusan karfe hudu inna na nn a xaune yasa inteesar ta fito da ruwa tana kallon mai gadi tace "don Allah don annabi malam ka dan bude gate din sae ka mika mata ruwan nn wllh tsohuwace," da kamr baxae tashi ba sae kuma ya mike ya karbi ruwan da take mika masa ya dan bude gate din yana lekota yace "ga ruwa kaka," ta mike tsaye tana kallonsa da shirin masifa ko me ta tuna sae kuma tafasa, ta karaso kusa da gate din kmr xata karbi ruwan ta bangajesa da karfi ta shige gidan da gudu. Me inteesar xata yi idan ba dariya ba, ta durkushe kasa ta dinga dariya kmr cikinta xae kulle, mai gadin ya bude baki yana kallon inna dake huci tace "don buhun ubanka ni xaka hana shiga gidan jikokina, mugu katon bnxa kawae, wllh baka sameni lkcn ina Rahmatu ba da yau bbu ubanda xae hanani faffala maka mari dan iska," Inna na kai wa Aya ta yi hanyar garden kmr xata tashi sama tana huci Inteesar ta bi ta da sauri tana ci gaba da dariya tace "ba nn bane hanyar shiga inna," Mai gadin ya sauke ajiyar xuciya yana bin inna da kallo, bae taba ganin tsohuwa da karfi hka ba, har suka shiga falo Inteesar bata daina dariyar da take ba inna ta hade rae tace "ke ni fa ban san tsiya meye abun dariya a nn, wlkncin da katon can yyi min ko me" kan Inteesar tace komai inna ta rike haba baki bude tace"A'aah bene kuma cikin gida ni Rahmatu naga abinda ya ishe ni," Inteesar tace "kuma shi xaki hau muje daki ba," inna tace "ni ina xan iya," inteesar na dariya ta ja ta suka haura sama tana mitan kafafunta na ciwo, sae da inna ta fara sllh snn Inteesar ta kawo mata abincin da ta dafa kmr dae tasan inna xata shigo gidan daga karshe, inna aka xauna aka bubbude kafa tana ci tana xagin mai gadi da Aliyu, sae da inna ta gama cika cikinta snn Inteesar ta xaga da ita ko ina na gidan har dakin Aliyu sae da suka shiga, inna sae washe hakora take tace "ashe dae xan ga wnn rana da xan taho gidan jikokina ni rahmatu, ae Bukar bae yi ba, ni ban san meyasa yake min hka ba gidan jikokina ma ya hanani xuwa sae da ixininsa sae kace ubana, daba dan hka ba ae sae na dawo nn ma gaba daya gani ga ku, ni dae ynxu 'ya yana nake son gani duk da bamu san gawan fari ba, xan so naga yayanku da Aliyu," Inteesar dae bata ce komai ba a xuciyarta tace Allah shi kyauta na Haihu da Aliyu, inna ta juya tana kare mata kallo tace "wae ni ya naji shiru ne har ynxu Inteesar ga fadila can da ciki, anya kuwa bakwa shan abu yaran nn, barin ke, nafi tausaya maki don shegen yaron nn kai ki xae yi ya baro ki" Inteesar ta hade rae tayi gaba ta barta nn tsaye, inna ta bita a baya tana cewa "to ni dae banga abun bata rae ba a nn daga fadan gskya" suna komawa daki inna ta xauna ta hade rae tana kallon Inteesar tace "ki maxa ki hada kayanki tafiya na xo yi dake dama, wae ashe gantalallen yaron nn aure xae yi ban sani ba," sae kuma ta fashe da kuka tace "sakayyar da xae mana kenn, wllh sae ya baki takardar ki ba rasa masoya kika yi ba," Inteesar tayi shiru da mamaki tana kallon inna kmr ba ita ba kuma mai son ganin ya'yansu, inna ta gama ta mike ta koma kan gado tace "bari na dan runtsa kafin nn kin gama hada kayanki," Inteesar dae bata ce mata komai ba har ta fara bacci, ta kalli agogo ta ga biyar ya gota ta mike a sanyaye ta shiga kitchen tana tunanin abinda inna ta gama gaya mata ynxu, to ynxu knn hada kayan nata xatayi gaba daya su koma gida, jikinta ba kwari ta shiga girka mata tuwan shinkafa da miyar vegetable don tana da kayan girkin gaba daya a deep Freexer, sae kusan Maghrib ta gama komai snn ta koma daki tayi wanka tayi alwala ta fito ta tada inna tayi sllh, karfe bakwae da rabi ta shigo ma da inna abinci inna tace "uban wa yace kiyi girki mu da xamu bar gidan ynxu, kin gama hada kayan naki" ta hade rae tace "to inna ki ci abinci dae tukunna mana," inna ta sauko tace "Atoh don xaman ki ya xo karshe a gidan nn yyi ta xama da amaryar tasa, wae in tambayeki wnn me sa kayan 'yar bbyn mai kaman xabiyar nn ce xae auro," Inteesar ta gyada mata kai kawae, inna tayi kwafa tace "xasu ci ubansu," snn ta fara kai loman tuwo, a tare suka gama cin abincin da inna ta kwashi kwanukan ta kai kitchen ta shiga wanke wanke ta gama ta fito knn Aliyu ya shigo gidan, suna hada ido ta

Chapter 16 of 32