Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
da zaiyi amfani daita wurin rarrashinta "dan allah kibar kukan nan haka, insha allah allah zai tashi kafadunshi, a halin yanzu yafi buqatar addu'armu fiyeda komai, kiyi hqr allah baya dorawa bawa abinda bazai iyaba" yafada cikin rarrashi Hakan ya dan taimaka don ta rage kukan sai shesheqa datakeyi akai2 jin kanta take kamar ba nata ba, kamar ta cire ta jefar ko zata huta Shiru wajen ya dauka kowa da saqe saqen dayake duk suna jiran tsanmmani yayinda hankalin mai adaidaita duk yayi gida yasan matarshi nacan hankalinta atashe, sake duba agogon wayarshi yayi yaga 11 takusa gashi batada waya bare ya kirata ya gayamata halin da ake ciki Gashi ita kadai ke gidan kasancewar duka2 watansu bakwai da aure yanzu haka ciki gareta na wata biyar Hakan yasa yaji duk hankalinshi yayi gida don yasan duk inda take hankalinta a tashe yake shi gudu ma yake kar tace zata fita cikin daren nan don yasan halinta qaramin aikinta ne tace zata tafi nemanshi gidansu, gashi Tundazu yake neman wayar qannenshi bata shiga Komawa yayi ya jingina da kujerar ya harde hannayenshi a qirji yana karkada kafaffu, allah allah kawai yake mutumin dasukayi waya dashi yanzu din ya qaraso ko zai samu shima yatafi don bazai iya barinsu ba a wannan halin... ✍️ Manage👏 Ummin fasihu 🧚🏻‍♀? 8/2/21, 9:34 PM - Buhainat😝: *🙍🏻‍♂️DEEN 🙍🏻‍♂?* *024* Zaune suke Shiru na wani lokaci, can ringing wayar mutumin ta dawo da kowanne daga duniyar tunaninshi Duba wayar yayi yaga daddy ne Dagowa yayi ya kalli zee dake kallonshi itama "shine, qila sun qaraso" yafada yana dan yimata murmushi sannan ya daga "assalamu alaikum" "wslm, d'ana gamunan mun qaraso kuna ina ne?" "ok bari nazo reception sai nataho daku" inji mai adaidaitan sannan ya katse kiran Kallon zee dake suraronsu Tundazu yayi "bari naje na taho dasu" Kada mashi kai kawai tayi ya tashi ya tafi Lumshe idanu tayi tana jin yadda kanta ke sara haryanzu Koda mai adaidaitan yaje reception waige2 yashigayi don ganin inda zai hango mutumin Yana cikin haka yaji an dafashi saurin juyowa yayi saiyaci karo da wasu yan sanda biyu, daya hannunshi riqe da waya yana kira yayinda daidai lokacin wayar mai adaidaitan tafara ringing "shine" inji mai kiran yana sauke wayar daga kunne Binsu da kallo mai adawo keyi gabanshi na faduwa, shine wa? Meye kuma nashi da yan sanda? Kamar sun karanci tsoronshi don haka daya yace "karka damu abokina, ni sunana A.s.p Jamal Qaseem, muna tareda mahaifin wannan yarinyar, fatan kaine mukayi waya dashi dazu" Kada masu kai kawai yayi don shi bega abin tattago yan sanda ba a wannan case din "ok muje, gasucan ku gana" inji dayan yana gwadamashi hanya Ba musu yawuce suka takemashi baya har suka isa parking space daga gefe inda wata dalleliyar mota ke a parke securities takoina Qarasowarsu wajen yasa A.s.p Jamal yawuce wajen motar ya kwankwasa Mai adaidaitan besan ko me yace ba sai gani yayi an bybbude back seat din an fito Wani mutum yagani wanda kallo daya zaka mashi ka gane ba qaramin mutum bane saboda cikar haiba da qwarjini irinna masu arziqi sai macen da kallo daya zaka mata kasan jinin zee ce saboda matsananciyar kama dasukeyi Cikin nutsuwa suka qaraso wajensu mai adaidaitan, daddy na kafeshi da kallo Sauke kanshi yayi cikin jin nauyin daddyn ya shiga gaidasu yana dan russunawa cikin zuciyarshi yana gulmar wai ashe masu kudine wadanda ya taimaka? Amsawa sukayi atare sannan daddy yace "bawan Allah kaine mukayi waya dakai yanzu?" Qara dan duqar dakai yayi yace "eh alhaji nine" Ajiyar zuciya daddy ya sauke na jindadi yace "to ina take? Ina daughter? Hope babu abinda ya sameta" yafada cikin damuwa Kada kai mai adaidaitan yayi yace "babu abinda ya sameta insha Allah, muje ku ganta" yafada yana basu hanya "yauwa muje" Nan suka shiga asibitin bisa jagorancin mai adaidaitan Zee dake zaune haryanzu Saidai yanzu ta hada kai da gwiwa tayi shiru taji alamun tafiyar mutane na kusantota Hakan yasata dagowa da jajjayen idanun ta Su daddy da mummy ta hango tafe da wasu mutane da bata wani tsaya tantancesu ba Tashi tayi azabure ta nufi daddy da gudu Fadawa jikinshi tayi ta kankameshi tana sake Fashewa da kukan da yanzu yabar zuwa da hawaye don suma idanun izuwa yanzu sun gaji da zubda kwalar Maida hannuwa shima daddy yayi a bayanta ya rungumeta yana sauke ajiyar zuciya Dagota yayi yayi cupping fuskarta a taffukan hannunshi yana bin fuskarta da kallo "are you ok daughter? What happened? Meya samu fuskarki?" yafada yana bin fuskarta da duk sahun yatsun marukan datasha suka fito sukayi jajur abinka da farar fata kuma ta hutu Batace komai ba sai qara komawa jikinshi datayi tana cigaba da kukan Janta yayi wajen kujerar data taso ya zaunar daita shima ya zauna ya cigaba da rarrashinta A dayan bangaren kuma mai adaidaita wanda yace sunanshi Ahmad yake bawa yan sandan bayyanin yadda suka hadu dasu dakuma inda yagansu Saida suka gama sauraron dukkan bayaninshi sannan ya nemi su barshi yatafi gida don yabaro iyalinshi ga kuma halin datake aciki Basu qi ba Saidai sun amshi number wayarshi sannan mummy tayita mashi godiya da fatan gamawa da duniya lafiya Saida zai tafi sannan daddy shima yataso daga wajen zee dake narke jikinshi yana ta rarrashi Tundazu yazo shima yaita yimashi godiya yakuma debo kudade masu yawa yabashi, dafarko yaqi amsa amma ganin ya nace yasa ya amsa ba don yasoba ya tafi da alqawarin zai shigo gobe insha allah yaga mai jiki Daga nan office din Dr Basira suka nufa don zee ta nace akan itadai Deen, karya mutu Sosai Dr tayi mammakin ganin babban mutum kamar Alhaji Farouq a office dinta Tarba tayi masu na mutunci sannan sukayi mata bayyani Tayi mammaki sosai ganin cewa ashe diyar dan faranshi tayima haka, Hakan yasa ta tashi tafara rawar jiki wajen ganin an kula da Deen yadda ya kamata sannan ta qara gayamasu ana buqatar jini cikin gaggawa don nashi yayi qasa kuma gashi babu irin nashi a hospital din Abunka da manya waya kawai Alhaji yayi wa family doctor dinsu ya fadamashi buqatar shi, cikin qanqanin lokaci saigashi a hospital din da jinin nan aka shiga qaramashi ana bashi taimakon gaggawa wanda za'a samu adan shawo kanshi kafin gobe da safe da za'a basu transfer sukoma wata asibitin Zee ma daga baya kwantar daita akayi saboda wani zazzafan zazza6ine ya lullu6eta itama, Hakan yasa aka bata gado itama aka duqufa akan su biyun don ganin an shawo kan matsalarsu. *KAKA* Tunda aka fara iska iskar hadari hankalin kaka yaqi kwanciya Sai duban hanya take taga ta inda Deen zai 6ullo amma Shiru kakeji Hankalinta ne ya ida tashi lokacin da aka kece da ruwa, idan ta tuna da kayan daya fita dasu sai hankalinta yaqara tashi Haka ta zauna bakin kofar dakinta ta buga tagumi tana hango qofar shigowa cikin jiran tsanmmani amma Shiru kakeji wai mallam yaci shurwa Tun tana daukar abin wasa har abin yafara bata tsoro, tun tana jiran agama ruwan har taji bata iya wannan haqurin. Hakan yasa tafito cikin ruwan tareda yar lemar ta (umbrella) ta nufi gidan maqofcinsu wanda ya samomashi form din company dinnan Ta dade tana bubbugawa sannan aka bude gidan Sosai maqofcin wato mallam Nasiru yayi mammakin ganin kaka cikin wannan ruwan da ake tsugawa Iso yayi mata ta shigo ciki nan tashiga gayamashi abinda ke faruwa cikin matsar qwalla Kwantar mata da hankali mallam Nasiru da matarshi suka yi da cewa wataqila fakewa yayi har ruwan ya dan tsagaita sannan yataho tunda shima yasan da lalurarshi bazai yarda yashiga ruwan ba Da wannan hankalin kaka ya dan kwanta Saidai still takasa komawa daidai, bini bini ta kalli agogo zuciyarta na qara tsunduma cikin fargaba Haka dai matar mallam Nasiru ta zauna da ita suna jiran tsanmmani Ganin har magrib ta gabato babu Deen ba alamunshi yasa hankalinta ida dugunzuma Kuka kawai takeyi tana cewa itadai makarantar nan zata tafi, tana ji aranta duk inda Kamal yake ba lafiya ba Tun Mallam Nasiru na rarrashinta akan tabari ruwan ya tsagaita har ya haqura yaje yasamo mai adaidaita na cikin unguwa suka shiga dashi da kakar mai adaidaitan yajasu zuwa makarantar Kafin su isa makarantar ruwa ya tsagaita sosai don harya koma yayyafi A bakin gate din makarantar suka sauka sukaje nufi wajen mai gadi Sosai mai gadin yayi mammaki jin wai wani suka zo nema nan yace musu gaskiya baya tunanin akwai sauran student ko daya a school din don tun hadarin nafara taruwa suka fito dama ba yawa garesu ba yan qallilan ne dake qarasa Jarabawarsu yau kuma suna fitowa motar school ta kwashesu ta tafi dasu don kosun tsaya ba samun abin hawa zasuyi ba Dukda haka kaka tayi insisting akan itadai a duba wataqila shi be fitoba Babu yadda suka iya haka suka shiga makarantar aka fara nemanshi Every nook and cranny saida suka duba babu Deen babu alamunshi, kuka kau kaka ta shashi harta godewa allah Dakyar aka rarrasheta akan su koma gida sugani qila yakoma, wataqila harda shi aka shiga bus din saiya fake cikin unguwa kafin ruwan ya tsagaita Haka suka fita suka shiga napep din kaka nata kuka suka nufi gida kowa na addu'ar allah yasa su taddashi gidan Fitarsu kaka daga school din keda wuya motarsu daddy ma tashigo Suma the same story ne da kaka don ruwan saman ya hana bala zuwa daukanta sai yanzu suka samu yadan tsagaita suka taho Saidai suma the same amsa mai gadin yafada masu Suma basu yarda ba suka shiga school din suka duba koina babu ita ba alamunta Saidai duk nemansu babu wanda ranshi yabashi su duba can bayan school din don basu ta6a kawoma ransu ba don school din nada girma da fadi kuma can bayan school din duk jejine bazasu ta6a kawo ma ransu zasu nufi wajen ba Suma haka suka haqura suka tafi Wasa wasa abu qarami yazama babba don koda su kaka suka dawo gida babu Deen Hakan yasa hankalin kaka yayi qololuwar tashi, kuka take tana fadin dan allah a nemomata dan marayanta, bashi da kowa sai ita itama batada kowa sai shi Cikin qanqanin lokaci labari ya kewaye unguwa, Deen din kaka ya 6ata Saigashi cikin daren nan gungun mazan unguwar, matasa da dattijawa suka bazama neman Deen yayinda mata sukaita shigowa gidan kaka suka zauna daita anata rarrashi da jaje A bangaren su daddy kau koda labari ya riskeshi akan ba'a ganta a school ba hankalin shi ne ya tashi, gashi anata neman number ta bata shiga Hakan yasa shima fitowa aka shiga neman dashi Dafarko police station suka nufa inda daga nan aka qara komawa school din don qara bincikawa Agefe kuma aka kira school authority din aka gayamashi abinda ke faruwa Hankali tashe shima yakira wasu manyan school din suka dunguma sukayi school din Sosai aka shiga nema again ana chaje koina na school din Saidai babu ita. Hankalin daddy yatashi sosai Hakan yasa ya baza jami'an tsaro akoina don nemo mashi tilon diyarshi Itama mummy hankalinta ya tashi sosai, tsakanin uwa da 'ya sai allah saigashi sai dauke hawaye take akai2, addu'arta kawai allah ya karemata diyarta a duk inda take Sai wajajen shadaya ne kira yashigo wayar mummy, tana ganin kiran taji ajikinta cewa kiran nada alaqa da Zainab Hakan yasa tayi saurin dagawa Jin kukan Zainab yasata yin sallalami takira sunanta wanda Hakan yaja hankalin daddy dake gefe baya zaune baya tsaye yana amsar kira takoina To shine fa yazo ya amshe wayar hannun mummy inda anan sukaji ainahin inda zee din take. A bangaren kaka kau kwanan zaune tayi akan sallaya don wajajen shabiyu tawagar neman Deen suka dawo basu ganshi ba amma sun aje akan gobe da angama sallar asuba zasu qara bazama nemanshi dukda sunkai rahoto a station din unguwar Abinda zai burgeka shine yadda kowa ke jajjantawa al'amarin dakuma yadda kowa ya damu don masha allah Deen mutumin mutane ne bayada matsala ko kadan Duk wanda ya budi bakinshi a wajen sai kaji yanata kwararo yabone akanshi Dakyar dai matan suka samu suka lalla6a kaka tabar kuka sannan dayawa suka koma gida suna fatan allah ya bayyanashi inda wasu kamar su matar mallam Nasiru da wata dattijuwa tsarar kaka wanda suke amintaka sosai da ita suka tayata kwana Yadda kaka taga rana haka taga dare don kwana tayi zaune akan sallaya tana kwararo ma Deen addu'o'in tsari a duk inda yake *WASHEGARI* Alhamdulillah zee taji sauqi sosai don yanzu babu wani zazza6i a jikinta sai murar datake dakuma yan ciwukkan dataji da akayi treating dinsu Da safen akayiwa Deen da har yanzu bai farkaba transfer daga wannan asibitin zuwa asibitin kudi inda family doctor dinsu yake Duk yadda akaso zee tabi mummy su koma gida don itama ta huta qi tayi da taga za'a matsamata ma saita sa kuka Hakan yasa daddy yace abarta don idan akwai abinda ya tsana to kukan shalelenshi ne Acan private hospital din yan sandan jiya wato su A.s.p Jamal suka iskesu, lokacin har anyi admitting din Deen likitoci sun duqufa akanshi suna baje kolin basirarsu ta wannan fannin Zee suka samu suka nemi ta gayamasu duk abinda yafaru Bata 6oyemusu komai ba ta warware masu duk abinda yafaru tana kuka Ran Alhaji farouq ya 6aci sosai yabada umarnin aje akamo masu sa hannu a wannan abin duk inda suke sannan a dayan 6angaren kuma a nemo dangin Deen don yasan suma sunacan cikin tashin hankali Amsawa sukayi da angama suna bashi tabbacin cika aikinsu yadda ya kamata *UMYAU* School ne ya rikice lokacin da labarin abinda yafaru jiya ya riski yan tsirarun mutanen dasuka zo school din Abin be ida rikicewa ba saida yan sanda suka dira school din Can bayan school din kamar yadda zee tayimasu bayani suka nufa inda anan suka tsinci littatafan Deen dasuka jiqe suka 6aci da cha6i sai jakkar zee da gyallenta sai agogon daya daga cikinsu master Sosai hankalin mallaman makarantar yatashi jin abinda yafaru a bakin polisawan Nan da nan aka fifiddo files dinsu master dasu sumee na makarantar don bincike Babu 6ata lokaci aka watsa yan sanda don kamo mutanen da ake zargi Cikin sauqi aka ritsa dasu sumee kowacce a gidansu Zokaga tashin hankali wajen wadannan ahali dasu kansu su sumee Abin yazo masu mugun bazata don ko kusa basu ta6a tunanin abin zai juye masu haka ba tunda su aganinsu an riga an gama daita babu yadda za'ayi a zargesu Duk hada kansu akayi akayi station dasu aka garqame A bangaren su master kau, anyi neman duniyan nan ba'a gansu ba don kowannensu babu wanda iyayensu ko danginsu suka san inda suke, wasu ma rabon da susasu dansu a idanu mantuwar harta manta musanmman ma iyayen master wadanda sun tsufa ga talauci daya qarawa tsufan tsanani Abin tausayi haka aka kama uban kowanne aka riqe akan idan aka ganosu za'a sakesu Zokaga kuka a wajen wadannan ahali musanmman na master, uwar tayi kuka kamar zata shide, fadi take allah ya isa tsakaninta da murtala, bazata ta6a yafemashi ba kuma tayi danasanin haihuwarshi datayi Abu dai ba dadi, sai bayan an kukkulesu ne sannan aka samu wani yazo yafadama yan sandan gidan da su mastern suke kwana amma koda sukaje babu su babu alamunsu donma ga yadda suka iske dakin a hargitse wardrobe dinsu babu komai ya tabbatar musu sun gudu. Hakan yasa aka baza matakan tsaro akoina harda tashoshin motoci da airport don kama wadannan shaidanun *KAKA* Kamar yadda mutanen unguwa sukayi alqawari saigashi suna gama sallar asuba suka sake taruwa don fita nemanshi Kasa kansu sukayi kashi2 inda kowa da inda ya nufa yadda abin zaifi zuwa da sauqi sannan suka bazama Kaka kau kallo daya zakamata tabaka tausayi saboda har ramar dare daya saida tayi Kan kace me? Gida yafara cika da mata yan jaje, a unguwa duk inda ka wuce sai kaji ana labarin 6acewar Deen din Kaka mai koko. Wajajen qarfe tara saura yansanda suka dira kofar gidansu Deen. Nan suka nemi iso cikin gidan sannan suka shiga Haka aka rakasu dakin Kaka inda take zaune ba uhm ba uhm uhm sai yar charbinta datake ja Ganin yansandan hankalinta yaqara tashi jin maganar Deen ce takawosu Saida suka kwantar mata da hankali sosai sannan suka sanar daita Deen na asibiti dukda basu fadamata halin dayake ciki ba Nan take gida ya kaure da koke koke, Kaka nayi mutane nayi, yan kadan ne masu rarrashi Haka Kaka tafito tana shar6ar kuka da ita da matar mallam Nasiru da Baaba Abu aminiyarta suka bi yansandan bayan kowacce mace tafito an rufe gidan A motar ne matar mallam Nasiru ta bugawa mallam Nasirun waya akan anga Deen yana asibiti takuma fadamashi sunan asibitin Su zee na zaune a waiting room tareda daddy su Kaka suka iso Sosai Kaka ke kuka akan abari ta ganshi Haquri akaita bata akan tayi Haquri likitoci ke ciki tabari sugama aikinsu Dukda Hakan batayi Shiru ba sai kuka take tana su taimaka mata shi kadai gareta Haquri duk akaita bata akan ta kwantar da hankalinta insha allah komai zaizo da sauki Dakyar aka samu ta zaune tayi shiru Saidai kwata2 hawayenta sunqi tsayawa Zuwansu Kaka ba qaramin sake dagulama zee lissafi yayi ba don itama kukan nata da akasamu yayi sauqi ta cigaba dayi, tanajin cewa duk itace silar komai, idan wani abu yafaru da Deen tasan bazata ta6a yafewa kanta ba Ana haka su mallam Nasiru da kingin yan tawagar neman Deen din suka qaraso, nan aka hadu aka tsaya jiran tsanmmani... ✍️ Manage 👏 babu dai editing, mugun wuya yake mun aradu☹️ Ummin fasihu 🧚🏻‍♀? 8/2/21, 9:34 PM - Buhainat😝: *🙍🏻‍♂️DEEN 🙍🏻‍♂?* *025* Sun jima anan sosai sannan likitocin suka fito daga dakin da aka kwantar da Deen din Mutanen na kyalla ido suka ga fitowarsu duk sai suka tashi kowa cikin jiran jin abinda likitocin zasu ce Matsowa kaka tayi gabansu likitocin cikin hawaye tace "Likita ya ake ciki? Ina jikana? Meya sameshi?" Shima daddy ya taso ya matso wajensu, zee a gefenshi itama cikin zaquwar tasan halin da Deen din ke ciki "Dr how is he now?" inji daddyn Family Dr dinsu dake kan gaba a kula da Deen din yace "Alhamdulillah, ku kwantar da hankalinku. Insha allah zaiji sauqi kai yama ji sauqi insha allah, yanzu dai Alhaji muje office akwai bayyanan da zan maku gamedashi acan" Caraff kaka tace "harda ni za'aiwa bayanin, ni kakarsa ce bayada kowa saini nima banida kowa saishi ku taimaka ku fadamin wani hali yake ciki, ku kaini wajenshi don Allah" ta qarashe tana rufe fuska da gefen zani Dafa kafadarta Baaba Abu tayi cikin sigar rarrashi itama tana matsar kwalla "eh, ita grandma dinshi ce, i think itama tanada ikon jin abinda ke faruwa tunda itama makusanciyarshi ce" inji daddy "ba damuwa, muje office din" inji Dr din yana yin gaba Juyawa daddy yayi ga zee datake tsane idanunta da farin hankin hannunta yayi cupping din fuskarta "dear, bari muje uhm? Kijiramu anan ok?" yafada a tausashe Ahankali ta Kada kai, kiss ya mannamata a goshi sannan ya nemi wani acikin maxan yazo shima, nan mallam Nasiru yazo suka wuce tare, ita kau kaka tuni tayi gaba Binsu da kallo zee tayi har suka shige sannan ta maida kallonta kan kofar dakin da Deen din yake ta kafeta da ido, jitake kamar taje ta bude tashige ta ganshi ko zataji sanyi sanyi a ranta Komawa tayi ta zauna ta jingina da jikin kujerar tareda lumshe gajiyayun idanunta tana jiran fitowarsu daddy *OFFICE* Tunda Dr yafara bayyani kaka keta kuka harya kai aya "innalillahi waina ilaihi rajiun, innalillahi waina ilaihi rajiun. Dama haka wancan Likitan na Janaral (General) yace, sosai ya gargademu akan kar ya shiga ruwa, ko iska ake sosai yace karya sake yafita babu kayan sanyi, yanzu idan Kamal yatafi yabarni ya zanyi? Ya zanyi da rayuwata ni Ma'u?" taqara Fashewa da kuka tana rufe fuska da gefen zane "Hajiya kiyi hqr, insha Allah Allah zai tashi kafadunshi, insha allah zai samu lafiya" inji Daddy cikin sigar rarrashi Dan kallonshi tayi ta gefen ido ta kauda kai tana cewa "ai dama haka za'ace, dama ai wanda aka cuta ake ba haquri, yaro besan hawaba besan sauka ba anjamashi jinya, yaron daba ruwanshi da kowa, harkar gabanshi kawai yake yanzu gashi anjamashi shiga halin rai ko mutuwa, wannan abu da me yayi kama?" saikuma taqara Fashewa da wani kukan Kasa cewa komai daddy yayi sai mallam Nasiru dayayi saurin cewa "haba kaka? Komai fa muqaddarine daga allah, Duk abinda kike ganin yafaru da mutum to allah yariga da ya qaddara Hakan zai faru dashi don Allah kiyi hqr insha allah Deen dinmu zai tashi akan kafafunshi nan kusa" Bata sake cewa komai ba sai kukan data cigaba dayi "yanzu Dr zamu iya ganinshi?" inji mallam Nasiru "A'a Gaskiya don a halin Yanzu baya buqatar hayaniya ko kadan.." "Dan Allah likita kubari naganshi, wlh bazanyi hayaniya ba, yadda na shiga haka zan fito ko kwakwarar motsi bazanyi ba, Don Allah" inji kaka cikin muryar kuka "kaka bawai hanaki nayi ganinshi ba, wlh dokace idan mutum na a wannan condition din ba'a barin ashiga dakin, kiyi hqr" inji Dr "Nidai Don Allah kayi hqr inganshi, bakasan yadda nakeji a zuciyata bane da kasani daka bari na ganshi, don Allah Alhaji kacemashi yabarni na ganshi, shine kadai sanyin idanuna, sanin halin dayake ciki zaisani jin sauqin abinda nakeji a raina, don Allah" tafada tana kallon daddy pleadingly Kallon Dr daddy yayi yace "Dr please do something, abarta ta ganshi ko daga nesa ne" Shiru Dr din yayi na wani lokaci cikin nazari sannan yace "ok, Gaskiya Saidai ta cctv don it's a strict law patients dake cikin irin wannan condition din babu mai shiga wajensu sai likitoci, wannan dokace akowanne hospital ba a wannan kadai ba Amma tunda ta nace zamu kaita recording room saita ganshi ta cctv, wannan shine iya taimakon dazamu iya yimata Gaskiya" "eh babu komai, akaini rekodin din, naji akaini" tafada tana share hawayenta da ha6ar zane Tashi Dr din yayi yace "to bismillah" Duk tashi suma sukayi Dr yayi gaba suka maramashi baya Jin tafiyar su yasa zee bude idanunta ta dago tana kallonsu Ganin zasu nufi wata hanyar yasata saurin tashi ta nufo daddy Ba musu ya miqamata hannu ta kama suka cigaba da bin Dr Recording room din suka shiga inda duk zirga zirgan da akeyi a hospital din ana ganinshi a wani qaton majigi Dr din ne yayi ma mutumin dake in charge of wajen magana akan ayimasu zooming din room 12 Yadda yace din haka mutumin yayi, yayi zooming din abinda ke faruwa a dakin da Deen ke kwance Gasping both kaka da zee sukayi suna rufe baki cikin tashin hankali Deen ne kwance kan gado sanye da blue kayan asibiti da akewasa marassa lfy Kanshi nannade da bandage, hancinshi sanye da abin oxygen dake taimakawa wajen jawo numfashi sai hannunshi dakeda cannula anamashi qarin ruwa Zamewa kaka tayi zata fadi zaune mallam Nasiru yayi saurin kamata ya zaunar daita kan wata kujera Kafe Deen din cikin majigin tayi da kallo idanunta na tsiyayar hawaye, ganinshi a wannan condition din ba qaramin ta6amata zuciya yayi ba hakan yasa tashiga yin kuka kamar zata shide Zee kau Fadawa jikin daddy tayi ta rintse idanunta gamm Bazata iya jurar kallon Deen a wannan halin ba hakan yasa taqara rintse idanunta gamm tana shesheka Shafa bayanta daddy keyi cikin sigar rarrashi idanunshi na kan Deen din cikin majigi Dole duk mai imani idan yaga Deen a halin dayake aciki ya tausayamashi "Dr please do everything you can to save him, please" inji daddy "insha allah sir, ku kwantar da hankalinku insha allah zai tashi zai koma kamar be ta6a kwanciyaba insha allah" inji Dr din cikin son qarfafa musu gwiwa Dakyar aka samu aka rarrashi kaka tareda yimata nasihohi sannan suka fito Alhaji ne yabiya duka bill din treatment din Deen din Saida suka qara tattaunawa da Dr inda aka fadama kingin yan unguwansu Deen dake wajen halin da ake ciki, sosai kowa ya jajjanta tareda yimashi addu'ar samun sauqi Nan mazan duk suka tafi da tabbacin zasu dawo anjima da marece aka bar kaka da matar Nasiru da baaba abu sai daddy da zee Basu dade da tafiya ba motar

Chapter 17 of 81