isa hakanan, mushiga ciki, sun kwaso gajiya zaku qaramasu wata gajiyar" inji ummy
gabadaya suka dunguma suka nufi ciki Zainab still a maqale jikin Daddy
binsu da kallo Aymaan da babu wanda yayi ta tashi yayi saiya girgiza kai yanufi booth yafara sauko kayan ciki
muryar batool ce ta katseshi daga abinda yakeyi
"oyoyo Akhie! ashe harda kai aka dawo? wlh nama manta dakai akayi tafiyar sai yanzu dana hangoka"
wata lafiyayyar harara ya makamata ya cigaba da fiddo kayan
"da fatan dai kayomin tsarabobi na don ina ganinka naji babu Abinda nake kwadayi kamar goruba"
daukar jakka daya yayi ya rataya yajawo dayan trolley din yanufota
juyawa tayi saurin yi tanufi cikin gidan dagudu don tasan Idan ya kamata saita gane kurenta
a tsaitsaye a falo batool ta taddasu hakan yasa ta qaraso da sauri jim kadan saiga Aymaan shima yashigo
bude baki ummy tayi sannan tace
"Allah sarki, wlh na manta dakai"
6ata fuska Aymaan yayi yaqaraso dakin yana cewa
"ai dama nasan ba'aji dani"
dariya duk sukayi daidai lokacin zee ta dago suka hada ido da Aymaan
wani kyakyawan murmushi tasakar mashi wanda yakusan melting zuciyarshi, hakanan tayi hasashen qila wannan shine tsarabar dayace zaiyi mata wato ya kawomata su Daddy
shima mayarmata martanin murmushinta yayi yana jin wani sanyin farinciki na ratsa zuciyarshi sannan yayi hanyar sama yana cewa
"to nidai na haye kafin gajiya ta kadani"
Jin hakan yasa Abbu cewa suma su Mummy arakasu masaukinsu su Dan huta kafin sufito cin abinci
su zee suka rakasu har masaukin nasu dayasha gyara sai qamshi yake
badon zee tasoba suka juyo suka barsu don sudanyi freshning up
basu dade ba suka sake dawowa main falo din inda suka dunguma gabadaya sukayi dining inda aka baje kolin girke girken da akayimusu kowa yashiga kwasa
fira ce sosai ta 6arke a tsakanin wadannan families din biyu, hira suke cikin raha da barkwanci, zee haryanzu tana maqale kusada daddynta murmushi yaqi barin fuskarta shima aymaan sosai ake firar dashi don nan take fara'arshi da surutunshi yadawo kamar bashine yakoma wani dunkum ba a Nigeria
sun raba dare sosai atare suna maida yadda akayi saida sukaga barci yafara cin qarfinsu sannan suka haqura kowa yaje ya kwanta.
*WASHEGARI*
Ranar fashin school sukayi sukaqi zuwa sai sukayi qaryar basuda lecture ranar
Haka sukayi zamansu suna aikin bude tsarabobin dasu Mummy sukayi musu suna hira cikin nishadi
Mummy kau dik inda zee ta gifta saita bita da kallocikin sha'awa don taga zee taqara hankali sosai kamar ba itaba ga kuma tausayinta datakeji a qasan zuciyarta don sosai taji dadin yadda ta taimakama Deen batareda tayi la'akari da Abinda yayi mata ba, that's shows tanada good heart.
sai bayan asr Ahmad shima yaduro gidan.
dama jiya tun a airport suka rabu shi yawuce gida kasancewar dare yayi lokacin kuma dama yayimusu alqawarin zai dawo yau don akwai zaman da Daddy keso suyi ayau din.
bayan sun gama gaigaisawa cikin mutunci shima ya zauna aka dasa firar daga inda ta tsaya.
can Daddy yayi gyaran murya wanda ya tattaro hankalin kowa zuwa wajenshi suka zubamashi ido cikin son jin mai zaice
"to Alhamdullilah, muna godewa Allah daya hadamu cikin aminci da qoshin lfy muna kuma roqonshi ya cigaba da wanzarda farinciki da hadin kai atsakaninmu"
"wannan zaman namu yanada.dalili koko ince zuwanmu qasarnan ma gabadaya, wasu acikinku sunsan dalilin wasu kuma basu saniba ammazasu sani very soon inshaAllah.
amma dafarko zanfara nuna jinjina da yabawa ga jajircewar wadannan samarin biyu wajen qoqarinsu na aikin qwarai dasuka sanyo gaba, haqiqa kun cancanci yabo akan jarumta da nargartattun halaye naku kuma muna fatan Allah yabiyaku yasaka maku da alhairinsa"
duk da Amin aka ansa wasu kuma kamar irinsu zee da batool basusan inda zancen yadosa ba haryanzu
"Aymaan da Ahmad sunje Nigeria akan wani aiki, aikin da babu mai iya biyansu sai Allah, kuma muna fatan Allah yabamu nasara yakawo mamu warwarewar wannan al'amari.
sunyi mana bayani, bayanin da nasan kowa anan yasanshi kuma mun gamsu hakan yasama muma muka shirya mukazo nan don ida warware matsalar dukda badamu aka faraba"
zee dai kallon Daddy take very confused don haryanzu takasa gane inda ya dosa
kamar ance ta dago kai sai sukayi ido hudu da Aymaan dake kallonta tundazu
wani guntun murmushi yaimata kawai ya dauke kai
"ga wadanda suka sani dakuma wadanda basu saniba ina farincikin sanardaku bayyanar KAMALDEEN MUHAMMAD wato DEEN"
wani irin bugawa zuciyar zee tayi har saida ta dafe saitin zuciyar tana miqewa tsaye batareda tasaniba
gasping batool tayi tana wara idanu kamar zasu fado cikin tsananin shock
murmushi Daddy yayi yana kallon zee dake tsaye haryanzu hannunta a saitin zuciyarta idanunta a ware tana kallonshi
"yes daughter, Deen is back. Deen yadawo, yana Nigeria. can su Aymaan sukaje kuma sun ganshi sunyi magana dashi"
girgiza kai zee take unbelievabling tanajin komai a mafarki tanason yin magana amma takasa
"eh Zainab, Deen ya bayyana, munsan inda yake. yana Abuja yazama mawaqi, munso mugayamaki tunda wuri amma muka yanke shawarar fara confirming.komai sannan, Deen ya bayyana, na ganshi Aymaan ma ya ganshi, munyi magana dashi"
cigaba da girgiza kai zee tayi don sam zee bata yarda ba, dole wani suka gani, wani mai kamadashi kokuma Mussadiq, yes qila Mussadiq suka gani sukayi tunanin Deen ne
"m..mussadiq ne" tafada cikin wata murya mai rawa sosai
"A'a Zainab, ba Mussadiq bane, Deen ne. look.. duba dakanki kigani" yafada yana fiddo wata laptop yabude
duk zubamashi idanu sukayi in curiosity harya gama yan danne dannenshi ya juyomasu ya ajiye akan stool din kusadashi yayinda image din laptop din yafito tarr kowa na falon nagani
waqa ce ta video
da sajenshi tafara tozali kasancewar gefen fuskarshi akafara haskowa
bugun zuciyarta ne ya ninku lokacin da aka hasko pink lips dinshi wadanda bazata ta6a qin ganesu ba daidai lokacin lips din suka fara motsawa cikin salon waqa
_karki barni.. sahibata_
_karki qini... ki fahimta_
_sai dakee... zani huta_
_zuciyata ga kece ta lalla6o_
_ta amince ki maidata yar dako_
_kinga qaunarki taimun riqon la6o_
_wani reshe ya kama ya jijjigo_
zee batasan sadda takoma kan kujerar data tashi ba jagwab lokacin datayi tozali da full face din Deen din.
_kingani ban iyawa da So haka_
_magani zaki ban don na waraka_
_kinga ya maidani wani sa d'aka_
_yafi qarfina sai yaita ha66aka_
_tunda nabaki raina da zuciyaa!_
_me kikeso nayimiki zan iyaa!_
_yau dake gobe na shaida tunjiyaa_
_kinga nazam kamar marar lafiyaa_
_zuciyata ❤️ tanaimun bugun tara💗_
_gashi nikuma naqi na haqura_
_dukda nasha wuya bani daddara_
_kai bala'i na So🤍 nada takura😭_
_wai ina kika jene masoyiyaa!_
_nayi nemanki naqara tambaya!!_
_har wadansu sunaimini dariya😔_
_ni bazan daina sonki ba kinjiya_
_dukda yasani ban jiyo Dan kira_
_tallafa min kissamini lafiya🙏🏻😭_
(sai dake ? hamisu breaker)
Ummin fasihu🧚🏻♀?
8/2/21, 9:43 PM - Buhainat😝: *🙍🏻♂️DEEN🙍🏻♂?*
*079*
*wannan page din nakine takwara, nagode da ziyarar jiya fatan kun koma gida lafiya🥰*
Rufe baki batool tayi da hannunta dake dan 6ari idanunta cikeda kwalla, she's shocked Idan akwai kalmar datafi shock ma tayishi.
she can't believe Deen ne wannan, she can't believe Deen is back!
dauke idanunta tayi daga screen din laptop din takalli saitin zee
haryanzu zaune take inda take motionless, idanunta dasuka sauya launi kafe a screen din babu ko kyaftawa
haka suka cigaba da kallo har waqar taqare
kowa Juyowa yayi yana kallon zee don ganin reaction dinta amma haryanzu tana a yadda take yadda kasan statue
"munfara ganinshi ne ta media, mawaqine sosai wanda ke zamani. yana xaune a Abuja kuma acan yake gudanar da rayuwarshi, wannan tafiyar ma damukayi duk don muganshi ne kuma muga inda yake yadda komai zaizo mana da sauqi" inji Ahmad yana kallon zee
Aymaan kau hannunshi ne rungume a qirji ya sadda kai qasa bakama ganin fuskarshi bare kasan halin dayake ciki.
kuka ne ya kufcema batool tayi saurin rungume zee dake gefenta tanayi ahankali
"Zee Deen is back"tafada cikin rawar murya tana qara qanqame zee dahar yanzu batayi motsiba
ganin batace komai ba yasa batool dan sakinta ta dago ta kalleta ganin still idanunta na saitin laptop saita sa hannu tajuyo fuskar saitinta
"kinji zee, Deen is back, say something. abun farinciki ne right? abun farinciki ne" inji batool tana hawaye sosai
kallonta zee kawai keyi batace komai ba sai gangarowa da hawayen dake maqale a idanunta sukayi
ahankali tasa hannu ta janye hannayen batool daga riqon datayiwa fuskarta ta miqe ahankali
kowa dagowa yayi yana kallonta harda Aymaan da shima idanunshi sun chanza launi sosai
ahankali tafara takawa ta wuce ta nufi stairs
ahankali Aymaan daya lura da yanayin tafiyarta ya miqe idanunshi akanta
takai bakin stairs ta daga kafa kenan zata fara taka stairs din wani wawan jiri ya dibeta tayi baya baya
Aymaan da dama kamar yasan da hakan yayi wuff cikin zafin nama ya qarasa kafin takai qasa ya tarota tafado jikinshi har yana durqushewa akan gwiwa daya
farr farr idanunta keyi kamar mai qoqarin budesu yayinda sukuma suke rufewa
kafe fuskarta Aymaan yayi na kallo yana jin yadda jijjiyoyin kanshi ke tashi rudu rudu
"Zainab.." yafada ahankali kamar a rad'a
"Deen..." itama tafada ahankali daidai lokacin da idanunta suka ida rufewa ruff
tsayawa yayi yana kallon fuskarta kawai batareda ya iya ko motsawaba
kingin yan dakin ne suka qaraso wajen a gigice kowa na kiran sunanta.
dagudu batool tadawo hannunta riqeda bottle water ummy ta amsa aka bude murfin aka shashafamata ruwan a fuska amma shiru
qara yayyafamata sukayi nanma ko motsi batayi ba
ganin hakan yasa Aymaan dake jin kanshi kamar zai rabe gida biyu don sara yunqurawa ya tashi daita a hannunshi
hanyar fita falo yanufa hakan yasa Ahmad saurin ficewa yanufi parking space.
kafin Aymaan ya isa harya bude mashi back seat Aymaan ya sunkuya ya sakata ciki sannan ya nufi gaban motar yana barma su ummy kofar bayan bude don su shiga.
ummy da Mummy ne suka shiga bayan while Aymaan da Ahmad ke gaba sukuma Daddy suka hau dayar motar tareda batool daketa qoqarin dakatar da hawayenta
cikin qanqanin lokaci suka fice daga gidan suka nufi hospital din da Aymaan ke aiki.
babu 6ata lokaci aka kar6eta aka kuma shiga bata taimakon gaggawa
Aymaan baya cikin likitocin dake dubata don suna kaita dakin da aka kwantar daita yafice daga asibitin
su ummy sune suka zauna waje jugum kowa abin duniya ya dameshi
ba'a dade ba akafara kiraye kirayen sallar magrib hakan yasa duk mazan suka wuce massalaci suka bar matan anan.
dawowarsu daga massalacin yayi daidai da fitowar likitocin daga dakin da aka kwantar da zee
saurin qarasawa sukayi suna tambayar yadda ake ciki
ataqaice suka amsamasu yanzu komai yayi daidai amma zasuso ganin mahaifanta personally a office
Abbu da Daddy suka bisu suka wuce office din.
bayani marar dadi likitocin suka basu na hawan jinin zee daya qara tashi ya hau sosai
sunkuma sanar dasu damuwa tayimata yawa har abin na neman ta6amata zuciya
shawarwari suka basu na yadda yakamata su bar barinta tana shiga damuwa domin hakan ba qaramin illa bane agareta yanzu
sannan sukace zasu daurata akan magani wanda zai taimaka mata sosai akan halin datake ciki.
sosai jikinsu yayi sanyi sunajin badadi sosai
Abbu ne yayi qarfin halin tambayarsu halin datake ciki yanzu sukace yanzu sun shawo kan komai don yanzu haka barci take sanaddiyar allurai da akayimata.
sosai suka qara yimasu bayanai akan ciwon zee din da shawarwaru sannan suka shaidamusu mutum daya kawai za'abari yayi jinyarta kingin saidai sukoma gida.
Tare da likitocin suka sake fitowa daga office din suka nufa ward din da aka kwantar da zee din gabadaya
a kwance suka taddata tana sauke numfashin barci ahankali hannunta daure da drip
babu wanda be tausayamata ba a wannan halin don she looks so pale kamar wadda tayi wata tana jinya.
basu dade ba aciki suka fito waje inda anan suka hau shawarar wadda za'a bari wajenta tunda sunce mutum daya suke buqata.
daga qarshe dai ummy aka bari daita kingin duk suka fito zasu gida batool sai 6atarai take don ita da so samune ta zauna.
haka suka bar asibitin cikin nauyin zuciya da jimami kowanne tausayinta danqare a zuciyarshi.
koda suka isa gida kowa shigewa yayi part dinshi kasancewar dare yayi hakan yasa kowa shigewa sashenshi with heavy heart.
batool na zaune bisa sallaya bayan tagama sallolinta wayatafara Ringing
waigawa tayi taga wayar zee dake kan mirror ke Ringing din
tashi tayi ta dauka da niyyar kasheta amma ganin mai kiran yasata dakatawa
kallon wayar ta cigaba dayi tana shawarar ta daga ne koko
ganin zata tsinke yasata saurin dagawa ta kara a kunne
"Aslm Ummie na" inji Aysha daga dayan bangaren
"wslm Ayush" inji batool cikin son daidaita yanayinta
"laa sis batool, ya kike"
"lfy lau, ya kike yasu Ummie?"
"duk lfy, ina mutuniyar?"
Dan shiru batool tayi saikuma tace
"oh tayi barci"
"barci yanzu? this is just to 9"
"ai... qila agajiye takene shiyasa" tafada adan daburce don dama batool bata iya qarya ba
Dan shiru Aysha tayi can tace
"this is not true, gayamin meke faruwa? ina Ummie?"
"ai...ai gaskiya nake.."
"no sis batool kada muyi haka dake, kifadamin gaskiya please, tsakaninki da Allah ina Ummie?"
rolling idanu batool tayi, batajin tana iyayin qarya kuma bayan ta hadata da Allah
Ajiyar zuciya ta sauke
"tana hospital"
"what!!"
"erm... look da sauki sosai kawai dan zazza6ine bawani abu ba"
"innalillahi waina ilaihi rajiun, wane hospital? meya sameta?" tafada hankali tashe
"zazza6ine kawai kuma nace miki dasauqi"
"wane hospital take?"
"A-shifa'u hospital amma nama san gobe za'a sallame... hello? hello?"
ina har an katse kiran
sauke wayar tayi daga kunnenta tana sauke Ajiyar zuciya ahankali.
***
ahankali ya murda handle din kofar ya turo ahankali batareda tayi qara ba sannan yashigo shima
hango ummy yayi saman dayan gadon wanda dama na masu jinya ne tana barci
ida qarasowa yayi dakin idanunshi akanta har saida yazo gabb da gadonta
kafe fuskarta datayi fayau yayi da idanunshi dasukayi ciki ciki
ya dade sosai ahakan kafin ya motsa yabar wajen yanufi yar locker kusada gadonta ya dauki file din dake kai ya bude yashiga going through dinshi
saida yagama sannan ya maida ya ajiye ya gyaramata tafiyar ruwan drip din sannan yajuya yafice daga dakin as quietly as he entered
*WASHEGARI*
Da wuri mutanen gidansu batool suka bar gidan suka nufi hospital don dama jinsu suke kamar akan qaya, saida suka hadama yan asibitin breakfast sannan suka fito suka hade dasu Daddy suka kamo hanya.
lokacin dasuka isa har lokacin zee bata farka ba amma likitocin sun tabbatar musu komai is normal kawai alluran ne basu gama sakinta ba.
haka suka zauna don ana barin zama a ward din suna fira wanda duk ta Deen ce da zee.
suna ahakan har wajajen 11am lokacin harda su Daddy cikin ward din aka kwankwaso kofa
izinin shigowa sukabada don sunyi tunanin Ahmad ne ko Aymaan dukda Aymaan din be dade da fita ba
murda kofar akayi aka turo
Dan wara idanu batool tayi ganin mai shigowar
Aysha ce sanye cikin milk abaya tayi irin shigarsu ta larabawa saidai fuskarnan dauke take da alamar damuwa
mammaki ne yakama batool don ita tama manta dawata wayar dasukayi daita jiya
mammaki be ida kasheta ba saida Aysha tashigo na bayanta ya bayyana
sakin baki tayi cikin tsananin mammaki bama ita kadai ba harda dukkan mutanen dakin
zuciyar Daddy da Mummy sukayi wata iriyar faduwa lokacin da idanunsu sukayi tozali dashi
sanye yake cikin simple qanannun kaya sa6anin suit da aka saba ganinshi dasu saidai wannan baqin tabarau din nashi na gado nanan maqale da idanunshi
kowa na dakin idanunshi nakanshi yayinda shikuma idanunshi ke kanta ya kafeta dasu babu kyaftawa.
gaisuwar Aysha ta dawo dasu daga duniyar kallon Mussadiq duk suka maido hankalinsu kanta
yan dakin suka shiga amsa gaisuwar tata banda Mummy data kafe Aysha itama da kallo tana ganin wasu qanannun qanannun kammaninsu da Deen kama daga coolness din muryarta da dimple dinta na tsakiyar gemu mai lotsawa koda magana take.
kasa janye idanu Mummy tayi akanta tanajin zuciyarta na melting ahankali cikin shauqi, tabbas wadannan jinin Deen ne ko makaho tashafa saiya gane.
cikin damuwa Aysha tawuce gefen zee dake kwance takama hannunta ahankali tana tambayarsu yamai jiki asanyaye kamar mai shirin kuka
cikin sigar kwantar da hankali su ummy ke amsamata cewa da sauqi sosai yanzu ma barci take.
shiru Aysha tayi tana kallon fuskar zee kamar zatayi kuka don ganinta a wannan condition din ba qaramin ta6ata yayi ba.
ahankali shima Mussadiq dake bakin kofa har lokacin qarasowa dakin idanunshi dake lullu6e da tabarau akan sleeping zee
Daddy har wani dauke numfashi yayi saboda Juyowa dayayi ya kalleshi
cikin alamun girmamawa yadan russunar dakai yace
"good morning" ataqaice
dafarko kasa amsawa Daddy yayi saboda rikicewa saikuma yasamu ya fizgo muryarshi dakyar yace
"y..yes, g..good morning"
be qara bi takanshi ba yawuce wajenda su ummy ke zaune suma yashiga gaidasu cikin turancinshi mai slant din Arab
ganin hakan yasa Daddy saurin juyawa daga dakin ya bude kofa yafita duk arikice.
amsawa su ummy da Mummy data kasa janye idanu akanshi sukayi, gani take kamar batun wannan na gabansu ba Deen bane ba qaryane don itadai idanunta Deen yake gwadamata
tambayarsu yayi jikin mai jiki suka amsamashi cikin fara'a
daga nan yaja bakinshi yayi shiru.
batool ce ta dago tadan saci kallonshi sannan ta gaidashi
beko kalli gefenta ba ya amsa ahankali ya cigaba da tsayuwarshi yana kallon zee dake barcinta ahankali
"Aysha meet Mummy, maman zee" inji batool tana nuna Mummy
tare suka kalli Mummy da Aysha da Mussadiq
wara idanu Aysha tayi cikin mammaki
"really?"
kada mata kai batool tayi hakan yasa Aysha wucewa wajen Mummy dasauri tayimata side hug cikin jindadi tana dariya
wani farinciki ya kama Mummy itama tanata murmushi suka shiga sabuwar gaisawa Aysha na tambayarta ya Nigeria kuma yaushe sukaxo Mummy na amsa mata.
ummy ce tadago ta kalli Mussadiq dake tsaye daga nesa dasu kamar wani saqago cikin larabci tace mashi
"ko ka iya cire drip kunga yaqare gashi basu shigo ba"
kallonta yayi saikuma yakalli drip din sannan ahankali ya qarasa wajen batareda yace komai ba
duk binshi da kallo sukayi harya qaraso yafara cire drip din daga cannula din hannun zee
yana cikin hakan idanun zee suka fara motsi arufen dasuke
shidai Mussadiq belura ba don hankalinshi nakan Abinda yakeyi
ahankali tafara bude idanunta dake ganin biji biji harsuka ida budewa tangaram
again wannan fuskar ita taqara yin arba dashi
kafe gefen fuskar tashi tayi da ido babu ko kyaftawa harya gama yajuyo shima ya kalleta suka hada ido.
Shima kasa dauke idanunshi yayi akanta suka kafe juna da idanu na wani lokaci
tunawa dayayi akwai mutane a dakin yasashi saurin janye idanunshi daga kanta yajuya zai wuce
caraff yaji an cafko hannunshi wanda hakan yasashi tsaya cak daga tafiyarshi
Dan shiru yayi sai kuma yafara Juyowa ahankali harya ida Juyowa ya sauke idanunshi cikin nata dake qyallin hawaye
tsayawa yayi yana kallonta kawai batareda ya iya amsar hannunshi daga nata ba.
"Deen..." tafada in whisper...✍?
*kuyi hqr, haryanzu jikin sai a slow, acigaba dasani a du'a🙏🏻*
Ummin fasihu🧚🏻♀?
8/2/21, 9:43 PM - Buhainat😝: *🙍🏻♂️DEEN🙍🏻♂?*
*080*
ahankali yasa hannu yaxare glasses din idanunshi yana kafeta da oily eyes
kamar wadda idanun suka tunama wani abu saitafara releasing hannun nashi ahankali still idanunsu acikin najuna
dukkan mutanen dakin idanunsu na kansu not moving
"waye shi?" yafada ahankali idanunshi anata
kowa wara idanu yayi yana kallonshi in outmost shock
"who is Deen?" yaqara tambaya yana kallon tsakiyar idanunta
bazai manta ba farkon haduwarshi daita Abinda takirashi kenan, wancan haduwar tasu a library ma ta kirashi da hakan and know? waye mai wannan sunan? meyasa Idan ta ambaci sunan saitayi hawaye?
su ummy ko kallonsu suke hankali a mugun tashe kowa yakasa motsi
"tell me, who the hell is he!" yafada da Dan qarfi idanunshi na dan sauya launi
"hey Mr, incase ka manta this is hospital ba filin kasuwanciba"
Juyowa duk sukayi suna kallon Aymaan dake tsaye bakin kofar ward din hannunshi zube a aljihu
wani qololon baqinciki ya tsayawa Mussadiq awuya daga ganinshi hakan yasashi jan guntun tsaki yajuya ya cigaba da kallon zee data maida idanunta ta lumshe
"Ummie..."
"muna buqatar kowa yafita don zamu dubata" yaqara jin muryar Aymaan na katseshi da hakan
su ummy dai kasa cewa komai sukayi sai binsu da kallo dasuke da daddaya
ignoring dinshi Mussadiq yayi ya cigaba da kallon zee
"are you ok?"
"wannan likitan ta zai iya gane hakan wanda hakan zai yiwuwu ne Idan kuka bashi wuri ya dubata, don't ask her if she's ok cos you can only get the answer from her doctor.. that is Me" inji Aymaan yana qarasowa gaban gadon shima
Juyowa Mussadiq yayi yana kallonshi in the eye sternfully shima Aymaan na maida martanin irin kallon yadda kasan zakaru biyu masu shirin afkawa juna
kingin mutanen dakin kallonsu kawai suke sunkasa cewa komai kowa da Abinda ke jeka kadawo a zuciyarshi
Mummy ce tayi qarfin halin tankawa ta hanyar cewa
"it ok, Bari mufita dama tunda ta tashi kamata yayi adubata, batool, daughter kutaso mukoma waje" tafada reffering to Aysha da batool
kamar jira sukayi duk sai suka tashi harda ummy sukayi waje
har lokacin da Aymaan da Mussadiq basu Bar jifan juna da mugun kallon dasukeyi ba can ahankali Mussadiq ya maida shade dinshi yana cije lower lip dinshi sannan shima yajuya yafice daga ward din kamar zai tashi sama
da kallo Aymaan da zee suka bishi harya fita.
Dan tsaki Aymaan yaja sannan yajuyo ya kalli zee, sauke idanunta zee tayi kawai batareda tace komai ba
qarasowa gefen gadon yayi yana kallonta
"ya jikin?" yafada yana zura hannu daya a aljihu idanunshi kanta
kadamashi kai kawai tayi batareda tace komai ba
shima batareda yasake cewa komai ba yashiga dubata
saida yagama sannan yadanja baya yana sauke abin kunnenshi qasa ya dauki file dinta ya ciro pen yafara rubutu
"I hope kinsan condition din heart dinki"
dagowa tayi takalleshi taga hankalinshi ma na kan rubutun dayake
"Idan ta cigaba da samun attack irin wannan am sorry to say komai na iya faruwa... ciki harda bugawarta"
sauke idanunta tayi batace komai ba
"the heart is the strongest organ of the body and at the same time the most fragile organ, ya danganta da yanayin datake ciki at the particular time, saidai akowanne yanayi take yakamata mai ita yasan cewa it's the most important organ that without it no other organcan perform it's function"
daidai nan yadago ya kalleta yaga itama shi take kallo
"without out heart there will be no life, tana bugawane tareda rayuwa, tana tsayawa rayuwa ma zata tsaya.. cak kamar tsayuwar agogo"
still idanunsu nacikin najuna
"mutuwa abuce data zama dole, mutuwa ta sanaddiyar bugawar zuciya is very normal don mutuwa daya ce amma silolinta nada yawa kuma bugawar zuciya na daya daga cikinsu Don haka don zuciyar mutum tabuga yamutu abune da bazai zama na alhini ba... saidai Idan zuciyar tabuga a dalilin Abinda be cancanci bugawar zuciyar ba ko akan wanda be cancanta ba.. za'a kira hakan ne bada tsautsayi ba saidai ganganci"
kallonshi take sosai lokaci guda kuma hawaye suka fara taruwa a large eyes dinta
"zaya mutu ne akan wanda be cancanci hakan ba yabar wadanda suka cancanci hakan, wadanda kullum burinsu farincikinshi, walwala da nishadi. wadanda suke iya sadaukar da komai akanshi tunkafin yazo duniya har yashigo duniyar har wannan lokacin dayake qoqarin wancakalar da rayuwarshi akan wani abin daban.. har abada"
"zaya tafi yabarsu suna baqinciki, baqincikin da wanda yatafi dominshi bazaiyi rabin rabinshi ba saboda shi bashida asara ko yanada ita yar kadan ce batakai ta wadannan mutanen ba... kuma ba kowa bane wadannan mutanen face IYAYE"
"Iyayenka ne zasu iya xama dakai akowane irin yanayi, suyi sharing kowane feeling dakai, farinciki? baqinciki? qunci? damuwa? komai.
kuma duk lalacewarka bazasu ta6a rabuwa dakaiba duk wahalar dakake basu bazasu ta6a yin watsi dakai ba.. duk runtsi"
"wadannan mutanen?.. su ya kamata mutum yafara sawa agabanshi, yafara duba wane hali zasu shiga Idan har ya aikata wani abin bawai mu rufe zuciyarmu ba mu makance qarshe muzo muyi Abinda zaiyi hurting our beloved ones na har abada"
Dan shiru yayi yana kallon yadda hawayenta yaqi tsayawa
Dan murmushi yayi yana sauke idanunshi kan file din dake kan locker haryanzu
"hawaye... wani lokacin rahamane domin yana gangarowane tareda kaso mafi yawa na damuwa amma Idan yayi yawa harya rikida yakoma jini yana zama babban illa.. ga zuciya da gangar jiki gabadaya"
sake dora pen yayi kan file din yasake yan rubuce rubuce sannan ya maida yarufe
dagowa yayi batareda yasake kallonta ba yace
"za'a doraki akan magani, please endeavor to take them at the right time ko don beloved ones dake damuwa da damuwarki"
yana kaiwa nan yajuya yanufi kofa.
binshi da kallo tayi da rinnanun idanunta harya fice
fashewa tayi da wani kuka mai tsuma zuciya tajawo pillon kusada ita ta cusa fuskarta aciki tana cigaba dayi.
***
A bangaren Mussadiq kuwa yana fitowa beko kalli kowa ba yanufi hanyar fita daga wajen.
sosai ranshi ke a 6ace don ba qaramin qonamashi rai Abinda Aymaan yayimashi yayi ba.
harshi zai mashi taqama da matsayinshi? harshi zai koro waje don kawai taqamarshi shi likita?
a stairs suka kusa cin karo da Daddy dake tareda Abbu suma sun karyo kwana
saurin sake dauke numfashi Daddy yayi ganin kamar ya kalloshi ya kauda kai har Mussadiq da 6acin rai bemasa yawani tantancesu ba yayi wucewarshi
sauke numfashi yayi nannauya yana bin bayanshi da kallo sannan yajuyo gun Abbu dake kallonshi
"lafiya daiko?" inji Abbu
"lfy... kawai Idan nadora idanuna akanshi.. sainaga kamar Deen ne" inji Daddy yana qara bin inda Mussadiq yabi da kallo
murmushi Abbu yayi yace
"ai ikon Allahn kenan, wani abin saisun hadu su biyun ankasa tantancesu, Allah dai ya nunamana ranar"
"Amin" inji Daddy sannan suka wuce saman
Direct parking space din asibitin Mussadiq yanufa ya nufi
All Chapters
Chapter 1
Chapter 2
Chapter 3
Chapter 4
Chapter 5
Chapter 6
Chapter 7
Chapter 8
Chapter 9
Chapter 10
Chapter 11
Chapter 12
Chapter 13
Chapter 14
Chapter 15
Chapter 16
Chapter 17
Chapter 18
Chapter 19
Chapter 20
Chapter 21
Chapter 22
Chapter 23
Chapter 24
Chapter 25
Chapter 26
Chapter 27
Chapter 28
Chapter 29
Chapter 30
Chapter 31
Chapter 32
Chapter 33
Chapter 34
Chapter 35
Chapter 36
Chapter 37
Chapter 38
Chapter 39
Chapter 40
Chapter 41
Chapter 42
Chapter 43
Chapter 44
Chapter 45
Chapter 46
Chapter 47
Chapter 48
Chapter 49
Chapter 50
Chapter 51
Chapter 52
Chapter 53
Chapter 54
Chapter 55
Chapter 56
Chapter 57
Chapter 58
Chapter 59
Chapter 60
Chapter 61
Chapter 62
Chapter 63
Chapter 64
Chapter 65
Chapter 66
Chapter 67
Chapter 68
Chapter 69
Chapter 70
Chapter 71
Chapter 72
Chapter 73
Chapter 74
Chapter 75
Chapter 76
Chapter 77
Chapter 78
Chapter 79
Chapter 80
Chapter 81
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 65 Chapter of 81