mamar taki?"
"wlh lafiya lau kaka, tana gaida ki tama so zuwa amma allah beyi ba"
"ai ba komai wlh, kunga Deen kwarai mace mai kirki, kai allah dai yasaka da alhairi, bari na zubomiki abinci" tafada tana niyyar tashi
Saurin Dakatar da ita zee tayi da
"A'a kaka, alhamdullilah azumi ma nake"
Dan waro idanu kaka tayi tana komawa ta zauna tace
"azumi? Ca6 shiyasa baki sha ruwan ba ashe, amma duk mai azumi yau sai yaji a jikinshi wannan kwala rana haka masha allahu"
Murmushi tasakeyi
Firarsu suka cigaba dayi wanda kaka ce keyin kusan rabi da kwata zee sai murmushi take don sosai takejin dadin firar tata
Suna ahaka sukaji sallamarshi wanda ke daidai da bugawar zuciyar zee
Saurin kauda kai tayi daga kofar Shigowa ta maida kan jakkarta dake gabanta ajiye tana jin kaka na amsa mashi
Jimm aka dan yi sai kuma taji kaka na cewa
"qaraso mana, ita ce din dai"
Sai a lokacin ta dago bata sauke idanun a koina ba sai cikin nashi
Saurin Janye nata tayi tana runtse su gam
_ya sallam!_ ta fada a zuciya
Bata ta6a sanin tayi missing dinshi har haka ba sai yanzu, jitake zuciyarta na kumbura tana sacewa don shauqi
Qarasowa Deen daya kafeta da idanu yayi kamar meson gasgata abinda idanunshi ke gani
"wlh itace, ina sallame sallah naji sallamarsu bama su dade da zuwa ba" inji kaka
Ida Qarasowa yayi ya cire takalminshi ya zauna kan tabarmar still idanunshi kanta
Be ta6a jin ya ta6a missing wata hallita ba kamar ita, ganinta kuma yau ba qaramin tado mashi tsumin kewar yayi ba
Dukda bashi take kallo ba tasan ita yake kallo don tana jin idanuwanshi akanta Hakan yasa taqi dagowa ta cigaba da kallon qasa tana wasa da zoben yatsarta
Cool voice dinshi taji yana cewa
"Kaka yaushe tazo?"
Lumshe idanu tayi ta bude, ya Allah! Tayi missing komai gameda gayen nan, har muryar
"basu jimaba wlh, nima abin yazo mun a bazata wlh kuma naji dadi sosai"
Maida kallonshi yayi akan zee din dataqi sake kallonshi can kuma yace
"yasu mummy?"
Dan dagowa tayi ta kalleshi saikuma ta kauda kai tana dan murmushi
"tana lfy, ya qarfin jiki?" tafada trying so hard wajen controlling muryarta
"Alhamdullilah, longest time"
Dan kallonshi kawai tayi sai kuma ta kauda kai tana jin takaicin maganar shi
Wai longest time, da yaso da ya kirata ko gaisawa sunayi amma ya share amma har yanada bakin cewa longest time
Haka kawai taji rashin kiran nashi na cimata rai, batama san tun ranar daya ajiye wayar be qara waiwayarta ba
"to kaka bari mutafi" inji zee din tana kallon kaka avoiding Deen's gaze
"haba badai tun yanzu ba Zainabu"
Qoqarin miqewa tsaye zee keyi tana cewa
"wlh kaka, mummy tace karmu dade ne"
Tashi itama kakan tayi da zee da Tundazu yakasa janye idanunta akanshi
"to ai mungode qwarai ma wlh, gashi dama azumi kike, to allah yasa asha ruwa lfy, kice ina gaida mamar taku sosai da sosai, ya kamata kyakyawana ka amshi lambar su yadda zamu dinga gaisawa" inji kaka
Kada kai Deen yayi alamun to saikuma yajuya yashige dakin kaka
Da kallon qasan ido ta rakashi sannan ta dauke kai ta duqa ta dauko ledar dasuka shigo daita ta ajiye gaban kaka tace
"gashinan kaka ba yawa"
"meye din? A'a wlh abin ai saiyayi yawa ga wancan ga wannan?"
"Kaka dan allah ki amsa ba yawa kawai kayan marmari ne"
Da farko qiyawa tayi amma daga baya saboda nacin zee ta amsa tana Godiya
"dan allah ki miqamin godiyata gareta idan kin koma, insha allah zan kira ma da kaina mu gaisa kibashi lambar ki"
Da to ta amsa kawai tana murmushi sannan tayi mata sallama ta nufi hanyar fita
Daidai nan Deen yafito daga dakin kaka yaga ta danyi nisa ma
"Kaka ina zuwa"
Da to kaka tabishi tana kallonshi ganin ya nufeta
Dukda tanajin alamun binta dayake Hakan besa ta nuna tasani ba bare ta tsaya
Daidai tashiga zaurensu taji muryar shi na cewa
"Zainab!.."
Cak ta tsaya ba don ta shirya ba sai don tasirin da kiran yayi agareta sosai
Qarasowa yayi ya tsaya bayanta yana dan basu tazara
"Tafiya zakuyi?" yafada yana kallon bayanta don bata juyoba
Ahankali ta juyo ta kalleshi suka kafe junansu da idanu without saying anything
Ahankali zee ta motsa baki tace
"eh, ko kanada matsala da Hakan ne?"
Murmushi ya dan saki yace
"A'a... Ga wannan" yafada yana miqamata wata baqar leda
Kallon ledar tayi saikuma ta kalleshi da ayar tambaya
Qara miqo mata yayi murmushi a fuskarshi Hakan yasa ta amsa ta bude tana leqawa
Kanta ne ya sara ganin kwalin wayar data siyomashi ce
Dagowa tayi ahankali tana kallonshi still da ayar tambaya
"ki maidama mummy kice mun gode qwarai amma bazan iya amsa ba, dawainiyar da kukayi akanmu ta isa, muna Godiya. Dama tun ranar dana ganta na maidata na adana akan idan kuka zo kamar yadda mummy tace ko muka hade a school inbaki, mun gode qwarai amma bazan iya amfani da wannan ba, yanzu haka ma nayi wata so no need na damuwa, kinga saiki samin number mummyn don su dinga gaisawa kamar yadda tace and also na warware please ku daina mana dawainiya haka nan, the one you did is appreciated and we'll continue to appreciate it..."
Saka hannu yayi a aljihu don lalubo wayarshi batareda ya lura da irin kallon da zee ta kafeshi dashi ba
Zaro yar qaramar wayarshi keypad qirar itel yayi ya miqamata yana cewa
"here, samun number"
Kallon nata ne ta janye daga kanshi ta maida akan yar ficikar wayar hannunshi tana feelings din da bata ta6a jin irin shi ba kuma ta rasa taqamaimai me takeji
Haushi? Takaici? Dana sani ko embarassment?
Ashe duk haukan ma datakeyi na jiran kiran shi ita kadai keyi?
Ko ta6a budewa beyi ba, wai ya adana ta don ya maida mata? And qarin gishiri a ciwo wai tabashi number mummy don su dinga gaisawa da kaka bama tabashi tata ba A'a ta mummy wato ita kadai ke haukanta he Don't care a bit about her
Wani abu mai daci2 taji ya ziyarci maqoshinta tana jin kamar ta dora hannu aka taita ihu
Ganin tayi tsaye tana kallonshi dakuma irin kallon datake mashi yasashi dan wara mata oily eyes dinshi yana cewa
"are you ok?".... ✍️
Ummin fasihu 🧚🏻♀?
8/2/21, 9:35 PM - Buhainat😝: *🙍🏻♂️DEEN 🙍🏻♂?*
*032*
*BAYAN KWANA BIYU*
Shiru zee tayi takasa cewa komai sai ma wasa datake da zoben hannunta
"am talking to you Zainab"
"mummy babu komai fa"
"babu komai kika koma haka? Just look at yourself amma kice babu komai? Ke kanki kinsan you're lying"
Sauke idanunta tayi tana kallon yatsun hannunta cikin rashin ta cewa
Dawowa mummy tayi ta zauna kusada ita tana kallonta
"Zainab..."
Dagowa zee tayi ta kalleta da idanunta dasuka fara salqin hawaye
"meke damunki? Are you sick?"
Girgiza kai tayi ahankali tana maida kanta kasa, ita kanta da tasan abinda ke damunta datafi kowa murna
"Zainab am your mother kuma bakida kamar ni.. Bakida wanda zaki fadawa matsalar ki kamar ni don haka karki 6oyemin komai, ki gayamin komai I can understand"
Yadda mummyn tayi magana tenderly yasa zuciyarta qara tsuma kan kace me sai hawaye
Kamo hannunta guda mummy tayi tana murzawa ahankali cikin sigar rarrashi wanda ta rabu dayi mata Hakan yasa zee kwantowa a kafadarta tana cigaba da hawayen
Hannu mummy tasa around her tayi mata side hug wanda Hakan yasa taqara narke mata
"tell me" inji mummy
Sniffing tayi sannan tace
"mummy am bored, am lonely. Banajin dadin komai, ina kadaici sosai"
Shiru mummy tayi can kuma tace
"shiyasa kika takurawa kanki har haka? Duka yanzu kwana nawa ya rage kuyi resuming school?"
"dukda haka mummy, am very lonely banida wanda zamu dinga hira, am always bored"
Ajiyar zuciya mummy tayi sai kuma tace
"ok, yanzu ya za'ayi? Kina son insamo miki training class, kona girki ko kwalliya or something like that?"
_no i want to see Deen_
Abinda tafada a zuciyarta kenan amma azahiri tace
"no mummy, I want to travel"
"travel? Ina?"
Dagowa zee tayi daga jikin mummyn sannan ta marairaice fuska
"Ruma, don Allah mummy kibari intafi"
Sakin baki mummy tayi tana kallonta
"ke kecewa zaki Ruma da kanki yau? Wonder shall never end"
Dan tura baki zee tayi tace
"mummy nafa rabu da zuwa"
"kin rabu da zuwa amma wancan zuwan qarshen ya kikace? Cewa fa kika yi baki qara zuwa kuma ma bazan bari kije ki takurawa mutane da daukar maganarki ba, never"
Sake marairaicewa tayi don sosai takeson tafiyar ko zata manta da wannan annoying fring din
"mummy please, nafa shiryu baki gani ba"
Sosai maganar zee taba mummy Dariya amma sai tayi dan murmushi tace
"kin dai shiryu and also duka yanzu saura kwana nawa kuyi resuming? Da zuwan ne ai da tun farkon hutun ya kamata kije amma yanzu kije hutu be kai sati biyu zai qare ba wannan zuwa hutu ne?"
"mummy ko sati daya ba sai nayi ba na dawo? I promised mum baxanyi komai ba nafa shiryu mummy na daina abubbuwa marar kyau"
Harararta mummy tayi ta tashi ta nufi closet dinta
"kinji mummy? Please.."
Batareda mummy ta juyo ba tace
"kije zan gayawa daddy duk yadda yace shikenan"
Dadi ne ya ziyarci zuciyarta taji kamar tayi ihun murna don tasan idan daddy ne batada case dashi amma sanin halin mummy abu kadan zaisa ta chanza ra'ayi yasa ta danne tace
"to mummy, allah yasa ya yarda"
Juyowa mummy tayi ta gallamata harara
"kamar duka kenan, salan kije ki kallalameshi kafin na gayamashi kiga idan ban soke tafiyar ba"
Daga hannu zee tayi tace
"A'a ni bazan kirashi ba, how dare me"
Ta6e baki mummy tayi ta cigaba da abinda take
Tashi zee tayi taimata sallama ta fita cikin zumidin tafiyar tanajin atlast zata rabu da kadaici bare har tunanin Deen ya samu gurbi a zuciyarta don ita duk tunaninta kadaici ke jawo tunanin nashi
Tana shiga daki ta murza key ta nufi bedside locker dinta ta dauki phone dinta ta zauna can qarshen gado ta lalubo number daddy ta dannamashi kira
Ba'a daga ba har Saida ta yanke tana qoqarin sake kira kiranshi yashigo
Cikin zumudi ta dauka ta kara akunne
"daddy na!"tafada cikin tsananin murna
Dariya daddy yayi daga can 6angaren yace
"na'am daughter din daddynta"
Murmushi tayi tace
"daddy I missed you!"
"missed you more and more jewel, amma alhamdullilah am coming back soon, me zan miki tsaraba?"
"komai ma daddy don kafini sanin abinda zai sani farinciki"
"really? To angama I'll make you happy insha allah"
"Allah ya yarda daddy"
Sai kuma tadanyi Jimm sannan cikin shagwa6e murya tace
"daddy?"
"yes? Daddy's pet"
"daddy am lonely, banajin dadin komai kullum kasa barci nake har kuka nake yi ma" tafada cikin narke fuska
"subhanallilah, but why?"
"am lonely, every thing seems boring gashi babu school kullum zaman gida na gaji" tafada kamar zatayi kuka
"oh please kar Kiyi kuka kinji? Ba gashi na kusan dawowa ba? Idan nadawo kullum saimun fita shaqatawa, idan bazaki iya jira bama gobe balarabe ya fita dake duk inda kikeso Kiyi shopping and every other thing that will make you happy uhm? Nakusan dawowa everything will be ok"
6ata fuska tayi don ba abinda takeso ba kenan
"Nidai daddy duk wadannan baxasuyi ba, na gaji ne da komai da garin, I want to go to Ruma, please"
"Ruma kuma daughter?"
"yes dad, please! Kaga na rabu dazuwa"
"to yaushe zaki dawo idan kika tafi yanzu, and kun kusa resuming ai"
"daddy yanzu saura kwana 12 muyi resuming, Kaga sai inyi 1 week acan kuma dama naji ance aunty Feenah tadawo kaga zamu ga juna dama rabona da ita tun kafin ta tafi a waya ma bamu cika magana ba, please kabarni naje daddy just 1 week zanyi nadawo, zanji dadi sosai zanyi farinciki" inji zee don tasan idan akwai abinda yakeso to farincikin ta ne
Ajiyar zuciya taji ya sauke daga can 6angaren yace
"Alright then, kin gayawa mummyn ki?"
Cikin zumudi tace
"eh daddy, tace ma zata kira ka ta gayamaka"
"ok idan takira zance mata tabarki kawai, yaushe kikeson zuwa?"
Ihun murnar da batayi ba dazu tayi tana cewa
"yes! Thank you my sweet daddy"
Murmushi mai sauti daddy yayi yace
"you're welcome, nace yaushe kikeson zuwa?"
"dad ko zuwa gobe haka, please kace tabarni natafi gobe"
"to shikenan an gama princess"
"yauwa daddy kuma fa karka cemata munyi maganar dakai don Saida tayimin warning akan Hakan, kawai kayi pretending bakasan da maganar ba if not she'll slaughter me"
Dariya daddy yayi sosai a dayan 6angaren sannan yace
"to angama dear, sai kuma me?"
"shikenan sweet daddy"
"to shikenan, I'll pretend bansan da maganar ba and also zanmiki transferring din sum amount sai ayiwa mutanen Ruma tsaraba"
Cikin jindadi sosai tace
"thank you so much daddy, muah! I love you"
Cikin Dariya yace
"love you more sweetie"
Da haka sukayi sallama ta koma ta jingina da gado beaming with smiles tanajin atlast zata rabu da qaya
Duk a tunaninta zama lonely ke kawo tunaninshi shiyasa ta yanke wannan shawarar na tafiya Ruma tasan ko yaya ne she'll feel better from what she's feeling now
Da wannan tunanin ta kwana ta tashi, haka taita baza kunnuwa taji me mummy zatace gameda tafiyar amma shiru
Tun tana jira harta sire don har magrib shiru batace mata komai ba
Sai bayan isha'i suna tsaka da dinner mummy tace mata ta shirya gobe zasu wuce Ruman
Dukda da farko fushin sharetan da mummy tayi take Hakan be hanata yin murna ba
A cikin daren ta harhada kayanta wadanda zasu isheta na zaman sati da tarkacen kayan amfani na yau da kullum
Medium trolley guda tacika ta ajiye gefe sannan ta kwanta tana Allah Allah gobe tayi ta shilla
*WASHEGARI*
Sai wajajen 12 rana suka bar gidan a motar da bala ke ja suka nufi garin Ruma dake qaramar hukumar batsari bayan mummy ta gama cikasu da tsarabobi da zata kaiwa yan uwanta mutanen Ruma
Tunda suka kamo hanya zee keta sauke Ajiyar zuciya tana fatan Hakan zai ragemata abinda takeji acan din
Bluetooth ta maqalawa kunnenta wanda cool music ke tashi a cikinshi ta dawo kusada window ta jingina tana kallon yadda suke wuce dajika da gudu, sosai abin ya nishadantar da ita don koina luff yake da ciyawu sunyi green abin sha'awa abunka da damuna wannan scene din ya mantar da ita abubbuwan dake damunta a zuciya ta kama jinta wasai
Anata sallar azahar suka isa cikin garin.
Direct gidansu mummy suka wuce wanda keda girma ba laifi kallo daya zakayi mashi kasan na masu rufin asirine sosai
Saida yayi horn sau uku sannan aka bude qaramar kofar gate din aka leqo sai kuma aka koma can aka shiga bude dan madaidaicin gate din
Shigar da motar bala yayi, yayi parking a parking space din wajen da beda girma sosai sannan ya fito ya zagayo ya budemata
Saka bluetooth din data ciro daga kunnenta tayi cikin jakka sannan ta zuro kafarta tafito daga cikin motar
Shaqar iskar garin tayi sannan ta fesar tana jin wani dadi har cikin zuciyarta
Rataya jakkarta tayi a kafada ta saka siririn spec dinta sannan ta nufi cikin gidan yayinda bala da maigadi da shima ya qaraso wajen ke qaqaniyar ciro kayanta dake booth
Knocking tayi a main door sannan ta murda handle din ta bude tashiga bakinta dauke da sallama
Da farko tayi tunanin babu kowa a falon Saida ta qarasa shigowa ciki sannan taga wata budurwa kwance cikin kujera waya kare a kunnenta tana kallon zee din data shigo
Murmushi zee tayi mata itama ta dan maida mata martani sannan tace
"I'll call you back" Daga nan ta katse kiran
Qara dagowa tayi ta kalli zee dake kallonta itama fuska dauke da murmushi
"mutanen katsina ne a wannan tsakar ranan?" tafada cikin maqaqqiyar murya datafi kama data mage
Qarasowa zee tayi ta zauna a kujerar dake facing dinta
"yeah, hope mun sameku lfy"
"lfy lau" inji budurwar sai kuma ta maida kanta kan wayar ta
Bata damu ba don tasan wacece Feenah da hallayenta kuma wai nan don ma suna d'asawa da zee saboda halinsu daya kusan zuwa daya yasa ta tsaya ta tankamata haka
Feenah itace autarsu mummy, mace mai shegen yanga da jin kai
Ga tsiwa don bata ragawa kowa, duk cikin 'ya'yan *Umma* wato kakar zee babu wanda ya kaita kyau
Tanada kyau irin na asalin rumawa ga jiki dan d'as daidai ita. Feenah irin classic ladies dinnan ne masu ji da wayewa don tama lunka zee ta shanye a wannan fannin.
Tanada fada sosai ga batason raini kwata2 shiyasa basa shiri da 'ya'yan yayyanta dasuke a matsayin 'ya'yanta itama sai zee da halinsu yakusan zuwa daya don dama kowa cewa yake ita ta gado a halin jin kai da yanga da gayu
Feenah yar gayu ce ta qarshe mai jida wayewa, yanzu haka ko sati batayiba da dawowa daga france inda take karatu wanda dawowar ta din din din ce don ta riga ta kammala karatun
"kunyi graduating, allah ya sanya alhairi"
Dagowa Feenah tayi ta watsamata wata harara tace
"Sai yanzu zaki yimin allah sanya alhairi? Kwana na nawa da dawowa amma ko kira bayan am very sure kinsan da dawowata"
"kai Aunty Feenah! Shiyasa fa na taso takanas nazo don nayimiki, ai kinfi qarfin nayimiki ta waya shiyasa na shiryo na taho"
Wata hararar Feenah taqara watsamata tace
"eh, maidani shashasha wacce batasan abinda take ba, yarinya gaba na aka haifeki tun kafin kisan kanki nasan basaja, ehe"
Dariya zee tadanyi tace
"haba uwas! Kar kisa ajimu aimana Dariya, ni da uwata haka muke🤞🏻babu mai jinmu"
Wani kallon sheqeqe tayi mata tace
"ku nawa kuke Hakan 🤞🏻? Keda waya ma Dakyar kike kirana sau daya a wata kuma ki kirani da uwa? Ina kika ta6ajin haka?"
"yanzu dai komai yawuce aunty Feenah, allah ya huci zuciyarki ai tsakanin uwa da diya sai allah, shiyasa ma nazo takanas don na goge laifina"
Harararta Feenah tayi ta kauda kai
Dariya zee tayi tace
"tuba nake ran uwata ya dade"
Dan ta6e baki tayi a yangace sannan tace
"ya wuce.. How's your studies?"
"Alhamdullilah aunty, hutu ma muke amma zamuyi resuming very soon"
"Ayyah, allah ya taimaka"
"amin... Ina hajiya granny?"
"hmm tana can dakinta yanzu ta koroni da chazbi"
Tashi zee tayi tana Dariya
"kin ta6ota kenan?"
"wai don nayiwa wannan qazamin yaron sultan tsawa shine ta koroni ita mai jika"
Dariya zee tayi ta nufi hanyar dazai sadata da cikin main gidan tana cewa
"Allah dai granny nayi missing dinta ai"
"ai gaki gata wannan karon ma da fada zaku rabu i bet you"
Dariya Kawai zee tayi ta shige itakuma Feenah ta maida hankalinta kan wayar ta
Direct part din Umma ta wuce cikeda dokin ganin ta
Da sallama tashiga falon umman tana cewa
"granny! Granny! Am back!"
Jin shiru yasata ajiye jakkarta a sofa tana qara cewa
"granny! Wai ina kike..."
Bayyanar umman ya katseta saitayi wajenta aguje ta rungumeta tana Dariya
Qoqarin kwace kanta take daga riqon zee tana cewa
"wai wace yar malfar uba ce wannan?"
Dagowa zee tayi tana Dariya
"kai Umma, nice yar malfar uba?"
"yo banda shaqiyanci saiki shigo min gida ba sallama ba komai sai iface iface, shegiya mai kama da uwarta ta falo, dama yanzu itama nagama zaneta saura ke wlh"
"haba dai, ai muda duka sai ruwan sama kiji ingayamaki, don ma kinsamu anzo ana murnar ganinki? To nafasa murnar ma" tafada tana komawa kan kujera ta zauna ta rungume hannaye a qirji tana kumburi
"kanki akeji" inji Umma tana qarasowa itama ta zauna
"wai yama naga qaffafunki a gidan nan? Jinake ke da kanki kikace ke da nan har illa masha allahu"
"yo dama in don takece wazai zo? Ni wajensu kawu nazo da Aunty Feenah"
"haka fa, ai kin aikata, tunda ga uwarki dakikayo gadon komai nata ta dawo ai dole kema kizo yadda zaku taru ku samun ciwon kai, to wlh kubi a sannu, yanzu ba da bace yanzu kana yimin abinda bemun ba zan zane mutum radam da wannan charbin" tafada tana daga mata chazbahar hannunta
"inyee! Su granny an qaro wulaqanci, to bari na kama kaina, nama fasa zama dakinki dakin Aunty Feenah zan sauka, kar kin tashi cikin dare kin kasa barci ki juya kiga ina nawa cikin kwanciyar hankali kiji haushi kihau zugamun ita" tafada tana miqewa tsaye tana wucewa dakin Feenah dake kusada dakin Umma tana cewa
"mutum yayo tafiyayya yazo ganinka ko sannu da zuwa bare Ayi maganar ruwa saima maganar charbi da aka tareshi dashi, kai wannan grannyn her wahala is too much" tafada tana shigewa dakin
"eh zaggani dakyau kinji? Ja'ira mai zubin mami water idan abin Gaskiya ne Kiyi yaren dazan gane mana kuma anqi ayimiki sannu da zuwan, dake da sannu da zuwan na hada ku nayi muku qumuss, dama zuwa na kika yi da zan wani fara yimaki maraba, kijuya ki koma inda kika fitomana kiga wazai damu, aikin banja kawai" tafada tana tashi ta koma dakinta itama tana cigaba da surutai
Bata dade da shiga ba Feenah ta shigo ta tararda zee tafito daga toilet daure da alwala
Bata cemata komai ba sai wucewar datayi kan gado ta zauna
Qarasowa cikin dakin zee tayi tana gyara yafin gyalenta
"Aunty Feenah, ba'a shigo da kayana bane?"
"suna falo" inji Feenah
"kai Aunty Feenah, shine ko ki taimaka ki qarasomin dasu"
Wani kallon up and down tayi mata ta kamar dakai batareda tace komai ba
Wucewa zee tayi closet dinta ta zaro daya daga cikin hijjabin Feenah da sallaya tana cewa
"baqonka dai annabinka Aunty"
Ta6e baki Feenah tayi tace
"su ru6e a falon indai ni zan qaraso miki dasu ciki"
Zee bata qara cewa komai ba ta kabbara sallar zuhr daya riskesu kan hanya
Lokacin da tagama Feenah bata dakin Hakan yasa ta miqe ta cire hijab din ta linke ta maida da sallayar sannan ta yafa gyalenta ta zauna gefen gado ta dannama mummy kira don fadamata isarsu
Saida tagama wayar daita sannan ta bugama daddy shima ta fada mashi sun dan dade suna fira sannan sukayi sallama ta tashi ta fita
Falon farko tafara komawa ta dauko kayanta ta kawosu dakin Feenah sannan ta bude jakkar tsarabobin datayi ta warewa kowa nashi sannan ta tashi ta fita da nasu kawunnanta
Gidan dama part uku ne, na farko na kawu yusuf yayan mummy yanada mata daya da 'ya'ya hudu
Na biyu na kawu Umar qanin mummy mai bimata yanada mata shima da 'ya'ya biyu
Sai na ukun part din Umma wato mahaifiyarsu mummy inda take zaune da Feenah don dama' ya'yanta hudu rayyayu mijinta kuma tun Feenah na qarama allah yayi mashi rasuwa
Part din kawu yusuf tafara zuwa
Tun daga bakin qofa yaran suka tareta sunata tsallen murna
Itama zee rungume su tayi tana Dariya don Allah yayi ta da son 'ya'ya sa6anin Feenah da bata son 'ya'ya sam shiyasa yaran su kawun basa shigemata don sunsan sauran
Tare suka qarasa cikin falon sunata tsallen murna suna ina tsarabarsu
Zama tayi tana dora sultan akan cinyarta tana Dariyar musun da sukeyi akan wa za'a fara ba tsarabar
Ahaka mamansu tafito ta taddasu, riqe baki tayi cikin mammakin ganin ganin zee kamar daga sama
Qarasowa tayi tana tsawatarwa yaran akan su rufewa mutane baki sun bi sun cika mutane da surutu
Duk shiru sukayi kowanne na turo baki gaba
"A'a Aunty Raliya, kawai sai ki hana yara taryar yayarsu, kai kowa yazo, line up according to your age sai na baku"
Kamar jira suke sai suka taso cikin zumudi sukayi layi kowa fuska washe
Nan tashiga ciro tsarabar su tana basu daya bayan daya kowanne murna da Godiya
Sai da tagama basu sannan Aunty Raliya ta kada kansu ta korasu dakin su ko kunnensu zasu huta sannan ta juyo kan Zainab
"zee baby! Saukar yaushe? Har angama fushin? Ina alwashin kuma?"
Dariya tayi tace
"hmm kedai bari Aunty ai haryanzu alwashin na nan daram dam yanzu ma ai ba zuwanku nayi ba zuwan Aunty Feenah ce"
"to? Muma ai bamu gayya, can ku qarata daga ke har Feenar dama ina ciki daita dazu ta gigitomin auta to wlh ki gayamata ta kiyayi haduwarmu"
Tashi zee tayi tace
"A'a nan fa daya, gwara ki sameta da kanki don waqa a bakin me ita tafi dadi, ina uncle?"
"ana wajen aiki, yasu Aunty maimunar?"
"tana can lafiya lau tana gaidaku ga wannan bari nawuce part din kawu umar"
"to? Harda mu tsarabar? Gaskiya mun gode qwarai allah yasaka da alhairi"
Da amin ta amsa tana ficewa daga dakin tabar part din tawuce dayan part din na kawu umar
Suma a falo yaran suke suna homework
Jin sallamarta yasa duk suka
All Chapters
Chapter 1
Chapter 2
Chapter 3
Chapter 4
Chapter 5
Chapter 6
Chapter 7
Chapter 8
Chapter 9
Chapter 10
Chapter 11
Chapter 12
Chapter 13
Chapter 14
Chapter 15
Chapter 16
Chapter 17
Chapter 18
Chapter 19
Chapter 20
Chapter 21
Chapter 22
Chapter 23
Chapter 24
Chapter 25
Chapter 26
Chapter 27
Chapter 28
Chapter 29
Chapter 30
Chapter 31
Chapter 32
Chapter 33
Chapter 34
Chapter 35
Chapter 36
Chapter 37
Chapter 38
Chapter 39
Chapter 40
Chapter 41
Chapter 42
Chapter 43
Chapter 44
Chapter 45
Chapter 46
Chapter 47
Chapter 48
Chapter 49
Chapter 50
Chapter 51
Chapter 52
Chapter 53
Chapter 54
Chapter 55
Chapter 56
Chapter 57
Chapter 58
Chapter 59
Chapter 60
Chapter 61
Chapter 62
Chapter 63
Chapter 64
Chapter 65
Chapter 66
Chapter 67
Chapter 68
Chapter 69
Chapter 70
Chapter 71
Chapter 72
Chapter 73
Chapter 74
Chapter 75
Chapter 76
Chapter 77
Chapter 78
Chapter 79
Chapter 80
Chapter 81
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 23 Chapter of 81