daddy na iya sadaukar da komai akan farincikinta ciki harda farincikinshi, Hakan ne yaqara qarfafa mata gwiwa akan Deen Amma kuma ta rasa dalilin dayasa kuma zuciyarta ke rawa akan haka, tarasa dalilin dayasa take fargaba dukda tabbacin datake dashi, ta rasa meyasa takeji ajikinta wani abu marar dadi zai faru daita, dasu, ita da Deen.
Ringing din wayarta yasata sauke wata Ajiyar zuciya tana lumshe idanu tareda budewa
Shine, ko bata duba ba tasan shine.
A halin yanzu babu muryar wanda take buqatar ji kamar tashi haka zalika kuma babu wanda bata fatan yaji muryarta ahalin yanzu kamar shi
Jin Muryarshi zai kawo sauqi wa zuciyarta shikuma jin muryarta zai jawo fargaba da rashin kwanciyar hankali gareshi
Kiran farko ne ya katse, ba'a jima ba wani yasake Shigowa
Cigaba da kallon wayar take tana bin sunanshi dake motsi a screen din da kallo batareda ta Ko motsaba har itama ta katse
Daukar wayar tayi dafarko kamar ta kashe sai kuma ta chanza shawara ta sata a silent ta ajiyeta kan bedside locker itakuma ta zame ta jingina da frame din gadon
Idan akwai abinda bataso to tashin hankalin Deen ne don haka dole ta hadiye kwadayin jin muryar tashi ta zauna da nata damuwar ita kadai don tasan dayaji muryarta zaisan babu lafiya kuma zaiso tilasta mata ta fadamashi abinda ke faruwa wanda ita a ganin ta bashi da amfani don abune da bazaiyi wuyar warwarewa ba, tasan daddynta so batada case.
This is just a minor challenge.
*08:35pm*
Kwance take kan gadonta tana danne dannen wayarta tana iyakar qoqarinta na ganin ta kauda duk wani damuwa dake son yin tasiri a zuciyarta Saidai dannar wayar kawai take amma ita kanta bata gane me takeyi da wayar ba
Knocking din kofarta taji anyi
Dago kai tayi ta kalli kofar batareda tace komai ba
Gani tayi an murda handle din anshigo dakin
Mummy ce
Sauke kai tayi cikin zuciyarta tana cewa itafa bata jin yinwa ko an tilastata bawani abin kirki zataci ba
"dress into something decent ki sauko kinyi baqo" inji mummy babu alamun wasa
Saurin dagowa tayi ta kalli mummy
"baqo kuma mummy?"
"eh baqo kuma"
"but I thought..."
"look karki 6atawa mutane lokaci, Kiyi abinda nace yanzu!"
Saurin sauko da kaffafunta tayi daga kan gadon don tasan halin mummy idan ranta ya 6ace
"nabaki 5 mins Kiyi ki fito tun kafin ranki ya 6aci" inji mummy sannan tajuya ta fita
Binta da kallo zee tayi harta fita ganin Hakan yasa tafara dirje dirjen kaffafu aqasa tana kukan ta6ara
"ni ya kukeson nayi ne nace banasonshi banasonshi inada wanda nakeso, haan!" tafada tana hucin kukan datakeyi
Sai kuma ta tashi a fusace tanufi wardrobe ta budeshi da qarfi taciro wata baqar gown ta dorama nightie din jikinta ta yafa gyale tadan fesa turare sannan ta fita looking so angry.
A falon ta tarda mummy ba ita kadai ba harda daddy zaune bisa kujerar dake facing stairs
Bata kalli ko daya daga cikinsu ba tawuce centre table din dake akwai tray mai dauke da kayan motsa baki sama ta dauka ta fice batareda ta yarda ta kalli gefensu ba.
Binta da kallo duk sukayi sannan suka sauke Ajiyar zuciya
"Alhaji baka ganin kamar dolen dakace baxaka yimata ba shi kake niyyar yimata?" inji mummy
Shiru daddy da ranshi ke duk a jagule yayi can sai yace
"haryanzu ba dolen zanyi mata ba, idan basu daidaita ba still zan bata damar samo wani amma ba wannan yaron ba ko makamancinshi, ta nemo miji gidan manya gidan mutunci ba inda zan kaita ba inkasa cin abinci ba saboda tunanin ko ita tasamu abin sakawa aciki"
Ajiyar zuciya mummy ta sauke not knowing what to say don haryanzu batada ra'ayi acikin wadannan ra'ayoyin biyu wato na daddy da na Zainab, Itadai fatanta dai allah ya tabbatar da wanda yafi alhairi
***
Da sallama tashiga guest room din ma wannan karon
The same voice daya amsa sallamarta ta jiya ta amsa yau ma
Bata yarda ta kallo gefen dayake ba ta nufi centre table din Wurin ta ajiye tray din datake jin kamar ta sakeshi Tundazu
Kujerar da ta zauna akai jiya tasake akai yau tayi crossing kaffafunta tafara dannar wayarta
Tunda tashigo yake Binta da kallon qasan ido ganin yau batada niyyar tankamashi yasashi cewa
"sannu" kamar mai ciwon baki
Ahankali ta dago ta kalleshi saikuma ta maida kallonta akan wayarta
"yauwa" tafada itama kamar wanda aka tilasta
Shiru yaqara biyo bayan haka. Ita hankalinta na kan waya shikuma hankalinshi na kanta yana studying dinta
Sun kusa minti 15 ahakan sannan Asaad ya gyara zamanshi a kujerar dayake akai
"Am Asaad Abubakar Dikko by name, ni d'a ne ga Alhaji Abubakar Dikko, a graduate with masters certificate a fannin business, and you?" yafada yana tsareta da madaidaitan idanunshi
Sai a lokacin tasake Dagowa ta kalleshi sama sama tasake Janye idanunta
"Am Zainab.. Zainab Dan faranshi" tafada a taqaice
Kada kai yayi
"Good, hope kinsan dalilin zuwa na nan?"
"zan sanine bayan ka sanar dani"
Dan murmushi yayi na gefen baki sannan ya kada kai yana dan mere baki
"well, ni nasani kuma zan sanar dake dukda nasan kema kin sani"
Dan daga kafadu cikin qara ta6e baki yace
"I was sent here by my Dad, akwai abinda suke son qullawa tsakanina dake for their benefits don Hakan zai qara zumuncinsu da amincinsu kamar yadda sukace, shiyasa aka turoni don wai mu fahimci juna which I think bazai yiwuba don ni atsarina mata Africans basuyimin ba kwata2, primary dina kawai nayi a Africa, secondary dina nayishi ne a france, nayi first degree dina a uk and yanzu na qarqare masters a India
A duk cikin qasashennan babu baqaqen fata duk jajjayene wataqila shiyasa kwata2 bana ra'ayinsu, babban burina shine auren one of those jajjayen ba baqaqen Africans ba dukda ke naga you're not that black" ya qarashe yana dan ta6e baki
Zee tunda yafara ta maida hankalinta kanshi tana kallonshi dumpfounded
"so nazo nan ne ba don mu fuskanci a sigar da tsoffafinmu keso ba sai don mu fuskanci juna na ainahi wato sanin ra'ayin juna akanmu, ni kinji ra'ayi na, so samu kiyi co-operating mu samawa kanmu mafita"
Wani murmushi ya su6ucema zee tadan kauda kai tanayi
Bece komai ba sai cigaba da kallonta dayake yana jiran jin me zatace
Dagowa tayi taqara kallonshi sannan ahankali tafara magana
"A ganina a smart guy with sharp brain tun zuwanshi na farko a wajen budurwa zai gane yasamu kar6uwa ko be samuba.
Me haja shike buqatar talla.
Gaskiya ra'ayinmu yazo daya don nima ban cika ganin mutuncin desperate African a qasashen masu jajjayen fata ba. Wadanda basa kishin kansu bare akai ga kare martabar asalinsu, bana masu kallon mutane at all saboda a qasarsu sunfita sahun mutane saboda basa kishinta a can inda suke marari kuma ba'ayimusu kallon mutane.
Nayi primary school dina a Nigeria, Secondary school ma haka, and now nakusan graduating still a beloved qasata Nigeria and after that ko zanyi aiki I'll proudly reject kowanne offer na kowane qasashe musanmman na jajjayen and proudly stick to my beloved country Nigeria kuma ko zan fita din it will be within Africa din not outside.
So inajin there's no need of worrying tunda ra'ayi yazo daya and am glad it does don ni dama ba kowanne namiji nake ma kallon namiji ba" tafada itama tana dage kafadu kamar yadda yayi dazu.
Tsit dakin yayi
Kallonta yake babu kyaftawa, yama rasa mai zaice ko zaiyi.
Ganin shirun yayi yawa kuma baida niyyar cewa komai ko motsawa yasata sake dagowa ta kalleshi
"mr.... Yama sunan?
Well, whatever. I think tunda mungama fuskantar juna yakamata musan inda dare yaimana ko? As you can see am sleepy already, ko da wata maganar ne?"
Cije lower lip dinshi kawai yayi ya Janye idanunshi akanta
"No, I don’t think so" yafada saikuma yatashi tsaye yana pocketing hannayenshi
"Good night"
"yeah, mu kwana lfy" tafada itama batareda ta kalleshi ba
Zuwa yayi ya wuce ya bude kofa ya fita ya maidota da qarfi har Saida zee tadan dode Kunnuwanta
"stupid fool!" tafada tana bin kofar da harara tareda jan dogon tsaki
Sai kuma tahau Dariya, wai jajjaye yakeso gashi shi kamar gawayi, saikuma ta cigaba da Dariya tana tunanin yan wahala fa yawa garesu a duniya, ita ko dauramata shi akayi a qafa saita kwanceshi ta yar don babu abinda zatayi dashi
Tsaki tasake ja sannan ta miqe tafito itama daga dakin ta nufi cikin gida
Luckily babu kowa falon Hakan yasata hayewarta sama ta maido dakinta ta rufe ta cire gown din saman nightie dinta ta qure a.c ta baje tana fesar da iska daga bakinta.
Bata dadeba ahakan barci yayi gaba daita saboda dadin iskar dake shigarta
*WASHEGARI*
Zaune take tana waya da Deen daketa yimata mita wai jiya yaita kiranta bata dagawa har hakan yaja yakasa samun isashen barci itakuma tana yimashi Dariya
Jitayi anyi knocking din kofarta aka bude aka shigo
Ganin daddy ne yasata saurin katse wayar batareda ta shirya ba ganin yanayin daddyn
"Daddy?"
"Why? Meyasa zaki yimashi haka? Yes nasan bakya sonshi amma abin har yakai kicimashi mutunci? Beci yaci arziqin mahaifinshi ba Zainab?"
Gaban zee ne yafadi Hakan yasa ta saukar da kaffafunta qasa ta miqe tsaye
"Dad meke faruwa ne?"
"look, karma ki fara, nasan ki nasan halinki, tsaf zaki iya finma abinda yace"
"daddy ni me nace? Shi be fadamaku abinda yace ba? Wai he hate Africans wai bayason baqar mace?
"koma me yace be kamata ki kirashi da dabba ba ko don albarkacin amincin dake tsakaninmu da mahaifinshi"
"dabba? Ni yaushe na kirashi dabba daddy?"
"kin fini sani tunda ke kika fada don nasani tsaf zaki fadi fin haka amma ko babu komai ya kamata ko beci darajar mahaifinsa ba ni yaci daraja ta tunda ni na gayyatoshi"
"daddy.." tafada cikin rawar murya idanunta na kawo kwalla
"ba komai ai, laifinane, kinriga kince bakya sonshi nikuma na saki kije wajenshi dukda Hakan, babu komai, tunda baki sonshi fine, bazan tilasta miki shi ba, kije ki samo wani na aura miki amma banda wannan yaron, kin dai jini ko? Banda wannan yaron ko wani talaka irin shi don bazai ta6a yiwuwa ba, so ko shi ke zugaki that won't change anything bazan ta6a hada zuri'a da tallaka ba wlh, tsakanina dasu sai kyautatawa da taimako idan naga dama amma bana alaqa ta surukantaka, never!"
Yana kaiwa nan yajuya yabar dakin a fusace
Binshi da kallo zee tayi harya fice ya maido mata kofarta
Ahankali tayi baya baya ta zauna jagwab kan gadonta tana sauke numfashi ahankali
_meke shirin faruwa daita ne?_
_meyasa wannan case din data raina keson girmama?_
_what went wrong?_
Hannu tasa ta shafo kanta zuwa baya cikin tsananin damuwa
Tanaji tana ganin wayarta nata ringing da tone din Deen Amma takasa dagawa... ✍️
Ummin fasihu 🧚🏻♀?
8/2/21, 9:38 PM - Buhainat😝: *🙍🏻♂️DEEN 🙍🏻♂?*
Hhh yau ga post din dare, Gaskiya yau typing ya wahalar dani 🥺
*046*
*THE CHALLENGE 2*
Wunin ranar haka ta qarasheshi rai a jagule, kwata2 tarasa abinda ke mata dadi.
Sosai fushin daddy da alwashinshi ya tsoratar da ita abinka da bata saba ganin haka ba
Da mummy ce tazo tayi mata wannan hargagin bazaiyi tasiri a ranta ba kamar yadda na daddy keyimata yanzu don ita mummy dama ta saba da ganin Hakan agareta amma daddy zata iya cewa tunda tayi wayau bazata iya tuna ranar da ya ta6a yimata fada ba shiyasa yanzu abin ya dameta fiyeda zatonta
Yinin ranar haka tayishi a dakinta ko abinci akazo akayi mata Maganarshi Saidai tace a hauro mata dashi sama kuma cikin sa'a mummy bata tankamata ba akan hakan, qila itama fushin takeyi
Wayarta kau kasheta tayi don tasan Deen bazai barta ta numfasa ba da kiraye kirayenshi gashi ita bata cikin mood din Waya dashi kwata2 don batama son ya fuskanci wani abu gameda abinda ke faruwa
Da daddare bayan wajajen 9:14pm tafito daga dakinta, tasan yanzu daddy na can yana kallon news while mummy na dakinta tana shiri
Dama wannan lokacin ta ware don tasamu daddy suyi magana takuma bashi hqr akan abinda yafaru.
Saukowa qasa tayi ta fita daga part din gabadaya ta nufi part dinshi tana saqa da warwara akan abubbuwan data shirya zata cemashi.
Doorbell ta latsa sau biyu a na ukun ne taji muryar daddy ta cikin dakin yana bada izinin Shigowa
Saida taja numfashi ta fesar sannan ta murda handle din ta tura kofar ta shiga da sallama.
Dagowa daddy yayi daga kallon labarai da yake a t.v yana amsa sallamarta
Ahankali ta qaraso cikin dakin cikin sanyin jiki tana jin hawaye na kawomata
Daddy kau kafeta da idanu yayi harta qaraso tsakiyar dakin Hakan yasa ya miqamata hannu alamun tazo ganin Hakan yasata da saurin qarasawa ta riqe hannunshi ya zaunar daita gefenshi
Dora kanta tayi a kafadarshi tafara sheshekar kuka ahankali Hakan yasashi dan rungumota a jikinshi yana rarrashinta ahankali
Saida ta dan tsagaita kukan nata sannan daddy yace
"am sorry shaleleta, nine ko?"
Ahankali ta girgiza kai
"nice daddy"
"bake bace, nine. I shouldn't have yell at you" yafada yana shafa kanta ahankali cikin sigar rarrashi
"A'a daddy, duk ni naja ai, da ban biyemashi ba Amma naji haushi ne dayace wai beson Africans bayan shima African din ne
Shiyasa nikuma nace mashi bana son wanda baya kishin kansa bare asalinsa don ni bana masu kallon mutane, shikenan fa abinda nace" tafada cikin muryar kuka
Murmushi daddy yayi ya sake rungumota a jikinshi
"na yarda dake daughter don baki yimin qarya, I know you amma kuma shima ai ba qarya yayi ba, baki fito fili kika kirashi da dabban ba amma shi ya gane abinda kike nufi tunda ba qaramin yaro bane, idan bakayima mutum kallon mutum ba To kallon dabba zakayi mashi cikin dayan biyu amma babu komai, karki damu nima dazu don raina ya 6aci ne shiyasa kikaga nayi reacting haka amma kar Hakan ya dameki, komai ya wuce, shima Alhaji Abubakar din be dauki abin da zafi ba tunda ko dazu muna tare dashi, so no need to worry"
Dagowa tayi ta kalleshi da watery eyes dinta fuska a marairaice tace
"daddy ka yafe min?"
Dariya daddy yayi
"ni dama ai bakiyimin komai ba, kima bar damun kanki kinji, pretend nothing happened"
Murmushi tayi cikin jindadi taqara kwantar da kanta akan kafadarshi tana lumshe idanu shikuma yayi mata kiss a tsakiyar kai sannan ya maida hankalinshi ga kallon dayakeyi
Shiru dakin ya dauka na wani lokaci babu abinda ke tashi dakin sai muryar yar jaridar dake karanto labaran duniya cikin t.v din.
Daddy hankalinshi kacokam yana kan news din itakuma zee saqa da warwara take akan yadda zata tado maganar Deen Amma takasa sanin ta ina zata fara
Haka sukaita zama har Saida aka gama news din
Ganin dai wannan shine daidai lokacin daya kamata ta tado maganar don mummy na iya Shigowa a kowanne lokaci yasata dan muskutawa ta daga kanta daga kafadarshi
"yadai? Barci ko?" inji daddy cikin kulawa
Murmushi kawai tayi sannan ta kuma sauke idanunta qasa tana wasa da yatsunta ta Wani yi kalar tausayi
Ganin Hakan yasa daddy riqo hannunta datake wasa dashi din yace
"tell me, wani abu ke damun ki?"
Shiru tayi kuma bata dagoba
Qara squeezing hannunta yayi
"tell me" yafada a tausashe
Hadiye wasu yawu ahankali sannan tace
"daddy, dama...maganar Deen ne.... Please daddy.."
"I thought mun riga munyi closing wannan chapter dake" daddy ya katseta da fadin Hakan
"daddy, wlh Deen beda matsala ko kadan, he's very nice and innocent, gashi yanada ilimi both boko da Arabic and he loves me so much more than I did to him"
"so? Don duk yanada wadannan abubbuwan Hakan na nufin zai iya riqeki? Anacin ilimi ne? Ko ana saka kyawawan hali? Meye aikinshi? Nawa yake samu a wata? Sune abubbuwan daya kamata ki gayamin"
"daddy he's still under-graduate wannan shine last year dinshi a school kuma yace min yana practicing carpentry work irin na funitures yana dan samu anan kuma ai kafin lokacin yagama school nasan ma yasamu aiki"
"carpentry? Nufin ki kafinta zaki aura? Diyar dan faranshi a matsayin matar kafinta?"
"daddy I told you zai samu aiki kafin lokacin" tafada kamar tayi kuka
"yaushe? A wannan Nigeria din kikeda yaqinin samun aikinshi da wuri? Masu kwallin degree har masters nawa ne ke kan titi Suna yawo kullum don neman aiki? Wasunsu sunfi shekaru biyar suna buga bugar neman aikin haryanzu basu samuba, ahaka zakiyita jiranshi har saiya samu aikin wanda allah kadai yasan lokacin?"
"Daddy, kana da companies dayawa, yanzu haka akwai dayawa dakake ginawa, kullum cikin daukan ma'aikata kake, a ganina samun aiki bazai yima wanda nakawo wajenka a matsayin wanda nakeso wuya ba don ko wasu nakawo Koda bansansu ba kawai nayi niyyar taimakonsu nakawosu wurinka gani nake zaka iya sama masu aiki a cikin kanfanoninka bare wannan"
Murmushin manya daddy yayi
"yanzu na gano komai, kuma na tabbatar da abinda nake zargi.
Wato dama don kudinki yake sonki, don yasan ke diyar wani ce wanda idan ya ra6a yasan zai kwashi arziqi, tunda harya fara sanya maki tunanin ni zan samomashi aiki"
"haba daddy" zee tafada hawaye na kawomata
"wlh daddy, kaji na rantse? Bamu ta6a wannan maganar dashi ba hasalima bayada kwadayi ko kadan wlh, abin hannun mutum be cika damunshi ba"
"haka zai nunamaki ai amma a zuciyarshi akwai wata manufa ta daban, auran jari yakeson yi dake yadda shima zai ra6i arziqi, nawa akayi? Nasha ganin irin case dinnan a wurare da dama, sai yaro yazo ya hurema diyarka kunne ya kasance ta aminta dashi dari bisa dari, ta nace sai an aura mata shi sai angama sannan tazama itace abin wulaqantawa na farko a Wurin shi sannan kuma yafara planning yadda zai handame komai nata yadawo qarqashinshi, that's it, that's their aim"
Hawaye sosai zee keyi tunda yafara maganar
"haba daddy, why zaka siffantashi da wadannan munnanan aiyukan? Don baka sanshi bane, da kasanshi da bazaka ta6a fadin haka akanshi ba" tafada cikin kuka
"kema ai iya abinda yakeso kisani gameda halinshi yabari kika sani, dama bari zaiyi kisan qudurinshi? Koko cemaki akayi hali a fuska ake ganewa, Zainab you're too young, bakisan komai ba a rayuwarnan.
Ni nasan duniya kuma nasan mutanen cikinta, huldata ta yau da kullum yasa nasan mabanbantan halayen yan Adam
Ba kowanne murmushi ke amsa suna murmushi ba, wani murmushin na mugunta ne, don mutum yayi looking innocent ba hakan na nufin he's innocent din har cikin zuciyarshi ba
Kin riga kin makance a soyayya, ya riga ya burkita tunaninki, bazaki iya gane komai ba yanzu don bakya a hayyacinki
amma ni ina a hayyacina kuma bazan ta6a folding hannayena ina kallonki ki fada halaka ba, never!
Don Haka ma mubar wannan maganar don rayyuka ne kawai zasu 6aci don abune da bazai ta6a yiwuwa ba"
Kuka sosai zee keyi, tama rasa abinda zatace
Bata ta6a sanin haka akeji ba idan akaqi fahimtarka, bata ta6a sanin haka akeji ba idan aka soki masoyinka ba aka laqamashi abinda kasan bazai ta6a iyawa ba
Wai Deen daddy ke cewa saboda kudi yake sonta, yaudararta kawai yakeyi saboda kudinta, how? Mutumin da abin duniya basa gabanshi? Be damu da abin hannun mutum ba? Tayaya?
Shigowar mummy da sallamar ta yasa duk suka dago suka kallo kofar
Mummy tadanyi Jimm ganin expression din fuskokinsu, zee idanu jajur ga hawaye a fuskarta shikuma daddy alamun 6acin rai a fuskarshi
Qarasowa tayi cikin dakin Hakan yasa zee miqewa tsaye
"Saida safenku" tafada idanunta a qasa sannan ta juya ta fice dakin
Binta da kallo duk sukayi harta fita
Maida kallonta mummy tayi akan daddy Saidai ko damar yin magana be bata ba shima ya tashi ya nufi bedroom dinshi rai 6ace.
Da gudu ta nufi gadonta ta fada akai ta cigaba da kukan datake
Tarasa meyasa daddy bazai tsaya ya fahimceta, tarasa meyasa daddy yayi ma abin mummunar fahimta.
A ranar barci rabi da rabi tayi sai can gab da asuba wani barci mai dadi ya dauketa Hakan yasa Saida mummy tasha wahala kafin tasamu ta tashi sallar asuba.
Koda tagama komawarta barci tayi bata farkaba sai wajajen 8:30am shima don mummy ce ta sake tadata.
Wanka tashiga tayi sharp sharp tafito ta shirya ta tsara makeup dinta sannan tafito cikin shirin school ta sauko qasa
A falo ta tarar da mummy, gaidata tayi ta amsa sannan ta nuna mata dining area tace taje tayi break
Babu musu tawuce don tasan dole tayi inba haka ba ranta ne kawai zai 6aci a banza
Tadan ci babu laifi sannan ta taso tazo tayiwa mummy sallama sannan tafice.
*UMYU*
Qarfe 9 da yan mintuna suka isa makarantar
Tana jin anyi parking ta bude lumssasun idanunta ta dan kalli waje sannan ta miqe zaune daga jinginen datake da kujerar motar ta tsaida waqar datake ji ta bluetooth din kunnenta
Jitayi an bude mata kofa Hakan yasata daukar jakkarta tafara yunqurin fitowa.
Dago kan da zatayi sai taga ashe Deen ne ma ya bude kofar, yana tsaye riqe da murfin motar yana kallonta
Dan wara idanunta tayi alamun dama kaine
Shikuma yayi mata murmushi tareda ja da baya yana bata hanya don saukowa
Ahankali ta sauko tana kallon smiling face dinshi tana jin damuwarta na yayewa a hankali.
Saida ta ida fitowa sannan ya maida kofar ya rufe sannan ya juyo wajen ta yana mata murmushi yace
"Good morning"
Murmushi kawai tayi mashi sannan tace
"ya weekend?"
"Bad.. That's the most boring weekend I've ever had"
Dan wara idanu tayi
"dagaske? Meyasa kace haka?"
"zan gayamiki, but first mutafi tukkuna"
Hannu ya miqamata yana dan russunawa
"may I?"
Tasan abinda yake nufi Hakan yasa tabashi jakkarta itama ta miqamashi hannu ya doro mata littatafanshi akai
Murmushi sukayima juna sannan suka nufi cikin school din.
Basu yada zango a koina ba sai library don dama yau sunyi zasu dan ta6a karatu
Kwana biyu soyayya ta hanasu karatu, da sun zauna sai su bige da firar soyayya before you know it lokaci ya tafi hakan yasa suka yanke shawarar fidda ma kansu timetable din karatu inda zasuyi scheduling komai yadda ya kamata.
Usual seat dinsu suka zauna kowa na ajiye abin hannunshi bisa desk
"Tundazu nake jiran zuwanki"
"to? Amma ai am not late ko?"
"you're not late amma son ganinki ne yasa naga kamar kinyi late din"
Murmushi zee tayi batace komai ba
"how's your weekend?"
"cool.. Kaifa?"
"not that cool" yafada yana yatsine fuska
"why not?"
"I was missing you, most especially muryarki, wai me yasamu wayarki?"
"kajita kashe jiya?"
"yes, tunda mukayi wayar nan da safe naketa neman wayarki amma shiru, what's wrong?"
"matsala tadan samu shiyasa, muna cikin waya ta dauke sai screen din yabar kawo haske sai kawai na badata aka gyaromin" tafada tana daukar jakkarta dake gabanshi ta fara zuge zip din
"ayyah, I thought as much. But are you sure you're ok?"
Dagowa tayi daga bude jakkar datake
"Me ka gani?"
Daga kafadu yayi
"kawai naga kamar you're not ok ne, kinmin wani iri"
Murmushi kawai tayi ta cigaba da leqa jakkarta
"then idanunka sun fara ciwo" tafada cikin tsokana
Murmushi shima yayi yace
"babu mammaki"
Ciro handout da wani littafin tayi tana cewa
"yanzu dai mufara, karka shagalar damu da surutunka"
Harararta yayi yafara Ciro Littafi shima
"ni dake wa yafi surutu?"
"ni dakai"
Dariya sukayi atare sannan duk suka bude Littatafan suka fara duddubawa
Sun dan jima ahakan kafin lokacin shiga lecture din zee yayi ta wuce ta barshi anan shima yana duba nashi Littatafan kafin shima lokacin shiga class din nashi yayi shima ya tashi.
Babu laifi zuwanta school a yau ya ragemata damuwarta sosai kuma ta cigaba da iya qoqarinta wajen 6oye damuwarta don ganin Deen be fahimci komai ba dukda dai yini yayi yana mata mitar shidai sai yaga kamar she's not ok
Abin na bata mammaki don sosai take qoqarin pretending komai is ok amma sai yace tayi wani iri kamar something is wrong, idan yace Hakan saita tsokaneshi akan qila idanun ke buqatar doctor sai suyi Dariya Hakan kuma bazai hana yasake yimata maganar ba idan yasake kallon fuskarta.
Sai wajajen 3pm bala yazo daukar zee
Har motar Deen ya rakota kamar yadda suka saba tun bayan fara soyayyarsu
Shi ya bude mata kofar tashiga sannan ya rufo mata yana cemata sai sunyi waya
Kada mashi kai kawai tayi tana murmushi
Dage tinted glass din motar tayi takoma ta jingina da kujera tana kallonshi
Jin an tada motar yasa Deen dake waje fara daga mata hannu dukda
All Chapters
Chapter 1
Chapter 2
Chapter 3
Chapter 4
Chapter 5
Chapter 6
Chapter 7
Chapter 8
Chapter 9
Chapter 10
Chapter 11
Chapter 12
Chapter 13
Chapter 14
Chapter 15
Chapter 16
Chapter 17
Chapter 18
Chapter 19
Chapter 20
Chapter 21
Chapter 22
Chapter 23
Chapter 24
Chapter 25
Chapter 26
Chapter 27
Chapter 28
Chapter 29
Chapter 30
Chapter 31
Chapter 32
Chapter 33
Chapter 34
Chapter 35
Chapter 36
Chapter 37
Chapter 38
Chapter 39
Chapter 40
Chapter 41
Chapter 42
Chapter 43
Chapter 44
Chapter 45
Chapter 46
Chapter 47
Chapter 48
Chapter 49
Chapter 50
Chapter 51
Chapter 52
Chapter 53
Chapter 54
Chapter 55
Chapter 56
Chapter 57
Chapter 58
Chapter 59
Chapter 60
Chapter 61
Chapter 62
Chapter 63
Chapter 64
Chapter 65
Chapter 66
Chapter 67
Chapter 68
Chapter 69
Chapter 70
Chapter 71
Chapter 72
Chapter 73
Chapter 74
Chapter 75
Chapter 76
Chapter 77
Chapter 78
Chapter 79
Chapter 80
Chapter 81
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 35 Chapter of 81