gidansu zee tashigo hospital din
Wata dattijuwa cikin ma'aikatan gidansu zee ta tafito ita da bala driver daya kawota
Hannunta dauke da basket din abinci wanda mummy tasa akawo musu
Saida suka gagaisa da kowa sunamasu ya jiki sannan daddy da zee suka tashi akan zasubi bala ya ajiyesu gida, ita kuma dattijuwar mai aikin saita tsaya dasu
Godiya su matar mallam Nasiru da baaba abu suka shiga yimashi saboda sosai ya nuna hallaci duba da yadda ya tsaya akansu sosai batareda yayi la'akari da matsayinshi ba na babban mutum
Itakau kaka batama san da tafiyarsu ba don tunda tadawo ta zauna ta buga tagumi ba tace komaiba sai Kafe waje guda da ido datayi
Bayan tafiyarsu daddy ne dattijuwar yar aikin mai suna Inna Binta ta gabatar masu abincin datazo dashi, duk sunci sai kaka da sukayi juyin duniyar akan taci amma taqiya haka suka haqura suka kyaleta
A bangaren zee kau koda suka isa gida mummy ce ta tisata gaba tayi wanka da ruwan masu dumi sosai ta gaggasa jikinta sannan ta tilasta mata taci abinci dukda bada wani yawa taciba sannan tabata maggugunanta tasha tasata ta kwanta
Ko minti biyar ba'ayiba da kwanciyarta barcin gajiya ya saceta
Tasha barci sosai wanda ke cike da mafarkan Deen kala2 wanda tana tashi duk ta mance mafi yawa a cikinsu
Sosai taji dadin jikinta yanzu duk wata gajiya ta tafi sai dan abinda ba'a rasaba saikuma murar datake fama daita haryanzu
Miqewa tayi tashiga toilet ta dauro alwalla sannan tazo ta gabatar da zuhr daya wuceta ta dora da asr da ake cikin lokacinta yanzu
Ta dade tana yima Deen addu'ar samun lafiya sannan ta nemi sakayyar allah akansu nurr dasuka ci amanarta da su master dasuka nufeta da sharri
Saida tagama sannan takoma kan gado ta zauna ta lula duniyar tunani
Ahaka wata maid tashigo kiranta inji mummy
Tashi tayi bayan ta yafa veil din gown dinta ta bita
Kamar yadda ta hasaso abinci mummy zata sata ci
Saida ta gaidata mummy ta amsa tana mata ya jiki ta amsa da da sauki sannan mummy ta zubamata farfesun kan rago wanda yaji kayan yaji sosai ta turamata a gabanta
Babu musu tashiga sha don itama tana buqatar abinda zai dan warware mata toshewar hanci datake fama dashi sai gashi kuma ya taimaka sosai don taji dadin jikinta bayan tasha
Haka taita kasa kunne taji ance ta taso su koma asibiti amma shiru
Gashi batada waya yanzu bare takira daddy ta narkemashi yasa akaita gakuma batason ta tambayi mummy, haka taita jira amma shiru
Daga baya ma saita daure taje tasamu mummyn da maganar sai cemata tayi ba yanzu ba
Abin ya 6ata mata rai sosai Hakan yasa takoma daki ta kulle taita kuka
Sai bayan isha'i mummy ta aika agayamata ta shirya suwuce hospital din
Tuni ta mance da zuciyar datake tayi saurin chanzawa tana addu'ar allah yasa su tararda ya farka
Da ita da mummy dawata maid dinsu suka tafi wannan karon ma da abinci a basket
A asibitin taga daddy Hakan yasa tawuce wajenshi da sauri ta Rungumeshi tana tura baki
Dagota dadi yayi yajamata hanci yana tsokanarta yana kiranta cry cry baby ita kuma sai qara zunbura baki take
Binsu mummy dasukayi gaba suma sukayi suka shiga dakin dasu kaka suke
Saida su mummy suka gama gaisawa dasu kaka sannan itama zee ta gaidata cikin jin kunya kuma ba kunyar komai bace saina tasan tanamata kallon itace silar rashin lfyar jikanta
Amsawa kaka da yanzu ta dan kwantar da hankalinta tayi tana tambayar ta ya jikinta, Amsawa tayi da dasauqi sannan itama ta tambayi lafiyar mai jiki itama ta amsa da dasauqi daga nan kowa yayi shiru
Mummy ce ta gabatar musu da abinci, amsa sukayi suna godiya suka ajiye ko don anjima don basu dade dacin abincin da matar mallam Nasiru takoma gida tayi musuba
Sosai mummy tasaki jiki dasu sukaita fira kamar dama sunsan juna, yadda mummy tasaki fuska tanata fara'a yasa suma suka saki jiki daita sunata hira harda kaka dake tofa nata akai akai
Zee kau tun bayan gaisuwarnan bata qara cewa komai ba saima sadda kai datayi tana wasa da zoben hannunta tana sauraronsu
Hankalinta gabadaya baya tareda su kawai dai tana wajen ne amma ko wuqa za'asa mata bazata iya recalling kalma daya a abinda suke cewa ba
Hankalinta gabadaya na kan Deen, idan akwai abinda tafiso yanzu to sanyashi a ido ne
Sun dan jima a Hakan sannan tadan dago taga haryanzu firarsu suke hankali kwanta
Dan Hadiye yawun bakinta tayi sannan tayi gyarar murya wanda Hakan yasa duk suka kallota, sai kuma taji ta takura da kallon amma saita basar tace
"zan dan je wajen daddy" tafada tana qirqirar wani busashen murmushi
Da to saita dawo su baaba abu suka amsamata suna kallonta yayinda mummy batace komai ba sai kauda kai datayi
Tashi tayi tana dan satar kallon mummy sannan tanufi hanyar fita ta fice
Duk binta da kallo sukayi harta fice sannan baaba abu tayi fuska kalar tausayi tace
"baiwar Allah, kai allah ka cigaba da karemu da zuri'armu wannan abu da me yayi kama? Yarinya nitsatsa amma anason wargazamata rayuwa, allah kacigaba dayimana katangar tsari da ire iren wadannan azzaluman bayin naka"
Duk da amin aka amsa banda mummy da tadanyi murmushi kawai
Wai nitsatsa, Yarinyar da shegen rawar kai yayima yawa wataqila garin Hakan taje ta tsokano ma kanta su don ita haryanzu bata yarda haka kawai zasu nemi wargazamata rayuwa ba
Nan akalar hirar tasu takoma kansu, inda suketa addu'ar tonuwar asirin su master da kuma yin allah wadai dasu sumee dakuma fatan waraka wa Deen
*ZEE*
Ajiyar zuciya ta sauke bayan tafito tana dan juya manyan idanunta
Wawaigawa tayi don ganin inda zata hango su daddyn amma bata gansu ba
Har tayi hanyar office din Dr dinsu saikuma tafasa
Dawowa tayi ta nufi recording room dasuka shiga dazun dasafe
Saida tayi knocking sau hudu sannan aka bude kofar mutumin wata mata ta bayyana
Dan murmushi matar tayimata tace "hi"
Itama maida mata murmushin tayi tace
"hy"
"how may I help you miss?" inji matar tana kallonta
Rasa abinda zatace tayi Hakan yasata fara kame2
Ganin Hakan yasata cewa tashigo ciki sai suyi maganar
Shiga zee tayi tana wondering ina wancan mutumin yake na dazun?
Saida ta zauna sannan matar tace
"yes miss? How may I help you?" inji matar tana folding hannunta tana kallonta
Taking deep breath tayi sannan tace
"amm.. Dama sonake ayiman viewing wani dake kwance a room 12 ne please, patient ne amma anhana shiga ganinshi shine nakeso please kiyimin viewing dinshi"
Shiru matar tayi tana kallonta na dan wani lokaci sannan tace
"am sorry, amma ba'a zuwa ganin mutum anan, kiyi hqr kijira har abaku izinin shiga ku ganshi Hakan ma zaifi"
Shiru zee tadanyi tana kallon zoben hannunta sannan tasake dagowa ga matar
"please, kawai ganinshi zanyi koda flashing dinshi zakiyimin nadan ganshi ki kashe, I want to know how he is please" tafada pleadingly
"idan kinason sanin yadda yake likitanshi zakije ki nema ba nan ba, am sorry but it's strictly against the law, da ana yin haka da kowa ma nan zaizo don ganin nashi, kiyi hqr please ki jira har lokacin da za'a baku izinin shiga ganinshi, am sorry"
Kada kai zee tayi a sanyaye tana qoqarin maida hawayenta sannan ta miqe tsaye
"thank you" tafada ta nufi kofa
Binta da kallo matar tayi har Saida tadora hannu akan handle zata murda
"wane ward yake?" zee ta tsinkayi muryar matar
Juyowa zee tayi da sauri kamar dama jira take tace
"12... Ward 12"
Murmushi matar tayi tace
"ok zo kiganshi na seconds biyar kiwuce kafin azo akamamu anan babu ruwana" tafada tana operating din mouse din hannunta
Da sauri zee tadawo ta zauna tana murmushin jindadi dabatasan tanayiba
Kunnomata matar tayi tayi mata zooming dinshi sannan ta kaucemata don tagani
Tsayawa zee tayi tana kallonshi
Kwance yake kamar dazu haryanzu abin oxygen a hancinshi Saidai yanzu babu qarin ruwa a hannunshi da alamu an cire
"Don.. Allah ma, kidanyimin zooming face dinshi" tafada cikin sanyayar murya
Murmushi matar tayi tayi yadda tace, nan take fuskar Deen yafito daro2 a screen din majigin
Kafeshi tayi da idanu tanajin zuciyarta na kumbura don shauqi
Dukda abin oxygen din ya kare kaso mai yawa na fuskar Hakan be hanata ganin yanda fuskar tayi fayau ba
Idanunshi a lumshe sai lashes dinshi dasukayi zara zara suka hade dajuna sanadiyar lumshe idanun dayayi, ga girarenshi masu cika da baqi dasuka kusan hadewa
Maida kallonta tayi akan ciwon dake akanshi wanda aka nannade da banda sannan akan tulin lallausan sumarshi dake tuje as usual
Kafeshi da idanu tayi bako kyaftawa tanajin kamar zai bude idanu at any moment
Batasan iya lokacin data dauka a haka ba sai jitayi an dafa kafadarta hakan yadawo da ita daga duniyar kallonshi
Dariya matar tayi tace
"haba madam? Daga ganin marar lafiya saikuma a bige da kuka?"
Sai a sannan tasan ashe kuka takeyi
Hanki din hannunta tasa tana tsane fuskarta tana murmushin jin kunya
"to ai kiganshi yanzu, 5 seconds na neman zama 5 minutes, allah yabashi lfy insha allah very soon za'a barku kushiga wajenshi kiyita ganinshi babu mai takura maki" tafada tana Dariya
Dan murmushin kunya tayi tana tashi
"thank you very much" tafada tana murmushi
"Don't mention.. Amm, nace dan uwanki ne?" tafada tana qumshe Dariya
Kada kai kawai zee tayi sannan ta nufi hanyar fita tana mata sai anjima
Cikin Dariya matar tace
"to allah yaqara donqon zuminci, allah kuma yaqaro afuwa"
Itadai zee fitowa tayi murmushi a fuskarta
Tana fitowa daidai su mummy ma na fitowa da niyyar tafiya gida Hakan yasa suka wuce bayan itama zee din tayimasu kaka sallama suka shige mota harda daddy suka wuce gida
*BAYAN KWANA UKU*
Cikin kwanakin nan abubbuwa da dama sunfaru ciki harda nasarar damqe su master da akayi a gidan wani abokin huldar kayan mayensu inda wani dan leqen asiri yakawoma yan sandan rahoto sukuma basuyi wata wata ba suka yiwa wajen tsinke inda sukayi ramm da dukkansu aka kwashesu sai magarqama
Ciki kuma harda sauqin da Deen yasamu dukda ba farfadowa yayi ba Amma an chanza mashi daki inda ana iya shiga aganoshi Saidai kwata2 ba'ason ayi hayaniya
Tsakanin zee da kaka saina rasa wanda yafi farinciki da wannan cigaban dukda ita zee nata farincikin be bayyana ba kamar na kaka amma a badini tafi kaka murna da Hakan
Kullum sai sunje asibitin Sau biyu, dasafe da kuma bayan isha'i
Sosai su daddy ke hidimtamasu kaka wajen abin da yashafi lafiyar Deen don haryanzu ko sisin kaka beyi ciwon kai ba da sunan maganin Deen
Hakan yasa kaka ke ganin girmansu sosai don ita kaka dama batada babban masoyin da yawuce mai nunawa dan jikallenta qauna
A bangaren zee kau duk lokacin dasuka zo daga gaisuwa da tambayar mai jiki bata qara cewa komai sai kallon Deen da zata cigaba da yi
Su kaka da mummy sunsha kamata ta kafeshi da ido dukda yadda take kallon a fakaice
Izuwa yanzu babu wannan abin oxygen din a hancinshi Hakan yasa fuskar shi ke afili Saidai tayi fayau taqara haske lips dinshi kuma sunqara pink sosai
Yau sunyi baqi yan dubiya sosai ciki harda yan makarantarsu dama mallamai, Cikin mallaman harda mr ibrahim
Rasa inda zata sa kanta tayi don kunya lokacin da mr ibrahim ya yimata jaje da fatan Allah ya tsare gaba
Haka dai ta amsa da amin batareda ta iya hada idanu da ko daya daga cikin su ba
Haka akaita zuwa ganinshi, a yan kwanakin nan tasan Deen mutumin mutane ne don sai zuwa dubanshi ake takoina kuma duk wanda yazo da kalar yabon da zaimashi na kyawawan hallayenshi Hakan yasa taji ya qara burgeta akan nada kuma take kwadayin itama watarana tasamu mutane masu yaba hallayenta, wadanda zasu nuna damuwarsu sosai idan wani abu ya sameta
Ahmad mai adaidaita ma yazo dashi da matarshi ganin din, Saidai lokacin dasukazo su zee basukai ga zuwa ba saida sukazo sannan aka gayamasu
Zaune suke suna dan fira jefi jefi
Kaka ce da baaba abu sai mummy da zee a dakin
Can su ukun ke firarsu yayinda zee ke gefe tana yan danne dannenta a sabuwar wayar da daddy ya siyamata tanayi tana dagowa tana kallon Deen lokaci bayan lokaci
Dagowa tasakeyi ta dan kalleshi saitaga kamar yatsun hannunshi sun dan motsa
Qara dan waro idanunta tayi tana kallon hannun sannan ta maida kallon ga fuskarshi amma bataga yakuma motsin ba
Bata Janye idanun ba akanshi ta cigaba da kallonshi babu ko blinking don idan idonta ba qarya sukayi mata ba tabbas taga yatsunshi sun motsa
Qara girma idanunta sukayi ganin idanunshi sunfara motsi a runtsen dasuke
Cigaba da kallonshi tayi idanu a ware bata ko kyaftawa don gani take idan ta kyaftasu zataga akasin abinda take gani yanzu
Cigaba na motsi idanun sukayi da alama soyake ya budesu
Can eyelids din suka fara rabawa idanun suka shiga budewa ahankali
Biji2 yafara gani Hakan yasa yashiga kyafkyafta idanun
Ahankali ganin nashi yafara clearing tun yana ganin abubbuwa blurring har ganin nashi yadawo clearly
Be sauke idanunshi koina sai cikin nata large pure white eyes din... âœï¸
Ummin fasihu 🧚ðŸ»â€â™€ï¸?
8/2/21, 9:35 PM - BuhainatðŸ˜: *ðŸ™ðŸ»â€â™‚ï¸DEEN ðŸ™ðŸ»â€â™‚ï¸?*
*026*
Cak komai nata ya tsaya ta kafeshi da idanu kamar yadda shima nashi ke kafe da ita
Sotake ta tashi tayi ihun murna ta nufeshi ta kamo hannunshi tayi mashi magana amma duk ta kasa, ko kyafta idanu batasonyi don gani take data kyafta ta bude zataga idanunshi a rufe kamar kullum
Mummy ce kema Zainab magana akan ta miqo ledar kusada ita amma shiru ko motsawa batayi ba
"bakiji ba?" inji mummy tana kallonta bama ita kadai ba harda su kaka
Still bata motsaba ko ta nuna alamun taji don bama lallai ne intaji dinba
Ganin ta zaune ta kafe wuri guda da ido yasa suma bin inda take kallo da ido
Atare duk suka miqe kowa bakinshi bude
"Deen!!" Duk suka fada atare
Kaka ce farkon qarasowa gabanshi tana riqo hannunshi cikin tsananin farinciki
Sai a lokacin ya janye idanunshi da basu ida washewa ba daga kan zee ya maidasu kan kaka dake kuka da Dariya lokaci guda
"kyakyawa na, katashi? Alhamdullilah! Alhamdullilah! Allah mun gode maka, allah mun gode maka" tafada tana Rungumeshi qamm
Lumshe oily idanunshi dasuka dan dishe yayi ya bude yana qara narkewa a wuyan kaka
Dago idanunshi yayi a hankali ya saukesu akan zee da yanzu take tsaye tana kallonshi itama idanun na kyallin hawayen dasuka taru aciki
"wai bazaki tafi ki kira Dr din bane?" inji mummy ganin tayi tsaye taqi gaba taqi baya
Magana mummy ya dawo da zee daga duniyar kallon Deen tayi saurin Juyawa ta nufi kofa
Binta da kallo Deen dake rungume still ajikin kaka yayi kamar yau yafara ganinta
Harta dora hannu a handle din kofar saikuma taqara juyowa ta kalleshi
Lumshe idanu yayi ya qara budesu akanta wani slight murmushi wanda yayi mugun tsayawa aran zee ya su6ucemashi
Saurin bude kofar tayi tafita ta rufo
Saidai maimakon tayi gaba saita koma ta jingina da kofar ta Lumshe idanu wanda Hakan yaba hawayen dasuka taru a idanunta damar gangarowa
Ahankali ta silale awajen tana dafa saitin zuciyarta datakeji tana kumbura da sacewa
Hawaye sosai take wanda ita kanta batasan na meye ba yayinda murmushin Deen na yanzu yaqi 6acemata a idanu
Rabashi kaka tayi da jikinta ta dago fuskarshi tana shafawa tana murmushi da hawaye a lokaci guda
Shima mayar mata da martanin murmushin yayi yana Lumshe idanu tareda budewa
Suma su mummy qarasowa sukayi cikin farinciki suna miqa godiya ga Allah (s.w.t) daya tasheshi
"sannu son, ya jikin?" inji mummy tana kallonshi tana kuma qara hango zallar qaunar da kaka kemashi
Dan kafeta da idanu yayi saikuma ya Lumshe idanu ya bude alamun da sauqi
Itakau baaba abu cewa tayi
"Allah mun godemaka, raggon maza an leqo lahira an dawo, to ya hanya?" tafada cikin sigar tsokana don dama haka takemashi
Itama murmushi yadanyi mata sannan ya maida kallonshi kan kaka da haryanzu ta tisashi gaba tana kallo kamar tasamu t.v
Murmushi yasake mata Hakan yasa takai hannunta a kumatun haggunshi tana shafawa, Lumshe idanu yayi ya sake budesu yana son dago hannu ya dora akan nata dake dafe da kumatunshi amma yakasa don kwata2 beda wani qarfi ajikinshi
"kyakyawa na, nayi zaton tafiya zatayi ka barni, nayi zaton barina zakayi ni kadai a duniyar nan, da katafi ka barni da bansan yadda zan kuma cigaba da rayuwa babu kai ba, rayuwa batareda kai ba rayuwar kunci ce Hade da dawwamammiyar kewa"
Girgiza mata kai yayi ahankali alamun ta daina kuka Hakan yasa taqara rungumeshi tanajin farinciki na huda zuciyarta takoina
Share qwalla mummy da baaba abu sukayi na tausayinsu, mummy na qara jingina soyayyar dake tsakanin wannan kakar da jikan
Jin shirun yafara yawa yasa mummy cewa
"bari naje na dubo likitan narasa abinda yasa basu qarasoba Tundazu"
Bata jira komai ba tanufi kofa
Murda handle din tayi ta tura sai taji abu ya tokare kofar cikin mammaki taqara turawa taji har lokacin atokare
Cikin mammaki tace
"ikon allah" taqara turawa wannan karon da qarfi
Firgigit zee ta dago daga hada kanta da gwiwa datayi
Jin ana turo kofa tabayanta yasata saurin miqewa tana ja baya
Gani tayi an bude kofar mummy ta leqo
Wara idanunta zee tayi don sai yanzu ta tuna abinda ya fiddota
Saurin yin u-turn tayi ta nufi hanyar dazata sadata da office din Dr din
Binta da kallo mummy tayi baki sake sannan ta ida fitowa itama ta nufi hanyar office din Dr din don bazata qara jiran gawon shanu ba
Tana shawo kwanar dazata sadata da office din Dr din sukayi kici6us da Drn da zee
Batabi takan zee ba tace ma Drn
"yauwa Dr, yafarka yanzu yanzunnan"
"ok muje mugani" inji Drn
Nan tajuya suka koma ta hanyar dasuka taho zee a bayansu
Shigowarsu yasasu duk dagowa suna kallonsu
Qarasowa Drn yayi ciki fuska a washe
"masha allah, alhamdullilah! You're back" yafada yana dan dafa goshinshi
Murmushi kawai Deen yayi kamar yadda yake tun lokacin daya tashi
Ciro abin wuyanshi Dr din yayi yasa a kunne sannan ya dora a qirjinshi yana feeling heartbeat dinshi
Duk tsit akayi a dakin ana kallonsu kowa fuska bayyane da farinciki
Saida likitan yagama duka gwaje gwajenshi sannan juyo gasu kaka, kaka bakinnan kamar gonar auduga
"to kaka ina tayamu murna, yatashi kuma alhamdullilah jiki da sauqi sosai sai dan abinda ba'a rasaba, yanzu ayimashi brush asamar mashi abu mai dan ruwa ruwa da zafi zafi yasama cikinshi
Ayanzu beda qwarin jiki sai ahankali qarfinshi zai dawo kuma don Allah banda hayaniya, please"
Duk amsa mashi sukayi da insha allah
Yan rubuce rubuce yayi a memo din hannunshi sannan yace
"abashi wani abin yasa a cikinshi kafin indawo mashi da maggungunan dazai dinga sha, Allah yaqaro afuwa"
Duk da amin suka sake amsawa sannan yafita
Waya mummy ta dauka bayan fitar Dr itama tafita don kiran daddy
Ita kuma kaka ta shige toilet don tarar ruwa itakuma baaba abu tafita sai dakin ya rage daga zee dai Deen
Kafe juna da ido sukayi expressionless
Ahankali Deen ya dago hannunshi ya miqomata yana dan murmushi
Hakan yaqara tsumata tayi saurin qarasawa wajenshi ta kama hannun ta damke gaam takifa fuskarta akai tana shesheka
Binta kawai yake da kallo not saying anything
Saida tayi mai isarta sannan ta dago da watery eyes dinta ta kalleshi taga shima ita yake kallo
"am so sorry.. Am sorry for everything, nina jawo komai, nakusan sanadin rayuwarka, daka tafi da bansan yadda zanyiba don bazan ta6a yafewa kaina ba, am sorry for causing you pain upon pain, forgive me.. Please" ta qarashe tana lumshe idanu hawayenta na gangarowa
Dora dayan hannun yayi akan nasu dake wuri guda sannan ya girgiza mata kai yana murmushi saikuma ya bude baki kamar zaiyi magana amma taqi fitowa
Ganin Hakan yasata cewa
"menene? Baka iya magana ne?"
Murmushi yayi ganin yadda take tambayar cikin damuwa saikuma ya nunamata cikinshi yana yamutsa fuska
Ganin Hakan yasata saurin tashi tana raba hannunsu tanufi wani flask dake kan wata locker wanda dama ana ajiyeta ne da ruwa ciki incase ya farfado don dama Dr yariga ya fadamasu zai iya farfadowa a kowanne lokaci
Tana cikin fiddo cups din kaka tafito hannunta riqeda bowl da dogon kofi dake dauke da ruwa
Daidai nan baaba abu tadawo ita da mummy dasuka Hade a waje
Maclean din da baaba tasiyo ta matsa a sabon brush data siyo ta miqama kaka da zatayi mashi brush
Daukan cups din zee tayi taje ta daurayo sannan ta dawo ta jawo flask din da kayan shayin dake cikin leda tashiga hadawa
Sosai tasa ginger powder aciki tayimashi hadin mai citta
Deen da kaka kema brush sai 6ata fuska yayi kaka nata qara lalla6ashi har aka samu aka gama brush din
Daidai nan zee tagama hada tea din taba kaka
Cikin jindadi tashiga sama zee albarka sannan tazo tafara ba Deen din shayin
Ana haka daddy yashigo tareda Dr
Tashi zee tayi tanufi daddy da sauri ta fada jikinshi cikin tsananin farinciki
Shima daddy riqeta yayi fuskarshi awashe suka ida qarasowa ciki
Deen tunda zee ta ruga wajen daddy yake binsu da kallo harsuka qaraso wajenshi, yama bar amsar shayin hankalin yakoma can
"masha allah, sannu kaji?" inji daddy cikin kulawa
Kada mashi kai Deen yayi yana dan murmushi sannan ya kalli zee da itama murmushi yaqi barin face dinta
"Allah ya sauwaqe ya qara lafiya, allah yakuma kiyaye gaba" inji daddyn
Duk da amin suka amsa banda Deen din dayayi murmushi kawai
"Gaskiya kayi mana hallacin dabazamu iya sakamaka da komai ba, ba don kai ba da yanzu wani zancen ake, babu abinda zamuce illah allah yasaka da alhairinsa" inji mummy tana murmushi
"hakane kam, babu abinda zamuce face allah ya sakamaka da alhairi, ka ceci rayuwarmu don rayuwar Zainab tamuce idan muka rasata komai na iya faruwa, words can't express how gratefull we are kuma insha allah saimun tabbatar an hukunta wadannan shaidanun daidai da abinda suka aikata don yanzu haka magana takai kotu on monday za'a fara zama" inji daddy
"Allah yakaimu, ai abinda yakamata kenan dama, yaran yanzu ka haifesu ne baka haifi halinsu ba, kuduba qannanun yara irin wadannan sun iya munafurci ni Zainabu, kuma wai qawayenta ne na qut da qut, duniya ina zaki damu? Idan wadanda ka yarda dasu suna maka zagon qasa ta bayan fage dawa zaka yarda ni Abu?" inji baaba Abu tana riqe ha6a
"shiyasa ai qawayen basuda wata amfani, ni dama basuyi minba tunda nafara ganinsu nakuma yimata magana amma taqi rabuwa dasu ai ga irin abubbuwan danake guje miki nan kinfara gani" inji mummy tana eyeing dinta
"wlh kam, qawayen yanzu ko bam (bomb)? Ke kina nan kin saki jiki dasu kina zama dasu da zuciya daya amma su basuda maqiyi daya wuce ke kuma basuda burin daya wuce suka bayan ki, ai da akayi abota ba wannan zamanin ba" inji kaka tana ajiye kofin shayin ganin besha
"To allah ya kyauta, yaranma naji ance cocaine dealers ne suna safarar miyyagun qwayoyi da hodar iblis yanzu haka da akaje gidan da aka kamasu akayi bincike saigasu nan birjik anata zaqulosu yanzu kunga abin yaqara tsawo ga wannan ga wancan" inji daddy
Riqe ha6a baaba abu tayi tace
"danqari! Ashe yan kwaya ne? Ca6 aikau sun aikata tunda dasun shawu suka bugu tafara gayamasu qarya kome yazo kansu yi zasuyi"
"To allah dai yashiryasu idan masu shiryuwa ne" inji kaka
"fatan kenan" inji mummy tana Kada kai
Dr ne yaqara duba Deen sannan yabasu maggungunan shi bayan ya gayamasu yadda qa'idar shan yake
Da zasu tafi zee jitayi kamar karta tafi kamar tayita zama anan
Don dole tabisu daddy tana waigen Deen dashima yake kallonta yanajin kamar karta tafi
Ranar nan zee ta dade batayi barci ba, duk motsin da zatayi saiya fado mata arai duk kuma lokacin daya fadomata a rai saita tsinci kanta da murmusawa
Barci 6arawo ne ya sadado batareda ta farga ba ya saceta
A bangaren Deen kuwa saida ya rama sallolin da ake binshi cikin daren nan sannan yasha maggungunanshi wanda Dakyar aka samu ya hadiyesu don dama shi kwata2 beson magani duk lokacin dazaisha magani sai kaka
All Chapters
Chapter 1
Chapter 2
Chapter 3
Chapter 4
Chapter 5
Chapter 6
Chapter 7
Chapter 8
Chapter 9
Chapter 10
Chapter 11
Chapter 12
Chapter 13
Chapter 14
Chapter 15
Chapter 16
Chapter 17
Chapter 18
Chapter 19
Chapter 20
Chapter 21
Chapter 22
Chapter 23
Chapter 24
Chapter 25
Chapter 26
Chapter 27
Chapter 28
Chapter 29
Chapter 30
Chapter 31
Chapter 32
Chapter 33
Chapter 34
Chapter 35
Chapter 36
Chapter 37
Chapter 38
Chapter 39
Chapter 40
Chapter 41
Chapter 42
Chapter 43
Chapter 44
Chapter 45
Chapter 46
Chapter 47
Chapter 48
Chapter 49
Chapter 50
Chapter 51
Chapter 52
Chapter 53
Chapter 54
Chapter 55
Chapter 56
Chapter 57
Chapter 58
Chapter 59
Chapter 60
Chapter 61
Chapter 62
Chapter 63
Chapter 64
Chapter 65
Chapter 66
Chapter 67
Chapter 68
Chapter 69
Chapter 70
Chapter 71
Chapter 72
Chapter 73
Chapter 74
Chapter 75
Chapter 76
Chapter 77
Chapter 78
Chapter 79
Chapter 80
Chapter 81
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 18 Chapter of 81