mugun 6ari
Gaskiyar hausawa dasuka ce sarkin yawa yafi sarkin qarfi don tun Aymaan na iya maida martanin har yakoma kare kanshi har daga baya ma yakasa kare kanshi din.
Ganin Hakan yasa zee nufar Deen dake tsaye yana kallonsu ta Kamo hannunshi
"Deen na roqeqa, kace subari zasu kasheshi"
Wani irin fizge hannunshi yayi wanda har Saida takai qasa
Juyawa yayi zai wuce wajen motar shi tayi saurin rarumo qafarshi daya
"Deen! No! Karka tafi zan mutu!" tafada tana rungume qafar da dukkan qarfinta
A matuqar hasale ya fizge kafar itama yana ja baya yana kallonta da bloodshot idanunta sannan yana nuna ta da yatsarshi datake karkarwa saboda yadda jikinshi ke tsuma don 6acin rai
Sai kuma ya juya ya bude kofar baya na motar ya bude wani akwati ido rufe ya fiffido wrappers din kudinsu nacan ya farka wrappers din yashiga watsamata kudadden ajiki, tsayawa tayi Cak da kukan tana kallon yadda yake warwatsa nata kudadden akai, da wani yaqare Sai ya farka wani har Saida ya qarar da wrappers biyar akanta
"Go away, you brat!!" Yafada cikin hargowa sannan ya juya ya shige motar ya rufo da qarfi.
Ganin Hakan yasa guards din kyale Aymaan da suka yima lilis suka rugo wajen mottocin suka shishiga suka tayar suka bar wajen a 360 suna badesu da qura
Ahankali Aymaan ya bude idanunshi dasukayi mashi mugun nauyi yabi motocin dasuka fita a harabar wajen da kallo sannan ya maido kallonshi akan zee dake zaune har lokacin bata ko motsi
Maida idanunshi yayi ya lumshe cikin azaba yana kiran sunan allah under his breath.
Saida yayi yunqurin tashi sau biyu ya kasa, ana uku yasamu ya tashi zaune Dakyar yana cije lip dinshi na qasa
Koina na jikinshi ciwo yakeyi kamar ana dandaqarsu ga bruises a jikinshi sunyi jaa abinka da fatar hutu dama
Ahankali yasake bude ido ya sake kallon zee dake a sitting position dinta har lokacin
Bude bakinshi yayi Dakyar yafara magana
"kin gani.. Ko? Kinga.. Abinda kika jawo ko?"
Shiru
Shaqar numfashi yayi sannan ya fesar yafara yunqurin tashi, sosai jikinshi yayi laqwas don babu qarya ya jibgu don shi tunda yayi wayau bazai iya recalling lokacin da aka ta6a yimashi irin wannan dukan ba
Ganin bazai iya tashin ba yasa ya qara Dagowa ya kalleta yaga still wuri guda take kallo sai jiyayi ranshi ya kuma 6aci
"ki tashi mutafi" yafada yana kallonta but still bata motsa ba
"Zainab! Am talking"
Nanma shiru
Shima shiru yayi ya tsaya yana kallonta yana qoqarin gano wani abu
Abinka da medical doctor nan take ya gano
Wara idanunshi dasuka tattaso yayi sannan yayi saurin rarrafawa gabanta
"Zainab" yakira sunanta yana waving a gaban fuskarta amma bata ko kyafta idoba
"zee?" yafada yana dan ta6ata kawai sai yaga tayi baya baya
Ba don yayi saurin tarota ba da tasha qasa
"Zainab! Zainab!!" Yafada yana jijjigata amma shiru
Tara yatsarshi yayi a hancinta sannan ya dora kunnen shi daidai zuciyarta yana feeling heartbeat dinta
A rikice ya dago ya karkata ya zaro wayar shi dake aljihunshi still tana jikinshi
Lalubo number Ahmad yayi ya danna mashi kira
Saida takusan katsewa sannan aka daga
"hey!" inji Ahmad daga wancan bangaren
"Ahmed kana ina?"
"lafiya?" inji Ahmad jin muryar Aymaan wani iri
"answer the damn question!" inji Aymaan yana qara jijjiga zee dake sheme ajikinshi
"ina gida, meya faru naji voice dinka wani iri?"
"kazo Ni'ima shopping mall, urgently please"
Daga Hakan ya katse kiran ya maida hankalinshi kanta
"Zainab! Zainab!! Wake up zee!" Yafada yana dan marin fuskarta amma shiru
Waige waige yafara, kasancewar babu mutane sosai a wajen ga kuma motoci dayawa dasuka kakkaresu shiyasa tunma lokacin dasu Deen ke nan ba'a gansu ba.
Ahankali ya maida ta ya kwantar daita sannan ya tashi Dakyar yafara dangyasawa ya fito fili
Waige waige yafara can ya hangi securities, daya na bude gate daya na a zaune
Da dingishi ya qarasa wajensu, tun daga nesa dasuka hangoshi suka fara kallonshi harya qaraso gabansu Dakyar
I.D card dinshi yafara nunamasu, Ganin ko waye yasasu saurin tashi suna tambayarshi lfy suka ganshi haka
Briefly yayi musu bayanin he's attacked By some thugs shi da sister shi dake can unconscious sannan ya gayamasu abinda yake buqata don yimata taimakon gaggawa.
Cikin sa'a aka samu most abubbuwan daya lissafo suka koma wajen zee dake sheme har lokacin
Dukda yadda yakejin kamar kanshi zai rabe gida biyu don sarawa haka ya daure yafara bata taimakon gaggawa
Suna haka Ahmad ya iso supermarket din.
Kasancewar Aymaan dama yariga ya fadamasu wani nanan tafe wajensu yasa yana isowa aka rakoshi wajensu
Sosai hankalin Ahmad ya tashi ganin halin dayaga Aymaan dama zee dake unconscious har lokacin
Cikin qarfin hali Aymaan yace ma Ahmad ya kaisu hospital
Da taimakon Ahmad aka saka zee back seat sannan sukuma suka dawo gaban seat, Ahmad ya tada motar yayi reverse suka fice daga supermarket din.
Asibitin da Aymaan ke aiki suka zarce.
Tun kafin su iso Aymaan ya bugama wani colleague dinshi waya ya sanar dashi Zuwansu shiyasa Koda suka isa akayi saurin kar6ar zee aka shige daita
Da farko Aymaan qin yarda yayi ayi treating ciwukkanshi har Saida ya tabbatar da sun ceto rayuwar Zainab from danger sannan Dakyar su Ahmad suka samu suka lalla6ashi ya yarda.
***
Kwance yake bayan angama treating dinshi idanunshi a lumshe kamar mai barci amma ba barcin ba yake
Shi kadai ne dakin don tunda nurse tagama treating dinshi suka fita suka bashi wuri don ya huta sosai
Qarar bude kofa yaji amma Hakan besa ya bude lumssasun idanunshi ba
"bismillah ummy" yaji Ahmad na cewa Hakan, Hakan yasashi bude idanun babu shiri ya juyo yana kallon saitin kofar
Ummy yagani agaba sai batool a bayanta sai Abbu a bayansu
Yunqurin tashi zaune yafara sai ummy tayi saurin Qarasowa tana taimaka mashi ya ida tashi zaune ta karamashi pillow a baya
Dagowa yayi yana kallonsu sai yaga suma shi suke kallo cikin tausayawa
"sannu Akhie" inji batool kamar zatayi kuka
Dan murmushi yayi mata sannan ya kalli su ummy
"ummy, waya gayamaku?"
"Ahmad ne habiby, muna can hankalinmu Kwance ashe babu lafiya"
Dagowa yayi ya watsama Ahmad mugun kallo shikuma yayi murmushi yana daga kafadarshi
"sannu son, allah ya kyauta gaba amma nayi mammaki ace thugs a supermarket, how come?"
Shiru Aymaan yadanyi sai kuma ya sauke Ajiyar zuciya
"Abbu nidai bansan ya Hakan yafaru ba, kawai nagama siyayya ta nafuto saina hangeta inda nace ta jirani
Amma kafin na qaraso sai naji qarar faduwar abu daga hannunta sai kuma naga tayi wajensu dagudu
Na kwalamata kira amma bata saurareni ba shiyasa nima na qaraso wajen da sauri sai naga ashe wayarta ce ta saki
Saina dauketa na tashi nabita lokacin harta fita waje
Nima saina bita Saidai Koda nafita ban ganta ba don har titi saina nakai amma banga wulginta ba
Dawowa nasake yi da niyyar komawa ciki again sainaji kamar magana a ta parking space din wajen
Saina zagaya, kawai saina hangeta daidai wani ya tureta
I thought faduwa zatayi amma sainaga bata fadi ba, sai nayi saurin nufar wajen
Ina qarasawa wajen ya daga hannu zai mareta saina dakatar dashi..."
Duk tsit mutanen dakin sukayi ya cigaba da basu labarin har kawo yanzu dasuke asibitin nan
Duk salati suka shiga yi cikin tsantsar mammaki da alhini
"innallilahi waina ilaihi rajiun, to shi mutumin waye? Kawai daga ganin mutum sai tace shine Deen? Haka fa tayi muku a park rannan ko?"
Ajiyar zuciya kawai Aymaan ya sauke don shi kadai yasan abinda yakeji a zuciyarshi
"to Gaskiya ya kamata nakira yaya na fadamashi, idan aka tafi Hakan akwai matsala, ace duk wanda tagani tace Deen ne, idan ta qara gamuwa da muggai kamar na yau fa babu wani dazai iya taimakonta a kusa fa?"
"A'a, be kamata a kirasu ba, hankalinsu ne zai tashi sosai, kawai mu nemo mafita da kanmu" inji Abbu
"nima Gaskiya am scared Abbu, gwara asan yadda za'ayi don nima abubbuwan datake yi sunfara bani tsoro, haka fa rannan ta dage akan ita dole shi tagani tasamu mukaita zagaye a banza" inji batool
"kai, amma dai yaron nan ya cuceta wlh, cutar da dole sai allah ya sakamata, daga wannan sai wannan? Sai abu yayi kamar yafara warwarewa sai kuma yaqara ta6ar6arewa, kullum abu beci baya sai gaba?" inji ummy hawaye na taruwa a idanunta
"Addu'a yakamata mu dinga tayata dashi Abbu, allah ya kawo mata rangwame a halin datake ciki" inji Ahmad da Tundazu bece komai ba
Kada kai kawai duk sukayi cikin amincewa da Maganarshi
Shidai Aymaan bece komai ba sai kafe waje guda dayayi da ido kawai, allah kadai yasan meke kai kawo a qwalwarshi
Ranar aka sallamesu suka koma gida
Zee ta farfado and she's ok physically amma karka bincika zuciyarta
Zuciyar tata data samu ta lilliqeta da gum tun bayan rarratsata da Deen yayi tasake Fashewa, fasuwar da mawuyacine taqara iya yimata paci kamar yadda tayimata da farko
Tun daga ranar ta chanza, chanzawar da tafi duk na baya
Bata cin abinci sai an tsareta an tilasta mata to anan zataci kadan
Kuma ko zaka yini kanta kana magana bazata cemaka komai ba har ka gaji don kanka ka kyaleta
Daga baya kuma saita fara zazza6i, irin zazza6innan mai zafi sosai
Dr Aymaan ne kullum mai treating dinta, yana iya qoqarin shi na ganin ya bata dukkanin kulawar datake buqata amma a banza, kullum cikin ciwo take ga wani bushewa datakeyi a tsaye
Sosai wannan ahalin suka sake shiga damuwa mai tsanani
Suna son su sanar dasu daddy na Nigeria amma Aymaan ya hana yana cewa it's not proper gwara suyi iya qoqarinsu akanta basai sun sanar dasu halin da ake ciki ba.
Haka Aymaan dama sauran ahalin gidan sukaita iya bakin kokarinsu akanta
Duk safiya bayan sallar asuba zasu shigo dakinsu zee din su zauna tilawar alqur'ani kowa da nashi a hannu itama a bata nata tana dubawa while su suna karantawa
Sosai Hakan yayi tasiri sosai akanta don duk lokacin da suke wannan karatun takan tsinci kanta cikin nutsuwa, zuciyarta ta ragemata zugin data keyi
Da rana kau wuni suke garden da batool wanda zataita iya qoqarinta wajen sanyata nishadi
Da daddare kuma Aymaan zaizo ya fara karanta mata littatafai masu dadi masu sanya nishadi
Haka sukaita iyakar bakin qoqarinsu akanta suna kuma hada mata da addu'a don tabbas lamarinnan sai an hada da addu'a
Wata rana jikinta yasake tashi, zazza6i mai mugun zafi ya rufe ta.
Ranar kowa na gidan beyi barcin kirki ba Haka suka tare wajenta Aymaan na iya bakin qoqarinshi akanta a matsayinshi na qwararren likita
Dakyar suka samu jikin ya lafa tasamu barci drip maqale da hannunta
Su ummy da batool sai dauke hawaye sukeyi akai akai shikuma Aymaan idanunshi sun Kada sosai, jiyake da shima zai iya kuka da yayi mata
Haka yafita dakin ya barta dasu ummy da anan zasu kwana wajenta
A ranar besamu rintsawa ba, haka ya zauna ya kafe waje guda da ido
Tunanuka kala2 ke kai kawo akanshi
Ko yatafi Nigeria neman Deen?
Ko yaje a chanza mashi fuska irinta Deen?
Me zaiyi? Me zaiyi dazai dauke ma zee abinda takeji?
Shi da yasan yadda zai dauke mata abinda takeji a zuciya shiya dinga ji da yayi Hakan, daya jure kowanne irin wahalar da zaisha muddin zai dauke mata wahalar
Yadda yaga rana haka yaga dare, asuba nayi ya miqe ya fice massalaci
Koda ya dawo dakinsu yafara shiga ya tarar da har lokacin barci take
Sake dubata yayi sannan ya cire mata qarin ruwan don yaqare sannan yafita
A gaggauce yayi shirin asibiti ya fita don dama kwana biyu be cika zaman asibitin ba saboda tattara hankalinshi dayayi akan zee
Yauma wani emergency aka kawo wanda lallai ana buqatarshi a aikin shiyasa ya shirya a gaggauce yayi sallama da mutanen gidan yatafi
Bashi ya fito daga asibitin ba sai wajajen 3pm Hakan yasa ya wuce gida kawai don duk hankalinshi yayi gida kuma yanason yaje yaga wane hali zee din ke ciki
Koda ya shigo gidan parking space yashiga yayi parking sannan ya fito
Kamar kullum yau ma lapcoat dinshi riqe take a hannunshi ya fito ya rufe qofar sannan ya fito daga parking space din
Hangen batool yayi ta fito daga garden tayi hanyar cikin gida batareda ta lura dashi ba
Ganin Hakan ya tabbatar mashi cewa zee tana garden din itama don Mafi yawancin lokaci irin wannan can suke zama don sudan debe kewa.
Hakan yasa ya chanza akalar tafiyar tashi zuwa garden din don dama babu wanda yakeson gani kamar ita yanzu
Cikin takunshi ta nutsuwa ya taka zuwa garden din
Tun daga nesa ya hangota zaune bisa wata yar doguwar kujerar garden din ta juya mashi baya so be ganin fuskarta itama kuma batasan da shigowarshi ba garden din
Wasu yan moli moli take kallo dake tsaye a kan wani reshen bishiya suna dan tsuwarsu suna ra6ar juna
_*look*_
Ta tuna abinda Deen yace wancan ranar da suka gansu a school
_*A Good example of us, ko?*_
Lumshe idanu tayi akansu ta bude sannan ahankali tafara waqa
_the word around town.._
_is that you're back in town_
_and I tried not to think about you_
_I tried_
_but it's been so long.._
_and I thought I moved on.._
_but now I really doubt it_
_I do_
_I wonder why you even come_
_it's almost like you're having fun with me_
_and though if I set my eyes on you, it's on avoidable_
_how come oh boy?_
_I thought you've gone for good_
_so how do you!.._
_have to pull me back!"
_I thought you said, you won't be coming back_
_then why did you?!_
_this is really bad!_
_I thought you said you're gone for Good_
Dakatawa Aymaan yayi daga tafiyar dayakeyi yana kallonta cikin wani irin yanayi
_what you did is wrong_
_cos you know all along am doing ok without you_
_you don't want me to.._
_try to move on.. Try oh_
_the heart is too strong_
_can't be with you and can't be without you_
_the truth is that I.._
_wonder why you even come_
_is almost that you're having fun with me_
_and though if I set my eyes on you, it's unavoidable_
_how come oh boy?_
_I thought you've gone for good_
_so why did you?!_
_have to pull me back?!_
_I thought you said, you won't be coming back_
_then why did you?_
_this is really bad!_
_I thought you said you're gone for Good_
Ahankali yafara takawa da baya baya still idanunshi akanta making sure be ankarar daita dashi ba
Saida yayi nisa sannan ya juya yayi saurin barin garden din
Saboda rufewar idanunshi baya ma ganin gabanshi clearly wanda Hakan yasa yaci karo da batool a bakin kofar shiga falo
Daga mata hannu kawai yayi ya wuce don ga yadda yakeji dinnan yasan ko yayi maganar bazata fito ba
Binshi da kallon mammaki batool tayi, kamar ta bishi sai kuma tafasa don wataqila 6ata mashi rai akayi kuma tasanshi idan yana cikin 6acin rai beson kowa ya ra6eshi, Hakan yasata juyowa kawai ta koma garden din.
A daddafe Aymaan yasamu ya haye saman ya qarasa dakinshi ya bude yashiga ya maido ya rufe
Jingina yayi da kofar ya saki lapcoat din hannunshi qasa yana sauke wani irin numfashi mai nauyi idanunshi a lumshe
Kamar da wasa sai jiyayi wani abu na silalowa daga idanunshi zuwa kan kumatunshi
Ahankali ya bude idanunshi sannan ya kai hannu ya dangwalo ya duba
Hawaye?
Kuka yake?
Sake maida idanun yayi ya lumshe wasu nasake gangarowa.
Jingina kanshi yayi da kofar yana maida lower lip dinshi aciki ya datse da haqora
Besan iya lokacin daya dauka ba ahakan Saida yagaji da tsayuwar sannan ya dago daga kan kofar ya wuce wajen gadonshi ya zauna gefenshi ya dafe kanshi da hannaye bibbiyu yana kallon qasa
Ya jima ahakan yanata saqa da warwara sannan ya Janye hannayen daga dafe kan dayayi ya karkata ya zaro farin hanki dinshi a aljihunshi na wando yashiga wiping fuskarshi
Qara cije lip dinshi na qasa yayi yana kafe waje guda da idanunshi dasukayi ja sai kuma yasake karkatawa ya ciro wayar shi ya kunna ya lalubo number batool ya bugamata
Ringing biyu aka daga
"Akhie?" yaji tafada a can bangaren
"ki riqe wayarki a hannunki zanyi miki sms, it's privacy"
Be jira cewarta ba ya tsinke kiran
Batool acan gefen jin ya katse mata hanzari ta hanyar kashe wayar ta sauke wayar cikin mammaki tana kallonta, itakau zee hankalinta ma ba kanta yake ba, tayi nisa as usual
Ko minti biyu ba'ayi ba text message yashigo wayar tata
Saurin budewa tayi sai taga yasa
_*kisan yadda zakiyi ki dauki phone din Zainab ki kawomin yanzu, it's urgent*_
Shiru tayi tana qara karanta text din
Me zaiyi da wayar zee kuma?
Dagowa tayi ta kalli zee dake zaune har lokacin ta kafe waje guda da ido batama san me takeyi ba.
Ba'ayi Mintuna uku ba yaji an kwankwasa mashi kofa Hakan yasashi saurin tashi kamar dama kan qaya yake ya nufi kofar
Budewa yayi sai ga batool ta bayyana
"yauwa, bani" yafada yana miqomata hannu
"Akhie? Meya sameka?" tafada tana kallon yadda idanunshi sukayi jajur
Be amsa mata ba sai jan hannunta dayayi suka shiga dakin ya rufo kofa
"the phone" yafada cikin kosawa
Dagota tayi ta gwadamashi
Amsa yayi da sauri ya kunna yayi sliding sai yaga ta bude
Direct contact yashiga yayi searching 'Deen' amma babu result saiya tuna ashe wannan sabon layine ma ashe don dama tunda tazo nan ta chanza layi irin na qasar
Shiru yadanyi kamar mai tunani, Itadai batool Binshi kawai take da idanu
Dagowa yasake yi ya kalleta
"ta ta6a nuna miki hotonshi?"
"wa?"
"wannan mayaudarin" yafada kai tsaye
Tasan wanda yake nufi don haka sai tace
"eh, folder daya gareshi ma sunkutukum"
Miqa mata phone din yayi
"gwadamin shi"
Amsa tayi ta shiga inda tashiga rannan nan da nan ta shiga cikin hotunan
Daya tafara shiga sannan ta miqama Aymaan din dake kallonta hannaye rungume da qirji
Amsa yayi ya juyo wayar sannan ya sauke idanunshi akan photon
Idanunshi ne suka fara warawa akan hoton yana kallonshi a mammakince
Ganin yana kallon hoton hankali a tashe yasa itama batool tazama so curious
"Akhie, menene?"
Dagowa yayi ya kalleta
"Are you sure wannan gayen ne Deen?" yafada yana qara nunomata hoton
Sake dubawa tayi itama sai ta Kada kai tace
"eh Akhie, kaga nan a library din school dinsu ne.."
Saita wuce ga wani hoton
"wannan kuma ma a school ne.. Wannan kuma a garinsu mamansu zee din lokacin daurin auren nan na sister din mummyn, to shima yaje daurin auren, nan zaune suke dashi ta daukeshi"
Aymaan sai baza idanu yake da kunnuwa yana sauraron batool
Qara kallon hoton yake, ba fuskar kowa yake gani ba sai fuskar wannan gayen na supermarket
Kenan ba haukan zee bane? Kenan dagaske wannan gayen Deen ne? Kenan ba gizo fuskarshi yake mata ba kamar yadda suka zata?
Kenan Deen ne wannan gayen da yakusan marin zee?
"unbelievable!!" Yafada in total shock
"yaya wai menene? Ka sanshi ne?" inji confused batool
Dagowa yayi ya kalleta saikuma yasake kallon hoton
"shine" yafada yana kallon smiling face din Deen na cikin wayar
"shine wa?" inji batool cikin rashin fahimta
"shine gayen da muka gani a supermarket" yafada yana kallonta
Wara idanu batool tayi in out most shock
"mene?"
"shine, kenan dagaske shine? Tabbas wannan fuskar ce, bazan ta6a mancewa ba. Kenan dama Deen ne wannan gayen?"
"Are you kidding me Akhie? Kana nufin wannan gayen na cikin wayar nan kuka gani?" tafada zuciyarta na bugu sosai
"shine batool, tabbas shine, ya sallam!" Yafada yana dafe goshi in confusion
To kodai shima yafara zaucewan ne? Kodai shima idanunshi sun fara gayamashi qarya ne kamar dai zee?
"but Akhie meya kawo Deen dubai?" inji batool cikin confusion
Shiru yayi yana kafe hoton da idanu hoping zaiga fuskar ta chanza zuwa wani, hoping idanunshi ne ke mashi qarya
"zanje na gayawa ummy, I can't believe this!" inji batool tayi hanyar waje
Saurin dakatar daita yayi ta hanyar riqo hannunta
Juyowa tayi ta kalleshi
Girgiza mata kai yayi sai kuma ya sauke Ajiyar zuciya
"No, ba yanzu ba. Karki sake ki fadawa kowa, zanyi confirming, kibari mu tabbatar sannan"
Batool bataso Hakan ba Amma ya ta iya
Wayarshi dake kan bedside locker ya dauko yashiga xender ya tura pics din Deen din biyu daga wayar zee din zuwa tashi sannan ya miqama batool din wayar
"jeki, zanyi confirming and also karki bari kowa yaji wannan zancen kinji?"
Kada mashi kai tayi sannan ta fita jiki a sanyaye
Komawa yayi ya zauna yana tunani, be ta6a kawowa ranshi ya bincika ko dagaske wannan gayen Deen ne don shi duk a tunaninshi kawai haukace irin ta soyayya, to amma abin da kulle kai, Tunawa yayi da yadda ya daga hannu zai kifamata mari wanda da badon yayi saurin qarasawa wajen ba da babu abinda zai hanashi marin ta din, Tunawa yayi da kallon kyamar da yake Binta dashi, kamar ma beta6a sanin ta ba a duniyar nan
Abin Tambayar anan shine dama can soyayya sukeyi koko dai ita ke sonshi tana liqemashi don shidai bega alamun so ko sannaya ba a qwayar idon wannan gayen ba
Idan ma shine yaushe yazo dubai?
Yaushe yayi kudi?
Mutumin da ummy tace koko da kosai sukeyi for living, yaushe yayi kudi haka harda bodyguards?
Hannu yasa yana scratching kanshi in confusion, kanshi a mugun kulle
Batool ma dai kasa komawa daidai tayi tunda tafito daga dakin Aymaan
She can't believe Deen din zee ne dagaske suka gani anan
Daba Aymaan yafada ba da ta qaryata, meke faruwa to?
Haka Itama ta qarashe wunin cikin tunanin wannan rudaden al'amarin.
Aymaan da shirinshi yafito sallar isha'i
Saida yafara biyawa dakinsu batool inda ya tadda zee zaune kan sallaya da alamun itama jiran afara kiran isha'i take tayi, batool kuma na linke wasu kayan su data Fiddo
Jin batool na yiwa Aymaan sannu da zuwa yasa zee Dagowa
Tsaye taganshi idanunshi akanta
Sanye yake cikin lallausan milk din yadi mai kyau anyi kayan aikin dark brown
A dan zaman nan datayi dasu ta lura Aymaan masoyin manyan kayane don yana sasu sosai kuma suna mashi kyau sosai suna sake fito da cikar kamalarshi
Sauke idanunta tayi daga kanshi ta maida kan sallayar gabanta
Ahankali ya qaraso wajenta ya tsugunna
"patient" yafada yana kallonta yana murmushi
Dagowa tayi ta kalleshi batareda tace komai ba
"ya jiki?" yafada ahankali
Kadamashi kai kawai tayi ahankali sai ta maida kanta qasa
Binta da kallo ya cigaba dayi yana imagining pain dinta
Na farko wanda take bala'in so ya karya mata zuciya ta hanyar gujemata batareda wani dalili ba
Na biyu ta sake ganinshi amma kuma bata gabanshi sam
Na uku mutanen daya kamata su fuskanceta wanda a wajensu zata dan ji sanyi sanyi suna mata kallon zautatta, basa yarda da duk abinda take cewa sai suyita mata kallon mahaukaciya wacce so ya haukata
How painful is that?
_very painful_
Ajiyar zuciya ya sauke yana maida lower lip dinshi aciki ya danne
Tabbas shikuma yayi alqawarin kawo farinciki a rayuwarta, zai sake maido mata lost murmushinta a fuska, zaiyi koma menene don wanzar da farinciki a rayuwarta, saiya maida mata komai tarihi insha allah
Dagowa yayi ya kalli batool yaga itama shi take kallo
Dan murmushin gefen baki yayi saiya miqe tsaye
"Allah ya sawwaqe, batool make sure tasha magani data ci abinci, zan fita"
"insha allah Akhie allah ya tsare" inji batool
Qara duqawa yayi wajen zee din
"natafi dear" yafada ahankali
Dagowa tayi ta kalleshi jin abinda ya kirata
_Dear?_
Kada mashi kai tayi sannan ta bude baki ahankali tace
"Allah ya kiyaye"
Murmushi yayi mata
"Amin dear" yafada sannan ya miqe tsaye yajuya ya fita
Duk Binshi da kallo sukayi atare harya fice.
Saida yayi sallama da ummy sannan yafice cikin motarshi
Saida ya tsaya yafara yin sallar isha'i sannan ya wuce gidansu Ahmad don dama sunyi waya yace mashi yana gida
Gidansu Ahmad shima babba ne don yafi nasu Aymaan ma don sunfisu kudi dama.
Parking yayi sannan ya fito yana dan wurwura keys dinshi
Saida yafara shiga suka gaisa da maman Ahmad din sannan ya fito yawuce part din Ahmad din don dama shi part dinshi daban a gidan
Cikin fara'a suka gaisa
"Dr! Dr!! Ganinka yanzu sai an cika form" inji Ahmad cikin tsokana
Harararshi Aymaan yayi ya wuce wajen dan fridge din dakin ya
All Chapters
Chapter 1
Chapter 2
Chapter 3
Chapter 4
Chapter 5
Chapter 6
Chapter 7
Chapter 8
Chapter 9
Chapter 10
Chapter 11
Chapter 12
Chapter 13
Chapter 14
Chapter 15
Chapter 16
Chapter 17
Chapter 18
Chapter 19
Chapter 20
Chapter 21
Chapter 22
Chapter 23
Chapter 24
Chapter 25
Chapter 26
Chapter 27
Chapter 28
Chapter 29
Chapter 30
Chapter 31
Chapter 32
Chapter 33
Chapter 34
Chapter 35
Chapter 36
Chapter 37
Chapter 38
Chapter 39
Chapter 40
Chapter 41
Chapter 42
Chapter 43
Chapter 44
Chapter 45
Chapter 46
Chapter 47
Chapter 48
Chapter 49
Chapter 50
Chapter 51
Chapter 52
Chapter 53
Chapter 54
Chapter 55
Chapter 56
Chapter 57
Chapter 58
Chapter 59
Chapter 60
Chapter 61
Chapter 62
Chapter 63
Chapter 64
Chapter 65
Chapter 66
Chapter 67
Chapter 68
Chapter 69
Chapter 70
Chapter 71
Chapter 72
Chapter 73
Chapter 74
Chapter 75
Chapter 76
Chapter 77
Chapter 78
Chapter 79
Chapter 80
Chapter 81
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 47 Chapter of 81