harta haye saman sannan yasake daga girarenshi biyu ya kada kai ya cigaba da cin abincinshi
A daki zee ta tararda batool Kwance tana waya cikin harshen larabci
Zama tayi gefen gadon tana sauraron batool din absentmindedly
Idanunta ne suka sauka akan Ring din yatsarta dake sheqi sanadin hasken rana dayayi reflecting akanshi ta window din bayanta
Qurama zoben idanu tayi tunanuka kala kala na kai kawo a kwalwarta
Yanzu Deen na ina? Me yakeyi? Yana tunawa da ita kau? Koko ya riga ya shafe babinta a tarihinshi? Yana cikin farinciki koko akasin haka?
Yana kewarta? Koko bayayi?
Ta yarda ta biyo Ummu batool nan ne don aganinta zata iya mancewa dashi with time, amma daga jiya zuwa yau tafara tantamar yiwuwar Hakan
Don duk motsin da zatayi saiya fadomata arai, duk blinking idanun da zatayi sai yayi mata gizo a idanu
Anya zata iya mantawa dashi? Anya?
She doubt it, tana tantama sosai akan haka, don Deen acikin zuciyarta yake, yariga yabi Jinin jikinta, mantawa dashi daidai yake da musanya zuciyarta da wata wanda babu Deen aciki kokuma musanya jininta da wani wanda babu shi a gudanuwarshi
Jitayi an dafa kafadarta Hakan yasa ta dawo daga duniyar tunanin data lula
Batool ce zaune kusada ita tana mata murmushi
Kamo hannunta batool tayi tana kallon zoben yatsarta itama
"shi yabaki?" inji batool tana kallon Ring din
Dago idanunta zee tayi ta kalleta batareda tace komai ba
Itama batool ta dago tana kallonta sai tadanyi murmushi
"yanada kyau sosai" tafada tana dan Kada kai
Nan ma batace komai ba
"sister, wani lokacin you have to let go abinda kake matuqar so sosai, ba wai don son ranka ba sai don Hakan shi zai fiyemaka alhairi.
Wani sa'in abubbuwa masu kyau basu cika zama masu amfani ba, misali wannan zoben dake hannunki
Kina Ajiyarshi ne bayan kinsan bazai amfaneki da komai ba Saima ya jefaki a wani hali idan kika kalleshi, why not ki cireshi tunda kema sanin kanki ne be cancanci zama a yatsarkiba yanzu"
Dan murmushi zee dake kallonta Tundazu tayi saikuma ta maida kallonta akan zoben
"a tunaninki cireshin zai sauya wani abin ne?"
Saita girgiza kai
"babu abinda zai chanza, babu.
Rashin shi ne ma zai jawo wani abin"
Kallon zoben tasakeyi
"idan na kalli Ring din sai natuna da ranar, ranar dayake gabana, zube a gwiyagunshi begging me to marry him.
The love, affection, seriousness dana gani a qwayar idanunshi a ranar yana sani tantamar abinda nagani a takardar da yabani, yana sani tunanin anya shi ya rubuta takardar, da hannunshi?
But sadly shine, shine, dalili kuma shine ban sani ba, abinda yafi komai tsayamin arai kenan.
Meyasa zai tafi batareda gayamin atleast dalili qwara daya ba? Meyasa?
Atleast yafada min Koda kuwa zuciyata ce zata buga, Koda qarya zaiyi min yayimin amma bawai yatafi hakannan ba, leaving me like a lost cat in the jungle"
Batasan hawaye takeyi ba Saida batool ta jawo ta ajikinta tana share mata su
"it ok zee, nasan yadda kikeji.."
"baki saniba batool, kuma bazaki ta6a sani ba sai idan kin tsinci kanki a wannan halin, nikuma bana maki fatan haka"
Qara rungumeta sidely batool tayi sannan tace
"ki gayamin, ki gayamin tarihin soyayyarku"
Girgiza kai zee tayi
"A'a, nima da nasan abinda zanyi inmanta da tuni nayi Hakan"
"unfortunately baki sani ba, amma kuma idan kikayi sharing dinshi da wani zakiji sauqi.
Tunda abin yafaru kin ta6a zaunar da wani kinyi pouring out abinda ke a zuciyar ki?"
Ahankali zee ta girgiza kanta
"you see? Fadama wani damuwarka ma yana rage damuwa.
Problem shared is Problem solved.
Idan kin fadamin zaki samu abu daya zuwa biyu
Nafarko zuciyarki zata rage nauyi saboda kinyi pouring out abinda ke cinkushe a cikinta wanda ke hanaki saqat
Na biyu kuma, who knows wataqila ina iya hango maki wani abu a soyayyar taku ko kuma na sama muku solution, bawai don am perfect ba saidon kowa da irin nashi baiwar da hangen"
Murmushi mai ciwo zee tayi tace
"zan fadamiki saboda dalili na farko da kika fada, wato don naji sauqin abinda nakeji a zuciyata
Amma batun samun solution ba be tasoba, sai idan akwai Problem ake samun solution, anan babu wani Problem idan ma akwai to bansaniba, tayaya za'a samu solution din?"
Ajiyar zuciya batool tayi tace
"to shikenan, ki fadamin din, am all ears"
Itama zee Ajiyar zuciya ta sauke sannan ahankali ta maida kallonta akan zoben hannunta
"Sunanshi DEEN... KAMALDEEN MUHAMMAD...."
****
Ummy ce tashigo falon bayan taga tafiyar Abbu
A dining din ta iske Aymaan yanata aika abincinshi hankali kwance
Qarasowa wajenshi tayi taja kujera itama ta zauna
"Likita bokan turai" inji ummy cikin tsokana
Murmushi yayi sannan ya dauki glass cup din gabanshi yayi sipping ruwa
"Umminmu! Ashe jiya zaki dawo da nasani da banje aiki ba"
Harara ta gallamashi
"kamar duka kenan"
Dariya yayi
"Allah ummy jiya munshiga busy sosai, surgery hudu nayi da daddaren nan"
Girgiza kai Ummy tayi
"Allah sarki, ai mata na shan wuya, haihuwa yaqin mata, allah yasa kowacce tagamata lfy"
Sipping ruwa yasake yi sannan ya amsa da amin
"kaga qanwarka ko?" inji ummy tana kallonshi
"baquwa?"
Harararshi tasakeyi
"sunanta kenan?"
"I don’t know her name ai"
"shame on you, ace bakasan sunan cousin dinka ba"
Sosa kai yayi yana dan 6ata fuska
"kai ummy"
"to ai Gaskiya ce, to sunanta Zainab"
"oh kinga kina fadi na tuna, ai na santa lokacin danaje Nigeria last ai naganta lokacin yar qarama ce nasan bazata wuce 15 ba kuma she's a talkative tana magana sosai gashi batajin magana amma yanzu ta chanza sosai, naga ko magana batayi, ko haka girman yazo mata?"
Murmushi ummy tayi
"eh to, kasan ana qara girma ana qara nutsuwa, tabbas ta nutsu Saidai wannan nutsuwar haka bata lafiya bace don kamar yadda kace magana ma wuya take mata gata always moody"
Ajiye spoon din hannunshi yayi
"to meya faru? Meya maidata haka to?"
Ajiyar zuciya ummy tasakeyi tace
"she's heartbroken"
"heartbroken?" inji Aymaan yana kafe maman tashi da hazal eyes dinshi
"yes, wanda takeso ne ya yaudareta, kwanan nan ba kaji muna maganar introduction daza'ayi a Nigeria ba?"
"yes, naji kuna discussing dinshi da Abbu"
"to itace, yaron asalinshi dan talakawa ne don koko da qosai suke saidawa for living
Sun hadu da Zainab dinne a school and they both fell in love
Amma da maganar tazo wajen daddy saiyaqi yarda saboda yaron ba Dan masu hali bane plus yana gudun ace ba sonta ba yake kawai yaudararta yake yana sonta saboda kudin da mahaifinta kedashi
Daddy yayi iya qoqarinshi don ya rabasu amma a banza don she's deeply in love with the guy don a sanadin haka ta kamu da hawan jini saboda damuwa.
Ganin babu sarki sai allah yasa kawai ya yarda yakuma cema yaron ya turo magabatanshi suzo ayi introduction idan dagaske yake.
Lafiya lau aka fidda ranar introduction din har ya bugomin nan munata murna
Saidai ranar da aka fidda don yin introduction din babu yaron babu magabatan nashi babu alamunsu.
An jira anjira shiru gashi wayar yaron bata shiga
Ganin Hakan yasa daddy aika drivernshi don ganowa ko lfy?
Wai dayaje saiya iske gida garqame da kwado
Aranar dai Saidai aka watse ba'ayi introduction din ba
Washegari shiru, babu su babu alamar su
Hankalin Zainab ya tashi don tana sonshi Sosai fiyeda tunaninka
Ganin ta tashi hankalinta yasa daddy shiryawa washegari yaje yagano da kanshi and the same story ya tarar still gidan kulle
Zainab dai taqi yarda ta nuna tanaso taje tagani da kanta
Koda sukaje din saita tarar da abinda suka tarar suma, suna ahaka wani abokin yaron yazo wajen da shar6e6iyar envelope wai gashi inji yaron da sukaje nema
And could you believe what she saw inside?
Letter ne ya rubuta yana magangganu marassa kan gado wai he's gone wai tayi haquri wai he's gone forever"
"what? But why?" inji Aymaan
Watsa hannuwa ummy tayi
"oho, beyi stating dalili qwara daya ba nayin Hakan, kawai wai he's gone.
Anan take tayi collapsing a wajen daga nan aka kwasheta sai hospital
Saida tayi kwana uku kafin ta farfado, blood pressure dinta yayi high ga difficulty in breathing.
Dakyar aka shawo kanta a kwana na uku ta farfado kuma daga ranar takoma haka, babu uhm babu uhm uhm, yanzu ma fa wai da dan sauqi ne ma tunda idan akayi magana tana amsawa da kau bata magana Saidai tayi smiling painfully.
Ganin Hakan yasa kawai na yanke shawarar tahowa daita nan don am very sure zatafi saurin healing nan bisa ga can, don ko babu komai ta chanza environment. Shiyasa kaga na taho daita har lokacin da zata warware kamar babu abinda yafaru"
Sosai jikin Aymaan yayi sanyi, nan take yaji abincin gabanshi ya fita ranshi
"so sad" yafada ahankali
"very sad indeed wlh, donma kamar yadda nafada maka ta dan warware da lokacin danaje Nigeriar ne da sai kayimata qwalla"
Wani zafi Aymaan yaji ya ziyarci zuciyarshi nan take yaji ya tsani koma waye wannan mayaudarin
"amma wannan ya cika butulu wanda besan alhairi ba, ko babu komai ko don soyayyar Gaskiya data nunamashi be kamata ya badamata qasa a idoba"
"hmm ai kai kasan da Hakan shi besaniba"
Shiru yayi ya cigaba da huci, yana jin ranshi na 6aci sosai
"shiyasa nazo daita nan don tasamu sallama, Aymaan wannan aikin tareda ku zamuyishi, help her, help her forget her past, mu Hade qarfi wajen ganin mun mantar daita past dinta, tayi moving on kamar babu abinda yafaru"
Dagowa Aymaan yayi ya kalli ummy
"yes ummy, we'll do everything, everything wajen ganin mun mantar da ita past dinta, I assure you, insha allah zata yi farinciki fiyeda da"
Murmushi ummy tayi cikin jindadi
"barakallahu fika Aymaan, allah yayi muku albarka gabadaya, idan kukayimin haka kun biyani wlh"
Wani qayattacen murmushi Aymaan yayi yace
"karki damu ummy, wataqila dama basu daceba, wataqila ba alhairi bane agareta shiyasa allah ya kawar dashi, insha allah zata samu wanda ya dace daita, insha allah zatace gwara da akayi hakan, shikuma zaiyi nadama har qarshen rayuwarshi"
Murmushi jindadi ummy tasakeyi
"Alhamdullilah! Allah yasa Hakan Aymaan, allah ya tabbatar mana da alhairinsa"
Da amin Aymaan ya amsa yana daukar ruwan gabanshi yakai baki
"bari naje sama ok? Kayi sauri ka qarasa abincin karya huce" tafada cikin yanayin farinciki
Kadamata kai yayi kawai yasake jawo abincin gabanshi
Ganin Hakan yasa ummy wucewa tana jin wani madaukakin farinciki a ranta, tabbas da alamu haqanta zai cimma ruwa, taga alamun abinda takeso zai faru, idan kau Hakan yafaru sai tafi kowa murna a duniya.
Aymaan kau tana wucewa ya ture abincin gabanshi ya koma ya jingina da kujerar bayanshi ya harde hannayenshi a qirji
Fuskarta tayi mashi gizo a idanu, yes! She's in pain, yaga Hakan a fuskarta, to amma wane asarrare ne marar hankali da zai rasa wanda zaiyi hurting sai damsel irin wannan
Wani kayattacen murmushi ya su6uce mashi
Lallai, to koma waye yayi sakaci, sakacin dazai qare rayuwarshi yana cizon yatsa, har qarshen rayuwarshi, he'll make sure he did that.... ✍️
_wasa farin girki🤸🏻♀️_
Ummin fasihu 🧚🏻♀?
8/2/21, 9:39 PM - Buhainat😝: *🙍🏻♂️DEEN 🙍🏻♂?*
*056*
*KADDARAR SO ❤️*
Kuka sosai Batool keyi lokacin da zee takai aya a labarin soyayyarsu da Deen datake bata
Jawota tayi jikinta suka rungume juna suna cigaba da kukan atare.
Sun dan jima ahakan sannan sukayi breaking hug din
"Am sorry" inji batool tana kallon zee idanunta jiqe da hawaye
Girgiza kai zee tayi tace
"Don't be"
"labarinku is so touching, rabuwarku is so disheartening" inji batool
Kada kai kawai zee ta iya yi tana share hawayenta da bayan hannu
"Inaji ajikina ba laifinshi bane zee, inajin koma menene ba da son ranshi ba ya barki"
Dan murmushi zee kawai tayi tace
"nima Hakan nake tunani don na yarda da soyayyarshi agareni amma koma menene yakamata ya gayamin, who knows muna iya working together musama ma kanmu mafita, koma menene be kamata ya karya alqawurranshi da yayi min ba"
Kada kai batool tayi tace
"Kiyi hqr zee, nasan duk inda yake shima yana can yana kewarki kamar yadda kike kewarshi"
Girgiza kai zee tasake yi
"I don’t miss him, I miss who I thought he is"
"kibar fadin haka zee, insha allah watarana qaddarar data rabaku zata qara hadaku and at that time zai fayyacemiki komai"
"babu qaddarar dazata sake hadamu batool, mun riga mun gama da juna a duniyar nan, shi yana Nigeria ni ina nan, bazan koma Nigeria ba kamar yadda shima bazai ta6a zuwa nanba, tell me, tayaya qaddarar zata hadamu"
"zee kenan, qaddara ta wuce tunaninki musanmman qaddarar so, you dont know what allah have in stock for you dahar ya rabaku, wataqila ba alhairi bane agareki ko kuma akwai wata manufa akan Hakan"
Daga kafadu kawai zee tayi tace
"mubar maganar haka, atleast na danji sauqin zuciyata danayi sharing damuwata, nagode"
Murmushi batool tayi
"never mind, amma idan bazaki damu ba zan dan nemi alfarma awajenki"
Komawa Zee tayi ta jingina da frame din gadon tace
"Inaji"
"please idan kinada picture din gayen ki gwada min inason ganinshi"
Shiru zee tayi
"please.." inji batool pleadingly
Dan murmushi tayi sannan ta nuna mata wayarta dake kan mirror
Da sauri batool ta tashi ta dauko wayar ta miqa mata
Girgiza mata kai tayi tayimata nuni da ta bude
Swiping wayar kawai tayi ta bude don dama ita bata sakawa waya security
"ki shiga gallery"
Yin yadda tace tayi
"shiga folder mai suna DEEN"
dubawa tayi saita ga folder saita danna ya bude
Hotuna tagani masu yawa duk sun bubbude
Na farkon ta danna nan take smiling face din Deen ya mammaye screen din wayar
Dan Wara idanu batool tayi tana gasping
"woooow!" tafada ahankali tana qarema fuskarshi kallo
Itadai zee mayar da idanunta tayi ta rufe kawai tana sauraronta
Wuce hoton na farko tayi na biyun ya bayyana nanma Saida tayi gasping
Haka taita bin hotunan daya bayan daya wanda duk hotunan fuskarnan dauke take da wannan murmushin nashi mai tafiya da zuciyar mutane kuma ga dukkan Alamu ma babu hoton da aka dauka da saninshi, wani Wurin yana magana ne, wani Wurin idanunshi nakan littafin dake hannunshi, babu wanda yafi burgeta sai wanda akayi mashi yana dauke da sultan suna Dariya.
Saida tagama going through duka sannan ta dago ta kalli zee da haryanzu idanunta ke a lumshe
"wow sis, Gaskiya guy dinnan ya hadu, dole rashinshi yasa ki shiga hali" inji batool cikin santi
Bude idanunta zee tayi ta gallamata wata muguwar harara sannan ta maida idanunta ta rufe
Dariya batool tayi tace
"Allah kau karki ji wasa sis, wannan na sameshi ai tusashi gaba zanyi ina kallo inajin dadi, ko laifi yayi min dana kalli fuskarshi zan huce, wayyo allah amma ya hadu dama ana samun ire iren hot guys dinnan a Nigeria?"
Banza zee tayi ta kyaleta kawai
"wayyo, aikau Ahmed nafasa sonka, Nigeria zani! Wayyo hot Nigerian guys inanan tafe"
Dan murmushi ya su6uce ma zee, sosai shirmen batool ke bata Dariya, haka taita sauraronta tayita zuba ita kadai ko gajiya batayi.
*AYMAAN*
Aymaan kau da maganar zee ya yini ya kwana ya kuma tashi
Sosai abin ya tsaya mashi arai.
Ga wani gizo da fuskarta keyi mashi duk lokacin daya motsa.
Tunawa yayi jiya a wajen dinner
Kasa concentrating yayi akan abincinshi banda satar kallonta every now and then babu abinda yakeyi
Itakau batama san yana yi ba don bayan Gaisawar dasukayi sama sama ko gefen shi bata qara kallo.
Koda ya dawo sallar asuba shirin fita asibiti ya hau yi don yau aikin safe garesu.
Qarfe 8:00am yafito daga dakinshi cikin shigarshi ta qanannun kaya, baqin dogon wando da farar shirt yaci zanzaro ga lapcoat dinshi dake sagale da hannunshi sai briefcase riqe da dayan hannun.
Yayi kyau sosai a shigar ga wani irin cool qamshi dake tashi a jikinshi
Fara saukowa yayi daga stairs din Waya kare a kunnenshi yana amsa kira har ya ida sauka.
Dago idanunshi yayi sai suka sauka akan zee dake jejjera flask akan dining table
Kafeta da idanu yayi yana kallon every movement dinta Yayinda can qasan zuciyarshi yake jin wani feeling da bazai tantance kona menene ba
Zee dake aikinta hankali kwance tadan dakata jin kamar ana kallonta
Ahankali ta dago sai caraff suka hada ido dashi tsaye a inda yake yana kallonta itama
Ahankali yadan sakarmata wani cool murmushi
Dauke kai tayi kawai ta cigaba da abinda takeyi
Hakan yasa ya qara fadada murmushin shi sannan ya nufo dining area din
Jan kujera dake facing dinta yayi bayan Qarasowarshi ya zauna still yana kallonta
Bata dago ba ta kalleshi haka kuma bata dakatar da abinda takeyi ba
"sabahal khair ukhtie" yafada jovially
Sai a sannan ta dan dago ta kalleshi, kamar bazata yi magana ba sai kuma ta motsa bakinta ahankali tace
"sabahan-nurr"
Dan Wara idanunshi yayi jin ta maido mashi da larabcin
"dama kinajin arabic?" ya tambaya yana kallonta
"No" tafada tareda Juyawa tabar wajen
Binta da kallo yayi harta shige kitchen din, daga girarenshi yayi sannan ya danyi murmushi ya kada kai sannan ya sa hannu yajawo abubbuwan kan table din yana bubbudewa don serving kanshi.
Yana cikin cin abincin ne suka sake fitowa daga kitchen din da zee da batool
Dagowa yayi daga shayin dayake sipping yana kallonsu har suka qaraso
"sabahal khair Akhie" inji batool cikin fara'a
"sabahan-nurr" yafada yana dan satar kallon zee dake dora tray din hannunta kan table din
"yau kuma tunda safe zaka fita?" inji batool tana taya zee jejjera abubbuwan dasuka kawo
"ga zahiri?" yafada a taqaice yana sipping shayinshi ahankali yana satar kallon zee ta saman kofin
"da ace yau lecture din safe gareni da kayi dropping dina"
Dagowa yayi ya gallamata harara yace
"ke da wa?"
Dariya tayi
"Don't even try that, rannan ma dakikaga na kaiki don ummy tayi magana ne shiyasa amma wlh kika qara yimin Hakan zan daukeki ne naje na watsar gefen titi babu ruwana"
Dariya batool tasakeyi tace
"babu komai saina tashi na nemi cab ya qarasa dani school din, what matters shine kadai tuqani"
Dagowa yayi ya gallamata harara Hakan yasa ta koma bayan zee datayi kamar batasan sunayi ba tana Dariya
Kwafa yayi sannan ya turama zee plate dinshi
"zubamin wannan kadan ukhtie"
Kallon plate din tayi saikuma ta dan jawoshi tashiga zubamashi
Saida yaga yakai daidai yadda yakeso yace
"yauwa ukhtie, shukran. Ke kuma ki koyi yadda ake girmama na gaba kamar dai ita" yafada yana nuna zee
Ta6e baki batool tayi tace
"nima ai inayi, Ganine ba'ayi"
"a ina kike yi? Kin maidani abokin wasanki, shi yaya girmama shi akeyi sosai, don babban wa uba ne, koba haka ake cewa ba ukhtie?" yafada yana maida kallonshi kan zee
"yes" tafada simply sannan tajuya ta bar dining din ta nufi stairs
Binta da kallo duk sukayi sannan suka kalli juna
Qumshe Dariya batool tayi tana rufe bakinta da tafin hannunta
Wani kallo ya watsamata yace
"bar nan"
Da sauri tabar wajen tana cigaba da qumshe dariyarta tabi bayan zee
Kwafa yayi sannan ya maida hankalinshi akan abincin gabanshi ya cigaba da ci
Bai qara 6ata lokaci ba ya tashi ya fice daga gidan.
Tunda yashigo hospital din aketa gaidashi, duk inda ya gitta sai an gaidashi shikuma yana amsawa cikin fara'a
Aymaan kenan, kyakyawan namiji mai cikar haiba da kamala, mutum ne faran faran ga yawan wasa da sakewa wanda Hakan yasa yakeda farinjinin mutane sosai
Aymaan ba fari bane haka zalika ba baqi bane, he's chocolate in complexion, chocolate dinma irin mai sheqin nan.
Dr Aymaan qwararren likitan mata ne wanda ake jidashi a daya daga cikin manyan asibitocin dubai saboda qwarewarshi da hazaqa da allah yayi mashi
Yayi suna sosai a asibitin dama sauran asibitocin qasar don sosai kingin asibitocin ke kwadayin samunshi a asibitinsu suma kuma sunsha kawo mashi tayin yadawo asibitin su akan farashi mai tsoka amma yayi turning down request dinshi politely don idan akwai abinda ya tsana to cin amana ne?
Ko patients sunfi son Dr Aymaan ya dubasu saboda qwarewarshi wajen aiki dakuma iya mu'amallantar patients dayayi, gashi qwaro ne a fannin aikinshi don wani lokacin idan wasu likitocin suka kakare to shi ake kira kuma cikin ikon allah da yazo komai zai warware. Shiyasa mafi yawancin lokuta ma bayada timetable na kanshi na aiki don ko lokacin aikinshi bane ana iya kiranshi at anytime kuma yatafi batareda gardama ba
Aymaan allah yayishi da tausayi musanmman akan mata.
Yana matuqar tausaya masu kuma beson abinda zai ta6asu don idan akwai abinda beso to kukan mace ne idan kuma akwai wanda ya tsana to mai sa mace kuka ne, duk wanda yasan Aymaan yasanshi da wannan tausayin na mata ko don shi likitansu ne kuma yasan matsalolin da suke fama dasu?
Akwai lokacin daya ta6a yiwa wata mata aiki dazata haihu don takasa haihuwar da kanta, haihuwar matar tabiyu kenan
Cikin sa'a akayi aikin lafiya aka gama lafiya don har Saida ya gwadama matar diyar daya Ciro yana Tambayarta me tasamu dayake aikin na ido biyu akayi.
Lafiya lau ta amsa mashi da mace aka samu Hakan yasa yabada diyar akaje wajen gyarata shikuma yafita yima ahalin matar albishir din yin aikin successfully.
Sosai ahalin sukaita murna suna godewa allah shikuma suna sanya mashi albarka.
Da farinciki ya dawo dakin da take Saidai me? Sai ya tarar matar nata kokowa da numfashi nurses nata qoqarin bata taimakon gaggawa.
A rude shima ya shiga iya qoqarin shi wajen ganin numfashinta ya daidaita Saidai kana naka allah na nashi don ko minti biyar bata qara ba a duniya ta rasu
Sosai mutuwar ta girgiza Aymaan a lokacin.
Sunfi Mintuna 10 ahaka dashi da nurses din dakin dasukayi cirko cirko cikin rashin sanin abin yi
Daga baya Dakyar ya iya summoning courage yafita Domin sanar da ahalin nata
Saidai ganinsu sunata daukar jaririyar anata murnar qaruwa
Sosai gwiwarshi ta sage yaji zuciyarshi ta karye
Koda sukaga Hakan sai suka fara Tambayar shi lfy?
Dakyar ya iya danne abinda yakeji yayi breaking din labarin mutuwar matar garesu
Dayake ba masu qarfin imani bane sai suka hau koke2 da iface iface har wata ma ta sha qwalarshi tana cewa qarya yakeyi ba yanzu yazo ya sanar dasu lafiyarta lau ba
Nan fa akazo aka taru mutane nata rarrashin ahalin mamaciyar suna yimusu tuni da qaddara.
Aymaan kau be cewa komai sai hawayen dayake wanda ba komai ya jawo Hakan ba sai kukan da jaririyar keta tsanyarawa.
Sosai jaririyar tabashi tausayi don bilhaqqi da Gaskiya take kukan kamar tasan abinda yafaru
Ganin Dr Aymaan na hawaye yasa duk jikin mutanen wajen yin sanyi suna kallon yadda ya dauki jinjirar yana kallo yana hawaye.
Saida ya dauki kwanaki sosai kafin abin yasakeshi kamar yadda yasaba dik lokacin da patient ya mutu a hannunshi.
Babu wanda besan wannan halin nashi na tausayi ba a fadin asibitin
Hakan yasa Koda yaji labarin zee sai yaji ta mugun bashi tausayi kuma yaji ya tsani wanda yaudareta don shi aganinshi mata hallitu ne na musanmman wanda ya kamata ayi treating dinsu specially don a gurinshi mata sune gift of life.
Aymaan yanada abokai wadanda shi kansa besan iyakarsu ba Amma acikinsu akwai babban amininshi wanda alaqarsu tawuce abota kadai ta koma kamar ta yan uwantaka.
Sunan aminin nashi AHMAD JUNAID, dan kasuwa kuma P.A a companin babanshi
Tare suka taso tun suna yara kuma tare sukayi karatu a makaranta daya sai course dinsu kawai daya banbanta
Sosai suke abota mai tsafta wanda Hakan yasa tun suna qananu suka qulla zuminci tsakanin iyayensu suma don sosai iyayen Aymaan da Ahmed ke zuminci
Zuminci yaqara karko ne lokacin da Ahmad da batool suka fara soyayya.
Babu wanda beyi farinciki ba da Hakan don ko babu komai Hakan zai qara qarfafa zumuncinsu kuma zai qara girmama abotar dake tsakanin Aymaan din dashi Ahmad din, Wannan kenan.
Sai da marece sosai sannan yabaro asibitin
Akan hanya ya tsaya yasayi kayan maqulashe da fruits sannan ya wuce gida.
Parking yayi a parking space sannan ya bude motar yafito
Kamar kullum lapcoat din na sagale a hannunshi ya riqo briefcase dinshi da dayan hannun
Rufe kofar yayi sannan ya zagaya ta dayan bangaren ya bude back seat ya Fiddo ledar tsarabar daya siyo yasake maida kofar ya rufe ya kulle motar gabadaya da key din hannunshi sannan ya juya ya nufi cikin gida
Da sallama yashiga falon, babu kowa aciki Hakan yasashi nufar stairs kawai yanufi sama
Yana qarasa hawa saman itakuma ta fito daga dakin
Turus tayi ganinshi haka unexpected
Murmushi yayi mata,
All Chapters
Chapter 1
Chapter 2
Chapter 3
Chapter 4
Chapter 5
Chapter 6
Chapter 7
Chapter 8
Chapter 9
Chapter 10
Chapter 11
Chapter 12
Chapter 13
Chapter 14
Chapter 15
Chapter 16
Chapter 17
Chapter 18
Chapter 19
Chapter 20
Chapter 21
Chapter 22
Chapter 23
Chapter 24
Chapter 25
Chapter 26
Chapter 27
Chapter 28
Chapter 29
Chapter 30
Chapter 31
Chapter 32
Chapter 33
Chapter 34
Chapter 35
Chapter 36
Chapter 37
Chapter 38
Chapter 39
Chapter 40
Chapter 41
Chapter 42
Chapter 43
Chapter 44
Chapter 45
Chapter 46
Chapter 47
Chapter 48
Chapter 49
Chapter 50
Chapter 51
Chapter 52
Chapter 53
Chapter 54
Chapter 55
Chapter 56
Chapter 57
Chapter 58
Chapter 59
Chapter 60
Chapter 61
Chapter 62
Chapter 63
Chapter 64
Chapter 65
Chapter 66
Chapter 67
Chapter 68
Chapter 69
Chapter 70
Chapter 71
Chapter 72
Chapter 73
Chapter 74
Chapter 75
Chapter 76
Chapter 77
Chapter 78
Chapter 79
Chapter 80
Chapter 81
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 44 Chapter of 81