yafi surutunshi
"Alhamdullilah, da sauqi gaskiya sosai. pressure din yarage"
"to Allah ya taimaka, more more grace to your elbow"
murmushi yayi yace
"Amin Amin, kefa? ya school?"
"school Alhamdullilah, munata fama ga exam nata gabatowa"
"to Allah yabada sa'a, adai cigaba da dagewa"
"insha Allah yaya"
haka suka cigaba da firarsu sama sama har suna haka abba yashigo.
sosai abba yaji dadin ganinshi dukda dama yasan da zuwanshi, cikin girmamawa Deen ya gaidashi yana amsar handshake din da abba yake miqomashi a kunyace
inda sabo yaci ace Deen yasaba da hakan don hakan nacikin al'adar abba miqama mutum hannu suyi musabaha duk banbancin shekarunsu kau
abba irin mutanen nan ne masu faran faran ga raha da dariya
nan ya zauna suka shiga labari wanda duk yashafi aikin Deen
a yanayin dasuke firar zaka hango tsantsar qaunar da abba keyima Deen shikuma Deen zaka hango tsantsar girmamawa da biyyaya dayakema abban.
can kuma suka tashi abba da Deen suka fita waje suka bar Lailah a falon
parking space suka nufa inda Abba yanunama Deen sabuwar motarshi daya saya kwana uku daya wuce wadda ke lullu6e cikin rigar motar
da taimakon Deen suka yaye lullu6in motar.
danqareriyar motace yar yayi mai mugun kyau, sosai Deen yayima Abba allah yasanya alhairi sannan yashiga duba mashi lafiyar motar kamar yadda Abba ya buqata don ganin ko tanada wani fault daya kamata agyara kafin afara hawanta
Lailah ce ta tashi daga inda take zaune taqarasa jikin Windows din falon tadan yaye labulen wajen tana leqensu
Deen ne tagani gaban motar ya dage murfin gabanta ya sunkuya yana dubata
tattare hannuwan rigarshi dayayi yaba farar fatar hannunshi bayyana mai cikeda kwanttatun gargasa
lumshe idanu tayi ahankali tasake budewa akanshi, tarasa meyasa komai Deen yayi saiyayi mugun yimashi kyau.
cigaba da kallonsu tayi har yagama yan gyare gyaren dayake, Abba ya zagaya yashiga motar Deen na gaban motar still harya tadata shikuma yaqara sunkuyawa yana duba engine motar
sun dan dade ahakan kafin abban yafito bayan yakashe motar shikuma Deen ya maida murfin gaban motar ya rufe alamun sungama Abinda sukeyi
sake lullu6e motar sukayi sannan sukazo suka wuce suka kama hanyar part din abban.
Ajiyar zuciya Lailah tasauke tana sakin labulen, sosai take tausayama kanta na fadawa son maso wanin datayi, fatanta dai Allah yabata mafita akan wannan matsalar tata yakuma sassauta mata.
sai bayan sallar isha'i Abba da Deen suka sake shigowa main house din don Deen yayi bankwana dasu mami.
basu dade ba suka fita da Abba da Deen da Afrah data liqemashi suka rakashi har wajen motarshi
ko anan ma sundan qara dadewa suna fira sannan Deen yashiga motar bayan sunyi sallama ya tada motar yajata.
bin motar da kallo Lailah dake leqensu ta windown dakinta tayi harta fice.
sauke wata nannauyar Ajiyar zuciya tayi sannan tasaki labulen takoma ta jingina da bango tana Lumshe idanunta.
ππππππππππ
Tun bayan rabuwar zee da Mussadiq bata qara walwala ba, haka ta qarasa ranar cikin qunci da rashin kuzari
sosai batool ta damu da hakan kuma tambayar duniyarnan tayimata akan meke damunta amma taqi gayamata saidai tace mata babu komai
dole ta haqura ta kyaleta saidai tasan akwai abinda ke damunta kuma tafi alaqanta hakan da qila mikin soyayyarta ne yatashi don dama haka take wasu lokacin, duk yadda takeson 6oye damuwarta tayi pretending she's ok wani lokacin kasawa, wani lokacin kawai sai kaga mood dinta yachanza takoma very depressed.
murda handle din kofar akayi tawaje aka turo kofar
batool ce tashigo dakin ta tsaya daga bakin kofar tana kallon zee
haryanzu zaune take inda tabarta rungume da pillow ta kafe wuri guda da ido
Ajiyar zuciya batool ta sauke sannan ta qarasa shigowa cikin tana sakin murmushi cikin son wartsakar daita
fadawa tayi kan gadon itama gefen zee tana dariya wanda hakan yadawo da zee daga duniyar tunanin data shiga tajuyo tana kallonta
"albishirinki" inji batool happily
dauke kanta xee tayi daga kallonta don kwata2 bata cikin mood din wasa, kamar bazatayi magana ba can kuma tace
"goro"
murmushi batool tayi tace
"to yarinya Akhie tafiya zaiyi, guess where?"
Dan kallonta zee tayi saikuma tasake kauda kai, da batool tasan yadda batason ko magana ce dabatazo tana takura mata ba amma sanin wacece batool din yasata sanin amsamata din kawai shine kwanciyar hankalinta
"where?" ta tambaya tana dan yatsine fuska cikin qosawa
"Nigeria!" batool tabata amsa cikin murna
saurin juyowa Zainab tayi ta kalli batool din
"Nigeria?.."βπ?
Ummin fasihuπ§π»ββοΈ?
8/2/21, 9:43 PM - Buhainatπ: *ππ»ββοΈDEENππ»ββοΈ?*
*076*
*THE TRIP*
"Are you serious?" inji zee tana kallon batool cikin mammaki
"wlh yanzu naji suna labarin da ummy, gobe ma zasu tafi zasubi flight din 12noon"
shiru zee tayi tana kallonta, kawai saita tsinci kanta dajin wani irin kewar kasar tata.
bata ta6a tunanin zatayi missing Nigeria nan kusa ba amma yanzu dataji wannan zancen saitaji tayi missing dinta sosai, tayi missing qasarta da mutanen ciki, jitayi dama daita za'ayi tafiyar amma kuma anya zuwan bazai famamata tsohon mikinta na zuciya ba? kodayake anan dinma ba tsira tayiba, tagudo nan don mance past dinta tayi moving on amma seems it's not easy don kullum past dinta cikin hunting dinta yake
kauda kanta tayi daga kallon batool din tace
"me zaije yi acan to?"
"asalin tafiyar batashi bace, Ahmad wani business trip zaikaishi can shine shima yace zayaje don yarabu dazuwa gashi dama kwanannan he's less busy"
"kenan tareda Ahmad zasu tafi?"
"yeah... did you want to go too?" inji batool tana quramata idanu
wani kallo zee tayi mata sai ta kauda kai
"never!" tafada tana hade fuska
murmushi batool tayi
"nayi tunanin kina kewan can ne"
"banayi" tabata amsa tana komawa ta jingina da frame din gadon
murmushi tasake yi tace
"A'a dole kiyi missing Nigeria, gida gidane ko don mahaifanki dake can"
"ai yanzun ma kamar tare muke don kullum muna waya kuma Idan naso ganinsu ma zan gansu ta video call so bana wani missing dinta"
murmushi kawai batool tayi bata qara cewa komai ba saidai talura da yadda mood din zee yaqara chanzawa wanda ta tabbata harda zancen tafiyar tasake dagulamata mood din
A daren ranar barci rabi da rabi zee tayi, sosai tunanin tafiyarsu Aymaan ya tsayamata arai yakuma tadomata tsumin kewar qasarta da mutanen cikinta.
washegari sukuku ta tashi, jiki babu kwari tahau daily chores dinsu da shirin makaranta.
suna zaune a dining suna breakfast Aymaan ya sauko daga sama shima yayi joining dinsu.
gaidashi batool da zee sukayi ya amsa cikin kulawa da barkwanci kamar yadda yasaba sannan shima ya gaida ummy
batool ce tayi serving dinshi sannan ta koma ta zauna tacigaba dacin abincinta
jawo abincin yayi gabanshi yafara ci saidai rabin hankalinshi nakan zee daketa tsakurar abincin sama sama
Dan murmushi yayi sannan yadauki mug din shayinshi dake tururi yadan kur6a ya ajiye yasake kallon zee
"ke yar Nigeria, hope kinsan yau zankaiwa qasarku ziyara?"
dagowa zee tayi ta kalleshi sai tadanyi murmushi
"hmmm jiya nakejin labari, Allah ya tsare hanya"
Dan daga gira daya yayi yace
"hakama zakice? nayi tunanin liqewa zakiyi kice kema kina zuwa"
Dan ta6e baki tayi tace
"saidai nace Allah yakiyaye hanya"
dariya batool tayi tace
"hmmm haka zakice ai, yarinya tazo qasar turai taji dadi ta manta da qauyenshi" taqara fashewa da dariya Aymaan na tayata
"kekau kullum tana cin dajajaπta larabawa tana shan ni'imttaciyar weather mu ba dole ta manta ba?" inji Aymaan
kumbura fuska zee tayi tana makamasu wani kallo
"wane ni'imttaciyar weather? ai wlh Nigeria tafi nan weather mai ni'ima. kuda nan da rana tsabar zafi kamar ana gasa mutum a oven? a qasarnan Idan kayi walwala da zirga zirga cikin kwanciyar hankali to darene, ahakan kuma kukeda weather mai kyau?" tafada tana harararsu
"ahaka kuma kike qara haske kina fresh, dakike can kauyen naku ko rabin kyan yanzu baki kaiba dukda ni'imttaciyar weather taku" inji batool
"wake haske? ai kuma kunsan nafi kyau danake qasarmu, anan banda tsabar rana da zafi me akeyi, badon ina kaffa kaffa da kaina ba da yanzu nazama duna qila sai an haska da touchlight za'a dinga ganin fuskata dakyau"
dariya duk sukayi harda ummy dake aikin sauraronsu
"aimu ranarmu fari takesawa ba baqi ba ko kin ta6a ganin balarabe baqi? koma akwaisu yan kadanne, mafi yawancinmu fararene" inji Aymaan
"Allah mai iko, yanzu nan kuma jinku kuke ku larabawa ne ko?" inji ummy da sai yanzu tasa baki
dariya zee tayi
"karfin hali kenan, dadai ba'a san asalin balbela ba"
kumbura fuska batool tayi tace
"yo Idan ba larabawa bane ba su wanene?"
"ato, tayani tambaya" inji Aymaan
"cikkakun larabawa nemu" inji batool
"fararen ma kuwa" Aymaan yabata amsa
dariya sosai zee keyi don sosai suka bata dariya
"A'a gwarama kayi shiru da bakinka Aymaan, Idan ana maganar farare kabar zazzaqewa don.kunya zakasha" inji ummy dake taya zee dariya
Dan 6ata rai Aymaan yayi yace
"to ni ba farin bane? wai batool ni ba fari bane?"
Dan kallonshi batool tayi saikuma tafashe da dariya
"wlh tlh Akhie kai baqine"
ta qarashe tana saurin miqewa daga kan kujerarta don dama kusadashi take
sakin bakinshi Aymaan yayi yana kallonta itakuma takoma bayansu ummy dake dariya tana dariyar itama
"kutt... nizakiba kunya muna team daya? lallai kin qoshi" yafada yana kwafa ya sake daukar mug din shayinshi
"yo ai gaskiya ne Akhie, kasan ni bana qarya" inji batool tana dariya
kada kai kawai Aymaan yayi bece mata komai ba ya cigaba dacin abincinshi
kujerar kusada ummy batool taja ta zauna taqi komawa kusadashi suka cigaba da breakfast din nasu cikin walwala, wannan karon murmushi kwance a fuskar zee dakejin duk wata damuwarta data tashi daita ta yaye
ganin hakan yasa Aymaan Dan murmusawa don dama burinshi kenan, kullum burinshi farincikinta, ya tsani ya ganta cikin damuwa ko yayane.
ahaka suka gama breakfast din su zee suka tashi don wucewa school
"ukhtie baki gayamin tsarabar dazanyi miki ba Idan zan dawo" inji aymaan yana kallon zee
kafin zee tayi magana batool tayi saurin ca6ewa da
"ka siyamin komai nacan dangin maqulashe na gargajiya irinsu magarya, goruba, taura, jawuwa, jan madam, kanya..."
"wa ake tambaya wake bada amsa? kinji na ambaci sunanki ne?" Aymaan ya katseta yana mata kallon up & down
kumbura fuska tayi tana kallon ummy
"nida kika kira baqi nikuma kikeso nayimiki tsaraba?lallai bakida hankali" yafada yana binta da mugun kallo
qara kumbura fuska tayi kamar zatayi kuka
"yauwa ukhtie inajinki" ya maida hankalinshi kan zee dake qumshe dariyarta
"nidai babu komai yaya, kawai fatana Allah yakaiku lafiya ya maidoku lafiya akuma gaidamun su mummy sosai ace nayi kewarsu sosai"
"kenan bakison tsarabar komai?"
girgiza kai tayi kawai
"to ni Idan nayimiki don karan kaina fa?"
murmushi zee tayi
"it ok, xanji dadi sosai"
murmushi shima aymaan yayi yadan kauda kai saikuma yasake kallonta
"to Shikenan, zan miki tsaraba, wadda bazaki ta6a mantawa ba"
Dan daga gira daya tayi
"dagaske?"
kadamata kai yayi alamun eh
"shukran so much"
kada mata kai kawai yayi ya kauda kai yacigaba da cin abincinshi dabe cinye ba
juyawa zee tayi tayima ummy sallama sannan tasake yima Aymaan bankwana tanufi kofa
batool daketa kumbure kumburenta itama tayima ummy sallama sannan ta kalli Aymaan da hankalinshi kekan abincinshi tace
"to nima Akhie Allah yakiyaye yakaiku lfy amma karka manta harda atamfofi irin nacan da shaddoji da kayan kad'i irinsu kuka, ku6ewa, ya6do, daddawa..."
duqewa tayi saboda jifanta dayayi da spoon din hannunshi tana dariya
"wlh yarinyar nan ta rainani nizakiba sautun daddawa da kuka?"
gwalo tayimashi sannan tanufi kofa tana cigaba dayimashi dariya suka fice itada zee.
binsu da kallo Aymaan da ummy din sukayi harsuka fice daga falon sannan kowanne ya janye idanunshi yana sauke Ajiyar zuciya
ummy ce tadago takalli Aymaan tace
"kana ganin komai zaitafi smoothly?"
qurawa plate din gabanshi idanu aymaan yayi sannan yadan sauke Ajiyar zuciya sannan yadago yakalli Ummin
"insha Allah ummy, just pray for us"
"to Allah yabada sa'a yakuma taimaka"
"Amin ya rabb"
haka suka cigaba da karinsu suna labari jefi jefi duk akan tafiyar.
sai wajajen 11am Ahmad yaduro gidan cikin shirinshi na tafiya
saida suka gaisa da ummy sannan ya haura sama dakin Aymaan
sai wajajen 11:30am suka sauko kowanne cikin shirin tafiya kowanne goye da jakkar goyawa wanda ke daukeda duk abubbuwansu na amfani.
saida sukayi bankwana sosai da ummy tayimusu addu'o'in tsari sannan suka bar gidan cikin motar da Ahmad yazo daita wanda drivern gidansu ke jansu.
lokacin dasuka isa airport din saura mintuna shabiyar jirginsu yatashi
nan suka shiga yin duk wani tantancewar daya kamata suyi kafin lokacin tashin jirgin.
cikin qanqanin lokaci suka gama all neccesary things dazasuyi suka bi ayarin passengers masu shiga jirgi suma suka shiga suka zazzauna a seats dinsu dake.kusada juna.
cikin qanqanin lokaci aka fara sanarwar tashin jirgin nan kowa duk ya daddaura belt din cikin few minutes jirgin ya daga ya lula sararin samaniya
***
Wunin ranar a school cikin walwala zee tayishi, bata yarda ko kadan taba tunani damar yin tasiri a zuciyarta ba.
yau bataje library ba kamar yadda tasaba saboda gudun sake haduwa da Mussadiq dukda tasan ba qaramin aikinshi bane ba yabiyota har class din dayake Idan yaga dama.
sai bayan asr sannan suka fito daga school din da ita da batool suka nufi motarsu suka shiga suka fice daga school din.
fitarsu keda wuya shima yaba drivernshi umarnin sutafi, drivern yataka motar yaja suma suka fice daga school din.
ππππππππππ
sai da marece liss jirginsu Aymaan ya sauka a babban filin jirgin sama na babbar birnin tarrayar Nigeria wato Abuja.
cikin qanqanin lokaci suka fito suka gama clearing din komai sannan suka kamo hanya suka nufi hanyar fita daga airport din
ganin ba'a dade da gama magrib ba yasasu fara tsayawa a massalacin dasuka fara cin karo dashi sukayi sallah sannan suka fito neman abin hawa.
basu wani jimaba suka samu adaidaita sahu suka hau suna gayamashi hotel din daxai kaisu
tafiyar mintuna shabiyar sukayi suka isa hotel din suka sauko suka biya mai adaidaitan haqqinshi sannan suka shige cikin hotel din.
cikin qanqanin lokaci suka kama daki suka biya sannan aka rakasu dakin
a lokacin har wasu massalattan sunfara sallar isha'i hakan yasasu sake fitowa sukaje sukayi sallar tasu a massalacin hotel din
sai bayan sun dawo sun nutsu har sunci abinci sannan suka doddora sabbin layyukansu dasuka siya.
nan Ahmad yajawo laptop yafara aikin gabanshi shikuma Aymaan ya shigewarshi toilet.
sai bayan awa daya aka turomusu sms na zasu iya amfani da layyukansu
nan take suka fara ma mutanen Dubai domin sanardasu isowarsu Nigeria lfy
sun dade suna waya dasu inda saida suka farayi da iyayen Ahmad sannan suka kirasu ummy suma daga nan suka maida akalar kiran wajensu Daddy(mahaifan zee) dake katsina don sanardasu isarsu don suma sunsan da tafiyar don dasun gama Abinda yakawosu zasu biya ta katsina din kafin sukoma Dubai
suma sundan jima suna gaisawa dasu sannan sukayi sallama.
daga haka Aymaan yawuce yayi shirin kwanciya yayi kwanciyarshi yabar Ahmad nan daya cigaba da aikin dake gabanshi.
yana jin lokacin daya kira abokin aikinshi nanan Abuja din suna tattaunawa akan abinda yakawosu dakuma fitarsu ta gobe.
maida idanunshi Aymaan yayi ya rufe kamar mai barci amma ba barcin yakeba, banda saqe saqe babu abinda ke kai komo a kwalwarshi.
ahakan har Ahmad yagama duk abinda yake shima yazo ya kwanta
ya dade sosai idonshi biyu kafin yasamu can cikin dare barci ya sadado shima ya daukeshi.
*WASHEGARI*
Sai bayan sallar zuhr suka fita daga hotel din.
dama abokin aikin Ahmad ne yazo daukarsu don haka gabadayansu suka nufi motar da mutumin yazo daita
duk sanye suke cikin qannanun kaya sunyi kyau sosai mussanman aymaan dayayi shigar all white wanda yayi mugun yimashi kyau sosai saidai fuskarnan tashi babu wannan walwalar da fara'ar da aka saba ganinta dashi.
kallo daya zakamashi kasan cewa yau baya cikin good mood kwata2
ko a motama Ahmad da usman (abokin aikinshi) kawai ke labarinsu shikau hankalinshi nakan wayar hannunshi dayake daddanawa tunda suka shiga motar
sunyi tafiyar kusan mintuna 30 sannan suka iso inda zasu.
jin tsayuwar motar yasa Aymaan sanin sun iso
duk fiffitowa sukayi banda Aymaan da saida ya mula yasha iska sannan ya bude kofar 6angarenshi yafito.
Ahmad tun jiya yake lura da take takenshi dakuma yadda yake wani shashan qamshi amma be kulashi ba don yasan abinda ke damunshi kuma yasan qiris yake jira ya burkuce musu shiyasa yake taka tsantsan yana lalla6awa harsuyi abinda ya kawosu sutafi.
maida kofar aymaan yayi ya rufe bayan yafito sannan yafara bin harabar wurin dasuke da kallo
wurin babban industry ne ya hadu daidai misali don koina is neat and well trimmed.
akwai mutane jefi jefi a harabar wasu tsaye wasu kuma na kaiwa da kawowa.
waya usman yazaro yayi kira, bayan yagama yajuyo kansu Ahmad yace suje.
gaba yayi suma suka maramashi baya har suka shiga cikin building din.
suna tafe Ahmad da usman na magana yayinda Aymaan dake bayansu yayi tsit sai bin wurare yake da kallo cikin nazari.
Ahaka har suka qaraso reception din.
anan suka hadu da managern wajen wanda yayi musu tarba mai kyau wanda da alamu akwai sannaya a tsakaninshi da usman
anan usman ya gabatar mashi da Ahmad da Aymaan suka gaisa inda har lokacin babu walwala tareda Aymaan.
iso managern yayi musu zuwa wani qayyataccen waiting room yakuma sa aka kawomasu abu mai sanyi sannan ya sanardasu sudanyi haquri ogan na studio yanzu amma insha Allah yakusan fitowa.
da hakan yafito yabarsu wajen don jiran isowar ogan.
tunda suka zauna Aymaan ya jingina da jikin kujera ya rungume hannayenshi a qirji ya sauke idanunshi qasa.
ko kallon kayan drinks din gabansu beyi ba bare yayi marmarin ta6a daya daga ciki kawai dai zaune yake yana kalkada kaffafunshi yana saqe saqen da shikadai yasansu.
sunyi 20mins ahakan sannan suka farajin alamun ana tunkaro dakin dasuke
su Ahmad daketa labarinsu daya shafi business tuni suka nutsu suka maida dukkan hankalinsu ga kofar shigowa wajen yayinda Aymaan ko motsawa beyiba daga position dayake ba.
qarar budewar kofar yaji sannan yaji sallamar manager din daya kawosu nan din, can saiya sake jin sallamar cikin wata very cool calm voice.
bugun zuciyarshi ce tafara sauya salo lokacin da wannan muryar ta dira kunnuwanshi.
su Ahmad ne suka samu damar amsa sallamar yayinda shikuma ahankali yafara dago idanunshi daga qasan dasuke kallo
cikin two pair of oily eyes dinshi ya saukesu wanda yaqara yin daidai da motsawar zuciya...βπ?
Ummin fasihuπ§π»ββοΈ?
8/2/21, 9:43 PM - Buhainatπ: *ππ»ββοΈDEENππ»ββοΈ?*
*077*
Kafeshi yayi da kallo shima Deen din ya tsinci kanshi da tsareshi da nashi idanun.
"bismillah, gasunan tundaxu suke zaman jiranka" maganar Habeeb ta dawo da Deen daga duniyar kallon Aymaan
janye idanunshi yayi akanshi ya kalli kingin mutanen dakin yana sakarmasu kyakyawan murmushinshi yana ida qarasowa dakin.
Ahmad tunda ya dora idanunshi shima akan Deen yayi suman zaune, be ta6a sanin kammanin nasu yakai hakaba, ba don yasani ba da yana iya rantsewa cewa wannan Mussadiq ne.
"barkanku da warhaka, sorry for keeping you waiting" yafada calmly cikin friendly tone yana miqamusu hannu don suyi musabaha
da usman dake farko suka fara musabahar sai Ahmad dayayi iya bakin qoqarinshi wajen daidaita nutsuwarshi yana murmushin yaqe sannan ya miqama Aymaan da har lokacin idanunshi bebar fuskar Deen ba
ganin be amshi hannun ba saima kallonshi daya tsaya yanayi yasa shima Deen cigaba da kallonshi trying to read his expression don shima tun kallon farko dayayiwa mutumin yakejin kamar akwai wani abu attatare dashi.
harya fara fidda rai da zai amshi hannun yafara shawarar saukewa Aymaan ya dago nashi hannun yabashi sukayi musabahar wanda ko second daya basuyi ba kowanne ya janye nashi hannun
iso Deen yayi musu akan sutaso sutafi office dinshi yadda zasu tattauna dakyau.
duk miqewa sukayi yayi gaba batareda ya qara kallon gefen aymaan da ko motsawa daga zaunen dayake beyiba yayi hanyar fita daga dakin.
Ahmad ne ya dafa kafadar Aymaan ganin beda alamun tashi din
dagowa Aymaan yayi yana kallon Ahmad da wani irin expression a idanunshi, fuskar roqo Ahmad yayimashi yana mashi nuni daya taso please.
dakyar yasamu yataso din yana cije lip dinshi na qasa.
suma hanyar fita sukayi Don kingin harsun fita.
basuyi wata doguwar Tafiya ba suka qarasa office din Deen din
duk yimasu iso managern yayi ya gwagwadamasu wurin zama duk suka zauna a kujerun dake facing table din daya raba tsakaninsu da Deen dake zaune yana facing dinsu ta dayan 6angaren.
tunda Aymaan ya zauna yayi crossing kaffafunshi ya sauke kanshi qasa yana danne2 a waya be qara dagowa ba
a bangaren su Deen kuma gaisawa suka sakeyi dasu Ahmad sosai sannan Habeeb yafara magana
"wannan shine wanda nacema zaizo yau dashi da abokanshi, sunanshi usman ya rako abokanshi ne akan wani aiki amma gashi nan ai, waqa abakin mai ita tafi dadi"
duk murmushi sukayi sannan usman ya amsa da
"hakane Mallam Habeeb, ni sunana usman mahmud wadannan abokainane kuma yan uwana da Ahmad da Aymaan, su yan Nigeria ne amma suna zaune ne a Dubai yanzu hakan ma aiki ne yakawosu nan din, wannan Ahmad din shi yayimin magana tun kafin suzo akan zasu shigo 9ja kuma xaiso haduwa da shahararren mawaqinnan balarabe don fan dinka ne sosai dukda yanacan amma yana yinka kuma yana sauraron waqoqinka sosai, kasan shahara babu abinda bata kawowa, kai kananan zaune waje daya amma bakasan iyakar inda ka zaga ba.
ganin yadda yake kwadayin ganinka yasa nikuma nace insha allah zanyi qoqari na hadaku... to Mallam Ahmad yau dai gaka ga balarabe face-to-face" yaqarashe yana kallon Ahmad daketa murmushi tunda yafara maganar
"aikaudai Dan uwa, yau gani ga wanda nadade ina mafarkin gani a zahiri.
gaskiya naji dadi sosai don I never thought ganinka will be this easy for me, ban ta6a tunanin zanganka anan kusa ba koda daga nesa ne bare ace har nasamu damar magana dakai, gaskiya am very happy today and ina farincikin gayamaka cewa.muna yinka sosai, more more basira insha Allah"
Deen dake murmushi sosai yace
"Thanks so much bro, am glad and happy I can statify your expectations without my knowledge, Allah praise be to Allah dayabani damar gamsar daku da guntun baiwar dayabani, allah yasaka da alhairi yakuma cigaba dabani ikon cigaba da gamsardaku da aikina"
"Amin ya allah, ai Mr balarabe sunanka yayi trending inda kwata2 baka tunani kuma bakomai yaja hakan ba sai irin yadda kake captivating zuciyar mutane da salon waqarka, ga sanya nutsuwa ga sanya shauqi don duk daskarewar zuciyar mutum dayaji waqarka saita motsa wlh, allah dai yaqara basira yasa afi haka" inji usman
"Amin amin, Allah yaqara daukaka yaqara zaqin murya da kaifin kwalwa.."
tashin da Aymaan yayi yasa Ahmad Dan yin shiru
wayace kare a kunnenshi hannu daya a aljihu
"hello..." daga haka yawuce hanyar kofar office din yafice
Duk binshi da kallo sukayi harda Deen harya ida ficewa daga office din
maido dubansu sukayi kan Deen da haryanzu idanunshi nakan kofar office din
yar dariya Ahmad yayi yace
"workaholic kenan, haka yake kodayaushe cikin aiki mutum kamar agogo"
duk dariya sukayi banda Deen dayayi murmushi kawai
"yes as I was saying Idan babu damuwa nima zanso adan yimin waqa ace yau gani da waqar actor na kuma ni akaiwa, gaskiya I'll be very happy Idan akayi granting wannan wish din nawa"
murmushi Deen yayi yace
"babu damuwa insha allah, hakan bazai gagara ba saidai wane iri kakeso? just waqar koko harda performing?"
dan wara idanu ahmad yayi
"wow performing? sounds nice. wane procedure akebi to Idan mutum nason ayimashi performing din?"
"gaskiya Idan performing ne ana sanarwane dawuri misali a month to the date yadda za'a riga akamamaka ranar"
"hakan yayi, insha Allah zamu dawo don performing din very soon amma yanzu kasancewar zuwa mukayi kuma ba dadewa zamuyi ba inajin waqar kadai ta wadatar"
"alright to wace iri kakeso?"
"waqar mahaifiya, umma ta nakeso ka waqe" yafada yana washe baki
duk murmushi mai sauti sukayi
"masha Allah, Shikenan insha allah yanzu Habeeb kar6i bayyanan komai da komai, yaushe kukeson waqar?"
"eto, kaga bawani dadewa zamuyi anan dinba kawai wani aiki ne yakawomu zamuyi mu juya, insha allah jibi mukeson juyawa Idan Allah yakaimu"
"alright, jibi da yaushe zaku tafi?"
"jirgin marece zamubi insha Allah"
"to kuna iya dawowa jibin dasafe insha Allah everything will be ready"
cikin jindadi Ahmad yace
"kai masha allah, mungode kwarai allah ya qara daukaka"
da Amin ya amsa yana murmushi sannan Habeeb yashiga yin abinda Deen din yasashi.
cikin qanqanin lokaci suka gama clearing komai suka dan qara ta6a fira cikin raha da barkwanci inda anan saida Ahmad yayi ya dauki hoton Deen shikadai sannan kuma yabada akayimusu taredashi.
lokacin da zasu tafi har waje saida Deen da Habeeb suka rakosu saboda dan sabo daya shiga tsakaninsu adan wannan lokacin suna tafe suna fira.
tundaga nesa suka hango Aymaan zaune kan wani benci dake karkashin wata bishiya dake parking space din kanshi sadde yana latse latsenshi a waya.
har suka qaraso dan nesa da wajen be dagoba don bema nuna alamun yasan dasuba dukda tun fitowarsu yagansu
tsayawa sukayi adan nesa da wurin sukayi bankwana cikin aminci sannan Deen ya juya batareda shima ya kalli gefen da Aymaan yakeba yatafi Habeeb na takemashi baya.
saida sukaga wucewarsu sannan suka nufi inda Aymaan yake
"haba aymaan, meye hakan dakayi? you just walk out without even excusing yourself, hakan dakayi is not proper" inji Ahmad
dagowa yayi ya makamashi wani kallo sannan ya tashi yana pocketing wayarshi
"kunga muje, abinda yasa kuka iskeni anan ma don babu car key a hannuna ne" yafada yana wucesu
"aida kabi adaidaita tunda garin ba baqonka bane bare ka 6ace" Ahmad yabashi amsa
"I thought as much saidai earliness dinku na minti biyar ya hana hakan, dakun qara minti biyar aciki da yadda kace din za'ayi" Aymaan yabashi amsa
Ahmad zai sake magana usman
All Chapters
Chapter 1
Chapter 2
Chapter 3
Chapter 4
Chapter 5
Chapter 6
Chapter 7
Chapter 8
Chapter 9
Chapter 10
Chapter 11
Chapter 12
Chapter 13
Chapter 14
Chapter 15
Chapter 16
Chapter 17
Chapter 18
Chapter 19
Chapter 20
Chapter 21
Chapter 22
Chapter 23
Chapter 24
Chapter 25
Chapter 26
Chapter 27
Chapter 28
Chapter 29
Chapter 30
Chapter 31
Chapter 32
Chapter 33
Chapter 34
Chapter 35
Chapter 36
Chapter 37
Chapter 38
Chapter 39
Chapter 40
Chapter 41
Chapter 42
Chapter 43
Chapter 44
Chapter 45
Chapter 46
Chapter 47
Chapter 48
Chapter 49
Chapter 50
Chapter 51
Chapter 52
Chapter 53
Chapter 54
Chapter 55
Chapter 56
Chapter 57
Chapter 58
Chapter 59
Chapter 60
Chapter 61
Chapter 62
Chapter 63
Chapter 64
Chapter 65
Chapter 66
Chapter 67
Chapter 68
Chapter 69
Chapter 70
Chapter 71
Chapter 72
Chapter 73
Chapter 74
Chapter 75
Chapter 76
Chapter 77
Chapter 78
Chapter 79
Chapter 80
Chapter 81
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 63 Chapter of 81