Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
hancinta yyi murmushi yace "tun kina karamarki kike da tsoro," snn ya juya ya fice daga bathroom din, hkn yyi mugun bata haushi, ita bata ma san lkcin da ta basa hkurin ba da bata bashi ba, ita dae ta na nn a tsaye a bathroom bata san yanda suka kaya da Hajiyasa ba, taji fitar motarsa a gidan, hajiyace har garden neman Aliyu. Tana xaune a garden abun duniya ya isheta, ita kam ta gaji da xaman kadaici a gidan Aliyu, gashi har lkcn ya kibata waya bare ta dan dinga kiran gida tana jin ddi, ga kewar momynta da inna da take yi, xainab dama tuni ta daina xuwa gidan kullum ita knn kmr mayya a gida ko nn da gate bata xuwa daga dakinta sae garden, ta kife kanta bisa gwiwowinta bata san lkcn da ta fara hawaye tana tausayin kanta, taji an sakale hannu a wuyanta, ta mike a tsorace xata fasa ihu, taga Aliyu ne, ya hade rai yace "meye hka, me kike yi a nn," ta kaudakanta ta tabe baki bata ce komai ba, rabanta da ganinsa tun lstwk sunday da hajiyarsa ta xo gashi yau har sati daya, sae dae taji ya shigo gidan da daddare da asuba yyi ficewarsa, ta riga ta gama ganesa . in har ya kulata a gidan to ganinta yyi ta basa sha'awa, sae ya nemi ya biya bukatarsa ita kuma taki basa hadin kai, don har lkcn bbu abinda ya sake shiga tskaninsu tun bayan daren ranar, ita dae tasan Aliyu ba sonta yake ba kawaesha'awace, ta mike a fusace xata bar wajen ya fixgota ta fado kansa yace "kin rainani yarinyar nn, ko gaida ni bakya yi a gidan nn fa," ta fashe da kuka, don tasan abinda ya kawo sa wajenta ynxu, don a bnxa Aliyu baya sake mata fuska duk da ya daina dukanta ko yi mata tsawa, ya dago fuskarta yana kallonta, yyi dariya yace "in kin yarda ki kwana dakina yau gobe na kai ki gida," ta dago da sauri tana kallonsa tace "gida?"yace "yea," ta daure fuska tace "kmr ya na kwana dakinka," ya daura kansa kan kirjinta yace "kmr hka," ta turasa da sauri, ya kashe mata ido yace "am serious fa" tayi shiru gabanta na faduwa ga haushinsa da ya cikata, ta dago kai tana kallonsa wani mugun tsanarsa na yawo a xuciyarta, lalle ma ya rainata, lst thing da xata so a rayuwarta knn wae Aliyu ya kusance ta, Allah ya kyauta, ganin amsar ta yake jira ne don ya tsura mata ido yasa ta dan marairaice tace "to ka bari muje gidan yau mana, idan yaso da daddare idan mun dawo sae na kwana dakinka," nn da nn ya rikice mata "ki rantse fateema," ta dan fara kame kame, can dae taga meye to, axumi ne dae guda ukukuma xata iya, ta gyara xama da kyau tace "wllh wllh," ya rungumeta ta turasa da karfi don tsanarsa kara yawa yake a xuciyarta idan yana hada jikinsa da nata, ta mike tsaye tace bari naje na shirya. snn ta shige cikin gidan ya bi ta da kallo, shikam baya son ya kara forcin dinta ya kwana da ita. Yana tsayebakin motarsa yana jiranta don tuni ya gama shirinsa, ta fito sanye da shadda brown colour am mata dinki riga da skirt ya sha aiki, tayi daurin dankwalin nata kmr headtie, tayi mugun kyau, ta rike handbag dinta brown colour, snn ta yafa mayafi light brown, flat shoe ta saka don ita bata sa heel sbda tsayinta, tun fitowarta Aliyu ke kallonta har ta karaso kusa da motar, ya tabe baki ya kauda kansa, bata burgesa ba kam, shi ma shaddar ce a jikinsa brown colour, intisaar bata ji ddin hkn ba, shima taga alamar bae ji ddi ba, ya shige motar, ita ma ta shiga gaba, snn yaja motar suka bar gidan. Karfe sha daya suka isa gida, har wani bari jikinta yake yi tun kan ya gama parkin din motar, ya fixgota ya hade rai yace "bana son hauka, don kika yi provokin dina wllh sae na juya motar nn," bbu ko alamar wasa a tare dashi, nn da nn ta kame kanta suka fito daga motar, suna fitowa kuwa ta kwasa a guje tayi cikin gidan Aliyu ya bi ta da sauri amma tuni ta shige gidan, hknyyi mugun basa haushi yyi kwafa ya bi bayanta, intisaar na shiga kan momynta ta fara daura idonta,ta fito daga bangaren inna, tayi 'yar karar farin ciki ta karasa da gudu da murnarta ta rungumeta, momy tayi mamakin ganinta sosae, ta dago kanta tana kallonta tace "meye hka fateema, daga ina hka" tayi dariya tace "daga gida mana momy" shigowar Aliyu yasa momy ta turata gefe ta fara wucewa abinta, ta juya tana kallon Aliyun har ya karaso inda take ta kauda kanta, ya riko hannunta yace "can xa mu fara xuwa," ya fadi yana nuna matabangarensu, . ita dae bata ce komai ba ya ja ta har suka isa sashinsu, yyi sallama snn suka shiga falon, ihsaan ta fito daga daki tana ganin yayarta ta rungumeta tana mata oyoyo da murnarta, ya nemi kujera ya xauna, ita ma ta xauna rungume da kanwartata tana kallonta tace "momy fa ihsaan," ihsaan tace ta kwanta a daki, ta juya ta sace kallon Aliyun, shi ma yadan kalleta snn ya jawo ihsaan yana mata wasa, intisaar ta mike jikinta a sanyaye ta shiga dakin da sallama, ta karasa kusa da momyntata dake kwance tace "momy ki fito ku gaisa da ya Aliyu," uwar ta galla mata harara tace"fice min a daki," jikinta a mace ta fito daga dakin, taxauna gefensa ta kirkiro murmushi xata yi magana ya riga ta, "momy na bacci ko," ta gyada masa kai kawae, yyi murmushi yace "to xo muje gun inna, ltr sai mu dawo," bata ce masa komai ba ya jawo hannunta yana rike da ihsaan suka bar falon, ita kam bata ji ddin abinda momy tayi ma ya Aliyu ba, suna tafe ne gabanta na faduwa kar su hajiya su gansu, don tasan su kursum duk sun tafi islamiyya sae karfe daya, ya lura da ita yyi dariya yace "ae su hajiya basa nn sun tafi biki kaduna tun friday, ammayau xasu dawo," hkn yasa ma ya sami confident din kawo ta gida, ita dae bata ce masa komai ba har suka isa sashin inna, tana gaban TV a xaune kmr xata shige ciki wae nn kallo take, intisaar ta fixge hannunta daga na Aliyu ta fada falon da gudunta, har sae da ta tsorata innar, ta fasa ihu "innata kina ina," inna ta mike da sauri tana mitsike ido, sae kuma ta fashe da kuka ta xube kasa tana cewa,"ashe dae xasu kawo min ke 'yar nn, kullum sae na xubda hawaye a kanki a gidan nn da daddare, ga Bukar gantalalle yaki barin a kai ni gidan shi da 'yar banxan yarinyar nn Nafisa, . intisaar ta kankameta tana tuntsira dariya, ita ma ta fasa dariyan suka dinga yi, ihsaan na taya su, Aliyu kam jingina yyi jikin kofa yana kallonsu yana murmushi, can inna tadago tana kallonsa tana washe baki tace, karaso mana jikalle,shigo ka xauna, ni anya ma akwae abinci a gidanka kuwa Aliyu, naga duk yarinya ta fiffige kmr kaxa," ya galla mata harara yace "to ki siya ki kai min mana," snn ya harare intisaar din yace "nn da minti talatin ki shirya xamu wuce," inna ta mike a fusace tace "ku wuce gidan ubanwa, dagaxuwan yarinya xata shirya ku wuce, ae in kaga fitarta a gidan nn sha biyun dare ne yyi wllh" ta koma ta xauna tana huci, ya girgixa kai, ya fice ya bar mata falon, nn inna ta sa ta gaba bayan ta hadata da fura mai sanyi tana mata tambayoyi, cutar ki yake yi a gidan ko, da gske ne bbu abinci a gidan nasa ko, to me kike ci ni Rahmatu, ynxu ma nasan kila Bukar ne yace ya kawo ki nn ko, to wae a ina gidan yake sun ki gaya min da na ringa xuwa kullum da kaina, intisaar ta fara tarin karya ta buge innar tace "kae inna ae gashi kinsa har ina kwarewada wa innan tambayoyin naki, inna ta koma gefe da sauri tace "yi hkuri to gama tukunna," hka intisaar suka dinga cafter da inna dake ji kmr ta maida ta ciki har su Zainab suka dawo gidan, duk suka yi murnar ganinta sosae suka sa ta gaba sae kallo suke, kursum tace kai kinga yanda kika yi wani fresh da kyau intisaar, intisaar ta galla mata harara tace "a inda bbu fresh din da kyau ba," duk suka dinga dariya, ita kanta tasan tayi kyau sosae, ramewa kadae ne tayi, inna tace "ku rabu da ita ciki ne da ita" nn da nn intisaar ta hade rai tana kallon innar, suko sae tuntsira dariya suke, inna kuwa ko a jikinta sae tauna goranta take, suna xaune a hka Aliyu ya shigo falon duk suka yi tsit bayan sun gaishesa bnda intisaar dake ta xuba abinta bata kara kallon inda yake ba, ya daka mata tsawa yace"kina jiran abba yaxo ya same ki a nn ne, kafin ki gaida shi," ta mike da sauri tace "lah na manta," ta ja gyalenta tabi ta gefensa ta fice daga falon tayi bangaren Abba, ya bi ta a baya, su xainab suka kwashe da dariya inna na taya su. . Da fara'arta ta shiga falon Abba ta rungumesa tana dariya tace"Abbana ina yini," shima yyi dariya ya amsa yana kare mata kallo snn yace "baki da lafiya ne fateema," ya juya ya hade rae yana kallon Aliyun da ya nemi kan tiles ya xauna yace "bata da lafiyane," ya fara kame kame kmr munafuki yace "Abba lafiyarta qlau ka tambayeta," abba yace wae hka fateema, Aliyu ya gyada mata kai da sauri yana kallonta, ta galla masa harara, snn ta mairaice murya tace "ni Abba makaranta nke son na koma lkci yana ta wucewa,"Haiydar Abba ya juyo yana kallon Aliyu yace, "amma lst tym da ka xo nn nai maka maganar karatunta me kace min," Aliyu aka fara kame kame da shafa kai "No Abba dama fa, dama tun lkcn nayi mata magana tace min ba ynxu ba tukun shine yasa ma ban sake mata maganar ba," Abba ya juya yana kallon intissar da ta tsaya kallon Aliyun da mamaki, yace"wae hka ne fateema" Aliyu ya shiga gyada mata kai wae tace hkne, ita kam ta rasa dalilin da yasa taga Abba da Aliyunsa kmr basa shiri kmr da, don dae tasan duk iskancin da Aliyu yake da wuya abba yace masa komai sae dae yyi ta kallonsa, yau kumataga ya hade masa rae kmr wanda yyi masa babban laifi, ta kalle Abba tace "ehh abba ya taba min mgna sau daya," Abba yace "ok, wni makarantar kike so," tace "bayero Abba," "medicine kika ce xa kiyi ko," ta gyada ma Abba kai, Aliyu yace"ke din ce xaki iya medicine? Abba baxata iya ba" abba ya galla masa harara yace "kai din da kayi kai goma gare ka?" Aliyu bae ce komai ba ya kauda kansa, Abba yace "sae kaje kayi abinda ya dace, ta fara karatu vry soon, idan nace vry soon, i mean vry soon" ba tare da ya kalle abban ba yace "to abba," intisaar ta mike tsaye tace " Abba sae anjima, ngd" abba yace "yaushe xaku koma gida," ta dan sace kallon Aliyu tace "aa abba ni kwana xanyi dama" Aliyu ya juya da sauri yana kallonta, amma bae ce komai ba, abba yace "to shiknn nima fita xanyi sae na dawo, ina da magana dake " tayi ma abba Allah ya kiyaye snn ta fice daga falon. Aliyu ya mike yyi masa sallama shima ya fice, da sauri ya bi bayanta,amma tuni har ta shige falon inna, ya shiga falon shima ransa a hade yace "wllh xuwa karfe shidda kishirya kafin na dawo," ya fice daga falon, ta tabe baki, tana kallon inna da ta bude baki tana kallon bakin kofar da ya bari, intisaar tayi dariya tace "innarufe bakin," inna tace "ae abun ne kmr wani mahaukaci," ynxu irin xaman da kuke yi knn intisaar, intisaar ta tabe baki tace "wae don nace xan kwana shine wae baxan kwana ba," inna tace"to uban me xaki masa a gidan, manta dashi kawae ai in kin koma gidan nn ke da kanki kika ce xaki koma," intisaar ta dinga dariya da jin ddin abinda inna ta ce mata, nn suka dinga hira har dae intisaar tace ma inna bari taje wajen momy, snn ta yi bangarensu. Bayan sllhn isha'i Aliyu ya shigo gidan,intisaar har ta fidda rai da ganinsa ta yi xaton ya hkura ne, ya tsaya masu kmr soja a bakin kofa wae ta tashi su tafi, intisaar ta yi kmr bata gansa ba tanata kallo abinta, kiri kiri inna tace bbu inda xae je da ita, kwana da kwanaki xata yi a gidan, sae ta gaji don kanta tace xata koma, ya hade rai yana ta kallon intisaar din dake kwance kan kujera tana taunar cingam, ko kallon inda yake ma bata yi ba, yasauke ajiyar xuciya tare da kwantar da murya ganinba ihunsa xae sa inna ta basa intisaar ba yace "don Allah inna ki bari, akwae fa inda xamu ynxu," ya kalle intisaar din yace "kiyi mata bayani mana fateema, wllh xuwa nxt wk sunday xan kawo ki kiyi sati ma idan kina so," intisaar ta tabe baki tace "ka dae je kawae nxt wk sunday din sae ka xo daukata," snn ta mike ta shige bedroom, ta barsa nn a tsaye, inna tace "to ka dae ji," snn ta kashe wutan falonta tace "Allah ya bamu alkhairi nima kwanciya xanyi, sae da safe," snn ta shige dakin ita ma ta kullo kofar.aleesat HaiydarAliyu ya kasa cewa komai sae kofar dakin da ya tsura ma ido, ya dde wajen a tsaye, can dae ya juya ya fice daga falon ya rufe kofar, inna na jin fitarsa tace "munafuki kawae, ki kwantar da hankalinki, ke da barin gidan nn sae ran da kika ce xaki tafi," intisaar ta gyara kwanciyarta don dama har tayi shirin bacci tace "kin ma san mene inna, bari na yake ni kadae fa kmr mayya a gidan, kuma bae ma san ci na da sha na a gidan ba, sae nayi sati ban gansa ba ma," inna ta bude baki tana kallonta "ke 'yar nn da gske," ta tabe baki tace "uhum ke dae barikawae, wllh kuwa inna," inna tace "to ni ae ca nke ciki ne da ke," intisaar ta galla mata harara tace " kaji ana mgnar arxiki wnn tsohuwar wae ciki, cikin lafiya, ni bnda komae" inna tace "ikon Allah, kina nufin har ynxu bbu abinda ya shiga tsakaninku intisaar" intisaar tayi mata bnxa ta juya mata baya snn ja bargo ta gyara kwanciyarta, inna xata yi magana wayarta ya shiga ruri, . ta mike da sauri ta dauko tana cewa "ina xan danna ke," intisaar tace"kai inna shekararki nawa da wnn wayar amma har yau baki san ina ake dannawa ba," inna tace "aa wani lkcn rudewa nake yi ne wllh," da kanta tayi pick din wayar dan intisaar kin mikewa tayi, ta doka uban sllma tana tambayar wanene, can kuma tace"A'a Bukar ne, lfya? Ayyo na ba fateema, to ga ta nn," inna ta mika ma intisaar wayan, intisaar gabanta yafadi ta amsa a sanyaye tace "Na'am Abba," murya can kasa tace "to Abba," snn ta kashe wayan, sae tafashe da kuka, inna ta rude "ke lfya me ya faru?" cikin kuka tace "kina ganin inna hada ni da abba yaje yyi ko," inna ta hade rae "to uban me Bukar din yace maki ynxu," ta goge hawayen idonta tace "waenaje yana nemana," inna tace "to bbu inda xaki je yi kwanciyarki, ni nn Rahmatu nace bbu inda xaki je, idan Bukar din ya isa yaxo ya tunkareni" intisaar ta mike tsaye ta dauki hijab har kasa tasa tace "ba dani ba xa ayi wnn ba inna, Abbana na kirana xanje na amsa kiransa," snn ta fice ta bar ta nn a tsaye. A hankali tayi sallama falon abba ta shiga, suka yi idohudu da Aliyu dake xaune falon a kasa gefen abba, ta nemi guri ta durkusa ta gaida abba, ya amsa yana kallonta yace "ki shirya maxa ku wuce gida fateema," a sanyaye tace "to abba" don bata iya ma abba musu, abba yace "ynxu meye naki a wajen inna, xainab taje ta dauko maki," ta girgixa kai tana kkrin maida hawayen idonta tace "bbu komai, kawae jakata ne, wani lkcn xan dauka," Abba yace"yauwa fateema, maxa tashi kuje kuyi ma momyntaku sllma, ku kama hanya ku wuce gida," ta mike tsaye ba tare da ta bari abba ya ga hawayen da take yi ba ta fice daga falon bayan tayi masa saeda safe , Aliyu ya mike shima yyi masa sae da safe, ya bi bayanta, bae ce mata ba, ita ma bata ce masa ba har suka isa sashinsu, falo suka tarda momy, ya nemi kujera ya xauna ya gaidata kmr wani munafuki, ta amsa batare da ta kallesa ba, ita dae intisaar tv kawae take kallo, suka dde a falon a xaune momy na gyara ma ihsaan gashi na xuwa sch gobe, ganin har karfe goma ya wuce Aliyu ya kasa tashi ne yasa intisaar ta mike tana kallon momyn tace "momy xamu tafi sae da safe," tace"Allah ya kaimu, . Aliyu ma ya mike tsaye yyi mata sae da safe tayi kmr bata ji sa ba, ya ajiye ma ihsaan dubu biyar ta sha ice-cream snn suka fice, ita kam bata ga laifin momy ba. Har suka isa gida bbu wanda yyi magana tsakaninsu, shi dae ne ke ta waya da safeenah suna soyewa, yana parkin ta bude motar ta fice tayi cikin gidan da sauri, ya bi bayanta tun kan ta hau sama ya risketa ya fixgota, yace "direct bedroom dina xaki shiga, ba sae kin shiga naki ba," ta turasa tana masa wani irin kallon raini, "nayi maka uban me," bata rufe baki ba ya dauketa da mari, ta fasa ihu ta durkushe wajen, ya bita da sauri, ya rikota, kuka ta shiga yi tana ihu, dukya gigice ya rungumota yace " don Allah kiyi hkuri fateema, am vry srry," ko sauraransa bata yi ba taci gaba da rusa kukanta, ya dauketa cak, ya hau sama yyi bedroom dinsa da ita, duk irin yanda yaso intisaar ta basa hadin kai kin yrda tayi, don kuka ta dinga masa sosai tana rokansa yyi hkuri bata so, hkn yasa ya kyaleta kawae yyi kwanciyarsa bayan ya lallasheta yace tayi baccinta baxae mata komai ba, ta jima bata yi bacci ba sbda tsoro, gnin kmr Aliyun yyi bacci ne yasa ta dan kwantar da hankalinta ita ma ta fara baccin, duk da kuwa idonsa biyu ba baccin yyi ba, yana ganin ta fara bacci kuwa ya mike ya bar mata dakin ya kohaleesat HaiydarDa asuba Aliyu ya shigo dakin yin alwala, tayi shame-shame hankali kwance tana bacci, kallo daya yyi mata ya dauke kansa ya shige bathroom, yana fitowa ya bude fridge ya dauko ruwan gora mai sanyi ya bude ya xuba a hannunsa ya watsa mata, ta mike xaune a firgice tana kalle kalle, ya juya ya fice daga dakin ya wuce masallaci, ta yi tsaki, a xuciyarta tace Allah ya isa na, snn ta mike tsaye ta shige bathroom tayi alwala, tana idar da sallah tayi jigum a dakin, can dae ta mike xata fita idonta ya sauka kan wayarsa da yyi haske a gaban mirror, ta dan kalli bakin kofar snn ta karasa ta dauki wayar, taga msg ne, ta bude taga na safeenahne, ta tabe baki bata damu ta karanta ba ta fita daga inbox din kawae,. ta xauna gefen gadon wayar a hannunta ta shiga hotuna, duk hotunansa da na safeena ne, wasu yana rungume da ita, wasu tana kwance jikinsa, wasu suna kiss, gasu nn dae ba kyan gani, duk da ba son Aliyu take ba sae da taji baddi, wani bakin ciki ya dinga yawo a xuciyarta, tana nn a hka har Aliyu ya shigo dakin tayi saurin boye wayar cikin hijab dinta, ya galla mata harara yace"fice min a daki kar nayi ball dake," ta mike ta fice daga dakin ba tare da ta kallesa ba wayar tasa a hannunta, yyi kwafa yace "xaki gane kuranki ne yarinya," har Aliyu ya fita ranar bata ji yyi mata maganar wayarsa ba, gabanta kuwa sae faduwa yake kar yaci ubanta. Da yamma wajen karfe biyar tana kwance a daki tana kallo, aka bude kofar dakin ta mike xaune a dan tsorace tana kallonsa, daga bakin kofar yace "ina jiranki a falo, kuma kar ki fito min da shigar nn na iskanci," ta tabe baki ta ci gaba da kallonta kawae, bayan kmr minti goma ya sake dawowa, ta mike a dan tsorace yace "kina hauka ne,me nace maki," ta hararesa tace "gani nn xuwa," yyi murmushi ya juya ya wuce, ta dauko hijab dinta har kasa tasa ta sauko falon, dama tasan bako na falon tunda har ya kira shigar ta ta iskanci, da can da take sa wa bae san na iskanci bne, ta karaso falon ta xauna tare da gaisuwa "ina yini," ya dago yana kallonta yyi murmushi yace "lfya fateema, ya gida ya amarci," komai nata ya tsaya cak ganin faruuq, ta kasa dauke idonta daga nasa, shi kansa yanayinsa ya canxa duk da yyi kkrin boyewa, yyi yake yace "kai wnn kallon kmr kin ga dodo intisaar,"ta dauke kanta da sauri ta kasa cewa komai ga hawayen da taji na neman cika idonta, Aliyu yana danna wayarsa duk da hankalinsa na kanta yace "kikawo masa ruwa mana" da kyar ta mike jikinta a sanyaye tayi hanyar kitchen ta dauko faranti da cupta daura juice da ruwa a kai ta dawo falon ta dire gabansa, yyi murmushi yace "thank yhu fateema" . tajuya xata bar falon Aliyu yace ina xaki, hira yaxo kuyi fa, kin juyowa tayi sae da ya sake kiranta snn ta dawo ta xauna tana kirkiran murmushi, Aliyu ya mike ya bar falon yana mata wani irin kallo, ko lura da hkn ma tayi, faruuq ya dago yana kallonta yace"kinyi mamakin gani na ko," bata ce komai ba yyi murmushi yace "ya amarci," nn ma shiru tayi, "yace common fateema, baki yrda da kaddara bne, ki tuna fa matar mutum kabarinsa," ta gyada masa kai kawae, yace "cheer up kanwata," tayi murmushi kawae, yace "yauwa ko kefa," nn dae intisaar ta sake suka dinga hira da faruuq din kmr ba komai, Aliyu ya sauko ya xauna falon shi dae bae sa masu baki ba sae dae yyi murmushi, intisaar tace "yayanain xubo maka abinci to?" faruuq yace "haba dae sae kace jaki daxu fa muka ci da Aliyu," ta juya tana kallon Aliyun ya harareta ya dauke kai, faruuq bae bar gidan ba sae kusan maghrib, har bakin kofa ta rakasu da yake shi da Aliyun xa su fita kuma, tace"yayana ina da magana da kai fa," ya juya yana kallonta yace "ina jin ki kanwata," ta harare Aliyu daya xuba masu ido tace "ba da kai nke ba," yyi murmushi yyi gaba, faruuq yyi dariya yace "to ina ji,"tace "yayana dama nace don Allah don annabi, tunda Allah yyi ni ba matarka bace, to ka nemi 'yar uwata mana," ya juyo da sauri yana kallonta yace"wa?" tace "zainab," ya harareta da wasa ya juya xae wuce tace "haba yayana, abinda yyi zainab shi fa yyi ni, ni da xainab daya ne" yace "haba dae, da gske?" . ta lura yana son shashantar da maganar ne, ta dinga masa magiya kmr xatayi kuka, daga karsheyyi murmushi yace "shkkn kanwata xanyi shawara,"ta ce "haba yayana kasan fa ba talarta nake mka ba,tana da manema dayawa, kawae dae xumuncin mu nake so yyi karfi kuma...." yyi dariya yace "to shknn fateema, ngd da kulawarki sae da safe," ya juya da sauri ya bar wajen, tayi dariya ta daga masa hannu ta koma cikin gida. Bayan kwana biyu da xuwan faruuq intisaar na daki a kwance tana ta game da wayar Aliyu da ta mayar nata don har lkcn bata gansa ba bare ta sa ran xae mata maganar wayar tasa, hkn yasa ko da yaushe cikin kiran inna da Zainab take su yi ta hira don akwae kudi sosai a wayar, momy dai sau daya ta kirata suka gaisa, abun da ya bata mamaki bae wuce na rashinganin kiran safeena ba don jira kawae take ta kira tayi mata rashin mutunci amma har lkcn bata kira ba kuma bata yo tex ba, sau dayawa kiran abokanansa da 'yan mata kan shigo amma ko sau daya bata taba dagawa ba, ta goge duk hotunan haukan da sukayi da safeenah dake cikin wayar, snn tayi deletin tex din safeenar da na mata da dama a wayar, karar bell taji downstairs ta mike a dan tsorace don Aliyu baya dannabell, ita tun ranar ma da ya fita raka faruuq bata sake ganinsa ba, kar dae Hajiyarsa ce ta dawo don ita tsoran matar nn take, a tsorace ta sauko kasa cikin sanda ta isa bakin kofar ta dan leka ta glass taga Anty Nafisa ce, ta bude kofar tare da doka tsalle ta rungumota tana mata oyoyo cike da farin ciki, Anty nafisa tayi dariya tace "ni kar ki karya ni," suka shigo falon intisaar na tambayarta Maryam fa, meyasa har ynxu bata xo ba, Anty nafisa tace sun fita waje da abbanta ai, intisaar tace Anty mu hau sama mana, Anty nafisar tace "ina fitsararren mijin naki," intisaar tace "uhm baya nn," snn ta mike ta kawo mata lemo a fridge ta dire mata a gabanta tana tambayr ya su shaheed da ummi, Anty Nafisa tace suna nn lfya, snn ta mike ta hau sama tana cewa "bara naje naga dakin amarya," intisaar ta bi ta a baya tana dariya, hira suka dinga yi da Anty Nafisa tana bata lbarai, duk da anty nafisar taso jin irin xaman da suke yi da Aliyun, amma intisaar ta dinga shashantar da batun, karfe sha biya tace bari taje ta daura girki tunda yini Anty Nafisar xata mata, Anty Nafisa ta mike tana inspect din dakin tace "duk da dae nasan ke ba kaxama bace intisaar bari dae na dudduba ko ina, don randa naje gidan fadila duka ne kadae ban mata ba, gskya mijinta na kkri don fadila muguwar kaxama ce ta karshe," intisaar dae tayi dariya ta sauka kasa don ita kam tun tana karamarta take da kyankyani, kuma ko a gida ma inna na yaba tsaftarta, ko shakka bbu tasan Anty nafisa baxata ga datti ko kadan a dakinta ba, dama ko ina na gidan, lafiyayyar jollof rice da plantain sai farfesun kaza ta shiga girka ma Anty nafisa, ta dan hada mata cream salad kadan, snn tayi ginger drink, gidan ya kauraye da kamshin girkinta, tana jerasu a faranti don sama xata kai mata taji an rungumota ta baya, ta tsorata sosae xata fasa ihu ya juyo ta yasaka bakinsa cikin nata, ta turasa da karfi tana maida numfashi, "meye hka," ta tambayesa tana hararan sa yace "ni kika yi ma girki?" tayi masa wani irin kallo tace "kai a su wa," ya tabe baki yace "kinga ina cin ko wani girki? Ae wnn kaxanta ce kika hada," bata kara ce

Chapter 14 of 32