cikin hade girare
"bakaso nashiga taka kashiga tawa?"
"to karka qara shiga tawa nima babu ruwana da taka"
"better" inji mussadiq yana kwama shade dinshi yafita yana dariya
kwafa Kawai Deen yayi yakoma ya kwanta jawo wayarshi don dama jira Kawai yake yafita yabashi wuri yasamu yin wayarshi hankali kwance don dama Habeeb na can part din kaka
cikin kwana biyunnan yafara samu zee na kulashi sama sama saboda nacin dayake mata
kusan kodayaushe saiya kirata ga lots of romantic SMS dake turamata akai akai
yanzu ba laifi relationship dinsu yafara farfadowa don abin ba yabo ba fallasa dukda bekai nada ba amma yana hango cewa zasu koma kamar da koma wucenan very soon
a bangaren su mussadiq kuwa tare suka fice gidan dashi da Lailah da Aysha
Lailah tayi mammakin jin zasu shopping din datayi, dafarko taso qi saida mamy ta tilasta mata sannan tashirya badon tasoba
har lokacin kwalwarta a birkice take akan magangganun mussadiq, takasa kaudasu daga kwalwarta sai sake bitarsu take tanason fahimtar every single word dayace
koda suka fito ta hangoshi a jikin motar saida gabanta yafadi don sosai yayi wani irin kyau cikin shigarshi ta larabawa sak
hakan yasata sauke kanta qasa bata qara yarda ta kalleshi ba saboda yadda zuciyarta ta chanza bugu adalilin ganinshi
back seat taso ta zauna amma Aysha tarigata hakan yasata bude front seat badon tasoba tashiga ta zauna ta maido kofar tarufe
tunda tashigo daddaden qamshin turarenshi ya ziryarci hancinta wanda ya saukar mata da nutsuwa nan take
komawa tayi jikin kujerarta ta lumshe ido ta cigaba da shaqar qamshin nashi, ahaka yaja motar suka bar gidan
babban shopping mall yakaisu, dukda yanadasu dayawa hakan besa yaje daya daga cikin nashi ba don shi dama haka yake he hates attention don yasan idan yaje cikin nashi dole a dakatar da siye da siyarwa har saiya gama yatafi hakan yasa ko shopping din takama zaiyi bayayi cikin nashi dukda da wuya ma yafita shopping komai order yake badawa akawomashi har gida
shopping sukayi sosai inda dafarko Aysha kadai keyi ganin hakan tayima Lailah dataqi daukar komai magana akan ta dauki abinda takeso mana
batajin shopping din don ita dukma atakure take saboda komawa gefen da mussadiq yayi ya rungume hannu yazubamata ido
talura mutumin nan ya iya kallo sosai babu ko irin basarwa dinnan don ko juyowa tayi takamashi yana kallonta baya janye ido
ahaka tadan tsinci abubbuwa yan kadan ganin hakan yasa mussadiq qarasowa dakanshi yafara za6armata abubbuwan dasukayi mashi
sosai mammaki ya kasheta ganin yadda yazage yana zazza6omata kaya yana lodamata a basket dinta hakan yasa tama kasa motsi a inda take
Aysha kau dama tana ganin hakan tayi saurin wucewa da nata basket din zuwa wani bangaren tana murmushi
kaya yake xa6armata masu mugun kyau kowanne hade da set din handbag da shoes dinsu har mammakin yadda,ya iya za6e take don ko ita albarka
saida yagama lodamata iya son ranshi sannan yayi gaba
binshi da kallo tayi batareda ta ko motsa ba shikau jin kamar bata biyoshi ba yasashi dakatawa ya juyo
hada ido sukayi tayi saurin janye nata
"c'mmon let's go" yafada yana kafeta da idanunshi
kasa musa mashi tayi hakan yasa tafara takowa batareda ta taho da basket din ba
ganin hakan yasashi dawowa ya jawo basket din yafara turawa sukayi bangaren turarruka
nan ma cewa yayi ta za6a saita dauki biyu batareda tama tsaya tantancesu ba tajefa cikin basket din hakan yasashi girgiza kai sannan yadawo gaba yafara za6armata yana tilamata su ciki, itadai kasa cewa komai tayi sai kallon bayanshi datake, she was wondering wannan besan zafin kudi bane? don daukar kayan yake yadda kasan ba biya zaiyi ba
ataqaice dai haka sukayi shopping din inda duk mussadiq yayimata, saida suka gama tsaff sannan suka wuce wurin cashier yabada a.t.m dinshi suka zare kudinsu
daga nan kuma suka nufi Icecream joint inda yasiyo masu snacks da Icecream sannan suka juyo gida
koda suka isa gida saida kowa yayi mammakin siyayyar daya yiwa Lailah,don sunyi over hakan yasa kowa qara gasgata tunaninshi akansu
Lailah ma ranar kasa janye tunanin fitarsu tayi, kwata2 tunanin gayen yaqi barin kwalwarta don tadade batayi barci ba tanata juyi zuciyarta fall tunanin mussadiq sa6anin na Deen datakeyi kullum.
WASHEGARI
kasancewar jirgin qarfe shabiyu zasubi yasa suka isa airport din tun 11 da yan mintuna
anan suka hade da family din zee ma dasuka rakosu daddy da mummy suma
sosai hira ta 6arke atsakaninsu don wuri daya suka zauna suna jiran agama every necessary thing dayakamata kafin lokacin tashin jirgin yayi
masu tafiyar acikinsu sune daddy, mummy, Abba, mamy, Habeeb da Lailah
kaka kau ba yanzu ba don da ita za'a daga saudiya😜
iya manyan Kawai ke firarsu while su qannanun suna zaune shiru sai exchanging kallo dasuke tsakanin juna
zee na zaune kusada Umminsu Aysha don tunda sukaxo ummie tajawota tazaunar daita kusada ita wanda hakan yasa takasa ko dago kai don sosai takejin kunyar ummie
a inda take zaunen tana jin hasken idanunshi akanta amma taqi dagowa tana kuma jin yadda wayarta ke beeping kai da kai na shigowar saquna taqi dubawa don tasan ko ba'a fada shine
a bangaren mussadiq ma ya tusa diyar mutane da kallo inda itama ta takura sosai da kallon qurillarshi
a bangaren batool kau tana gefe suna chatting da Ahmad da baisamu zuwa rakiyar ba saboda wata tafiyar dayayi tun shekaran jiya, shagala datayi da chatting din taqi bin Aysha data tashi zataje siyen ruwa mai sanyi saboda qishin datakeji
Aysha kadai tatafi tasiyo ruwanta bayan ta fadawasu ummie
saida tagama siyayyarta tajuyo zata taho sukaci karo dawani gorar ruwan ta sun6ule tafadi
"oh.. sorry" mutumin dasukayi karon yace yana sunkuyawa ya daukomata ruwan nata yatashi yana miqamata
ganin Aymaan ne yasata dan buda ido saikuma tasa hannu ta kwace gorar adan masife tana harararshi
"kuma ka iya kiran wani clumsy while you're clumsy yourself" tafada tana qara gallamashi harara tazo wucewa
riko hannunta yayi wanda hakan yasata saurin juyowa tana zaro idanu
"waye clumsy din?" yafada cikin hade
"let go of my hand" tafada adan tsorace tana qoqarin kwace hannun
"nine clumsy din?" yafada yana eyeing dinta batareda yasaki hannun ba
6ata fuska tayi kamar zatayi kuka har lokacin tana kicininyar kwace hannunta cikin rawar murya tace
"ni..ni kasake min hannu"
ganin dai da alamu kukan zatayi don har manyan idanunta sun duri ruwa yasa ya saketa yana cewa
"kika qara bin hanyar danabi saina tsonemiki wadannan idanun"
fashewa tayi da kuka tana saurin toshe bakinta sannan tabar wurin dasauri
sakin baki yayi yabita da kallo donshi bega abin kuka ba anan, saida tayi nisa sosai sannan tajuyo ta gallamashi harara da wet idanunta ta murgudamashi baki sannan tajuya,tabar wurin dasauri kamar wadda aka biyo
kasa daurewa yayi saida yasaki dariya marar sauti, lallai ashe dai wannan yarinyar matsoraciya ce? kwafa yayi Kawai yajuya ya qarasa wurin don siyen abinda zai siya don dama shima yabaro can ne don yin sayayya, izuwa yanzu yarage jin yadda yakeji towards zee wataqila allah ne ya qar6i addu'arshi don sosai wutar soyayyar zee tarage azuciyarshi kuma izuwa yanzu yagane cewa zee ta Deen ce kuma ya rage jin wannan zafin dayakeji duk lokacin daya gansu atare
siyayyarshi yayi yakoma can wajensu inda sai shirye shiryen tafiya su daddy keyi don jirgin yakusan tashi
tunda Aysha taga dawowarshi takoma bayan mussadiq don ya kareta don batason ma ganinshi kuma data dan leqo sai sun hada ido yayimata kallon zamu hadune saitayi saurin sake la6ewa abayan mussadiq
shidai mussadiq besan sunayi ba hankalinshi nacan kan Lailah
ahaka suka shiga bankwana inda zee kamar tayi kuka don sai jitayi tafara missing dinsu daddy tunma kafin sutafi
ahaka suka tafi suna dagawa juna hannu cikin mixed feeling suna binsu da addu'ar safe journey
Lailah duk yadda takejin idanun mussadiq akanta qin kallonshi tayi tajuya suka wuce
saida takai daidai kofar dazata shiga sannan tajuyo idanunta suka fada cikin nashi
murmushi ya sakarmata ahankali itakuma tayi saurin juyawa tashige.
ahaka suna tsaye har jirgin nasu yadaga ya lula sama
*AGURGUJE*
kingin ranakun sunzo suntafi very fast inda su Deen keta shirye shiryen tafiyarsu zuwa saudiya
sosai Deen ke doqin tafiyar don he can't wait yataka qasarshi ta haihuwa
a bangaren soyayyarsu da zee kuwa kullum qara cigaba ake samu don da alamu zee tagaji dajan ajin tafara bada kai sosai suke shan soyayyarsu tawaya saidai idan yajene bata cika sakin jiki dashi sosai ba kamar dai da
ranar daren tafiyar tasu sukaje gidansu Aymaan din don suyi bankwana
inda suna zuwa Deen yasamu ya ke6e da zee a garden suna zance sukuma Aysha sukayi sama tareda batool
sundan jima agidan kafin sufito zasu tafi inda su Aysha sukayi gaba ita da batool zasu fita suna gulmarsu zee wai suna can suna soyewa suga love birds
abakin kofa sukaci karo da Aymaan da dawowarshi kenan daga asibiti inda ganinshi kamar daga sama yasa Aysha fasa qara takoma falon aguje
da mammaki duk akabita da kallo harta qarasa wajen kaka ta la6e bayanta
girgiza kai Aymaan yayi Kawai yashiga don qararta ma firgitashi tasoyi, yawuce yabar batool dake tsaye cikeda mammaki abakin kofar
sadda yashiga ciki ya tadda anata tambayarta meye takema ihu
ganinshi yasata qara la6ewa bayan kaka Kawai tana turo baki
shidai bece komai ba yaqaraso yana gaidasu Ummie da murmushi
anan yaji ashe gobe zasu wuce saudiya
fatan sauka lafiya yayi masu sannan yawuce sama yana hararar Aysha dake la6e still abayan kaka ta gefen idanu
har parking space suka rakosu suna masu fatan isa lafiya
saida suka shiga motar suka ja suka tafi sannan suma suka juya ciki batool nata tsokanar zee
*SAUDI ARABIA*
lafiya lau suka sauka garin saudiya, fatherland din Deen inda yana taka qasar shima yaji eh wannan fatherland dinshi ne
farincikin daya tsinci zuciyarshi aciki baya misaltuwa don ganin abin yake Kawai kamar amafarki
twin din Abbansu Deen wato Al-hussain Kawai yasan da zuwansu kuma shi yaje tarbonsu a airport
saidai ganin mussadiq biyu ba qaramin burkitamashi kwalwa yayiba don shima kwata2 besan da bayyanar Deen ba
saida sukaje gida sannan sukayi mashi bayani dalla dalla inda fadin farincikin daya shiga ma 6ata lokaci ne sai godiya da kirari yake kwararawa allah mai yin yadda yaso maikuma maida abu marar yiwuwa abu mai yiwuwa
kaka kau tasha godiya da addu'o'i awajenshi kamar ya ari baki
haka suka kwana batareda sanin kowa a family dinba don Al-hussain yace kar agayawa kowa shida kanshi zai qirqiri family meeting gobe inda anan za'a bayyana Deen
haka kau akayi don nan take aka sanar da gobe akwai family meeting wanda dama abune da akeyi duk in wani abu yataso
Washegari a family meeting din inda babu wanda be hallara ba aka gabatar da Deen inda suka shigo shi da mussadiq cikin shiga iri daya
fadin hautsinewar da wurin yayi 6ata lokaci ne don nan take wurin ya rude
inda sai bayan Al-hussain ya gabatar da Deen amtsayin mujaheed daya 6ace awajen asiri yafara tonuwa inda matar Al-hussain ta tashi tana ihu tana bori wai qaryane mujaheed ya mutu saida aka tabbatar mata da hakan, wannan ba mujaheed bane mujaheed yamutu
nan hankali yadawo kanta don sosai mutanen wajen suka cika da mammakin ganin yadda take ihu tana sambatu inda acikin sambatun ta tonawa kanta asiri
asali dama matar Al-hussain bata qaunar Zainab matar al-hassan kwata2, wannan tsanar tasamo asaline tun lokacin dasuke amare kasancewar dama atare al-hassan da Al-hussain sukayi aure inda Zainab matar al-hassan tafi matar Al-hussain farinjini
sosai danginsu Al-hussain sukafi sonta saboda saurin shiga ranta da kirkinta
Duk abinda za'ayi itace kan gaba hakan yasa matar Al-hussain fara yimata hassada tana ganin duk ta saye soyayyar dangin mazajensu
matar Al-hussain tariga Zainab haihuwa don saida tayi haihuwa biyu kafin Zainab ta haihu saidai ga haihuwar Zainab anfi murna yadda kasan ba'a ta6a haihuwar jika a dangin ba hakan yaqara tunzura matar Al-hussain
abin be ida kasheta ba saida taga irin soyayyar da ake nunamasu mussadiq saboda wani irin jidasu akeyi a family din kamar su kadai ne jikoki kowa burinshi ya daukesu ga kyaututuka dasuke samu kota ina akai akai gashi kuma dama Al-hassan yafi Al-hussain wadata alokacin sai abin yataru yayimata yawa
ganin bazata iya cigaba da qunsar baqincikin bane yasata Kawai shirya tagayyara family din Al-hassan din inda da zugar wata qawarta suka sa akayi kidnapping dinsu inda basu samu nasarar daukarsu su biyun ba don allah ya ku6uto da mussadiq sai sukayi garkuwa da mujaheed (Deen)
duk tashin hankalin dasuka shiga alokacin matar Al-hussain jitake kamar ta taka rawa, sosai taji dadin ganin burinta na tarwatsa ahalin Al-hassan yafaru hakan yasa tama yanke shawarar salwantar da Deen a 6addashi daga doron qasa don su dawwama a baqinciki don sun lura sosai sukeson Deen
saida tasa aka amshi kudadde dayawa wajen Al-hassan sannan tasa a qone Deen acikin motar da xasu sashi ciki agaban idon Al-Hassan
hakan kau yafaru saidai abinda bata saniba shine alokacin jisukayi bazasu.iya qone Deen Acikin motar ba don he's way too innocent aganinsu be kamata yayi irin wannan mutuwarba hakan yasa Kawai suka jefashi aruwa aganinsu wannan mutuwar zatafi sauki
tofa! sosai hankalin family din yatashi jin sambatun matar Al-hussain
babu 6ata lokaci Al-hussain dayafi kowa rudewa alerting jami'an tsaro inda babu 6ata lokaci akazo akayi ramm daita aka wuce daita
sosai family din suka shiga tashin hankali sai koke koke akeyi, shikanshi Al-hussain kasa tsaida hawayenshi yayi don sai alokacin komai kedawo mashi fresh, wannan wace iriyar matace yake zaune daita tsawon shekaru? sosai kowa ke mammakin abinda ta aikata don koda wasa batayi kama da wadda ke iya aikata rabin abinda ta aikata ba
shima Deen sosai jikinshi ya mutu musanmman yadda yaga kowa nata rungumarshi ana kuka, kakarsu wato ainahin mamansu babansu babu wanda yakaita kuka tabi ta rungume Deen qamm kamar za'a kwace mata shi tanata sambatu cikin larabci
saida hankali yadan kwanta sannan suka nemi jin yadda Deen ya bayyana inda anan akayi musu bayanin komai
zokuga yadda akema kaka godiya kamar zasuyimata sujjada, addu'o'i kau aranar tashasu don acewarsu ba qaramin jihadi tayiba kuma sakamakonta na gun allah don dik abinda zasuyi mata bazasu iya biyanta ba...✍?
Ummin fasihu🧚🏻♀?
8/19/21, 6:46 PM - Buhainat😝: *🙍🏻♂️DEEN🙍🏻♂?*
*100*
*FINAL🤸🏻♀?*
Satinsu Deen biyu a saudiya inda acikin wannan sati biyun babu inda basu shiga ba domin zagayen dangi sai alokacin Deen yasan cewa ashe shi d'an dangi ne domin yanadasu ba adadi gashi sai nunamashi wani irin soyayya sukeyi suna jidashi suna riritashi kamar kwai
idan yajuya yatuna da rayuwarshi tabaya yayi comparing dinshi data yanzu saiya godewa allah bisa ni'imomin dayayi mashi, abin har mammaki yake bashi wai shi da tun tasowarshi beda kowa beda wanda zai kalla ya kira nashi bayan kaka amma yanzu jibeshi xagaye tsamo tsamo cikin dangi dangin ma masu tsananin qaunarshi, dole ya godewa allah
kaka ma abangarenta tasamu babban matsayi a wannan dangin don sosai suke qaunarta suke kuma girmamata, tuni suka qulle da ainahin kakarsu Deen suka xama kamar wasu aminnan juna
a bangaren matar Al-hussain kau tanacan anmakata kotu da ita da qawarta dasukayi qulle qullensu tare bayan Al-hussain ya yanke igiya daya ta aurenshi dake kanta
Satinsu biyu a saudiya suka daga zuwa misra garinsu ummie inda anan Deen yaqara ganin tsantsar qauna da tarairaya
kowa soyake ya kasance taredashi kowa soyake yanuna yadda yake qaunarshi hakan yasashi zama kamar wani cele acikinsu
Satinsu daya a qasar suka barota suka dawo Dubai inda dama Deen allah allah yake yadawo don sosai yayi missing *jewel* dinshi kamar yadda yasamata suna yanzu dukda kullum suna maqale awaya
a bangaren zee ma sosai take missing baby boo din nata, rabonta dashi tun daren dazasu tafi saudiya gashi ba video call sukeyi ba bare su dinga ganin juna hakan yasa tayi wani irin missing dinshi, kullum idan suna waya saita dinga damunshi kan yaushe xai dawo saidai yace mata very soon insha allah
relationship dinsu yanzu yayi improving sosai don har yana neman fin na da don sosai suke zuba soyayya mai tsayawa a qwalwa
shaquwarsu tada tadawo tama ninka nada don wani lokacin ma idan suna jin yan shiriritarsu haka zasu dinga musayar kalaman soyayya ta sigar waqa atsakaninsu ta waya
yanzu zee ita kanta tasan bazata gwadama Deen komai ba akan waqa don har mammaki yake bata idan yazaro mata wani baitin
daya daga cikin dream dinta na neman tabbata don aduniya tanason waqa tana kuma dreaming tasamu wanda ra'ayinsu zaizo daya suyita tisa kansu agaba suna zubama juna baitika
Yau tunda ta tashi takejin kanta cikin wani irin happy mood don Kawai tsintar kanta tayi dawani irin nishadi ayau din
kowa ma na gidan ya shaida haka don qarara hakan ya bayyana a fuskarta da ayyukanta don tariga kowa nagidan tashi saidai suka tashi sukaga tama kusan gama aikace aikacen gidan
haka tawuni cikin nishadi don abu kadan saita fashe da dariya dana dariya da wanda bana dariya ba har batool na tsokanarta kodai she needs psychiatric doctor ne? itadai Kawai saidai tayi dariya tace yau Kawai tana cikin nishadi ne without knowing why
da daddare bayan isha'i suna zaune cikin dakinsu suna kallon wani series film cikin laptop din batool wayar zee tayi ringing
ringing dinne yan dawo dasu daga duniyar kallon dasuka bada dukkan hankalinsu akai
"mtcheew don allah shut that phone up tana distracting dina" inji batool idanunta akan laptop din batason ko janyesu daga kan screen din
harararta zee tayi tasa hannu ta danna ma film din pause wanda hakan yasa batool tashi zaune azabure
"haba meye haka?" tafada a little upset
"saina gama wayar zamu cigaba" tafada tana jawo wayar dake gab da tsinkewa
danna play batool tazo zatayi zee ta suri laptop din ta miqe tsaye tana mata gwalo
itama miqewar tsaye tayi tafara kiciniyar kwace laptop din da zee ta6oye abayanta zee na zillewa tana dariya
ahaka har kiran ya tsinke bata saniba wani yaqara shigowa
dira zee tayi daga kan gadon still laptop din abayanta tana son rugama batool dake qoqarin kamota
dago wayar hannunta tayi da niyyar kasheta ma gabadaya don taji dadin rigimar dasukeyi da batool don dama sun saba saidai number data gani na yawo akan screen din yasata yin still tana waro idanu
batool dabata lura da yanayinta ba tasamu ta kwace laptop din tana
dariya tana cewa
"got yah!"
"OMG!" inji zee tana kallon wayar idanu abude
"meye?" inji batool tana matsowa
bata amsa mata ba sai daga wayar datayi takara akunne ahankali
sallamarshi dataji cikin cool voice dinshi ya ida tabbatar da zarginta, Deen is back!
sauke wayar tayi saurin yi ta katse kiran sannan ta wawuro batool dake gabanta tawani irin rungumeta tana ihun murna
"he's back! he's back! OMG!"
saurin qwace kanta batool tayi tana cewa
"wai meye haka? who is back?"
cikin tsananin murna tace
"my boo mana! kalla da number nan yakirani, wayyo! what a surprise!" tafada tana juyi
tsaki Kawai batool taja takoma kan gadon tana bude laptop din
saita kanta zee tayi kafin taqara daga kiran daya sake shigowa
"hello?"
taji anfada daga dayan bangaren
"hello... is this for real?" tafada ahankali cikin yanayin mammaki
sautin murmushinshi tajiyo sannan yace
"kifito and see for yourself"
"infito ina?" tafada tana dan wara idanu
yar dariya yayi sannan yace
"waje, ganinan a parking space kizo kiyimin iso"
"are.. you serious?"
yar dariya Kawai yayi yace
"saikin zo" daga haka ya,katse kiran
dungule hannayenta tayi tana ihun murna sannan tayi wani juyi tafada kan batool dake kallon ta
"wai meye haka?" inji batool tana tureta daga jikinta
"wai yana waje, what a huge surprise!" tafada cikin tsananin murna
harararta batool tayi tace
"ji gulma, kamar irin batasan dazuwanshi ba dinnan. ashe ba banza ba duk wunin yau baki yaqi rufuwa ashe kinsan abinda kika taka"
"ji banza, wlh bansan da zuwanshi ba"
ta6e baki batool tayi tana maida hankalinta akan laptop din gabanta tana cewa
"saikiyi"
dunguremata qeya zee tayi tana cewa
"banza joy killer Kawai" ta tashi tanufi closet dinsu tabude
cikin qanqanin lokaci tashirya cikin wata baqar abaya ta yafa gyallenta in a simple way tadan gyara fuskarta sannan ta feshe jikinta da turare
zuwa tayi taqara dungure ma batool kai tana cewa natafi sannan tajuya tawuce dasauri
kwafa batool data dago tana kallonta tayi sannan ta maida hankalinta kan abinda takeyi
fitowa tayi daga falon sannan tafara takowa ahankali ta entrance din tanufi parking space hoping badai tsokanarta yakeyi ba bezo ba
wata baquwar ash colour motar data gani pake a parking space din yasata jin wani irin sanyi na ratsa zuciyarta
ahankali take takawa tana nufar wajen inda ko rabin kaiwa batayi ba aka bude murfin kofar daga bangaren driver yafito
tsayawa tayi daga tafiyar datake tana kallonshi yana zagayowa dayan side din motar
bata ta6a sanin har haka tayi missing dinshi ba sai yanzu, jitake kamar sun shekara basu hadu ba gashi yawani chanza yaqara yin fresh dashi
shima bangaren Deen hakan take don shima sosai yaji yayi kewarta kuma ta chanza mashi sosai cikin dan lokacin dasukayi basuga juna ba
ahankali ya sakarmata wannan cool murmushin nashi itama saita tsinci kanta da mayar mashi da martani
ahankali yashiga takowa zuwa ina take tsaye hakan yasa ta cigaba da kallonshi abubbuwa dayawa nakai kawo azuciyarta
komai nashi na daban ne hatta tafiyarshi, komai nashi cikin nutsuwa yakeyi, kai she love this guy!
saida yaqaraso gabanta ya tsaya yana dan bada tazara atsakaninsu
kallonta yakeyi da oily eyes dinshi fuskarshi dauke da murmushi, kasa cigaba da jurar kallon tayi hakan yasata sauke nata idanun qasa tana d'an murmushi
"wow! you're welcome, dama yau zaka dawo baka fadamin ba? kai amma am very happy and surprise altogether, I missed you so much" inji Deen yana kallonta
dagowa tayi ta kalleshi tana dan daga gira
shima daga gira daya yayi yace
"koba haka kikeda niyyar cewa ba?"
harararshi tayi
"to ba haka nayi niyyar cewa ba, besides fushi ma nake dakai, ashe yau zaku dawo amma shine baka gayamin ba kuma har waya munyi dasafe?"
yar dariya yayi yace
"it's a surprise, yanzu da kika ganin kamar daga sama ba kinfi jindadi ba?"
kauda kai tayi tace
"ni banwani jindadi ba"
"ai bake zaki fadi jindadinki ko rashin jindadinki ba, fuskarki zata bayyana kuma tariga ta tonamiki asiri"
harararshi tasakeyi sannan tajuya
"muje"
"to ranki shi dade"
murmushi Kawai tayi suka jera atare suka nufi cikin gida
zee tafara shiga falon sannan tayima Deen iso shima yashigo ciki bayan ya cire takalminshi saura baqaqen socks akafarshi bakinshi dauke da sallama
falon babu kowa sai qamshin dake tashi afalon
nunamashi wurin zama tayi ya qaraso ya zauna ahankali ita kuma tawuce kitchen
ba dadewa tadawo da dan tray mai dauke da ruwa da drinks tazo ta ajiye akan stool din dake kusada kujerarshi
dagowa tayi ta kalleshi saitaga shima ita yake kallo ya sakarmata murmushi
kauda kai tayi itama tana murmushin tace
"bari nakira ummy"
"nabari" yafada yana kallonta
juyawa tayi tawuce sama tanajin idanunshi kanta
saida tahaye sama sannan ya daina kallon stairs din sannan yakoma ya jingina da kujera yana murmushi kai da ganinshi kasan yana cikin farinciki sosai
ba'a jima ba yaji motsin saukowarsu hakan yasashi dagowa yaga ummy agaba zee biyeda ita
cikin murmushin kunya ya miqe tsaye ya dan sinne kai har suka qaraso falon
"A'a? maraba da mutanen saudiya, saukar yaushe?" tafada tana qarasawa ta xauna
russunawa Deen yayi yana gaisheta cikin sinnar dakai
amsawa tayi cikin kulawa tana cewa ya zauna
maimakon yakoma ya zauna kan kujerar daya taso saiya zauna nan qasan carpet din
"A'a? ka koma sama mana" inji ummy
"A'a nanma yayi ummy" yafada akunyace
"to ya hanya? ya mutanen saudiyan?"
"alhamdulillah ummy duk suna gaidaku"
"muna amsawa, yasu kaka?"
"kaka na gida tana gaisheku itama"
"muna amsawa, fatan kundawo lfy"
"lfy qalau ummy"
"to madallah... daughter kawomashi abinci kinji"
dasauri yace
"A'a alhamdulillah ummy"
"to bari nahau sama, let me know idan zaitafi Zainab"
"to ummy" Zainab dake tsaye bayan kujerar ummy tundazu ta amsa
ummy ta tashi tawuce sama
ajiyar zuciya Deen yasauke bayan hayewarta sannan yadago ya kalli zee
dariya tadanyi
"kamar na allah" tafada tana dariya
dan wara idanu yayi
"to da na wanene?" yafada yana tashi yakoma kan kujera
itama dawowa tayi gaban kujerar da ummy ta tashi ta zauna
"wow! I missed this girl so much, kinsan daga saukarmu wanka Kawai nayi na chanza nayonan? I just can't wait to set my eyes on you"
murmushi zee tayi
"miss you too"
"A'a banga alama ba, naga nikadai ma ke doqi na"
"haka dai kace"
"hakane ma"
"to ya hanya? hope kun iso lfy"
"lfy lau wlh, hope munsameku lfy"
"lfy lau, so how's saudi?"
"alhamdulillah, duk lfy.. kinsan wani abu?"
girgiza kai zee tayi
"banta6a sanin haka mutum kejiba idan yana cikin family dinshi ba saida muke saudiya... wai nine tsamo tsamo cikin mutane kuma wai family dina, wlh ko amafarki banta6a hangowa kaina haka ba, jinike kamar ba gaske ba..I was just so overwhelmed.. banta6a sanin haka family keda dadi ba.. ranakuna a saudi da misra are one of my best moment ever"
Zainab kasa daina murmushi tayi tunda yafara magana, kallo daya zakayimashi kasan he mean duk abinda yake cewa, sosai farinciki ke bayyane afuskarshi, sosai taji tana tayashi murna da hakan don wannan abin abin atayashi murna ne
"congratulations, aidama family nada dadi bazaka gane hakan ba sai kana cikinsu, gaskiya ina tayaka murna, am very happy for you"
murmushi Deen yayi sannan ya kalleta
"and all these happened because of you, har duniya ta nade bazan ta6a mantawa da mutane biyu ba arayuwarta, dake
All Chapters
Chapter 1
Chapter 2
Chapter 3
Chapter 4
Chapter 5
Chapter 6
Chapter 7
Chapter 8
Chapter 9
Chapter 10
Chapter 11
Chapter 12
Chapter 13
Chapter 14
Chapter 15
Chapter 16
Chapter 17
Chapter 18
Chapter 19
Chapter 20
Chapter 21
Chapter 22
Chapter 23
Chapter 24
Chapter 25
Chapter 26
Chapter 27
Chapter 28
Chapter 29
Chapter 30
Chapter 31
Chapter 32
Chapter 33
Chapter 34
Chapter 35
Chapter 36
Chapter 37
Chapter 38
Chapter 39
Chapter 40
Chapter 41
Chapter 42
Chapter 43
Chapter 44
Chapter 45
Chapter 46
Chapter 47
Chapter 48
Chapter 49
Chapter 50
Chapter 51
Chapter 52
Chapter 53
Chapter 54
Chapter 55
Chapter 56
Chapter 57
Chapter 58
Chapter 59
Chapter 60
Chapter 61
Chapter 62
Chapter 63
Chapter 64
Chapter 65
Chapter 66
Chapter 67
Chapter 68
Chapter 69
Chapter 70
Chapter 71
Chapter 72
Chapter 73
Chapter 74
Chapter 75
Chapter 76
Chapter 77
Chapter 78
Chapter 79
Chapter 80
Chapter 81
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 80 Chapter of 81