kujera itama sai mussadiq kusadashi sai Habeeb sai Ahmad daga qarshe kuma Aymaan
kowannensu kansu aqasa suna sauraron kaka da dakyar ta iya bude bakinta tafara magana....✍?
Ummin fasihu🧚🏻♀?
8/10/21, 8:09 AM - Buhainat😝: *🙍🏻♂️DEEN🙍🏻♂?*
*097*
*WAIWAYE*
"Asalin sunana Asma'u Mamman, ni marainiyace banida uwa banida uba don agidan marayu natashi na tsinci kaina a garin komasi dake qasar ghana.
Acikin gidan marayu natashi kamar sauran yan uwana marayu damuke rayuwa a cikin gidan
baza'a kira rayuwarmu da ingantacciyar rayuwa ba don gaskiya bama samun kulawa yadda ya kamata, abinci ma kanshi bama samun ingantacce saidai kame2
ga rashin ilimi daga na bokon har na arabi bama samu (gwara gwara na arabin tunda munsan wasu abubbuwan kamar yadda akeyin sallah da yan gajerun surori) ga rashin suturun kirki
gidan marayun kasancewar anyi yawa sosai aciki yasa babu kulawa sosai gashi da dan tallafin da gomnati ke badawa duk wata aka dogara saidai idan allah ya taimakemu yajefo mana taimako daga ire iren mutane masu sadaka dasuke tunawa da yara marayu irinmu
zama gidan marayunmu zama ne marar dadi don kowa burinshi allah ya rabashi da gidan ko ta hanyar adoption (daukar yara don rainonsu) kokuma aikatau
don har taya wadanda xasu bar gidan murna mukeyi munaji dama mu
Haka nataso nima kamar sauran yaran babu ilimin arabi ba na boko sai qwarewa a iya aikace aikace da rainon yara don yawanci marayun dasuka tasa suke komawa masu kula da qanannu qanannun cikinsu
haka muka tashi cikin wata irin rayuwa marar alqibla, kullum a aiki da raino muke qarewa bamu fita daga gidan ko nan da wajen gidan, duk wanda kaga ta fita to ko ansamu masu daukarta ne ko tasamu aikin aikatau kokuma tayi aure don babu laifi akwai masu zuwa neman aurenmu agidan wani lokacin kuma marayu yan uwanmu maza ke auranmu
haka natashi agidan kullum inama kaina fatan fita daga gidan watarana nima nasamu ingantacciyar rayuwa koyaya ne
rayuwa awajen gidan na matuqar bani sha'awa musanmman idan ina ganin mutanen dakan shigo gidan marayun namu don daukarmu sai inji sunbani sha'awa ina kuma qara jin kwadayin son fita daga gidan inason jin yadda wajen yake
saboda kwadayin son fita daga gidan yasa duk lokacin da akazo dauka har addu'a nake aza6eni nima, bandamu ba ko aikatau xanje inyi burina Kawai nafita daga gidan
duk lokacin da akazo akayi dauka ba'a daukeni ba kwana nakeyi kuka bama ni kadai ba harda wasu acikinmu saboda yadda zaman gidan ya ishemu, burinmu Kawai mufita aganinmu rayuwarmu awaje saitafi tacikin gidan inganci
ahaka harna girma naxama budurwa, ina shekara 20 wani mutum yazo neman aure na agidan
da gudun tsiya na amince dashi batareda duba yanayin shekarunshi ba don babbane sosai don a haife ya haifeni gashi yanada mata biyu da 'ya'ya kusan goma sha
ban damu da duk wannan ba alokacin na amince nan da nan aka daura aurenmu bayan anyi dan bincike dasukeyi na sanin mazaunin mutum da sana'arshi inda aka gano sana'arshi qera tukane na qasa da tulu dadai sauran kayan qerawa na qasa
bayan daurin aurenmu aka damqani ahannun mijina daga ni sai yan kayana sai dan ihsani da manyan gidan suka hadamin wanda betaka kara ya karya ba nabi mijina bakina har kunne don tsabar murna muka bar gidan da tun haihuwata banta6a fitowa ba
abin hawa muka hau dani da mijina har gidanshi wanda yakasance na qasa ne duk ya tsufa ya zaizaye
gidan zagaye yake da yar gajeriyar katanga ta qasa inda idan kashiga ciki saika fara cinkaro da wani washeshen fili mai girma sosai inda daga nesa xaga hangi yan qanannu qanannun dakunnan dake gidan
dakuna hudu ne gidan masu yan qanannun taga (window) daga can sama
daki nafarko na maigidan ne sai biyu na kowanne matarshi daya kuma na yara inda na qarshen wanda da alamu saida akayimashi kwaskwarima saboda qamshin sabon shafen qasan dayakeyi nawane ni amarya
babu kitchen gidan don a tsakar filin gidan suke girki sai makewayi dake daga can qarshen gidan.
ahaka nashiga gidan ina kalle kalle inda yarane sosai tsakar gidan duk yan kuya kuya kusan duk kai daya kowa na,binmu da na mujiya, daga tagar dakunnan matan gidan kuma ina iya hango kawunnan mutane ana leqomu
ahaka muka shiga dakina wanda yasha gyara ga tabarmi anbaza takoina sai dan tulu dake daga can kusurwar dakin
ataqaice nan yazama dakina kuma ranar nazama cikkakiyar mace ta hanyar raya sunnar aure da mukayi da mijina
da farko farkon zamana gidan komai na tafiya min lafiya lau don sosai.mijina kesona don yamafi fifitani akan kingin matan
baya yarda inyi wahala don ko girkin gidan da sai andora qatuwar tukunya baya bari nayi kullum abinci na shi ke kawomin wanda duk yawanci kayan dadi ne
hakan yaqara sani jindadin auren don ina samun kulawa sosai fiyeda wanda nake samu agidan marayunmu hakan yasa kan kace me nayi 6ul 6ul naqara kyau
haka naita rayuwa mai dadi agidan mijina inda nalura kamar mijina bayason kingin matanshi saboda yadda baya shiga harkansu don becika shiga dakunnansu ba kuma maganar arziqi bata hadasu kullum sai fada ga yaranshi suma banga yana wani kula dasuba don suma rayuwarsu suke kara zube
ina mammakin abubbuwan dake faruwa agidan dakuma yadda yake watsar da sauran iyalenshi saidai ganin ni bayamin haka yasa Kawai nashare na cigaba da more rayuwata
acikin wata na hudu dayin aurenmu nasamu ciki
inda sai anan nagane waye ainahin mijina
tun lokacin dayaji batun cikina ya chanzamin kwata2 inda yafara tsiromin da wulaqanci iri iri inda tun bangane dalilin hakan ba harna gane ashe haihuwace bayaso
lokacin nasha wahala sosai saboda cikin yazomin irin mai shegen laulayinnan ne gashi mijina yajuyamin baya abinci kanshi yabar bani sai alokacin nagane ashe matan gidan suke ciyar da kansu ma
gashi matan gidan dama duk haushina sukeji saboda yadda mijinmu ke nuna kulawa agareni abaya hakan yasa alokacin babu mai tausayamin saima allah qara dasuke yimin da qannanun habaice habaice
ahaka naita kashe yan kudadden hannuna a lokacin inasamu inci abinci don ko shekara zanyi banci abinci ba babu wanda zai damu da hakan agidan
haka naita wahala ga laulayi ga rashin kula har na qulla wata biyu sai alokacin na yanke shawarar fara sana'a ganin idan nazauna hakanan yunwa zata kasheni ne abanza gashi duk na cinye yan kudaddena
ahaka nafara aikin wankau dukda yadda banida lafiya haka nake daurewa nayi wanki don samun abinda zansaka aciki
ahaka har cikina yayi wata biyar inda lokacin muka wayi gari mukaga ana tada daki daya a gidan
cikin qanqanin lokaci aka gama ginin yaji shafen qasa kamar nawa inda sai anan nakejin labarin ashe aure zaiyi
naji baqinciki sosai a lokacin don sai a lokacin nakejin ashe mutum ne shi daya saba da aure2
cikin sati biyu aka daura aurenshi dawata ta tare inda itama yakoma yimata duk abubbuwa na kyautata dayake yimin abaya
ahaka naita rainon cikina nikadai yau fari gobe baqi inda har lokacin babu wani jituwa atsakaninmu da matan gidan don kowaharkar gabanta takeyi, kowa kanshi yasani da 'yayanshi
ahaka naita rainon cikina da tun kafin na haifeshi allah ya dasamin qaunarshi sosai a zuciyata don koyaya nake cikin baqinciki na dan cikina ya motsa sainaji sauqi sauqi, kullum burina na haifeshi lafiya nima inga wanda zan kira nawa
cikina na shiga wata takwas mijinmu ya6ata da amaryarshi kasancewar itama ta dauki ciki
wulaqanci yafara mata itama kala kala hardamu ma yana cewa bamu iya komai ba sai haihuwa
ahaka ya watsar daita itama tafara dandana abinda muke dandanawa
ana hakan watarana yashigo dakina daya rabu dazuwa don har saida nayi mammakin ganinshi don rabonda yashigo dakina tun ina amarya
ashe shigowar ma bata alhairi bace don yana shigowa babu cass bare ass ya sakeni saki irinna jahilci wato uku gabadaya yakuma ce na tattara nafitarmashi agida aure zai qara
sosai naji ciwon abin sosai don abin nashi babu ko tausayawa, ga tsohon ciki ga saki sakin ma na wulaqanci
ahaka nabaro gidan bayan kwana biyu saboda budemin wutar dayayi na nabarmashi gidanshi
sanin babu inda zani don babu wanda nasani yasa ban zarce koina ba sai gidan marayunmu
koda naje nafadama manyan wajen yadda komai yafaru sai Kawai suka bani hqr don dama sunsaba irin wannan case din don yawanci ana sako wadanda sukai aure sukuma dawo gidan marayun su cigaba da rayuwa
haka nakoma cikin gidan da rayuwa har lokacin da allah ya saukeni na haihu lafiya inda na haifi d'a namiji saidai ko kwana beyiba yakoma
sosai naji rashin d'ana don na kwallafa rai akanshi sosai kuma inasonshi sosai tunma kafin na haifeshi
hakan yasa har ciwo saida na kwanta kafin daga baya na hqr na cigaba da rayuwata dukda har lokacin d'ana na maqale a zuciyata
haka na cigaba da rayuwa a gidan har tsawon shekaru takwas inda ana tara nasamu wata tazo daukar yan aikatau aka hada dani
matar munsanta sosai don tana yawan zuwa dibar yara agidan inda take rarrabawa aikatau kamar dai wata dillaliyace ta masu kudi mai kaimasu yan aiki
kasancewar angaji dani a gidan yasa aka hada dani dukda na girma don lokacin shekaruna talatin aka samu akatafi dani don dama yawanci abinda yasa suke badamu aikatau don susamu sauqin yawanmu ne don bawani iya riqemu sukeyi ba
nima dai naji dadin daukata da akayi agidan don nima nagaji da zaman gidan
ahaka aka tafi damu inda aka rarrabamu wa masu kudi inda ni dawasu guda biyar ne za'a tura saudiya aikatau don matar har qasashe take tutturawa mutane yan aiki
sosai naji dadi jin zanbar qasar gabadaya naje qasar da kullum nake burin ganinta koda a mafarki ne hakan yasa naita doqin tafiyar don har hangoni nakeyi acan ina shiga da fita da cud'anya cikin larabawa
cikin qanqanin lokaci akayimana shirye shiryen tafiyar inda mukabi jirgin ruwa (6arauniyar hanya) har muka samu muka shiga qasar
tunda nake ban ta6a ganin haddaden waje mai kyawun gaske irin na qasar. haka aka tafi damu munata zuba qauyanci har muka isa masaukinmu
anan muka kwana Washegari kuma aka rarrabamu a gidajen dazamuyi aiki
ni gidan wani attajiri aka kaini don kai koda ganin gidan kasan gidan masu dashi ne saboda haduwa, anan aka hadamu nida wadansu da suma aka kawo aikatau da matar gidan mai tsananin wulaqanci
kwata2 mutan gidan basa qaunar baqar fata don afili suke nuna qyamarmu ahaka aka rarrabawa kowa aikinshi dakuma fadamana kudin albashinmu
rayuwa agidan amatsayin yar aiki rayuwace ta wahala da qasqanci don kwata2 basa qaunarmu kamar ma ba kallon mutane suke mana ba don kuskure kadan idan kayi saika yabawa aya zaqinta
ahaka muke wannan qasqanttaciyar rayuwar wanda saida na gwammaci zamana a qasarmu akanta don abin nasu ba iya kyama da hantara ya tsaya ba, abin haryakai harda cin mutuncinmu na 'ya mace inda mazajensu keyimana kallon dabbobin dazasu iya zuwa sujuye qazanttaciyar buqatarsu akai suyi tafiyarsu
hakan dana gani yasa hankalina tashi ainun don abin abin tashin hankaline inda nan take nafara danasanin zuwana qasar
haka naita lalla6awa kullum cikin roqon allah ya kareni daga sharrin mutanen don naga yadda sukeyima kingin yan uwana masu aiki inda suke maidasu kamar karuwansu idan kuma baki yarda ba a laqamaki wani sharrin da za'ayi miki hukuncin dazakiji inama tunfarko kin yarda da buqatunsu (hakan nafaruwa a real wlh, mutane yan Africa masu zuwa wasu qasashen don aikatau dadai sauransu ba qaramin tashin hankali suke fuskanta ba acan saboda tsananin qabilanci da ake nunawa acan inda yawanci ake maidasu sex machine don yawanci sunfison Africans don acewarsu sunfi satisfying dinsu, allah ya kyauta)
ahaka nayi wata uku agidan ina kaff kaff dakaina ina addu'ar allah ya ku6utar dani saidai ba'a dauki lokaci ba wani d'an gidan yafara kawomun hari
sosai hankalina yatashi da ganin hakan, hakan yasa naita kakaucemashi ina addu'ar allah ya ku6utar dani daga sharrinshi
alokacin sosai zaman qasar ya gundureni don da nasan yadda za'ayi nagudu danayi gashi wacce takawomu tun ranar data kawomu bansake sata a idoba
ahaka har watarana saurayin yaso raping dina
lokacin babu kowa gidan don saida yayi yan dabarunshi na yadda zaisameni yaci karenshi babu babbaka
ranar naga tashin hankali don da tsiya yaso afkamin saidai allah yabani ikon makeshi da vase din tangarau mai nauyi akai inda nan take ya silale yasume jini nabin kanshi
ganin hakan yasa na rude don nasan shikenan tawa,ta qare don muddin akadawo aka taddamu haka shikenan nagama shaqar numfashi
hakan yasani fitowa agigice don ni duk tunanina mutuwa yayi, cikin sa'a kau ban tadda mai gadi a gate ba hakan yasa na afka waje nafara gudu irin gudun fanfalaki burina Kawai intsira da rayuwata
haka naita gudu shiga nan fita can batareda nasan inda na nufaba, kuka kau tun inayi harna kasa saboda muryata databar fita ahaka dare yayimin nasamu qarqashin wata gada na ra6a saboda yan kame dake kame da daddare na raku6e ina kyarmar sanyi ina addu'ar allah ya kawomin dauki
ahaka har dare yayi sosai koina yadauki shiru, motoci nawucewa jefi jefi asaman gadar dana 6uya
ahaka tun ban iya barci saboda sanyi da cizon sauro har wani barci marar dadi ya figeni
can cikin barci naji motsi sama2
abinka da dama atsorace nake sainayi firgigit na tashi ina zare idanu
ganin yadda hasken fitilu keta walainiya awajen yasani qara la6ewa ajikin bangon gadar ina toshe bakina don duk tunanina mutanen gidan danake aiki suka biyoni suna nemana kokuma yan kame
daga saman gadar suke haskowa da fitilarsu mai mugun haske kamar masu neman wani abu
nidai qamewa nayi wuri guda inata hawaye ina kyarma
bayan kusan minti daya da haske hasken naji qarar abu tsindum sunjefo cikin ruwan gadar dake gudana yana tafiya
atsorace nasake maqalewa ajikin bangon gadar ina qara toshe baki don atunanina su suka duro ciki
can sainaga nabar ganin hasken can kuma naji tashin mota tasaman gadar aka tafi
dukda antafi hakan besa na iya komawa barcin ba haka naita zaxzare ido cikin duhu ina kyarma saboda sanyin da akeyi gashi ina qarqashin gada
ahaka har haske hasken alfijir yafara ketowa inda anan na yanke shawarar barin wajen don nagaji da cizon da,sauro keyimin hakan yasa na lalla6a ina qoqarin fita daga gadar
kamar ance in kalli gabana saina hangi wani box mai dan girma daga nesa da inda nake
kasancewar akwai tazara,da inda nake yasa nakasa hango ko menene sosai
harzan wuce saina tuna da mutanen dasuka zo jiya suka jefo abu acikin gadar hakan yasa naji inason ganin koma menene
ahankali nake bin gefe gefen gadar ina tattaka dutsinan ciki gudun karna afka cikin ruwan
ahaka harna iso wurin kwalin daya jiqe jagab shima don dutsi ya tokareshi ne da,tuni yabi ruwa
tsayawa nayi ina kallon kwalin cikin dan hasken safiya daya farayi ina saqe saqe
zuciyata nabani qila sharace aciki suka jefar saidai kuma dukda hakan sainaji inason budewa inga me keciki
ahankali nasa hannuna dake kyarma kyarmar sanyin danake ji nabude kwalin inda ganin abinda yake ciki yasa numfashina daukewa cakk na wucin gadi
wani farin yaro nagani aciki hannayenshi da qafaffunshi a quqqule da igiyoyi bakinshi toshe da tsumma an daureshi tamau idanunshi alumshe babu alamun numfashi ko kadan attatare dashi....✍?
*manage banida charge, qila gobe inyi*
Ummin fasihu🧚🏻♀?
8/11/21, 2:03 AM - Buhainat😝: *🙍🏻♂️DEEN🙍🏻♂?*
*cigaban 097*
ja baya nayi amugun tsorace don ban ta6a tsanmmanin abinda zan gani kenan
nan take jikina yahau rawa nafara yin baya baya hannu toshe da baki
atsorace najuya nabar wajen dagudu ina bi ta duwatsun cikin ruwan harna samu na koma hanyar danabi nashigo qarqashin gadar nasamu nafita
daga saman gadar na tsaya ina kallon kwalin danake hange daga nesa har lokacin zuciyata banda bugawa babu abinda takeyi
sonike intafi amma kuma nakasa sai kallon kwalin nake batareda na iya motsawa daga inda nakeba
kamar wanda aka jawo saina tsinci kaina da komawa cikin gadar kuma ina tafiya ahankali nasake nufar kwalin
jiki na rawa nasake leqawa naga abinda nagani daxu
yaro ne da bazai wuce shekaru uku ba, farine dukda ba irin tass dinnan ba na larabawa don nashi irin farin nanne mai jajaja, gashin kanshi ajiqe kamar yadda sauran jikinshi yake ya kwanto yarufe rabin fuskarshi
nafi minti biyu atsaye ina kallonshi zuciyata na bugawa kafin cikin qarfin hali dasa hannu nadan ta6ashi
ko motsawa beyiba hakan yasa naqara ta6ashi duk atsorace
ganin be motsa ba yasa cikin qarfin halin na hau kekketa kwalin har ya ida fitowa fili sannan najuyoshi nasa hannu ina qunce mugun daurin da akayima bakinshi
saida nasha wahala sannan na kwance na zazzaro tsummunan da aka cuccusamashi cikin baki ina kuka sosai don an daure mashi bakinne cikeda mugunta ga bakin da kumatunshi sunyi jajur alamun kwanciyar jini
bayan nagama kunce bakin nakoma kan hannayenshi da qafaffunshi dake daddaure nahau quncewa, suma saida nashi wahala sosai kafin na samu kuncewa
saikuma narasa abinda zanyi mashi daganan gashi gari yawaye don haske yayi sosai
ganin hakan yasa nafara qoqarin daukarshi saidai yayimin nauyi sosai hakan yasa nadan kwantar dashi kan dutsin wajen nahau daddana mashi cikinshi daya dan yo sama
akau saigashi ruwa sunshiga fitowa ta hanci ta baki, haka naita dannawa har suka daina fitowa saidai har lokacin ko motsawa beyiba hakan yasa na cije na cicci6eshi dukda lokacin yadan rage nauyi nasamu dakyar nadorashi abaya na don har inayi ina faduwa sannan nashiga takowa ahankali don barin cikin gadar dashi
koda nafito rasa inda nanufa nayi gashi har lokacin ina tsoron kar ace yan gidan danake aiki nacan na nemana gashi nasan shima wannan yaron wadanda suka jefashi a gada sunyi hakan ne don son ganin bayanshi hakan na nufin daga ni har shi muna cikin hadari
hakan yasa maimakon nayi titi nashiga cikin mutane saina yanki daji kawai batareda nasan inda muka nufaba burina Kawai na tseratar da rayuwarmu dukda har lokacin banida tabbacin ba gawace goye abaya na ba
ahaka harna samu nayi nisa sosai harsaida naji ban iya tafiya sannan na haqura muka zube awajen ina sauke numfarfashi
dagowa nayi ina kallon yaron wanda farat daya yashiga zuciyata ina jinshi fiyeda nakejin d'ana dana haifa yakoma
bansan ko yana rayeba ko ya mutu don kwata2 baya motsi kuma natara yatsuna a hancinshi nidai banji yana numfashi ba
kunnena nasa a saitin zuciyarshi ina sauraro ko zanji bugun zuciyarshi saidai shima shiru saida na dade ina sauraro sannan naji bugun zuciyar can qasa qasa
sosai nayi murnar hakan don dafarko harna fara sadaqarwa dacewar yamutu
tashi nayi ina kallonshi batareda nasan wani taimakon dazanyi mashi ba, nasan asibiti yakamata na nema na kaishi amma zuciyata taqi bani hadin kai don gani nake kaishi asibitin daidai yake da jefashi cikin hadarin daya fito don qilan hakan yazamo silar dazaisa mutanen dasuka so ganin bayanshi dafarko susake dawowa
haka mukaita zama awurin cikin rashin sanin abinyi ga yunwa ga sanyi don daga ni har shi kayanmu ajiqe suke
haka mukaita zama har rana tafara fitowa inda anan nasamu nacire mashi jiqaqiyar rigarshi ko yadanji sauqin sanyin
haka natusashi gaba nabuga uban tagumi ina kallonshi batareda nasan abinda zanyi ba ahaka har rana ta take sosai
ganin hakan yasa nasake miqewa na daukeshi nasake goyashi nacigaba da tafiya acikin dajin
ranar naci baqar wahala don haka nawuni ina tafiya babu ci gwara gwara ruwa idan nahadu da matattarar ruwa ina dan kwalfa in jiqa maqoshina ahaka harna qarasa wani qauye qauye
anan qarfina yaqare bansan ya akayi ba kawai sainaji lumm idanuna na rufewa dakansu kaina na juyamin nazube awajen dani da d'an dake bayana
bansan iya adadin lokacin dana dauka ba asume saidai Kawai nafarka naganni cikin wani daki mai dan duhu duhu
firgigit nayi na miqe zaune ina waige waige anan nagane kamar ma cikin bukka nike
agarin waige waigena na hangi wannan yaron shima kwance daga dayan gefen dakin
bansan sadda naqarasa wurin ba da rarrafe nayi saurin tattaroshi ajikina na rungume
ga mammaki na sainaji yayi motsi yana yatsuna fuska saboda motsashi danayi saikuma yafara tari ahankali cikin wata iriyar dakussashiyar murya dabata fita sosai
farinciki ne ya lullu6eni ganin ya motsa hakan yasani sake rungumeshi ina jin wani irin sonshi har qasan zuciyata sai kallon kyakyawar fuskarshi nakeyi babu ko kyaftawa kamar nasamu madubi
ahaka wasu mutane suka shigo bukkar
jin motsinsu yasani dawowa daga duniyar kallon yaron naja dabaya atsorace ina binsu da kallo kamar yadda suma sukemin
suma larabawa ne saidai dagani yan qauye ne duba da yanayinsu
mace ce da namiji duk sun manyanta sun tsaya daga bakin kofa sun zubamana idanu
nima dai kallonsu nake amma atsorace sai qara rungume yaron jikina nakeyi qamm a qirjina yadda kasan za'a kwaceminshi
kallon juna naga sunyi sunyi murmushi sannan suka qaraso ciki suna kallon yadda nake qara jabaya ina mannewa da jikin bukkar
ganin yadda na tsorata yasa suka bar nufomu inda anan matar cikin murmushi don kwantar min da hankali tafara cemin na kwantar da hankalina babu abinda zasuyimin cikin larabci
dukda banajin larabcin sosai amma nagane abinda take nufi saboda gwadawar datakeyi da hannu hakan yasa hankalina dan kwantawa
miqomin hannu tayi akan nabata d'an nikuma saina qara matseshi jikina ina jada baya alamun ban badawa, murmushi sukayi sai mutumin cikin harshen larabci yake tambayata d'ana ne?
dan zaman danayi agidan danake aiki yasani dan sanin wasu guntayen larabci hakan yasa nagane abinda yace min hakan yasa na kada kaina cikin sauri
murmushi suka sakeyi nan suka hau nunamin baxasu cutar damuba taimaka mana zasuyi
dakyar dai suka samu suka lalla6ani na yarda dasu nabasu shi suka mayar dashi shinfidarshi suka kwantar dashi inda anan naga sun cigaba dayimashi wani hayaqi wanda yaita sashi tari da shaqaqiyar muryarshi
nidai ina gefe ina kallonsu harsuka gama yimashi duk maganin dasuke mashi suka kyaleshi yanata barcinshi
abinci suka bani wanda kamar jira nake na amsa hannu narawa nashiga ci saboda tsananin yunwar da dama nakeji
saida naci na qoshi sannan nadawo nutsuwata inda anan sukaso sanin wacece ni mekuma yakawomu qauyensu
dayake duk bajin yaren juna muke ba yasa maganar kurame (demonstration) duk tafi yawa a maganarmu inda anan nake kwantantamasu cewa gudowa mukayi za'a kamamu mu ba yan qasar bane nakuma nuna masu sonike mubar qasar
shiru sukayi suna kallona hakan yasa gabana cigaba da faduwa don duk a tunanina sungano yaron ba nawa bane don shi farine nikuma gaskiya baqa ce dukda ba irin qirin dinnan ba amma dai kwata2 bamuyi kama da yaron ba kuma gashi shi sak balarabe dukda jikinshi ba irin farinnan tass ba yake kamar na jikin kajin turawa amma farine irin mai jajaja wanda anasamun daidaikun masu irin fatar a Africa
tambayata sukayi wacce qasa nake nace Ghana a Africa
sai suka sake tambayata ina uban yaron
cikin qwarin gwiwa nabasu amsar yamutu nima nan aikatau yakawoni saboda tsananin rayuwa saina tsinci kaina da gayamasu duk abinda yafaru a tsohon gidan danake aiki da silar gudowata, abu daya ne ban gayamasu ba shine yaron tsintarshi nayi
sundade suna jujjuya maganata kamar dai basu yarda dani ba don saidai su kalli yaron su kalleni
can sukace karna damu zasu taimaka min nakoma qasarmu can Africa amma sai yaron ya farfado tukunna yasamu lafiya
ba haka nasoba amma babu yadda na iya haka na haqura ina addu'ar allah yarufamin asiri mubar qasar lafiya
saida muka kwana uku agidan kafin yaron ya farka
kuma abin mammaki yana farkawa yafara waige waige yana kiran ummie cikin muryar dabata fita munayin ido hudu dashi ya rarrafo wajena dasauri ya maqalqaleni
sosai na sauke ajiyar zuciya ganin yadda yaron yayi don da yaqi yarda dani da qila mutanen sun zargeni
duk yadda mutanen sukaso ta6ashi qiyawa yayi ya lafe ajikina yayi lamo kamar dagaske ni mamarshi ce
ahaka muka qara kwanaki biyu inda na matsa ni sonike nakoma qasarmu don har lokacin hankalina be kwanta da zamanmu qasar ba
izuwa lokacin sungama gamsuwa cewa d'ana ne saboda yadda yake liqemin kodayaushe yana maqale dani
duk yadda sukaso muqara zama ko don jikinshi dabe ida warwarewa ba qiyawa nayi nace idan naje can zankaishi ayimashi magani
ahaka suka haqura ranarda muka cika sati daya awurinsu namijin ya rakamu mukayi tafiya sosai bisa raqumma har mukazo wani qauye shima
anan ya hadamu dawani wanda aikinsu fitarda mutanen qasar ta 6arauniyar hanya
anan yabarmu bayan yadan bamu dan guzurin tafiya nikau naita godiya kamar zan ari baki
anan aka hadamu da wasu mutanen dasuma qasar za'a fita dasu rabi da kwatansu duk yan Africa ne inda aka lodamu awani qaton jirgin ruwa cikin dare muka daga
daren ranar ko rintsawa banyiba ina qanqame da KAMALDEEN kamar yadda nasamashi suna
hankalina be kwanta ba saida naga mun qetare iyakar saudiya sai lokacin naji sanyi sanyi araina
alokacin nakuma lura duk yawanci mutanen cikin jirgin yan Nigeria ne sannaniyar qasarnan datayi suna duk fadin Africa dama duniya bakidaya hakan yasa nima jin hankalina karkata acan
ataqaice dai saida mukayi kwana uku muna tafiya sannan muka iso Nigeria aka jibgemu garin lagos
lokacin jikin Kamal yaqara rikicewa saboda yanayin tafiyar tamu ga sanyin daya bibbigemu hakan yasa muna sauka na dangana da asibiti wanda dakyar dagano ta hanyar kwatance
ganin mawuyacin halin dayake ciki yasa aka kar6eshi cikin gaggawa inda anan likitoci suka shiga bashi taimakon nikau nakasa zaune nakasa tsaye saboda yadda
All Chapters
Chapter 1
Chapter 2
Chapter 3
Chapter 4
Chapter 5
Chapter 6
Chapter 7
Chapter 8
Chapter 9
Chapter 10
Chapter 11
Chapter 12
Chapter 13
Chapter 14
Chapter 15
Chapter 16
Chapter 17
Chapter 18
Chapter 19
Chapter 20
Chapter 21
Chapter 22
Chapter 23
Chapter 24
Chapter 25
Chapter 26
Chapter 27
Chapter 28
Chapter 29
Chapter 30
Chapter 31
Chapter 32
Chapter 33
Chapter 34
Chapter 35
Chapter 36
Chapter 37
Chapter 38
Chapter 39
Chapter 40
Chapter 41
Chapter 42
Chapter 43
Chapter 44
Chapter 45
Chapter 46
Chapter 47
Chapter 48
Chapter 49
Chapter 50
Chapter 51
Chapter 52
Chapter 53
Chapter 54
Chapter 55
Chapter 56
Chapter 57
Chapter 58
Chapter 59
Chapter 60
Chapter 61
Chapter 62
Chapter 63
Chapter 64
Chapter 65
Chapter 66
Chapter 67
Chapter 68
Chapter 69
Chapter 70
Chapter 71
Chapter 72
Chapter 73
Chapter 74
Chapter 75
Chapter 76
Chapter 77
Chapter 78
Chapter 79
Chapter 80
Chapter 81
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 78 Chapter of 81