Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
kuma inada Mama?" fadawa jikinshi tayi cikin kasa jurewa tafashe da kuka mai ta6a zuciya "eh yaya.. kanada Mama..mai sonka, tana sonka sosai yaya..muma muna sonka yaya.. bamu ta6a mantaka ba daidai da second daya ba tun tafiyarka, meyasa katafi kabarmu?.. meyasa kabarmu da kewarka yaya? karka qara tafiya yaya.. karka qara barinmu.. muna sonka yaya" kuka take sosai koina na ilahirin jikinta banda rawa babu Abinda takeyi, ta qanqameshi sai sheshekar kuka takeyi ahankali Deen yasa hannu ya zagayo bayanta ya rungumeta shima batareda ya iya cewa komai ba sai sauraron bugun zuciyoyinsu abin haryanzu bebar yimashi kama da mafarki ba, wai shikeda family, shikeda qanwa, shikeda mahaifiya lumshe idanu yayi yana sauraron sautin kukan Aysha yana Jin yadda kukan ke ta6amashi zuciya ahankali yaqara bude baki yace "stop crying.. please" kamar cewa yayi taqara saita qara rushewa da kuka tana qara cusa fuskarta a qirjinshi Ajiyar zuciya ya sauke sannan yabude jajjayen idanunshi ahankali "am here now, I promise bazan sake tafiya ba" ya tsinci kanshi da fadin haka qara fashewa da kuka Aysha tayi tana qara qanqameshi kamar zata shige jikinshi shima qara rungumeta yayi zuciyarshi na melting babu wanda zuciyarshi bata motsa ba don masu saurin kuka irinsu batool harsun bude shafi kamar ance yadago sai suka hada idanu da Mussadiq dake tsaye bakin kofa yana kallonsu kafe juna da kallo sukayi kamar sunsamu t.v shima Mussadiq idanunshi sunyi jajur sun dan kumbura harda lips dinshi yanzu babu coat ajikinshi sai t-shirt din ciki kamar dai Deen ahankali Deen yadaga Aysha daga jikinshi idanunshi still akan Mussadiq komawa gefe Aysha tayi tana kallon yayyen nata biyu tana hawaye cigaba da kallon juna sukeyi babu mai ko kyaftawa ahankali Deen ya dago hannunshi ya miqoma Mussadiq binshi da kallo Mussadiq ya cigaba dayi batareda ya motsa ba kowa na dakin shi yake kallo yaga me zaiyi Deen be sauke hannunshi ba kuma be janye idanunshi daga kanshi ba ahankali Mussadiq yashiga takowa yana tunkaro Deen harya qaraso gabanshi kallon hannun da Deen ke miqomashi yayi yana tuna kalamansu daddy *Mujaheed be mutu ba, yana raye kuma yadawo gareku* maida kallonshi yayi akan fuskar Deen yana kallo sannan ahankali kamar wanda ake controlling da remote yadago hannunshi ya dora akan na Deen wani irin electric feeling ya tsirgamasu gabadaya ilahirin jikinsu zubewa Mussadiq yayi on his knees the next minute sai gani mutanen dakin sukayi sun qanqame juna cikin wata iriyar wawiyar runguma "Mujaheed.." Mussadiq yafada cikin wata iriyar murya kamar ba tashi ba "Mussadiq.." inji Deen shima cikin rawar murya wasu hawaye masu zafin gaske suka gangaromasu alokaci daya suna qara qanqame juna "Mujaheed..😭" "Mussadiq😭"...✍? Ummin Fasihu🧚🏻‍♀? 8/2/21, 9:44 PM - Buhainat😝: *🙍🏻‍♂️DEEN🙍🏻‍♂?* *085* *THE REUNION* sun jima ahakan rungume dajuna kamar zasu shige jikin juna, feeling dasukeji yana tasomasu daga zuciya zuwa ilahirin jikinsu is unexplainable ahankali suka raba jikinsu dana juna suka hade goshinsu waje guda kowanne na mayar da numfashi dago wet eyes dinsu sukayi atare suna kallon juna batareda sun iya cewa komai ba "I thought you're gone..forever" inji Mussadiq cikin muryar rad'a daidai wasu hawayen naqara gangarowa daga idanunshi kasa cewa komai Deen yayi sai hannu daya daga yayi cupping fuskarshi "the memory is still fresh Mujaheed.. nakasa mantawa..lokacin..,lokacin dasuka sakaka amota suka tafi, nan kadai nake iya riqewa.. nasan ya isa na manta saboda dadewa da shudewar shekaru.. amma nakasa.. nakasa kullum sai wannan scene din yazomin a mafarki.. kullum sainayi mafarkinka da yadda aka rabamu..." in between kuka Mussadiq ke wannan maganar "ashe zaka dawo? ashe zanqara ganinka?.. kasan yadda rabuwarmu tayi affecting dina? kasan yadda rayuwata ta chanza bayan tafiyarka?" shidai Deen kallon yadda yake kuka sosai yake shima hawayenshi naqin tsayawa, besan meyake magana akai ba don shi betuna komai ba amma kalamanshi ba qaramin ta6amashi zuciya suke ba bare yadda yaga yana kuka sosai kukan da kallo daya zakayimashi kasan daga qasan zuciya yake tahowa shima Mussadiq grabbing fuskar Deen yayi "ina kashiga all these years? meyasa katafi kabarmu? karka qara wannan gangancin kaji? if you do I'll kill you" yafada yana riqe fuskar Deen sosai murmushi suka saki atare suka sake rungume juna "I won't, I promise" inji Deen yana qara rungume Mussadiq Aysha dake gefe itama ta rarrafo wajensu ta rungumo bayansu atare suka dago suka kalleta da wet eyes dinsu sai suka sakarmata murmushi suka sake rungume juna su ukun suka hade kansu waje guda kowa na dakin share hawayen farinciki yake kowa murmushi a fuskarshi mai nuna farinciki dasuke ta ya wadannan bayin allahn sun dade ahakan sannan suka saki juna kowanne murmushi afuskarshi sai a lokacin suka lurada yadda mutanen dakin suka qara yawa don harda su mummy adakin da kallo duk suka bisu suna kallon yadda suke masu murmushi kowanne farincikinshi yakasa 6oyuwa suma murmushin suka maida masu atare fuskarsu na nuna how grateful they are kafin wani yayi magana acikinsu wani Dr yashigo dakin riqeda waya sallama yayi sannan yace "wannan wayar tunjiya ake kiranta, a dayan dakin muka tsinceta" duk kallon wayar sukayi "akhie, your phone" inji Aysha Jin hakan yasa Mussadiq miqa hannunshi Dr din yabashi, saida yayimashi alamun thank you da ido sannan ya maida hankalinshi akan wayar, lokacin harta tsinke wani murmushi yayi sannan yadago yakalli Deen dake kallonshi "it's ummie" yafada yana nunamashi screen din wayar gaban Deen yafadi saidai bece komai ba sai cigaba da binshi da kallo dayayi ganin yana re-dialing number handsfree yasa shiyasa kowa na dakin kejin sautin ringing din alamun tashiga bugu uku tayi aka daga cikin wata kamillaliyar murya mai sirki da yanayin damuwa akayi sallama ta dayan bangaren gaban Deen yasake yankewa lokacin da muryar tadaki kunnenshi sai kallon wayar yakeyi kamar yana hango mai maganar ta cikinta amsa sallamar Mussadiq yayi cikin wata murya mai cikeda annushuwa yana gaidata da harshen larabci bema ida gaisuwarba ta katseshi itama cikin harshen larabci da "Mussadiq ina kake? dama kabaro Australia? nayita kiran numberka tacan bana samu, yaushe kadawo? kuma kasan jiya Aysha bata dawo ba? gidan wannan qawar tata taje birthday dinta tun yamma amma haryanzu bata dawoba gashi wayarta bata shiga, ina cikin damuwa sosai Mussadiq gashi kaima naita kiranka baka dagawa" tun sadda tafara magana Mussadiq keta murmushi yana kallon yanayin fuskar Deen dayayi kasaqe yana sauraron yaren da ummie keyi, yasan larabci ne amma besan metake cewa ba don bayaji kwata2 sai dan wanda ba'a rasaba wanda suke dan tsinta a islamiyya kallon wayar Kawai yakeyi yabata dukkan hankalinshi yana sauraron muryar da akecewa ta uwarshi ce dafa kafadarshi Mussadiq yayi still yana murmushi sannan ya amsa ma ummie "ummie muna tare daita" yafada yana kallon Aysha dake sauraronsu itama "kuna tare? yaushe kadawo harkuka hade?" inji ummie adayan 6angaren a mammakince "jiya.. karki damu gamunan zamu taho yanzu and guess what" yafada yana kallon Deen "what" inji ummie "zamu tahomaki da wani Abinda bazaki ta6a mantawa ba" yafada yana kallon Deen yana murmushi "menene abin?" inji ummie "sai munzo Kawai, gamunan" daga haka saiya katse kiran dagowa yayi ya kalli Deen daya maidashi t.v tundazu murmushi yayi mashi "are you ready to see your ummie?" yafada yana mashi murmushi gaban Deen ne yaqara faduwa "I..don't know" yafada ahankali murmushi duka yan dakin sukayi "c'mon akhie, just calm down, we'll be there for you and you'll like her I assure you" inji Aysha kada kai Kawai Deen yayi saidai he's very nervous zaije ganin wata kuma wai mahaifiyarshi, shida ya girma da tunanin baida mahaifa amma yanzu wai mahaifiyarshi zaije gani, wannan tunanin nasashi Jin wani iri. tashi Mussadiq yayi yaqarasa gabansu Abbu yana murmushin da ke nuna tsantsar godiya da hallarcin dasukayi masu cikin turanci yafara magana "bansan ta ina xanfara ba amma inaso kusani ko za'a tara dukkan kalaman duniyar nan babu wadda zatayi daidai da bayyana maku irin godiyar damuke muku, allah kadai zai iya sakamaku Abinda kukayi mana" duk murmushi sukayi abbu yace "mu godewa allah son, allah shine yanufi hakan zai faru, allah shine abin godiya" dik kada kai kingin sukayi atare kuma suka furta alhamdulillah cikin tsantsar nuna godiyarsu ga allah subhanahu wata'ala "zamuje gida, inaso kubiyomu don allah" inji Mussadiq din yadda yazage yana magana cikin Kasa dakai da fara'a zai baka mammaki kamar ba wannan proud Mussadiq dinba mai ego "eh to, bazamu ce A'a ba saidai ba dukkanmu zamuje ba, as you can see anan ma bamuda yawa don su daddy sun koma gida dazu saboda wata yar matsalar data taso, so muma munason zuwa can ne amma aymaan da Ahmad suna iya binku, muma lalurace zata hana hakan" inji Abbu basuji dadin hakan ba amma basuce komai ba "Ahmad ina aymaan?" "yana office I guess" inji Ahmad "to kayimashi magana kace yabiku injini" "to shikenan Abbu" "abbu don allah batool tabimu? pleeease?" inji Aysha cikin marairaicewa kallonta Abbu yayi saikuma ya kalli batool itama ta shagwa6e fuska "alright then" inji Abbu dadi sukaji wanda hakan.ya bayyana a fuskarsu "yanzu bari mu mutafi" da addu'ar tsari suka bisu suka fice suka bar daga Deen sai Mussadiq, Aysha, batool, Ahmad da habeeb anan Ahmad yafita don nemo aymaan shikuma Mussadiq yafiddo wayarshi yayi kira a office dinshi yasameshi tareda Abbu yanayin dayaga fuskar aymaan yasa yasan maganar me Abbu kemashi "kajini ko?" "to Abbu" inji aymaan fuskarshi na bayyana rashin jindadin shi "to saikun dawo mu muntafi" inji Abbu yana yin hanyar fita da addu'ar tsari suka bishi harya fita sannan Ahmad yajuyo kan aymaan da ranshi ke a6ace "meye fa'idar binsu din?" inji aymaan afusace "su suka buqaci hakan" "su wa?" "Mussadiq" "mtcheew, idan mukaje me xamuyi musu? ni wlh banason irin wannan tunda anyi mai wuyar ba shikenan ba?" ta6e baki Ahmad yayi yace "wannan Abbu ya kamata ka fadamawa mallam, saida yatafi sannan zakaita.tada jijiyoyin wuya, wannan ai ihu bayan hari ne" wata uwar harara aymaan ya makamashi yakoma ya zauna cikeda takaici dariya Ahmad yayi yace "saika shirya don't keep us waiting" yana kaiwa nan yafice tsaki aymaan yaja cikeda takaici, sosai yaji haushin binsu dazaiyi don shi yanzu haka shirin tafiya gida yake don ganin wane hali zee take don tun jiya take ranshi daita ya kwana gashi ankawo mashi kwafsi shi bega dalilin binsu ba, is not as if basusan hanyar gida bane, kwata2 bega amfanin binsu ba. haka yaita dacin rai shikadai a office din yanajin kamar yayi bindiga acan ward dinsu Deen kuwa Deen keta kallon Mussadiq daketa waya yana bada order daban daban azahiri kallon Mussadiq yake amma a badini hankalinshi ma ba akanshi yake ba, tunaninshi yayi nisa daga duniyar dasuke ciki jiyayi anja hannunshi hakan yasashi dawowa daga duniyar tunanin daya lula yakalli mai kama mashi hannu yaga Aysha ce tana mashi wannan cool murmushin nata irin nashi shima murmushin ya maida mata yana damqe hannunta itama sukayi interlocking yatsunsu ko mintuna shabiyar basu qaraba ordern da Mussadiq yabada suka iso sabbin qannanun kaya ne kala biyu iri daya kala daya ya dauka yaba Deen daya don shima ya chanza don duk kayan jikinsu sunyi squeezing cikin dan qanqanin lokaci suka chanza suka fito sakin baki mutanen dakin sukayi lokacin dasukayi arba dasu biyun ganin yadda suka fito a ainahin identical twins din komai nasu daya baka ta6a banbancewa, Abinda ma yasa yan dakin suka iya babancesu shine sumar kansu Inda na Mussadiq yafi na Deen yawa, baya ga wannan Babu wani banbanci. cikin qanqanin lokaci suka gama shirinsu sukayi shirin tafiya bayan wani Dr ya rubuta masu sallama. atare duk suka fito Inda saida Ahmad yayi excusing kanshi don zuwa tahowa da aymaan. saida aymaan ya6atama Ahmad rai da shiririta kafin yafito suma suka nufi parking space din wata shegiyar danqareriyar mota qirar Lamborghini suka gani awajen Inda ganin habeeb agabanta yasasu sanin aciki zasu dafarko aymaan yaso qin binsu cikin motar yace zai biyo bayansu Acikin tashi amma daga baya ya haqura saboda yadda Ahmad yaita lalla6ashi duk sunyi wannan abin ne kafin su qarasa wajen motar koda suka isa exchanging pleasantries sukayi tsakanin juna babu yabo babu fallasa suka shishiga motar Inda ta kwashesu duka saboda girmanta koda wasa aymaan be kalli gefen Mussadiq ba kamar yadda shima hakan take a 6angarenshi saima dai Aysha da idanunsu ke yawan hadewa Inda da hakan yafaru kowa zaiyi saurin kawar dakai haka sukayi wannan tafiyar in silent for fifteen minutes kafin su isa unguwarsu Mussadiq. tun a farko farkon unguwar zaka fahimci kashigo unguwar manyan mutane sakamakon manya manyan gidajen dasuketa wutowa ahaka har motar ta tsaya a bakin wani tangamemen gate basuyi one minute da tsayuwa ba aka wangale musu qaton gate din motar ta danna kai ciki. tafiya sosai sukayi yadda kasan ba gidan suka shigo ba sannan motar ta tsaya. guards ne takoina suka rurrugo suka tsaya agaban motar acikinsu wani yabude musu kofar duk suka dare suna basu hanya don saukowa da daddaya suka fara saukowa daga motar har suka gama fitowa sosai mammaki ya bayyana afuskokin guards din lokacin dasukayi arba da Mussadiq da Deen sai kallonsu suke dasun kalli wannan saisu kalli wannan saidai babu damar magana "welcome home akhie" inji Aysha tana ma Deen daketa bin harabar gidan murmushi Jin kalmar 'HOME' yasa Deen jin wani iri a zuciyarshi ga yadda bugun zuciyarshi ke qara tsananta at every passing minute "shall we?" inji Mussadiq yana kama hannun Deen daidai entrance aka kawosu so basai sunsha wahalar yin wannan uwar tafiyar ba don daga gate zuwa ainahin gidan akwai tafiya sosai hakan yasa nan da nan suka isa bakin kofar shiga doorbell Mussadiq ya danna sau biyu sannan yaqara juyowa yana kallon Deen da kejin wani uneasiness ajikinshi ga wasu gumin dasuka fara tsatsafomashi a saman goshi, tunda yake beta6a shiga halin nervousness irin na yau ba murmushin qarfafa gwiwa Mussadiq yayi mashi yana dan bugun shoulder dinshi daidai nan aka bude kofar. ganin Mussadiq yasa maid din data bude kofar saurin jabaya tana russunawa cikin girmamawa tana musu sannu dazuwa shigewa yayi still riqeda hannun Deen suka shiga qayyataccen falon daya bayan daya kingin ma suka shiga Inda aymaan ne qarshen shigowa duk sannu dazuwa maid din dake cikin uniform takemusu cikin girmamawa har suka gama shigowa sannan tayi saurin qarasowa falon tana nunamasu wurin zama duk suka zazzauna and within a twinkle of an eye anfara shigomasu da kayan ciye ana diddirewa Aysha taso yin sama dagudu tun shigowarsu amma Mussadiq ya hanata saidai ya tabbatar kowa ya zazzauna sannan yayi excusing kanshi ya haye sama domin iske ummie can. tun bayan tafiyar ummie falon yadauki shiru, Deen dai a zaune yake amma baya cikin nutsuwarshi kwata2 don ko a yanayin yadda yaketa gyara zama zaka gane hakan zuciyarshi bugu take kamar ganga jiyake kamar zai mutu saboda nervousness ahankali yaturahannayenshi biyu tsakiyar cinyoyinshi dake amiqe ta takure yana kallon qasa sunkusa mintuna biyar ahakan kafin sufara Jin tafiya natahowa daga saman stairs bugun zuciyar Deen yaqara speed nan take gumi suka fara tsatsafomashi takoina be dago ba amma yana jin yadda sautin tafiyar keqara kusanto falon ga faint voices dayakeji suna tunkarosu duk daga kai mutanen falon dasuka qagara suga ummie sukayi banda Deen suna kallon su ummie dasuke saukowa daga stairs din kallo daya wadanda basu ta6a ganinta ba sai yau sukayi mata suka san cewa tabbas itace ummie, ko mahaukaci ya laluba zai tabbatar saboda mugun kammanin dake tsakaninsu kamar tayi kaki tundaga nesa tafara sakamasu murmushi tana saukowa Mussadiq abayanta dukda bata shaida kowa ba acikinsu hakan be hanata tarbarsu da fafadan murmushinta ba har suka ida saukowa stairs din cikin larabci tafara musu lale marhaban cikin sanyayyar muryarta datadan manyanta tunda muryarta ta daki dodon kunnen Deen kanshi yaqara kwancewa, inner jikinshi yafara rawa ahankali qara cusa hannayenshi yayi tsakankanin kaffafunshi yana matsesu cikin rikicewa. ida qarasowa cikin dakin sukayi Inda Mussadiq yayiwa ummie masauki a kujerar dake facing dinsu cikin larabci tashiga sake yimasu sannu dazuwa fuskarta fall fara'a sosai tayimasu kwarjini hakan yasa duk suka sunkuyar dakai suna murmushi dan rad'a Mussadiq yayimata akunne hakan yasata yin Dan dariya sannan cikin harshen turanci tasake yimasu sannu dazuwa tana tambayarsu sun iso lfy? duk amsa mata suka shigayi cikin girmamawa suna gaidata daya bayan daya tana amsawa tana kallonsu idanunta ne ya sauka kan Deen da har lokacin kanshi ke akasa ya makure wuri guda kamar maijin sanyi Dan tsiramashi ido tayi sannan takalli Mussadiq dake kusada ita cikin tsokana a harshen turanci don Mussadiq ya gayamata akwai wadanda basajin larabci tace "shikuma wancan d'an nawa fa? tsoron mutane yake?" yar dariya duk sukayi sai Mussadiq yace "da alama" shidai Deen bedago ba saima lumshe idanun dayayi yana sauraron bugun zuciyarshi "d'ana? wai dagaske tsoron.mutane kake?" inji ummie tana kallonshi keenly tana lura da yanayi da dama dake kamanceceniya dana wani wanda tasani haka Kawai taji itama zuciyarta na halbawa tun lokacin data dora idanu akanshi soyake ya dago amma yakasa, tsoro yakeji yakuma rasa na menene "ummie da alamu dai tsoronki yakeji" inji Mussadiq yana murmushi "ni?" inji ummie a mammakince "ga alama nan" yafada yana kallon Deen fuskarshi fall murmushi sake kallon Deen da ina part dinshi kerawa sosai tace "d'ana dago ka kalleni kaji?" zuciyarshi ce tabada damm! lokacin dayaji ta kirashi da d'anta ahankali yashiga dago kanshi kamar mai tsoro cikin bin umarninta harya ida dagowa idanunsu ne suka sarqe dana juna wanda yayi daidai da bugawar zuciyarsu alokaci guda kafe juna sukayi da idanu Inda Deen ke kallon fuskar mahaifiyarshi for the first time in his life yayinda ummie afarko kallonshi take blankly kamar wanda hankalinta yagudu na wucin gadi saikuma ahankali tadawo daidai ahankali idanunta suka shiga warawa akanshi kamar kuma wanda aka tsikara tayi saurin juyowa ta kalli Mussadiq da har lokacin ke kusada ita maida kallonta tayi akan Deen dahar lokacin kallonta yake babu kyaftawa atsorace saikuma taqara kallon Mussadiq qara kallon Deen tayi dasauri sannan taqara kallon Mussadiq kamar wata zarrariya ahankali tafara qoqarin tashi jikinta na rawa, ganin hakan yasa Aysha saurin qarasawa wajen tana riqota juyowa tayi atsorace ta kalli Aysha din saikuma taqara kallon Deen ta kalli Mussadiq "Aysha.. idanuna gane gane sukemin, gani nayi yayanki yakoma biyu" tafada cikin rawar murya tana qoqarin tashi qoqarin maidata zaune Aysha tashiga yi tana cewa "ki kwantar da hankalinki ummie..." "yayanki biyu fa nake gani, ko idanuna sunfara lallacewa ne? kalla kigani ga wani can ga wani nan" tafada tana qara binsu da kallo kamar ta66a6iya "eh ummie su biyu ne, nima nagani" wani irin wara idanu ummie tayi "kema kingani? kinga su biyun" kada kai Aysha tayi tana qoqarin danne hawayenta "eh ummie, aidama su biyu ne, dama su biyu kika haifa" shiru ummie tayi tana kallonta saikuma tace "eh subiyu na haifa amma ai yanzu daya ke akwai, wancan ya... ya..." saikuma takasa idawa sai juyawa datayi tana kallon Deen dake kallonta har lokacin zuciyarta na wata iriyar bugawa kusada ita Mussadiq yazo ya duqa "beyi komai ba ummie, beyi komai ba... gashi nan yadawo gareki" kallon Mussadiq tayi shock all over her face kada mata kai yayi "yes ummie, Mujaheed dinmu beyi komai ba, gashinan yadawo, gashinan agabanki, yadawo garemu" girgiza kai ummie tashigayi unbelievable jikinta na rawa sosai "No" tafada unbelievable "yes ummie Mujaheed is alive"...✍? *I can't go futher, kuyi manage please banajin well🤒* Ummin Fasihu🧚🏻‍♀? 8/2/21, 9:44 PM - Buhainat😝: *🙍🏻‍♂️DEEN🙍🏻‍♂?* *086* girgiza kai ummie tashigayi cikin rashin yarda, tayaya za'ace Mujaheed na raye bayan an tabbatar agaban idanun mutane ya qone cikin mota "he was kidnapped ummie not killed, dama nasan Dan uwana bazai mutu hakanan ba, nasha ji ajikina akwai wani sashe na jikina a wani wuri, nasha jina incomplete, ashe shine kuma gashi cikin yarda allah yadawo, yadawo garemu ummie dawowa ta har abada" duk wannan maganar da Mussadiq keyi idanunshi nakan Deen dake kallon ummie still itama ummie idanunta na kanshi tana Jin wani irin feeling mai qarfi na yawo a ilahirin jikinta tashi Mussadiq yayi yaqarasa wajen Deen dake makure waje guda har lokacin yariqo hannunshi ya tadoshi tsaye sannan yanufo ummie duk da kallo mutanen falon sukabisu dashi harsuka qarasa wajenta jan Deen Mussadiq yayi qasa ya kasance sun duqa agaban mahaifiyar tasu "Mujaheed ga ummie, ummie ga Mujaheed, rabonku da juna shekaru ashirin da uku kenan amma na tabbata koda bayan shekaru dubu ne kuka hadu bazaku kasa gane juna ba" hawaye sosai kezuba a idanun ummie data kafe Deen dasu shima Deen hawayen yakeyi involuntary yana bin fuskarta da kallo hannu ummie tadaga ahankali tadora afuskarshi kamar mai tsoro, ahankali tashiga tatta6a fuskar "Mujaheed?" tafada tana cigaba da tatta6a fuskarshi "ummie.." Deen shima yafada ahankali "Mujaheed" "ummie na" "Mujaheed na!" tafada daqarfi tana jawoshi ajikinta lokaci daya cikin fashewa dawani matsanancin kuka wani irin warmness yaji lokacin data sakashi ajikinta, warmness din dabazai iya misaltawa ba yasha samun warmness ajikin Kaka idan ta rungumeshi amma wannan na daban ne don sai jiyayi kamar yanarke su cigaba daxama ahakan saboda wani unexplainable sense of comfort dayakeji a jikinta dama wannan ake kira da mother embrace? kuka sosai ummie keyi tana magana at the same time cikin larabci, tariqeshi gagam kamar zata sakashi ajikinta shima dai jiyake kamar yashige cikin jikin natan ne don shima gagam ya rungumeta bayajin Abinda take cewa amma ga duk kalma daya dazatayi saiya amsa da kalmar 'ummie na' kuka suke sosai su biyun kowanne uncontrollable ahakan wani irin tari ya sarqe ummie tashigayi babu kakkautawa Jin hakan yasa Deen raba jikinsu yadago yana kallonta sai yaga she's coughing blood, tana tari jini nafita abakinta arude ya riqota ahannunshi jikinshi na rawa sosai "ummie! no..No, ummie No!" yafada cikin ihun kuka yana dan jijjigata da gudu kingin yan dakin suka qaraso wajensu cikin tashin hankali "ummie kar kiyimin haka please! please stop am scared!" yafada cikin kuka sosai yana mannata ajikinshi not minding yadda jinin ya 6atamashi kaya har lokacin tarin ummie keyi amma a mugun galabaice Mussadiq kau tuni yatashi arude yakoma gefe yafara qoqarin lalubo number family Dr dinsu aymaan ne yaqaraso gaban Deen yana qoqarin amsar ummie ahannunshi amma Deen ya matsa baya yana qara qanqameta "No! go away!... ummie na" yafada cikin fitar hayyaci yana qara qanqame ummie din "calm down ok? she's gonna be ok, kabari nadubata" inji aymaan ahankali "No!" Deen yaqara fada cikin kuka sosai gani yake kamar sake rabasu za'ayi "idan baka bari nadubata ba zamu iya rasata, ka duba kagani she's in a very critical situation, tama suma zamu iya rasata" sai a lokacin Deen yafara dawowa hankalinshi saidai be saketan ba sai maida numfashin dayakeyi "kabari a dubata before it's late, kun dade ba atare ba nasan yanzu bazakaso kuyi rabuwar har abada ba" inji aymaan again cikin persuading voice maganar aymaan tashigeshi hakan yasa yafara nutsuwa qara matsowa aymaan yayi kusada ita yana neman kama ummie din "kawota na kaita saman kujera" maimakon yabashi din saiya qara qanqameta yafara qoqarin tashi daita "easy" inji aymaan yana dan tarosu ganin zasu fadi da taimakonshi Deen yakaita kan dagowar kujerar ya kwantar saidai yaqi matsawa ko inch daga kusada ita saima bake wajen dayayi "alright, kadan matsa nadubata" yafada gently ahankali Deen ya matsa din amma hannunshi na riqe da nata gamm kamar wanda za'a kwacemawa babu 6ata lokaci aymaan yafara dubata ruwa da tissue yafara buqata dagudu Aysha dake tsaye tareda batool sunci kuka sun godewa allah taruga ta dauko tabashi amsa yayi yafara bata ba ummie taimakon gaggawa cikin qwarewa Mussadiq daketa safa da marwa shima tsayawa yayi yana kallon aymaan don har lokacin Dr din daya kirawo be isoba cikin qwarewa aymaan yashiga ceto rayuwar ummie 🤍🤍🤍🤍🤍🤍🤍🤍🤍🤍 zaune take takafe waje da kallo ta glass window dake kusada ita kofin shayi ke hannunta wanda tuni yahuce ma don tunda aka bata kur6a biyu tayimashi takuma fita babinshi idanunta na kafe akan window daya kasance glass ne don ana iya hango waje tarr ta wajen kallo daya zakayi mata kasan bata awannan duniyar tamu kwata2 bude kofar dakin akayi ahankali aka shigo Inda ta barta nan tazo ta sake taddata girgiza kai Kawai tayi sannan tanufeta zee batama san da shigowarta ba saida taji an dafata saurin dagowa tayi daga duniyar tunanin data lula ganin ummy ce yasa tadanyi murmushi tana kai kofin shayin da har yayi sanyi baki murmushin itama ummy tayi mata taja kujera ta kawo kusada ita ta zauna "daughter" takirata ahankali dagowa zee tasake yi ta kalleta "haryanzu baki shanye shayin ba?" qara kai kofin zee tayi abaki ta kur6a dukda rashin dadin dayake mata gashi yayi sanyi "gashinan ina sha ummy" murmushi ummy tayi "ai yama huce ko? mugani kinasonshi ahakan ko ahada wani mai zafin?" saurin bata zee tayi cikin marairaice fuska tace "ni nama qoshi ummy kalla kigani nasha dayawa" kallon shayin da ba'asha ko kwata ba tayi tayi murmushi tace "to shikenan yanzu tashi ki chanza daddy na qasa yana jiranki kutafi yawo" nan take fuskarta tayi brightening "dagaske?" tafada cikin zumudi "dagaske, maza yi sauri kar yaita jira" da sauri ta tashi cikin jindadi dama tagaji da wannan zaman loneliness din tasan koyaya suka fita koda kaso kadan ne zai rage daga cikin damuwarta wucewa bathroom din dakin tayi ummy tabita da ido cikeda tausayawa saikuma tadan girgiza kai sannan ta tashi tafita riqeda kofin shayin zee din *** Ahankali tafara bude idanunta dasuka yimata nauyi da farko biji biji tafara gani sai ahankali ahankali ganinta yafara dawowa akan fuskarshi tafara sauke idanunta yana kallonta itama affectionately lumshe idanu tayi akanshi tasake budewa and he's still there hakan ya tabbatar mata ba mafarki bane kamar yadda tayi tunani "ummie na" yafada ahankali yana qara damqe hannunta dake cikin nashi idanunta ne suka fara qyallin hawayen dasuka fara taruwa a kwarin idanunta girgiza mata kai yayi yana kai hannunta dake hannunshi saitin bakinshi ya sumbata yace "don't ummie, you're sick, please no more tears.. am here" ahankali takai hannun nata tashafi gefen fuskarshi daidai nan hawayen suka gangaro dora nashi hannun yayi saman nata dake bisa kumatunshi yasa dayan hannun yana share mata hawayen "ina katafi kabarmu?" tafada in

Chapter 69 of 81