Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
jinina ke kan akaifa jinake kamar zan rasashi ahaka likitocin suka fito daya daga ciki yanemi tattaunawa dani inda anan yake sanar dani yaron yakamu ne da ciwon nimonia (Pneumonia) saboda sanyin dayayi mashi mugun kamu (wannan ne Asalin ciwon Deen) sannan ya rubuta min abbubuwan dasuke buqata tareda magungunna koda naje wurin sayen sai akayi min lissafin kudadde masu yawa dukda ga lokacin bansan sunada yawaba don bansan kan kudin Nigeria ba sosai tambaya nayi inda xa'a chanzamin yan kudaddena dana taho dasu daga Nigeria aka nunamin naje na chanzo inda anan na fahimci ko rabin kudin maganin banidasu komawa nayi asibitin wurin likitan nayimashi bayani akan cewa kudaddena kenan ya taimaka ya dubamin shi banida komai bayansu cewa yayi babu abinda zai iya yimin indai ina buqatar lafiyar yarona inje inkawo abubbuwan dasuka buqata haka nasake fita hankalina amatuqar tashe gashi bansan kowaba bare na nufeshi ya taimakamin haka naita yawo inda daga qarshe nayi abinda banta6ayiba wato bara haka naita tare duk wanda nagamu dashi akan ya taimaka min inda qalilan ke saurarona har sudan bani wani abu wasu kau ko kallo ban ishesu ba ahaka nasamu nadan tattara yan kudadden nakoma wajen likitan nazube mashi su da wanda nasamo da wanda dama nake dasu nace yaduba yaga ko sun kai gani nayi yabi kudadden da kallo wanda hakan ya sanyaya jikina saikuma ya sa hannu yafara tattarasu ya hadesu ya kirga yana gama kirgawa yadanyi murmushi yana girgiza kai wanda hakan yaqara sanyaya min gwiwa don da alamu dai basu kai ba nurse yakira yabata wasu kudin banda nawa da takardar maganin yace taje tasiyo sannan yaturomin kudaddena yace na ajiye Kawai godiya naita yimashi harda kukana don da be taimaka min ba bansan inda zankuma je insamu taimako ba ahaka nurse din tadawo da abubbuwan daya aiketa saye nan da nan yatashi yafita yakoma inda aka kwantar da kyakyawana.." dan shiru tayi ta dago tana kallon mutanen dakin daduk suka maidata t.v, daidaiku ne babu hawaye a idanunsu kowa idanunshi yayi jajir jikinsu duk yayi sanyi kamar wadanda akayima shegen duka kallon Deen tayi da fuskarshi tayi jajir idanunshi sunyi jajir sungaji da zubda hawaye sai kallon kaka yake kamar yau yafara ganinta ahankali takamo hannunshi tariqe tareda matsewa anata tana dan murmushi sannan tacigaba dacewa "ataqaice dai saida muka kusan sati asibitin inda likitan duk ya daukemana komai nakula da lafiyar shi sai abinci Kawai nake siye da yan kudadden hannuna acikin wannan yan kwanakin Kamal yasamu sauki sosai ya warware inda wata shaquwa tashiga tsakaninmu, yadda yake liqemin sai kayi tunanin dama can yasanni ko mun hada wani abu dashi kuma ba haka yakema kowaba don nalura yanada qiwuya don ko likitan baya yarda dashi amma ni yadda kasan uwarshi. ahaka har aka bamu sallama inda likitan yaita gayamin abubbuwan daxan kiyaye saboda gudun tashin ciwonshi sannan yabamu kingin magungunnanshi yayimana fatan alhairi. sosai nagodewa mutumin da bazan ta6a mantawa da alhairinshi ba, ahaka nafito dashi abayana don nalura yanada bala'in son jiki gashi dama yanzu yake samun sauqi bazanso yayi tafiya ya wahala ba ahaka muka fito batareda munsan inda muka dosaba ga garin babu ruwan kowa da kowa, kowa harkar gabanshi yake karnaja xancen da tsayi, iya wahala mun wahala don saida mukayi kwana uku batareda masauki ba inda darana muke yawo ina dan yimana barar abinda zamuci idan dare yayi muzo tasha mukwana. sosai nagaji da barar danake don bara wata iriyar qasqanttaciyar sana'a ce wanda batada dadi kwata2, na gwammaci aikin wahala abiyani da yinta gashi kuma banaso na cigaba ahaka har kyakyawana yatashi ahaka shima don sosai naci buri akanshi naji inason koyaya ne yasamu rayuwa ingantacciya ahaka nafara neman abinyi inda daga baya nasamu aiki acikin tashar wajen wata bayerabiya mai saida abinci, dafarko wanke wanke nakemata da share share tana bani abinci safe da rana kafin daga baya yazamana har girkin nake tayata inda anan nadan koyamata wasu abincicikanmu na ghana wadanda suka samu kar6uwa sosai awajen customominta hakan yasa bayan abinci tafara biyana kudi wadanda nake adanasu don burina lokacin insamu inkama mana ko daki dayane mubar kwana tasha don kwata2 banason kwana tashar damukeyi don yawanci yan iska sunfi yawa aciki haka zasu kwana suna shaye shaye da bushe bushensu da kayan hayaqi nikuma banison kyakyawana yatashi cikin irin wannan environment din ahaka nasamu dakyar dahada kudin kama daki daya na rabin shekara muka koma can inda daganan muke zuwa aikin kullum nida kyakyawana wanda ke maqale dani duk inda nayi baya yarda da kowa saini sosai kyakyawana keda shiga ran mutane don mutane dayawa sunsanshi suna kuma sonshi don mutane sunsha bashi kyautar abubbuwa don yana matuqar burgesu saboda kyawunshi (kunsan yare dason kyawawa) ataqaice dai saida mukafi shekara agarin kafin na tattara muka bar garin muka koma garin minna inda anan nasa kyakyawana Makarantar primary da islamiya nikuma nakama sana'a ina kula damu nabaro lagos ne badon komai ba saidon dama ni garin beyimin ba, banaso kyakyawana yatashi acikinta bare yatashi da al'adunsu don sai ahankali hakan yasa ina tara isassun kudadden danaga zai ishemu natattaro muka barota sosai na jajirce akan ilimin kyakyawana, komai dazanyi duk saboda shi ne, nayi sana'o'i kala2 wadanda nikaina bansan iyakarsu ba nidai burina na inganta rayuwar kyakyawana wanda shikadai nake iya kira nawa kuma shikadai nake kallo inji dadi ataqaice dai munyi zaman garruruwa daban2 nayi sana'o'i daban daban dik don riqe kaina da kyakyawana wanda nake mashi kallon duniyata ina qaunar Kamal qaunar dabaxan iya misaltawa ba don da ata6amin shi gwara ni ata6ani sau dubu Kamal yataso yaro mai matuqar sanyi da rashin hayaniya, bayada hayaniya kwata2 ga tsantsar biyayya ga nagaba, gashi allah yabashi kwalwar daukar karatu don tun yana primary yake ciwo kyaututuka na hazaqar karatu both islamiya da boko hakan yake qara qarfafamin gwiwa wajen qara zagewa don tallafawa karatunshi shaquwar dake tsakanina da Kamal bata misaltuwa, nice komai nashi kamar yadda shine komai nawa, Kamal yakasance yarone mai tsananin tausayawa da jin qai, bayada qiwuya ko kadan don duk yawancin sana'o'i na tare dashi mukeyi yana matuqar taimakamin sosai ahaka harya girma yagama primary yakuma yi saukarshi tafarko inda alokacin ne muka sake tattarawa muka bar garin muka koma Katsina lokacin yanada shekaru goma sha biyu zan iya cewa duk tafiye tafiyanmu da zama garurruwan damukayi babu wanda naji dadinshi kamar na Katsina cikin ikon allah na tsayar da sana'a datayi matuqar amsata na saida Koko da qosai inda da ita muka samu muka,cigaba da rufama kanmu asiri anan nasamoma kyakyawana Makarantar secondary ta gomnati ya cigaba da zuwa inda anan ma yayi fice saboda hazaqarshi ahaka harya kammala yakuma fito da sakamako mai kyau inada burin kyakyawana yayi karatu mai zurfi kodan inganta rayuwarshi gashi nalura shima yanason karatun sosai hakan yasa naji inason ya cigaba da Makarantar gaba da secondary kasancewar babu kudin shiga Makarantar alokacin hakan,yasashi zaman gidan shekara daya inda anan maqocinmu wanda yazama kamar dan uwanmu yasama mashi wani shagon kafinta ya dinga zuwa, acikin shekara guda din nayita tari don babu laifi inasamu sosai da sana'ar nan,tawa ta Koko da qosai gashi Kamal shima yana dan samo wani abu andcan shagon nasu ahaka muka hada mukaita tarawa har shekara tazagayo muka samu yashiga Makarantar gaba da secondary din wanda dik shine burinmu zan iya cewa nafishi farinciki da fara zuwa Makarantar dayayi don harwani alfahari nakeji araina idan na kalleshi naga wannan yaron nawane rainonane. Deen yarone mai,matuqar sanyi hakan yasa wasu ke amfani da sanyinshi wajen cutardashi hakan yasa yake matuqar bani tausayi kuma nake tsayamashi tsayin daka bana kyale duk wanda ya ta6amin shi, kowama yasan irin yadda nakeji dashi kuma banison komai ya ta6ashi shiyasa ake shakkar yimashi wani abin don akanshi banajin nauyi ko kunyar kowa haka muka cigaba da rayuwa har zuwa lokacin da Zainab tashigo rayuwar Kamal..." cigaba tayi dabada labarin yadda akayi case din incident dinsu master inda anan tafara saninsu Zainab da yadda Deen ya kwanta asibiti harwani da zumuncin dasukayi da ahalin Zainab bayan lokacin saita gangaro kan soyayyarsu dakuma yadda soyayyar tasu bata kwanta mata ba tunfarko saboda dama tunfarko tahangomasu matsala a soyayyar nan ta gangaro kan yadda su daddy sukazo dashi da abokinshi Alhaji Abubakar(baban asaad) sukazo suka nuna rashin son dangantakar dake tsakanin Deen da zee dakuma cewa tajamashi kunne yafita harkar yarsu harzuwa lokacin dasuka dawo kuma dakansu daga baya suka bada haquri akan abinda sukayi suka kuma yarda da soyayyarsu wanda itama dole ta amince saboda yadda talura Deen nason zee din saikuma tagangaro zuwa maganar data tadamata hankali na batun Introduction dinsu wanda dafarko bata tashi hankalinta ba sai lokacin da wannan abokin daddyn yazo gidan shikadai lokacin Deen bayanan yana Makaranta yafadamata batun Introduction din yana kuma cewa dangin Deen suke buqatar gani najini don gaskiya bazasu wani yarda da bayada kowa ba sai ita don ba'a ta6a yin hakaba tunda ita kakarshi ce dole dai ace yanada dangi bayan ita babu yadda za'ace ita kadai ce danginshi saidai idan akwai wata qullaliya don haka su bazasu lamunci rainin wayau ba don bincike zasuyi na sosai da sosai bazasu aurama diyarsu marar asaliba tofa abinda yatashi hankalin kaka kenan alokacin komai ya dagulemata taga kamarma sunsan babu abinda tahada da Deen hankalinta yatashi sosai don saitaga kamarma sosuke su rabata da Deen din gabadaya hakan yasa alokacin ta tashi hankalinta ta burkuce ma Deen akan dole subar garin don saitaji garinma yaficemata akai gabadaya hakan shine dalilin barin garin nasu har suka koma Abuja nanma tabada labarin irin rayuwar tsukun dasuka shiga a Abujan kafin allah ya dafamasu suka hadu da Alhaji Shamsu wanda ta silarshi Deen yazama abinda yazama yanzu, ahaka harta gangaro kan wannan tafiyar dayayi dakuma yadda ranta be kwanta da tafiyar ba don jitayi ajikinta kamar zata rasashi ne ashe kaddarace ta kirashi.. kaddarar haduwa da ainahin ahalinshi...✍? *insha allah page 100 littafin zai qare, so start saying byebye to DEEN👐🏻* Ummin fasihu🧚🏻‍♀? 8/19/21, 6:39 PM - Buhainat😝: ahaka suke firar inda jefi jefi zee da Lailah kesamusu baki Aysha da batool nema masu surutun sallama sukaji anyimusu daga bayansu hakan ya katsesu daga firarsu duk suka dago suna amsawa "barka" yafada cikin murmushi suma martanin murmushin suka maida mashi suna amsawa banda zee da tunda tadago suka hada ido ta kauda kai "please kudan bani aronta for a few minutes..please" yafada yana nuna zee kallon juna batool da Aysha sukayi sukayi murmushi "oh.. sure" inji batool sai takama hannun Lailah tana cewa "kinga mukoma daga can sis" suka wuce sukabar daga zee sai Deen awajen qarasowa Deen yayi ya tsaya yana fuskantar zee dahar lokacin bata qara kallonshi ba harde hannayenshi yayi a qirji yana kallonta fuskarshi dauke da murmushi jin shirun yafara yawa yasa zee dagowa sai taganshi a yadda yake yawani kafeta da ido hade fuska tadanyi taqara kauda face ahankali cikin muryar rad'a taji yace "angry bird" dagowa tayi ta kalleshi dan budamata idanu yayi yace "yes, my cute angry bird" harararshi tayi Kawai tafara qoqarin ra6ashi tawuce "you know what?" ya dakatar daita da hakan tsayawa tayi batareda tajuyoba "banta6a ganin hallita mai kwatankwacin kyawunki ba aduk duniyar nan" qarasowa yayi gabanta yana kallonta "tell me.. what did you do to me?" dagowa tasake yi ta gallamashi harara ta kauda kai "zan wuce" tafada ciki ciki kaucewa yayi daga kan hanyar yana dan bowing "as you wish ma'am" kauda kai taqara yi cikin qoqarin 6oye murmushin dake neman su6ucemata tazo tasake ra6ashi tawuce "please kibani digits dinki idan babu damuwa" yafada daidai tawuceshi batareda tajuyo ba ko ta dakata daga tafiyarta tace "akwai damuwa" "ok please ki taimaka ki daga idan nabugo" yasake fada da d'an qarfi don tafara yimashi nisa banza tayi dashi ta cigaba da tafiyarta "i'll take your silent as yes" yaqara yafada yana kallonta dan murmushi Kawai zee tayi tana cigaba da tafiyarta, Deen won't change, her silly timid guy agefe kuma bayan su batool sunbasu wuri suka samu wani wurin suka koma suka tsaya suna fira suna cigaba da jiran fitowarsu abbu Lailah kasa concentrating tayi a firar tasu don hankalinta gabadaya yana gasu Deen data baro, she can't help but feel jealous, wani irin kishi taji tanaji ganin wanda take mugun crushing tsaye da wata duk yadda taso maida hankalinta akan firarsu batool kasawa tayi don banda satar kallon inda suke tsaye babu abinda takeyi ahaka har zee tabaro Deen tadawo wajensu inda hakan yayi daidai da fitowarsu abbu da kingin daga cikin gidan suna fira suna dariya anan hankalinsu yadawo kansu gabadaya wata sabuwar sallamar aka sakeyi tsakanin juna kafin su rakosu har wajen motocinsu zee zata nufi motarsu ummy Aymaan yabude mata kofar tashi motar yana cewa tashiga fuskarshi da murmushi dan maida mashi murmushin tayi taqaraso tashige motar batareda ta yarda tajuya takalli saitin inda takeji ana kallonta ba maida kofar Aymaan yayi yarufe yajuyo zai wuce suka kusan karo da Aysha data gama bankwana da batool data shiga bayan motarshi saurin jabaya Aysha tayi tana cewa "oh..sorry" rolling idanu Aymaan yadanyi yazo zai wuceta ciki ciki yace "clumsy gal" binshi da kallo tayi don tajishi harya zagaya seat dinshi kamar ance yadago sai suka hada ido don har lokacin shi take kallo kamar dama shi take jira yadago ya kalleta saita gallamashi mugun harara tareda murgudamashi baki sannan tajuya tawuce wajensu ummie dake dagama su ummy hannu dan murmushi yayi yana dan girgiza kai Kawai sannan yashige motar shishigewa motocin kowa yayi suka rurrufo sannan suka tada har lokacin ummie bata daina dagamasu hannu ba fuskarta dauke da murmushi shikau Deen yakasa dauke ido akan zee dake cikin motar Aymaan Ahaka motocin suka jera suka bar gidan anan kingin suka juya suka koma ciki dayake dare yayi sosai yasa Kawai su mamy dasu kaka suka wuce masaukinsu shima Alhaji haka inda Lailah zata kwana tareda Aysha duk sukayima juna bankwana suka shishige adaren ranar Lailah kasa barci tayi, jitayi komai ya dagulemata ganin Deen nason wata ba qaramin jagulemata lissafi yayiba hakan yasa ranar banda juye2 babu abinda takeyi don barcin yaqi zuwa a bangaren Aymaan ma haka, zuciyarshi takasa sukuni, yakasa hqr da tunanin zee dukda yanajin qamshi qamshin rabuwa daita, ganin barcin ya gagara yasashi miqewa daga baya yayo alwalla yafara nafilfilu inda daga qarshe yaita addu'ar za6in alhairi yana addu'ar allah ya sassautamashi soyayyar zee a zuciyarshi yakuma bashi haqurin da juriyar rabuwa daita idan batashi bace....✍? *manage🙏🏻* Ummin fasihu🧚🏻‍♀? *🙍🏻? 8/19/21, 6:43 PM - Buhainat😝: *🙍🏻‍♂️DEEN🙍🏻‍♂?* *099* *SEMI-FINAL* *TWO DAYS LATER* Acikin kwanaki biyunnan sosai su kaka dasu ummie suka zama kamar family zama suke yadda kasan sun dade dasanin juna don sosai zumunci yaqullu atsakaninsu wanda ga dukkan alamu zaiyi qarfi sosai don juma'a mai kyau tundaga laraba ake ganeta kaka tazama kamar wata kakarsu ta gaskiya don yanzu ba iya Deen ba hatta mussadiq da Aysha sunyi wani irin shaquwa da kaka, musanmman ma Aysha don tazama kamar wata kaka's pet kullum tana sashenta fira inda tadage wai tana koyon hausa awajen kaka mussadiq ma babu laifi yana yawan zuwa sashen kaka saidai be faye surutu ba Kawai dai zaije ne yayi zaune yana kallon firarsu da Aysha sannan yasha furar kaka wanda tunda tabashi yafara sha sau daya yaji duk duniya babu abinda yata6a yimashi dadi irin furar hakan yasa kullum yake lalla6owa yazo part din ya zauna baya fita saiyasha furar, itama kaka lura datayi da hakan yasa kodayaushe take tanadarmashi furar don ta lura masoyinta ne sosai abu nabiyu dake kaishi part din kaka kuma Lailah ce, yarinyar da tunda yafara dora idanunshi akanta a airport yakejinshi ba daidai ba haka Kawai yake samun kanshi dason tsareta yaita kallo batareda shima kanshi yasan amfanin kallon ba agareshi, Kawai dai burinshi kullum ya sameta ya kafamata wadannan idanun nashi yana kallo saidai ya lura yarinyar kamar bata magana don dafarko yayi tunanin she's the silent type sai daga baya daya tattara hankalinshi akanta yana studying dinta yagano damuwace ta maidata hakan don akodayaushe haka zaka ganta so moody bata magana saita kama, mostly yafi ganinta tana danne dannen wayarta with unknown expression a fuskarta yau ma kamar kullum part din kaka yashiga sanye yake da kayan gida don bedade da fitowa wanka ba bayan sundawo daga Yawon zagayen companies dinsu dayayi da Deen he's too tired shiyasa suna dawowa yashige toilet yayi freshen up sannan yafito ya shirya cikin qanannun kaya yafita yabar Deen dake jibge a kujera tunda suka dawo waya kare a kunnenshi yana magana qasa qasa sai zabga murmushi yake kamar wanda akewa wani babban albishir direct part din kaka yanufa don alokacin saiyaji babu abinda yakeso kamar furar kaka da sallama yashiga part din inda as usual ya iskesu a qayattacen falon nata daita da Aysha data daddage tana koyon hausa sai mamy daga gefe tana gyara wasu kaya don gobe zasu koma 9ja atare duk suka dago suna amsa sallamarshi ya qaraso cikin falon "sannu.. dai zuwa" Aysha tafada cikin yanayin hausarta data fara koya tana kallon mussadiq fuska washe harara ya gallamata yana zama kusada kaka cikin larabci yace "idan na wanka maki mari ko?" 6ata fuska Aysha tayi tana kallon kaka dariya Kawai kaka tayi tana cewa "kyaleshi kishi yake don kinfara iyawa shi be iyaba" dukda Aysha batasan me tace ba amma tasan rarrashi ne hakan yasa tadan tura baki tana sake komawa gefen kaka tana dan murmushi shima mussadiq murmushin yadanyi sannan yashiga gaidasu kaka da mamy suna amsawa cikin fara'a, kaka sai tsokanarshi takeyi shikau saidai ya sunkuyar dakai yana murmushi don besan me take cewa ba ba jimawa kaka ta tashi ta tafi wurin fridge din dakin tabude taciromashi furarshi data dama donshi tazo ta ajiye mashi nan take fuskarshi ta washe babu ko kunya yaqara jawo furar yabude yafara aikata don shi kanshi har mammakin yadda yakeson furar nan yake, gani yake da za'a bar bashi komai naci acigaba da bashi fura as abinci tsaff zai iya rayuwa yana shanta ita kadai haka yaita shan furarshi yana sauraron su kaka dasuka dasa darasinsu inda mamy ce yar fassara don idan Aysha tayi tambaya da turanci mamy ke fassarawa kaka itakuma saita bata amsa yana cikin sha yafara yawo da idanunshi a falon something is missing, akwai abinda babu a falon _Lailah_ dan dakatar da shan furar yayi yana tunani gobe su Lailah zasu bar Dubai sukoma Nigeria and har lokacin magana bata ta6a hadasu ba saiko gaisuwa sama sama irin hyy hello. ya lura idan yazo waje taganshi saita fara quramashi idanu kamar Maison tantance wani abu, daga bisani kuma saita janye idanunta akanshi baxata qara yarda ta kalleshi ba shima most time yanason yimata magana amma saiya fasa saboda yanayin damuwar dayake hangowa qarara afuskarta hakan yasa saiya zubamata idanu instead yaita kallo kamar t.v saida yasha fin rabi sannan yarufe kingin furar yatashi ya maida a fridge din dagowa kaka tayi ta kalleshi bayan yadawo yazauna tace "harka qoshi?" yanayin yadda tayimashi nuni yasashi gane metace hakan yasashi yin dan murmushi yana kada kai "na'am shukran laki, jazakillah" yafada ahankali murmushi itama kaka tayi sannan tajuya kan Aysha daketa maimaita wata kalmar hausa cikin son riqewa yadan qara zaman yan mintuna sannan yatashi yayi musu sallama yafita, he was wondering ina tashiga don a irin wannan lokacin batada wurin zama sai part din kaka main house din yashiga inda ya tarar babu kowa dama kuma ummie batanan hakan yasashi fita waje haka Kawai zuciyarshi tabashi yaje garden din gidan wanda hakan yasashi nufar wajen hannayenshi zube a aljihu yana takawa ahankali cikin tafiyarshi tundaga nesa ya hangota zaune kan kujera ta kafe waje guda da ido glass cup mai daukeda fresh milk ahannunta tsayawa yayi yana kallonta kamar mai karantar wani abu tattare daita sannan yafara takowa ya nufota saboda zurfin datayi a tunaninta yasa batasan sadda yazo wajen ba sai jitayi an zare glass cup din hannunta adan firgice ta juyo sai taganshi zaune a kujerar dake facing dinta yakai kofin abaki yana sipping ahankali quramashi idanu tayi kamar mai son tantance wani abu kamar yadda tasaba kullum insun hadu can saikuma ta janye idanunta ta maidasu qasa ajiye cup din yayi yana gyara zamanshi yace "yes bashi bane.. ba wanda kike tunani bane, mussadiq ne" yafada da turanci dagowa tayi ta kalleshi "muna kama sosai ko? kamar da saikin dauki mintuna kina kallona kafin ki iya tantance waye agabanki, aganina da dagaske abinda kike tunani hakane da bazaki dauki lokaci kafin ki iya tantancemu ba don a kallo daya zuciyarki zata baki ko waye agabanki" kallon rashin fahimta take mashi don duk takasa gane kan maganarshi "you're confused gal... so confused, you're confusing your brain and mind, yakamata kiyi realizing gaskiya izuwa yanzu" "gaskiya? as in?" inji Lailah tana kallonshi still confused komawa yayi ya jingina da kujerar yana kallonta qasa qasa yace "as in abinda kike tunani bashi bane, abinda kwalwarki ke tunani yasha banban da abinda zuciyarki ke tunani" yanayin yadda tayi da fuska yasashi sanin yasake kullemata kai hakan yasashi yin guntun murmushi yace "you think you love him? No, kisake bincikar zuciyarki" wannan karon kallonshi take sosai "what did you mean?" "I mean you two don't really deserve each other, there's someone who deserve you most, zuciyarki tagane hakan amma haryanzu kwalwarki takasa gane hakan" shiru tayi tana kallonshi nawani lokaci, wai akan me yake magana ne? badai akan Deen ba, idan ma akanshi ne tayaya yasani? shi kanshi Deen din bata tunanin yasan tana sonshi bare ya gayamashi "look, wani lokacin zuciyarmu tafi kwalwarmu saurin gano abu, so goes yours don haryanzu zuciyarki bata iya gane mere presence din wanda kwalwarki take ikirarin kinaso, meyasa akallo daya zuciyarki bazata baki cewa eh shidin ko bashi bane? meyasa saikin dauki lokaci kafin ki iya tantance hakan... because your heart doesnt really beats for him, you're decieving yourself ne Kawai" jitayi ranta ya6aci, who is he dazaiyi judging dinta haka? zuciyarshi ce ko tata? tayaya zai fita sanin abinda takeso? daukar wayarta dake kan table din tayi tafara qoqarin tashi don iya abinda zata iyayi kenan yanzu, tabarmashi wurin don taga alamun abin ma harda rainin wayau d'an murmushi mussadiq yayi yasake jingina da kujerar yana harde hannayenshi a qirjinshi yace "you might be angry but that's it, zuciyarki ba wa Deen take bugawa ba, idan ma tana bugamashi ada yanzu tadaina, da alamu tafiki hangen nesa saboda tuni ta hangomiki wanda yafi cancanta dake" tunda yafara maganar ta tsaya daga qoqarin tafiyar datake tana sauraronshi batareda tajuyo ba tashi shima yayi yatako har kusada ita "stop wasting your time on someone who's not even aware of your feelings maimakon hakan kiba wanda yafi cancanta dake dama, damar wanke dukkanin damuwar dake a zuciyarki.. mai kwadayin ganin murmushinki wanda kuma zai iya komai don dawwamar da murmushin akan fuskarki" daga hakan yazo ya ra6ata yawuce walking in his usual majestical steps binshi da kallo tayi daga inda take tsaye kamar mutum mutumi, takasa koda motsi don komai ya tsaya mata cakk sai magangganunshi dake mata kai komo a kwalwa. part din kaka yakoma inda nan ya tadda dukkan mutanen gidan harda Deen dashima izuwa lokacin ya chanza shiga da ummie da bata dade da dawowa ba fira suke gwanin sha'awa don dama haka sukeyi sutaru dakin kaka suyita fira zama yayi gefen Habeeb yana maida mashi martanin barka dayake mashi nan ya cigaba da sauraron firarsu wanda duk na komawar su Abba Nigeria ne don gobe zasuyi tafiyar tareda su daddy da mummy agogon hannunshi ya kalla sai yadago ya kalli Aysha dake kusada kaka da harshen turanci yace "Aysha anjima bayan isha'i kushirya keda Lailah nakaiku shopping" wara idanu Aysha tayi cikin murna "dagaske Akhie?" harararta yayi "dawasa" dariya mutanen falon sukayi ummie tace "wai nikam tana inane lailan? duk yau banganta ba" kafin kowa yayi magana mussadiq ya amsa da "tana garden" duk kallonshi sukayi harda Deen dake danna wayarshi saida yadago ya kalleshi tashi yayi yafara shirin fita not minding kallon da mutanen falon keyimashi yace "karku sani jira ok?" yafada reffering to Aysha sannan yafita kallon juna mutanen dakin sukayi saikuma sukayi murmushi sannan suka dora da firarsu kowanne da tunanin dake zuciyarshi BAYAN ISHA'I kallonshi yake harya gama shiryawarshi ya feffesa jikinshi da turarrukanshi sannan yajuyo suka hada ido daga gira daya yayi "what?" murmushi Deen yayi "babu komai Kawai am smelling something fishy ne" "to? akan me kenan?" tashi zaune Deen yayi sosai sannan yace "is there something you're hiding to me about Lailah?" wani kallo yayi mashi "as in?" "dazu kace tana garden, ya akayi kasan tana can?" "saboda tare muke acan" yafada yana dan ta6e baki wara idanu Deen yayi cikin murna "as I thought! kenan you two are dating! wow!" harararshi mussadiq yayi "ni nafada maka hakan?" "saika fada? wow amma natayaka murna don Lailah mace ce mai hankali sosai" "ina ruwanka ko mahaukaciya ce? bansan sa ido" yafada yana harararshi riqe baki Deen yayi yace "to? abin yar haka ce" "eh din, ka tsaya kasamu kaji da wancan mai taurin kan taka karka qara shiga sabgata banaso" yafada yana gallamashi hararar wasa nan da nan Deen ya hade fuska jin anta6omashi jewel dinshi "I've warned you times without number karka sake kushemin mata" kallon dage mussadiq yayimashi "da wa yabaka? ji qarfin hali, kama samu tafara kulaka" yafada yana mashi dariyar shaqiyanci "waya cemaka bata kulani? ina ruwanka ma.idan bata kulani? bana hanaka shiga sabgata daita ba?" inji Deen

Chapter 79 of 81