tashi kagani, taso" tafada tana miqewa tsaye tana jan hannun Deen da kanshi yayi mugun kullewa
tashi shima yayi tajashi har dakinta yana biye daita suka shiga
"kagani? na tattara komai tafiya Kawai yarage, Kawai mutafi don allah"
tsayawa yayi yana bin jakunkunan kayansu dake tsakiyar dakin da kallo Speechless, yama rasa meke faruwa
"da daddare saimu tafi Kawai yadda babu wanda zai ganmu ko?" inji kaka da hawayenta yaqi tsayawa ga jikinta har lokacin rawa rawa yakeyi
dakyar Deen ya iya tattaro yawun bakinshi ya hadiye.sannan yace
"kaka.. wai meke faruwa ne? ina zamu?"
"koina ma,.Kawai muyi nisa danan"
"amma akan wane dalili kaka? Kawai saimu bar gari haka Kawai? haka Kawai saimu gudu mubar gari kamar 6arayi" yafada totally confused
"Kamal, bazaka ganeba amma ni nasan abinda na hango, wlh inaji ajikina idan muka cigaba dazama anan sai an rabamu, inajin hakan ajikina" tafada wasu hawayen nasake saukomata
"wazai rabamu kaka?"
"nima bansaniba Kawai mubar nan"
"amma kaka shikenan saimu bar gari? ina zamuje? wa mukedashi? wani wurin garemu bayan nan?"
"Kamal zamu samu wurin zuwa, nan ma ai sdaga wani wuri mukazo kuma muka samu nan din har muka zauna mukayi tsawon shekarunnan, mutafi insha allah zamu samu wurin zuwa allah na taredamu"
"amma kaka karatuna fa? bama wannan ba kin manta jibi za'aje tsayar da maganarmu da Zainab? duk ahakan zamu bar gari?" inji Deen dake cikin confusion sosai, kwata2 magangganun kaka doesnt make sense to him
"duk ina sane da hakan Kamal, duk wadannan basuda muhinmmanci yanzu"
"basuda muhinmmanci?" ya tambaya cikin tsananin mammaki
"eh Kamal, abinda yafi muhinmmanci shine mucigaba da rayuwa da juna..atare"
shiru Deen yayi yana kallonta kamar yau yafara ganinta saikuma ya girgiza kai yakama kafadun kaka da hannun bibbiyu ya zaunar daita gefen gadonta
"kaka meya faru? don allah ki gayamin meye silar dukkan wadannan abubbuwan"
"babu komai Kawai sonake mubar garinnan, hankalina be kwanta da zama anan ba kuma"
"meyasa hankalinki be kwanta da zamanmu anan ba din?"
"Kawai hakanan, Kawai mutafi"
tsayawa yayi again yana kallonta kamar yau yafara ganinta
"intafi inbar karatuna bayan befi shekara ba zan qarqare gabadaya?"
"wanda kayi allah yasamashi albarka, dama meye amfanin karatun don dai mutum ya iya rubuta da karantawa ne bayan hakan ko ka gama aibakada tabbacin cin abinci dashi tunda mutane nawa suke gararanba atiti da kwalinsu aiki ya gagaresu, idan mukaje inda mukaje saika samu aikin hannu mu cigaba da rufawa juna asiri"
sake sakin baki Deen yayi yana kallonta cikin tsantsar mammakin abinda take cewa can kuma yace
"maganata da Zainab fa?"
tsaki taja
"itama sai a haqura, aiba ita kadai ce mace aduniya ba ko?"
cikin tsananin mammaki yace
"a haqura?"
"eh, allah zai hadaka da wacce ta fita"
"haba kaka? jibi fa za'a tura..."
"babu inda za'a tura, kai nifa dama can bason abinnan nakeba shima munafikin uban nata baso yakeba, na me zanbari a tarwatsamin farinciki a banxa a wofi? kama cire wannan maganar aranka don yanzu kam babu ita"
jin magangganunta yayi kamar saukar guduma atsakiyar kanshi
kallonta Kawai yake totally Speechless
"kayi shiru kana kallona" tafada ganin kallon yayi yawa
"amma dai,wasa kike ko kaka?"
tsuke fuska tayi
"alamun wasan kagani a fuskata"
"to kaka idan ba wasa ba meye zamu kira wannan to?"
"kai yayi maka kama dawasa amma babu ko alamun wasa a magana ta, batunka da wannan yarinyar babu shi!"
"meyasa?" yafada ahankali yana kallon kaka da idanunshi dasuka kada sosai
"saboda nace babu shi don haka kama manta da batwwannan yarinyar don ba alhairi bace agaremu"
sosai zuciyar Deen take zafi jiyake kamar ana gasamashi ita
"amma kaka kinsan inason Zainab ko?" yafada yana kallonta da idanunshi dasukayi jajir
"zaka daina sonta ne ahankali"
ahankali yashiga girgiza kai
"kaka baxan ta6a daina sonta ba, babu ranar dazan daina sonta, kada allah ya gwadamin ranar kaka"
"Kamal ni kake fadawa haka?"
"kiyi hqr kaka, amma Zainab itace komai tawa, itace farincikina itace komai tawa bazan iya rabuwa daita ba"
hawayene suka saukomata
"itace komai taka Kamal, wato tafini matsayi agurunka?"
girgiza kai yayi yace
"ko daya kaka, kowanne da matsayinshi aguna kaka, bazata ta6a finki matsayi ba amma kamar yadda ban iya rayuwa babu ke haka itama bani iya rayuwa babu ita"
kuka sosai kaka ta fashe dashi
"ni kake fadawa bazaka iya rayuwa babu itaba Kamal? duka yaushe kasanta? kenan tafini muhinmmanci agurunka"
"kaka ba haka bane, nina rasa dalilin dayasa baki sonta bayan ita tana sonki" yafada kamar zaiyi kuka
"ni ba itace banisoba, bani daison munafikin babanta ya cutar damu ne"
"me babanta zaiyi mana? yafa amince da maganarmu kuma harnan yaxo yabaki hqr akan abubbuwan dayayi amma dukda haka bazaki sama abin albarka ba? ni yanzu meye hujjata ta janye wannan maganar? mahaifinta ya yarda har yasa aturo to menene kuma ya rage?"
"munafikine mahaifin nata, Kawai yanuna ya yarda ne amma hakan bekai zuciyarshi ba, turowan ma dayace ayi duk na manufa ne" tafada cikin kuka sosai
"manufar me kaka? meye manufarshi akai?"
"yasan bamuda kowa kamal shiyasa yace aturo, soyake ya titsiyemu"
"meye don bamuda kowa? ai ba daga sama muka fadoba, saimu fadamasu komai gameda mu, kuma koda bamuda kowa wadanda zasu tsayamana bazasu gagaremu ba, ga Mallam Nasiru da sauran mutanen arziqin unguwarnan nasan zasu tsayamana"
murmushin takaici kaka tayi
"hmmm yaro yarone, bazaka gane komai ba Kamal, bazaka gane ba"
"meye bazan ganeba kaka? kifadamin babu abinda bazan ganeba, idan akwai wani abu bayan wannan ki gayamin"
"nidai nace babu maganarka da wannan yarinyar kuma gari dolene mubarshi, kaji na gayamaka" tafada tana daure fuska don tasan duk abinda zatace mashi bazai ganeba
Tashi Deen yayi tsaye yana kallonta
"kiyi hqr kaka amma baxan iya ba, baxan iya barin Zainab ba, ina sonta"
daga haka yajuya yabar dakin
binshi da kallo tayi baki sake harya fice daga dakin
tunda suke bata ta6a sashi abu yaqiya ba sai yau
fashewa tasakeyi dawani kukan mai tsuma zuciya cikin rasa abinyi kuma....✍?
*manage please*
Ummin fasihu🧚🏻♀?
8/2/21, 9:45 PM - Buhainat😝: *🙍🏻♂️DEEN🙍🏻♂?*
*093*
Tunda Deen yake beta6a shiga halin damuwa da confusion irin ranar ba
koda yafita ma rasa inda zaya yayi Kawai saiyaita yawo batareda yasan inda zaya ba
sosai damuwa tayimashi katutu arai, yarasa meya samu kaka data burkucemashi lokaci daya ta bijiro da wannan buqatar tata marar yiwuwa
nan take yamanta dawani batun shirye shiryen Introduction, damuwa ta maye gurbin doqin dayakeyi
aranar sai bayan isha'i yashigo gidan yana addu'ar allah yasa kaka tadawo hayyacinta tabar wancan maganar marar ma'ana
saidai me? yana zuwa yatarar da wani tashin hankalin inda kaka ta tsaya akan bakanta na barin garin, qarshe ma tace idan shi bazai bita ba ita zata tafi ita kadai duk yadda allah yayi daita daidai ne
sosai Deen yashiga tashin hankali ganin dagaske fa kaka take
babu roqon da baiyi mata ba da magiya harda kukanshi amma firr kaka taqiya, takoma kamar wata zautatta bataji bata gani
ganin dagaske tafiyar zatayi tabarshi yasashi shima amincewa da binta din don baxai iya rayuwa batareda itaba, itace yabudi ido yasani duk duniyar nan bayada kamarta, itace uwarshi itace ubanshi itace komai nashi
xai iya rayuwa batareda zee ba dukda rayuwar bamai dadi ba don rasata yana daidai da rasa farincikinshi amma bazai iya rayuwa batareda kaka ba, bama zai iya misalta rayuwa batareda ita ba.
haka ya amince ba don yasoba amma ya roqeta akan tabari sai gobe sai sutafi din
kamar bazata yarda ba saikuma ta amince akan gobe tafiya babu fashi ko dashi ko babu shi tafiyarta zatayi
ranar yadda Deen yaga rana haka yaga dare
ganin komai yake kamar a mafarki, jiyake dama mafarki ne da babu wanda zaikaishi murna a duniyar nan
kwata2 he never saw these coming, abin yaxomashi ne Kawai daga sama, yakasa yarda cewa zaiyi nisa da zee, nisa na har abada, yakasa ma imagine din hakan aranshi Kawai gani abin yake kamar a mafarki
Washegari ko kofar gida be leqa ba, yana cikin daki idan kuma yafito to lokacin sallah ne yayi saiyayi alwalla yakoma dakin yayi abinshi
abinci ma kasa ci yayi haka kaka ke kawo abinta tana daukewa
itama kakar kallo daya zakamata kasan she's down sosai, she looks so pale and disturbed, komai na duniya bayayi mata dadi
ganin Deen a halin dayake ciki baqaramin qara dagulamata lissafi yake ba saidai takasa yin komai akai, takasa koda consoling dinshi
haka suka qarashe wuninsu agidan cikin wani irin yanayi marar dadi wanda basu ta6ayin irinshi ba tunda suke don kowa na qunqume a dakinshi babu mai fitowa saida dalili, magana ma kanta bata hadasuba sosai kowa nafama da zuciyarshi
sai a lokacin isha'i Deen yafita daga gidan yaje masallaci don yin sallah
sai bayan sunfito yahadu da wani dan unguwar nasu mai suna Salman wanda yakasance kamar aboki ne gareshi yabashi wani envelope tareda cemashi wata zatazo sunanta Zainab don allah idan tazo yabata saqon nada muhinmmanci
tsokanarshi Salman yashigayi akan saqon menene, badai na soyayya bace shidai dan murmushi kawai yayi yayimashi sallama akan zaishiga gida don samm he's not in the mood for any joke
koda yakoma gidan awaje ya tadda kaka tabuga tagumi very worried
be tankamata ba yashige dakinshi don shima kanshi nashi damuwar ta isheshi kaya
komawa dakin yayi ya raku6e wuri guda staring at space
har lokacin yakasa yarda da abinda yake faruwa, he can't imagine wane hali zee zata shiga idan taji labarin tafiyarshi
hakan yasashi lalubo wayarshi dake kashe tun jiya ya lalubo numberta ya bugamata
jin muryarta yasa wasu emotional feelings tasomashi, she sound so innocent and cool
nan take saiyaji tausayinta ya mamayemashi zuciya
bata cancanci abinda yake shirin yimata ba, bata cancanci yayi breaking heart dinta ba bayan tasoshi da dukkanin zuciyarta, tasoshi a yadda yake batareda tayi la'akari da tarin difference dake tsakaninsu ba
nan take yaji wani irin guiltiness a zuciyarshi, ya zaiyi? ya zaiyi da rayuwarshi?
haka sukayi wayar yana iyakar bakin qoqarinshi wajen controlling muryarshi don wayar yake yana hawaye, tunanin cewa qila muryarta yakeji na qarshe yasa yakasa tsaida hawayenshi
itama taso tagane kamar ba daidai yake ba don taji a yanayin muryarshi kamar he's not ok ganin hakan yasa yaimata qaryar mura yake.
kalaman dayake mata amfani dasu da ace mai saurin ganewa ce data gane ba lafiya amma dayake bata kawo hakan aranta ba yasa batabi takansu ba sosai
wannan innocence din nata kuma ba qaramin qara tsuma zuciyarshi yayi ba har hakan yasa daga baya yakasa cigaba da wayar daita sukayi sallama akan beda charge
bayan gama wayar ya kasheta gabadaya ya zare sim card din ya karya yana hawaye sosai
sannan yatashi ya tattara important stuffs dinshi ciki harda takardunshi, sannan ya dauko wannan band din da zee tabashi ranar Valentine wanda tun ranar ya adanashi cikin wani box yafiddoshi ya daura a hannu
komawa yayi kan katifarshi ya takure waje guda staring into space idanunshi jawur.
saida dare yayi sosai kafa dik ta dauke sannan suka fito daga gidan daga su sai kayansu wanda kecikin madaidaiciyar ghana must go sai qatuwar jakar goyo dake goye abayan Deen
kulle gidan sukayi da katon kwado sannan suka nufi hanyar barin layin
tafiya suke babu mai cewa kowa komai don duk yau maganar dasuka yiwa juna qididdigagga ce
babu dadewa suka isa titi don dama basuda nisa da titi
basu tsaya ba suka cigaba da tafiya gefen titin dake kwal don motoci ma sai jefi jefi suke wucewa saboda yadda dare yayi
sunyi tafiya sosai kafin susamu wata adaidaita data tsaya gabansu don jin ko tafiya ce
kaka ce tayima mai adaidaitan magana cewa tasha zasu
saida yaqaremasu kallo sannan yafadamasu kudin dazasu bada
kaka bata musaba tace suje dukda yasa kudi dayawa itadai burinta subar unguwar kwata2
ita tafara shiga sannan aka saka ghana must go din atsakiya inda akesa kaffafu sannan Deen da saikayi zaton kurmane saboda rashin maganarshi yashiga yana rufo yar kofar adaidaitan
babu 6ata lokaci mai adaidaitan yaja sukabar wajen
tafiyarsu zuwa tashar sunyishi ne silently don babu mai cewa komai cikinsu
sosai halin da Deen keciki ke damun kaka amma batasan mezata yimashi ba, batada kalmar dazata fadamashi dazaisashi jin sanyi hakan yasa tayi shiru tana hoping cewa komai zai wuce very fast insha allah
harga allah itama tasan wannan decision din yayi tsauri sosai musanmman ma ga Deen amma ya ta iya? hakan take ganin yafi musu alhairi don aganinta gwara wannan tashin hankalin da wanda take hangomasu nan gaba
tafiyar 30mins yakaisu tashar inda sa6anin koina wajen akwai mutane sosai ga fitilu takoina yadda kasan ba tsakar dare bane
biyan mai adaidaitan sukayi suka sauka da loads dinsu
ciki suka shiga inda yawanci duk travellers ne dazasu kwana a tashar da drivers din motoci
qarasawa ciki sukayi Deen biyeda kaka dake agaba yana sauraron yadda take tambayar inane wasu daga motocin zasu tafi
shidai haryanzu ko uffan bece ba sai binta dayake everywhere she go har daga qarshe tasamo masu motar dazasu shiga wacce zata Abuja itama ta za6eta ne don taga takusan cika kuma zatayi saurin dagawa
kayansu aka sakamasu a baya sannan suka kama seat suka shiga suka zauna saboda yadda iskan daren ke kadawa sosai
akwai few mutane ma acikin motar inda wasu ma barci suke wasu kuma idanunsu biyu, cikinsu kaka ta tambayi wani time akace mata yanxu uku da rabi na dare hakan yasata sauke ajiyar zuciya takoma ta jingina jikin kujerar
dagowa tayi ta kalli Deen dake zaune silently yana kallon yatsun hannunshi saitaji yayi mugun bata tausayi
ahankali ta kama hannunshi tadan matsa tana kallonshi
be dagoba bare ya kalleta sai cigaba da kallon hannayen nasu dayayi
"kayi hqr Kamal... insha allah hakan shiyafi alhairi" tafada ahankali tana kallonshi da idanunta dasuka duri ruwa
dan murmushi yayi wanda dagani kasan na qarfin haline Kawai ya kadamata kai batareda ya kalleta ba
"yanxu gayamin meke damunka? kana buqatar wani abu?" tafada tana kallonshi cikin kulawa
"inajin sanyi" yafada ahankali
kallonshi tayi cikin tausayawa sai tajawoshi jikinta yadora kanshi a cinyarta tashiga shafa mashi kai
"sannu, ai gari yakusan wayewa harda sanyin dare" tafada tana gyaramashi hular sanyin kanshi yadda zai rufemashi kunnuwa sosai don dama shigar sanyi yayi saboda yanayinshi
ahankali Deen ya lumshe idanunshi yana sauraron bugun zuciyarshi dake bugawa abnormally
ahaka har asuba tayi
duk fitowa sukayi sukai sallah sannan suka koma cikin motar da gab take da cika don saura mutane biyu
cikin qanqanin lokaci ta ida cika aka shishiga motar akayi duk abinda ya kamata sannan driver yahau ya tada motar yaja suka fice daga tashar
Tunda Deen yake beta6a long and boring tafiya ba irin wannan
tunda motar tafara tafiya ya maida kanshi ga window yana kallon waje yanajin cewa wai yau shi zaibar garinsu Katsina bawai bari na dawowa ba A'a na har abada
dukda shekaru sunja sosai amma yana iya tuna lokacin da suka shigota sama sama, lokacin yanada shekaru goma aduniya
tunawa yayi da fadi tashin dasukayi tayi da kaka kafin susamu wurin zama inda yazaman masu gida kusan na tsawon shekaru sha takwas
dukda yasan Katsina ba garinsu bane amma hakan be hanashi jin kamar yana barin bane don duk cikin garurruwan dasuka zauna babu wanda sukafi dadewa suka kuma yi rayuwa comfortably kamarta gashi yayi achieving abubbuwa dadama acikinta marassa goguwa a memory
lokacin dasuka fita kofar Welcome to Katsina wani feeling na emptiness ya ziyarci zuciyarshi
shikenan, shikenan yatafi, yatafi yabar abubbuwa masu matuqar muhinmmanci a rayuwarshi batareda sanin lokacin sake waiwayarsu ba
sai jiyayi kamar zuciyarshi tayi dropping daidai kofar yabarta abaya yayinda yanzu gangar jikin kecikin motar ana tafiya daita
ahankali ya lumshe idanunshi, imagining yafarayi me zee keyi adaidai wannan lokacin
wataqila tanacan cikin farincikin kasancewar yau zai turo magabatanshi, wataqila takirashi, wataqila sunacan sunata shirye shiryen Introduction din
ya Zainab zataji? ya zataji idan dagabaya tagane abinda yayi, ya zataji idan tagano he yayi betraying trust dinta
_*please don't leave me, no matter what*_
muryar zee tadawo mashi
_*never... I will never*_
yasake tuna amsar dayabata lokacin
sake maida idanunshi yayi ya lumshe yanajin wani irin zazza6i na tasomashi
yasan shi da farinciki kuma har abada, yasan wannan new chapter din daya bude na rayuwarshi is the worst chapter
lokacin dasuka tsaya sallar zuhr jikin Deen yayi ringis da zazza6i
sosai hankalin kaka yatashi ganin hakan
ahaka yayi qarfin halin saukowa shima cikin motar da niyyar yin alwalla yayi sallar saidai inda ya tsugunna yana alwallar yahau kwarara amai
sosai hankalin kaka yaqara tashi duk ta gigice tana kuka ganin yadda yake zazzaga aman kamar zai amayar da yan cikinshi gabadaya
da taimakon wasu daga mutanen motar yasamu ya tsaftace jikinshi ya daura alwalla yadawo wata yar rumfa dake wajen inda duk nan pasinjojin sukayi sallah
sosai mutanen suka tausaya mashi don kallo daya zakamashi kasan yana jin jiki sosai
adaddafe yayi sallar lokacin har ansiyomashi maganin masassara a wani dan chemist dake wajen kaka kuma ta siyamashi fura inda tabashi yasha kafin yasha maganin
ko rabin furar besha ba yashiga kwara wani aman kamar zai zazzago yan cikinshi
sosai kaka takuma rudewa, kuka take bilhaqi da gaskiya cikin tashin hankali tana ataimaka mata karya mutu shikadai gareshi
sosai mutanen wajen suke bakin qoqarinsu wajen taimakawa don sosai Deen kejin jiki, yayi laqwas ga wani irin zafi da jikinshi yadauka
kasancewar a inda suka tsaya qauye ne yasa babu wani clinic kusa gashi dan chemist dinma irin dan shagonnan ne da ake saide2 bawani abu suka saniba gameda lfy Kawai suna saida irin paracetamol ko maganin ciwon jiki saboda ire iren pasinjojin dakan tsaya a wajen idan suna buqata
ganin halin da Deen keciki yasa mutanen wajen ba kaka shawarar gaskiya idan suka cigaba da tafiyar nan ahaka jikin Deen ida rikicewa zaiyi Kawai susamu cab dazai shiga cikin gari dake kusa takaishi clinic ko babban chemist inda za'a dubashi abashi right meditation
hakan kau akayi, nan aka saukomasu kayansu dayake wurin kamar yar karamar tasha ce nan da nan suka samu mota Golf mai shiga cikin gari
ahaka suka shiga kaka nata dauke hawaye
babu 6ata lokaci motar tasu ta tashi tafita daga tashar
tafiyar awa daya sukayi suka qaraso cikin gari inda drivern yakaisu wata yar qaramar clinic ta gwamnati
lokacin Deen ko bude idanu be iyawa sosai
tareda drivern suka shiga ciki ganin yadda Deen kejin jiki ga kaka tsohuwace bata iya handling komai ita kadai hakan yasa yatsaya ya taimaka wajen yin zirga zirgan komai har suka samu nasarar ganin likita
anan aka dubashi aka rubuta mashi magungunnan daya kamata
drivern nanan har saida yaga ansiyo magani inda dakyar suka samu Deen yasashi bayan yasha wani dan shayin da aka siyomashi wajen clinic din sannan yatafi yabarsu anan yakama gabanshi shima
kasancewar basuda wurin zuwa yasa suka tsaya cikin asibitin don ga halin da Deen keciki tafiya bata yiwuwa agaresu
ataqaice dai cikin asibitin suka kwana, Washegari kuma suka sake daukar hanya ba don ya warware ba amma da dan sauqi
ataqaice dai sai wajajen 3pm suka isa garin Abuja a wurwurce har wani ramar dole kowannensu yayi
suna isa Abuja suka qara danganawa da asibiti don a lokacin sosai jikin Deen yasake rikicewa
wannan karon ganin yanayin da Deen keciki yasa aka basu gado
saida sukayi kwana uku a asibitin kafin yadanji sauqi aka sallamesu
a lokacin duk sun kashe yan kudaddensu wadanda suka rage basu wani taka kara suka karya ba gashi basuda mazauni dama acikin kwanakinnan asibitin ne yazama kamar gida agaresu
duk kaka takoma wani iri ta fiffige saboda damuwa, bata ta6a kawowa haka tafiyar zata juyemasu ba
gani take komai zaizo masu smoothly kasancewar lokacin dasuka fito sunada enough kudinsu wanda zasuyi tafiyar harsuzo susamu haya sukama inda zasu zauna amma wannan rashin lafiyar ta Deen dukta cinye kudin wajen hidindimun magungunna dana abinci
ganin halin da kaka tashiga na zullumin inda zasu koma lokacin da aka rubuta musu sallama yasa Deen dahar lokacin bawai ya warke garau bane ya dauki jakar dayayi parking important stuffs dinshi yazaro wayarshi wanda zee tabashi
anan yace ma kaka bari yaje ya siyar susamu ko kudin kama daki daya ne
dafarko kaka taso hanashi saboda batason yashiga gantsareriyar ranar da akeyi ya maidoma kanshi ciwo baya amma kuma saita haqura sanin cewa basuda wani option tunda ita ba iya zuwa zatayi ba
ahakan Deen yafita inda da tambaya yasamu shagon siyar da wayoyi yashiga don siyarda ita
jin tayin wulaqancin da akamashi a shagon farko yasashi fitowa yanufi wani inda nan ma kanwar ja ce
sosai abun yabashi mammaki ganin yadda suke mashi siyen wulaqanci bayan wayar babbace kuma mai tsada
kamar ya haqura da siyar da wayar amma ganin itakadai ce hope dinsu yasashi hqra inda yasamu ya saidata wani shago wanda yafi sauran siyenta da kudi
anan ya tambayi mai shagon inda zaisamu gida haya ko daki daya ne cikin sa'a saigashi mutumin ya hadashi dawani dilali da dama irin aikinsu kenan
hadashi yayi da dilalin inda dilalin yatafi dashi ya nunnuna mashi gidajen dakeda vacant na hiring
aciki Deen ya za6i daya inda yakama masu daki daya inda dakyar yasamu mai gidan ya yarda zai amshi kudin wata shidda daga baya sucika mashi sauran
gidan dakuna uku ne sai kitchen da bayi
akwai wasu occupant din aciki inda duk magidanta ne da iyalansu kowa da daki daya inda dakin da Deen yakama shine na qarshe
saida yabiya kudin hayan aka bashi makullin dakin sannan yafito yatari adaidaita don komawa asibitin
alokacin har jiyake kamar kanshi zai rabe gida biyu saboda sarawa haka dai yaita daurewa har suka iso asibitin ya sauka yabiya mai adaidaitan yashiga ciki
A reception ya tadda kaka don lokacin har an maye gurbinshi dawani patient a gadonshi hakanyasa dole tadawo reception din ta zauna
tana ganinshi tayi saurin miqewa tsaye don dama tundazu kamar a qaya take baxa idanu Kawai take taga ta inda zai 6illo
tararshi tayi tanamashi sannu don he looks so weak qarfin hali Kawai yakeyi
anan yafada mata yasamo masu mazauni amma daki daya
albarka taita shimashi tana jeramashi sannu tana tambayar yanzu me yakeji
cewa yayi babu komai Kawai ta tashi sutafi
anan suka tattara yan kayansu suka fito daga asibitin suka tari adaidaita yafada mashi inda zaikaisu
unguwar unguwar talakawa ce don ga yanayin unguwar Kawai zaka gane hakan
har kofar gidan adaidaitan ta saukesu suka sassauke kayansu suka biya sannan suka shiga
a lokacin har anfara kiraye kirayen la'asar
saida suka gaigaisa da occupant din gidan sannan suka qarasa dakinsu
anan Deen yake tambayarta yayi? hakan yasa tayi murmushi tana cewa yayi sosai allah yayi mashi albarka
da amin ta amsa sannan yace bari yaje yadawo
bejira cewarta ba yasake fita inda da kingin kudin hannunshi yayimasu sayayyar yan kayan daxasu buqata kama daga tabarma, bokiti, buta, yan plate biyu da cups sai tsintsiya kingin kudin kuma yasiyomasu kayan abinci wanda zasu dan fara dashi
sosai farinciki ya lullu6e kaka lokacin daya dawo da kayayyakin hakan yasa taita samashi albarka
tare suka tsaftace dakin suka shinfida tabarmar suka kuma ajiye kayansu da kingin kayayyakin da Deen yasiyo a wani Corner na dakin
sosai dakin yayi fili don bawasu kayan kirki aciki
sai a lokacin dik suka samu damar yin sallar la'asar din sannan kaka ta jiqamasu garin kwaki cikin wanda Deen yasiyo cikin kayan abincin suka sha Deen yasha maganinshi yakoma ya kwanta dukda babu kyau kwanciyar marece amma haka kaka ta kyaleshi don tasan yagaji sosai cos he looked so exhausted
haka Deen yaita kwanciya idanunshi alumshe dukda ba barci yake ba
tunanin zee Kawai ne dankare a zuciyarshi, yasan izuwa yanzu tagano komai kuma tasan ya yaudareta, yasan yanzu tana cikin wani hali don yaudara agun wanda kabama dukkan yarda ba qaramin ciwo gareshi ba
haka yaita kwance har wajajen magrib sannan yafito yayi alwallar magrib inda ya tadda kaka waje suna dan fira da matan gidan
alwallar yayi yafita inda bedawo ba sai bayan isha'i
yana dawowa yashige ya kwanta ya rufa da qaton bargonsu yana rawar d'ari sanadiyar sanyin dayakeji nakaimashi har cikin qashi
kan kace me har wani zazza6in yasake lullu6eshi inda kaka tashiga kuladashi cikin tsananin tausayawa jikan nata
ataqaice dai haka Deen yaita fama cikin kwanakin dasuka biyo baya, yau lafiya gobe sauqi
sosai rayuwa tayimusu wuya, ga ciwo ga babu kudi haka sukaita fama inda dan abincin da Deen ya siyamasu yaketa qasa every passing day
ganin hakan yasa Deen fara fita nema ganin kwanciyar bayi bace
haka yake fita ya yini waje yana yan buga buga qarshe yadawo da abinda be taka kara ya karya ba
abu ya hademashi goma da ishirin, ga ciwon dayake tsaitsaiye ga fita nema ga tarin damuwa dake danqare a zuciyarshi
gashi kaka bawata sana'a take ba bare itama ta taimaka don sana'a saida jari sukau ahalin yanzu ta cinsu ma Kawai suke, gashi rayuwa tafi tsada a Abuja bisa ga Katsina
haka sukaita rarrakawa Deen yana iyakar kokarinshi na ganin basu rasa ciba ko yayane
ahaka yasamu wani qaton shago a kasuwa na lemuna kala kala inda anan yake zuwa yatayasu safko carton cartons din juices ko ruwa daga manyan trailoli dake kawowa zuwa cikin shagon
shima dakyar yasamu aikin ashagon kasancewar akwai masu irin aikin sosai awajen
haka zasuyita zirga zirgan jigilar kayan daga motocin zuwa qaton store din shagon wasu masu barrow cikinsu kuma har dako sukema masu zuwa saye a shagon
kasancewar shagon babban shagone yasa kodayaushe cikin busy yake, kodayaushe cikin sauke kaya da siyarwa suke hakan yasa masu dakon wajen ke jigatuwa sosai musanmman
All Chapters
Chapter 1
Chapter 2
Chapter 3
Chapter 4
Chapter 5
Chapter 6
Chapter 7
Chapter 8
Chapter 9
Chapter 10
Chapter 11
Chapter 12
Chapter 13
Chapter 14
Chapter 15
Chapter 16
Chapter 17
Chapter 18
Chapter 19
Chapter 20
Chapter 21
Chapter 22
Chapter 23
Chapter 24
Chapter 25
Chapter 26
Chapter 27
Chapter 28
Chapter 29
Chapter 30
Chapter 31
Chapter 32
Chapter 33
Chapter 34
Chapter 35
Chapter 36
Chapter 37
Chapter 38
Chapter 39
Chapter 40
Chapter 41
Chapter 42
Chapter 43
Chapter 44
Chapter 45
Chapter 46
Chapter 47
Chapter 48
Chapter 49
Chapter 50
Chapter 51
Chapter 52
Chapter 53
Chapter 54
Chapter 55
Chapter 56
Chapter 57
Chapter 58
Chapter 59
Chapter 60
Chapter 61
Chapter 62
Chapter 63
Chapter 64
Chapter 65
Chapter 66
Chapter 67
Chapter 68
Chapter 69
Chapter 70
Chapter 71
Chapter 72
Chapter 73
Chapter 74
Chapter 75
Chapter 76
Chapter 77
Chapter 78
Chapter 79
Chapter 80
Chapter 81
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 74 Chapter of 81