Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
You know, bake kadai bace ke ganin haka ba, dayawa mutane na ganin haka, wasu ma sai suga soyyayar datake nunamin yayi yawa tana overpampering dina Abinda mutane basu ganeba shine, ita qauna daya ce Saidai kowa da yadda yake nuna tashi Akwai masu iya 6oyewa ma'ana masu kawaici akan nasu Akwai masu bayyana nasu afili kamar dai kaka To irin haka ne sai aga kamar yayi yawa bayan da za'a gwada wannan soyyayar tasu data wannan mai kawaicin da wata qila aga ko kama qafar ta mai kawaicin batayi ba Kakata bata nuna kawaici akaina, she loves me openly batareda damuwa da abinda mutane zasuce ba Bana mantawa lokacin da nake qarami kusan kullum sai kaka tayi hayaniya da mace akaina Bawai jawo magana ba nake, A'a ni ake ja itakuma bata iya kyalewa most especially idan tasan ni keda Gaskiya, kaka bata ta6a kawaici idan taga za'a kwareni saita tsaya mun batareda damuwa da abinda mutane zasu ce akan Hakan, Hakan yasa mutane ke ganin soyyayar datake nunamin tayi yawa bayan ba Haka bane Idan ma Hakan ne banga laifinta ba don tana taking role din mutane uku ne agareni Uwa, uba da kaka. Shiyasa soyyayar tayi yawa don tana min soyyayar dazan buqata a wajen wadannan mutanen wato mahaifiyata, mahaifi na da kaka ta Shiyasa bana missing iyayena ta fannin nuna qauna da kulawa don kaka tayimin komai, tana sona kuma nine komai nata kamar yadda nima nake sonta kuma itace komai nawa Duk duniya banida babbar masoyiya kamar kaka daga ita sai mai sonta sai mai son mai sonta sai mai son wadda taso wanda ke sonta" Dariya sukayi atare saboda yadda hausarshi ta qarshe take so confusing "to aku mai bakin magana, wai mai son wadda taso mai sonta, wannan love chain din fa?" inji zee tana Dariya Murmushi yayi yace "wai don ki gane" "tayaya za'ayi ingane wannan doguwar hausar? Gaka ba bahaushe ba sai fihili" 6ata rai yayi "nine ba bahaushe ba?" Dan bude idanu tayi tace "oh ashe bahaushe ne, mantawa nayi" tafada tana ta6e baki don ita haryanzu bata yarda shi bahaushe bane Akwai dai abinda yake 6oyemata "yanzu ai kin tuna" yafada yana harararta Qara ta6e baki tayi tace "aikau dai na tuna bawai don na yarda ba" Ta6e baki shima yayi yana daga kafadu sannan yace "dazu naji kina ba kaka labarin yadda akayi da qawayenki jiya" Mood dinta ne ya chanza, Ganin Hakan yasa yace "Allah ya tsare gaba, allah yasa kuma Hakan yazama silar shiryuwarsu, 2yrs kamar 2days ne insha allah" Kada kai tayi sai kuma ta dago ta kalleshi tana tuna abinda sukace shine dalilinsu na juyamata baya _*son Deen*_ Jitayi zuciyarta ta buga da qarfi Hakan yasa tayi saurin kauda kai daga kallonshi zuciyarta na beating fast Tasan kwata2 maganarsu ba Gaskiya bace amma tarasa dalilin dayasa daga jiya zuwa yau data tuna Da wannan kalmar sai zuciyarta taqara gudu musanmman ma yanzu datake tare dashi Haka ta danne abinda zuciyarta keyimata ta cigaba da sauraronshi suka cigaba da firarsu Basu qara jimawa ba suka tashi don komawa don kar kaka taita jira shiru Daga nesa daka hango yadda suke tafe suna hira kowanne da murmushi a fuskarshi sai sun burgeka don sosai sukayi matching dajuna ta kowanne fanni... ✍️ Tofa, munfara tsunduma cikin main labarin, muje zuwa 💃 yanzu ma za'a fara wasan😍 Ummin fasihu 🧚🏻‍♀? 8/2/21, 9:35 PM - Buhainat😝: *🙍🏻‍♂️DEEN 🙍🏻‍♂?* *029* Saida tadan qara jimawa hospital din sannan tawuce gida Tun daga ranar abin nema yasamu, duk lokacin dasu zee suka zo saisun fita da ita dashi wai miqe kafa wanda Dr ne yaqara qarfafa abin don acewarshi ya dinga yawatawa din Hakan na cikin abinda zai ida sawa yaji sauqi sosai Haka kullum zasu fita susamu quiet wuri inda ba'a cika zirga zirga ba suyi zamansu susha firarsu, sai sun gaji sannan zasu koma Acikin yan kwanakinnan wata muguwar shaquwace ta shiga tsakaninsu wacce tafi ta da Har takai idan basa tare sai sudinga jinsu empty kamar akwai abinda ke missing a rayuwarsu Sosai Deen yake samun sauqi don ba qarya yana samun kulawa na sosai da sosai, abinka da private hospital inda ake tarairayar patients sosai da sosai Gashi kuma patient din Alhaji farouq ne wanda yana daya daga cikin wadanda suke darrajawa sosai saboda gudunmawar dasuke ba asibitin shiyasa yake samun special treatment Ranar daren da za'a sallamesu ake amsar result a school Hakan yasa zee bata samu zuwa hospital din ba Koda ta isa school din saitaji komai na ranar nan na komamata sabo Duk inda tawuce sai an bita da kallo wanda tasan Hakan baya rasa nasaba da abinda yafaru dakuma makomarsu master Kamar yadda tasaba kallon be dameta ba harkar gabanta kawai take Wucewa tayi wurin da aka liqa nasu ta duba, babu abinda tafara nema sai subject din mr ibrahim Wani farinciki ya ziyarceta lokacin dataga abinda tasamu *57/100%* Hakan na nufin a exams taci 40% idan kuma aka jona da score dinta 17% na assignment dinnan saiya bada 57% Sosai taji dadi kuma ta godewa allah akan Hakan sannan tabi sauran subjects din wanda suma duk tayi qoqari acikinsu Koda tagama kamar ta tafi saikuma wata zuciyar tace mata ta dub a nasu nurr mana Dubawa tayi Saidai results dinsu ba kyan gani don duk tarin carryover(s) ne, bataji dadi ba sam don haryanzu suna ranta dukda kuwa abinda sukayimata don ita idan zata so mutum to da dukkan zuciya takesonshi babu algus Daga nan wucewa tayi department dinsu Deen don ta dubomashi shima As expected, shima yayi passing in flying colours don result dinshi is so amazing Ciro wayarta tayi tashiga snapping din daidai nashi murmushi a fuskarta Saida tagama komai sannan tawuce cafteria ta siya snacks da drink ta wuce wurin zamansu don jiran qarasowar bala Ga mammakinta tana zama wajen sai jitayi tana kewarsu sumee, sai tafara tunanin ko me sukeyi a yanzu? Da sunanan da yanzu suna tare ana maida yadda akayi Kawar da tunaninsu tayi tafara cin snacks dinta silently Tunanin Deen ne yafadomata, ko me yakeyi yanzu shima? Tambayar da tayiwa kanta kenan, tasan da yau ta tafi asibitin da yanzu suna tare suna firarsu mai dadi mai sa nishadi Sai jitayi tayi missing dinshi shima, murmushi kawai tayi ta cigaba da cin abin hannunta tana saqa da warwara ita kadai har bala ya qaraso Babu 6ata lokaci ta tashi tawuce parking space din tashiga mota suka fice daga harabar school din *WASHEGARI* Yau ce ranar sallamar Deen daga hospital, ya warke garau kamar be ta6a kwanciya jinya ba saima wani qara fresh dayayi da kyau Kaka yau baki be rufuwa, sai kai kawo take wajen ganin ta kammala kayyayakinsu waje guda Wajajen 12 su zee da mummy suka duro asibitin suma daddy kau dama yayi tafiya tun washegarin ranar da akayi zaman kotu, dama abinda ya tsaidashi kenan Koda suka iso sai tarar da kaka sukayi tagama kammala komai wuri guda jira kawai take a sallamesu su qara gaba don zaman asibitin ya isheta, sati biyu ba wasa ba Mummy ce tashiga tsokanar kaka akan zumudin datake wai kodai don taje ta cigaba da samun yan anninnan ta yasa take wannan zumudin? Dariya sukayi baki daya kaka nacewa ashe dai ta gano Kallon Deen zee tayi taga ya sakarmata murmushi Itama maida mashi martani tayi tana kauda kai tashiga gsida kaka itama Cikin fara'arta kaka ke amsawa tana tambayar ta ya sakamakon dataje dubowa jiya Murmushi tayi tace "Alhamdullilah kaka, sakamako yayi kyau sosai" "masha allah, ai haka akeso. Ai ina ganinki nasan zakiyi qwanya kamar dai kyakyawa na, allah sarki, kowa zaije ya dubomashi shi? Inajin nizanje in dubomashi bari dai komai ya lafa" Dariya duk sukayi jin abinda tace, Deen yace "to kaka ke ya za'a yi ki iya? Tayaya zaki iya gano sunana cikin jerin sunayen dake manne a wajen? Kuma ma Dariya zasuyi miki wlh, suga tsohuwa tazo duba result" yafada yana Dariya Daquwa ta watsamashi tace "ungo nan don qaniyarka, nice tsohuwa?" Dariya duk suka sake dauka "Ato, maganar shi dai na kan hanya" inji mummy tana Dariya "ba wata kan hanyar datake zaki wani goyi bayan shi, kubar ganin na haka to tsohuwa ce mai ran qarfe don abinda mai ji da quruciya bata iyayi ina iyawa, ko aminiya?" Murmushi zee tayi tace "kyalesu kaka, ai fadi ma 6ata baki kuma bama sai kin wahalar da kanki ba na dubomashi, bari kigani" tafada tana zaro wayarta ta lalubo result din ta nuna ma kaka, aikau ta amshe wayar tana dubawa baki washe kamar irin tasan abinda ke ciki dinnan "kai masha allah! Bana gayamaku ba, dan jikallen nawa ba dai qwanya ba, kalli wani dan abu abu nan nasan na masu qoqarine ko?" tafada tana nunama zee dake Dariya bama itaba duk mutanen dakin "eh kaka ai yayi qoqari sosai" inji zee tana kallon wayar "snapping dinshi kikayi?" inji Deen yana kallon zee Kada mashi kai kawai tayi alamun eh "mugani kaka" yafada yana miqa hannunshi Janyewa tayi tana cewa "tsaya mugani, meye wannan abin shikuma?" "ko an fadamaki ba ganewa ba zakiyi kaka, kidai bani ingani" Harararshi tayi tasake gwadawa zee Saida tagayamata ko menene sannan ta bashi tana jinjina kai alamun ta fahimta amma a zahiri babu abinda ta fahimta Amsa Deen yayi cikin zumudi yana dubawa Wani kyakyawan murmushi yayi yana maida pink lip dinshi na qasa ciki yana taunawa Batasan itama shi take kalloba tana murmushin da Batasan tanayi ba Saida ya dago suka hada ido Saurin janye idanun ta tayi cikin basarwa still murmushin a fuskarta "mugani son" inji mummy Miqamata yayi ta amsa itama tana dubawa "kai masha allah! Gaskiya result yayi kyau sosai" Cikin jindadin abinda tace kaka tace "kede bari, ai dan naki badai qwanya ba. Yo to Allah na tuba yadda yake raba dare yana karatunnan ai dole ma yaci, ko lokacin dayake firamari shi ke dauko na daya, duk lokacin hutu saiya dawo da kyauta, abashi a makaranta abashi a hanyar dawowa gida, duk wanda ya gamu dashi a hanya ya amshi takardar ya duba saiya bashi wani abu, tun sannan nasan yaron naki dan baiwa ne ba irin wasu ba masu kwalwar dusa, kullum Saidai a matse jakka a hammata azo amsar kudin tara, ja'irai dama kudin ke kaisu sudai abasu sutafi sukul din sukasosu sudawo suna zare idanu, ranar hutu kuma sunfi uban kowa kukan an kaddasu a jarabawa Haka kyakyawana yaita fama dasu, duk lokacin da aka bashi takardarshi sukaji yayo na daya sai suyita jin haushinshi wani sa'in ma su tareshi a hanya suyimashi duka su yaga takardar, dayake raggo ne babu abinda ya iya shiyasa suka bi suka rainashi Haka zai dawomin hurtutu idanu jajjaye ga yagaggiyar takarda, Saida na tashi tsaye sosai suka shafamashi lfy don bana jin kunyar kowa idan danki ya daki jikana har gida zan biyoshi na rama mashi, babu ruwana Sunyi surutun sunyi surutun amma ban fasaba don ko qarqashin gado yashuge saina zaquloshi na rama mashi saigashi sun daina ko kallon Banza ma basa mashi Ato idan kace ka nuna sanya sai a raina maka hankali..." Haka kaka taita zuba Sukau sai sauraronta suke suna murmushi, wani wurin kuma mummy tasa baki Suna haka akafara kiraye kirayen sallar azahar Duk tashi sukayi suka gabatar daita Basu dade da gamawa ba Dr yashigo Saida yaqara duba shi yaga komai normal sannan ya rubuta masu sallama bayan ya basu maggungunan Deen dazai cigaba dasha yakuma gargadesu su dinga kulawa abar barin sanyi na bugunshi Babu 6ata lokaci suka gama kimtse kimtsensu suka fito Motarsu mummy suka shiga mummy ce ke tuqi sai zee gefenta, abaya kuma Deen ne da kaka suka fice daga asibitin suka shilla Da kwatancen kaka suka qaraso unguwarsu Deen Zee sai kallon unguwar take tana ganin yadda aketa kai kawo jefi jefi A gaban wani dan gida kaka tasasu tsayawa Fitowa duk sukayi gabadaya suna maida koffofin suna rufewa Bïñ arear zee take da kallo tana kallon yadda yanayin gidajen unguwar suke Wucewa tayi wajensu kaka daketa qoqarin lalubo makullin gidan shikuma Deen rungume da qullin komatsansu Bude kofar kaka tayi tana cewa "to bismillah, kuyi hqr gidan dai gashi nan dan kuqut" Deen ne ke bayanta sai zee dake riqe da nad'ad'iyar tabarmarsu wanda kaka ke amfani daita a asibitin sai mummy Da sallama duk suka shiga gidan dake tass yasha shara don dama tun jiya matar mallam Nasiru taje ta amshi makulli tasa yaranta suka gyara gidan fess don tasan agajiye zasu dawo gashi dama gidan ya dade bega gyara ba "maraba damu, kai yaushe rabo? Nasan gidannan ma yayi kewarmu" inji kaka tana qarasawa kofar dakinta Murmushi duk sukayi sai mummy tace "ai dole, sati biyu fa?" Kaka data shige dakin tace "sati biyu amma jinshi nake kamar shekara biyu" Tafito hannunta da wata tabarmar ta shinfida masu tana cewa "bismillah, ku xauna munshawo rana, kamal tashi kasamomana pure water mai sanyi ko ma jiqa maqoshi" Tashi Deen da dama zamanshi kenan yayi ya amsa yawuce Binshi da kallo zee da mummy sukayi cikin sha'awa Sai ji mummy tayi yaqara kwanta mata don a duniya tana bala ' in son d'a ko 'ya mai biyyaya kuma a yan kwanakinnan datayi dasu kaka ta lura Deen akwai biyyaya ga sanyi bayada hayaniya ko kadan abinda take buri ga diyarta amma Saidai ba Haka take ba ko dayake taga acikin kwanakinnan kamar tafara dan hankali hankali Suna zaune suna dan fira Deen yadawo da rabin ledar pure water masu sanyi yawuce dasu kitchen can kuma yafito dasu bisa unbreakable plate mai dan fadi kamar yadda suka saba yiwa baqi yazo ya ajiye tsakiyarsu dan murmushi a fuskarshi Kaka da kejin kishi sosai tafara dauka tana cemasu ga ruwa su dauka Babu musu suka dauka zee na raka Deen daya nufi wani daki da kallon qasan ido Mummy ce tafasa tadan sha ba laifi itakau zee dauka kawai tayi badon tasha ba don bata iya shan wannan ruwan inba sotake cikinta ya rikice ba hakan yasa ta riqeshi a hannu kawai Saida suka qara dan jimawa sannan suka tashi da niyyar tafiya Tashi itama kaka tayi tanata kwarara masu Godiya da samasu albarka da addu'o'i suna amsawa, kiran Deen tayi don suyi bankwana Saida suka rakasu har kofar gida suka tsaya suna jiran ganin wucewarsu sai gani sukayi mummy ta tafi bayan booth ta bude sannan ta yafito Deen da hannu alamun yazo Babu musu ya qaraso wajen cikin nutsuwa Gwadamashi booth din tayi tace "ya za'ayi a sauko dasu ko wasu za'a samu su taimaka?" Dan wara idanu Deen yayi ganin abinda take gwadamashi "na menene wadannan din?" "naku ne and banason wani qorafi, maza samo masu dauka" Ganin yadda ta Hade rai yasashi kasa musawa sai kawai ya fara nade hannun shirt dinshi yace "bari na dauka zan iya ai" Zee na gefe tana kallonsu har suka gama fidda kayayyakin daga booth din Kaka tariga takoma ciki so Batasan wainar da ake toyawa ba Rufe booth din mummy tayi tana cewa "to mu zamu tafi amma insha allah zamu dinga dan leqowa tunda munga gidan, allah yaqara sauki" tafada tana kallon smiling face dinshi "to mummy mun gode qwarai, jazakillah bil-jannah" yafada cikin ladabi Wani kayattacen murmushi tasaki tana cewa amin sannan tawuce bangaren driver Kallon zee dake tsaye gefen kofar mai zaman Banza yayi yaga itama shi take kallo Murmushi yayi mata itama ta maida mashi martani slightly sannan tajuya ta bude kofar tashiga ta zauna maida ta rufe, mummy ma rufe nata tayi bayan tashiga tana daura seat belt Juyowa zee tayi ta kalleshi ta window taga shima still yana tsaye yana kallonta itama Tsayawa sukayi suna kallon juna kamar suna karanta wani abu a fuskar junansu Tada motar mummy tayi tafara reversing ahankali Ahankali Deen yaga zee ta dago hannunta sannan tayimashi waving murmushi nadan forming a fuskarta Shima dago hannun yayi yafara daga masu hannu fuska dauke da murmushi har suka bar layin Bïñ motar datayi nisa yayi da kallo yanajinshi awani yanayi dabazai iya pointing finger akai ba Saida ta 6acema ganinshi sannan ya sauke ajiyar zuciya yadawo da kallonshi akan kayayyakin dake gefe ajiye Wani yaro dan babba2 yazo wucewa ya kirashi yace ya taimaka mashi shigar da kayan ciki Tare sukaita shiga da kayan ciki har suka qare sannan Deen yaba yaron naira 20 yanamashi Godiya sannan yadawo cikin gidan inda kaka ta tisa kayan gaba tana binsu da kallon mammaki Shigowar Deen din yasa ta maida kallonta akanshi cikin ayar tambaya Hakan yasa yadan 6ata fuska yace "wlh kaka Saida nace a'a saita fara fushi wai saina amsa" "ita wa?" "mummy mana, zanyi magana ta hanani wai Batason qorafi" Shiru kaka tayi tana kallon kayan wanda duk kayan abinci ne, su cartons din taliya, macaroni, couscous, gallon din mai da manja, packs din maggigika sai wasu abbubuwa a leda wanda ahaka bazasu iya gane meke ciki ba saisun buda Ajiyar zuciya kaka tayi tace "kuma shine kabari ta tafi ko Godiya?" "ina gama saukewa ta tafi ai" Ajiyar zuciya kaka tasake yi tace "to allah yasaka masu da alhairi, allah ya biyamasu dukkan buqatunsu na alhairi, gashi ko unguwarsu bamu saniba bare muje Godiya, allah dai yaqara budi, sun taimaka sosai wlh kaga zasu riqe mu nawasu lokaci kafin mu maro, allah dai ya biya" Da amin Deen ya amsa, cemashi tayi yakama su shiga dasu ciki kafin afara Shigowa Da taimakon shi suka kwashesu duka suka kai dakin kaka suka adana sannan suka daura alwalar sallar asr don har anfara kiraye kiraye Wucewa masjid yayi ita kuma kaka tawuce d'aka *** Tunda suka kamo hanya take kallonshi ta side mirror din motar harya 6acema ganinta, sai jitayi kamar ta taho tabar wani abu nata acan Lumshe idanu tayi ta koma ta lafe a kujera tayi shiru tanajin yadda suke tafiya akan titi Basu wani dade ba suka qaraso gida Horn biyu mummy tayi aka wangalemasu gate din gidan suka shige Saida tayi parking sannan duk suka fito zee na jinta very empty Wucewa sukayi ciki suka haye sama kowa yayi sashenshi don gabatar da sallar asr da aketa kira *** Koda aka gama sallah gagaisawa Deen yashiga yi da mutanen cikin massalacin kamar yadda yasaba sunata tayashi murnar sauqin dayaji Koda yafito ma zai tafi gida haka yaita gamuwa da mutane sunata mashi barka yana amsawa da murmushi harya samu ya qaraso gida A gidan ma yan tsirarun mata ya iske wadanda suka shigo yima kaka barka Gaidasu yayi a ladabce duk suka amsa suna mashi ya jiki ya amsa masu sannan yatashi yashiga dakinshi Be dade ba ya fito yazo wajensu yaqara gaida wadannan suka sake Shigowa bayan shigarshi daki sannan yace ma kaka zai dan fita wajen aikinsu Fatan dawowa lfy tayimashi tana cewa kar yakai magrib Da to ya amsa ya tashi yayi sallama da mutanen yafita Direct wajen workshop dinsu yawuce inda ya ishesu suna dan ta6a aiki don yanzu sai ahankali abunka da damuna Duk sunyi murnar ganinshi Hakan yasa suka shiga gagaisawa cikin fara'a Suna tambayar shi ya jiki yana amsa masu da ya warware Haka ya zauna cikinsu anata fira wanda becika sa baki ba Saidai da anyi abin Dariya yayi murmushi kawai Be baro wajen ba sai wajajen magrib Saida yafara gabatar daita sannan yashiga gida inda ya iske duk matan sun tafi sai kaka dake daki bisa sallaya ita kadai Saida yayi mata barka da gida sannan yawuce dakinshi Be sake fitowa ba sai lokacin isha'i yawuce massalaci don dama da alwalarshi Koda aka gama ya dan jima awaje sannan ya dawo gida Abinci kawai sukaci suka kwanta saboda dama a matuqar gajiye suke shiyasa suna kwanciya barci yayi awon gaba da kowanne A bangaren zee kau yau Dakyar tayi barci, wani irin kewa takeji sosai musanmman da lokacin Zuwansu asibiti na dare yayi Haka taita juyi a gado don kwata2 babu barci a idanunta Ganin Hakan yasa tajawo wayar ta tana yan danne danne amma a Banza don Hakan bewani hanata jin abinda takeji ba Haka taita fama har tasamu Dakyar barci yayi gaba daita can wajajen 12 dare... ✍️ Ummin fasihu 🧚🏻‍♀? 8/2/21, 9:35 PM - Buhainat😝: *🙍🏻‍♂️DEEN 🙍🏻‍♂?* *031* "Are you ok?" yafada yana tsareta da ido Kauda kai tadanyi gefe tana hadiye qululun takaicin daya tokaremata maqoshi Kallonshi tayi tadanyi murmushi irin na takaici tace "am fine, kawo nasa maka" Amsa tayi tana jin kamar ta kwalata da qasa amma tayi qoqarin controlling emotion dinta Saboda tsabar yadda takeji har wani dishi dishi take ganin screen din wayar Dakyar tasamu ta daddana nambobin mummy data riga ta riqe ta offhand sannan ta miqamashi Ganin be amsa ba yasa ta dago ta kalleshi taga ita shima yake kallo Sake miqamashi wayar tayi batareda tace komai ba Amsa yayi ahankali sannan yace "Are you sure you're ok?" "more than you are" tabashi amsar tana juyawa kwalin wayar a hannunta Kafin yasake wata maganar harta fice daga zauren ta nufi Motarsu Dayake a fusace take ko jira a bude mata motar batayi ba ta bude abinta dakanta tashige Tsayawa Deen daya biyo ta shima yayi a bakin kofar gidan yana kallon motar dukda baya iya hangota taciki saboda tinted glass dinta Da sauri bala ya zatayi ta bangaren mai tuqi yashiga shima yarufo qofa Yana tsaye yaji qarar tashin motar sannan tafara yin reverse tana barin layin Bin motar yayi da kallo abubbuwa da dama na kai kawo a zuciyarshi Tabbas she's not ok, ya hangi wani abu a fuskarta dukda 6oyemashi datayi qoqarin yi, kamar fushi kamar takaici bazai dai iya pointing finger akai ba To idan ma fushin ne meye silar? Tunda yashigo gidan ya lura da wannan expression din a fuskarta Duk sai yaji ba dadi, satinsu daya rabonsu da juna and he's longing and waiting for the day they'll meet, a tunaninshi bayan wannan lokacin da sukayi basu ga juna ba haduwarsu zaya zama very memo ranar one, zasu dade suna firar yaushe gamo amma yaga akasin haka saima qin Sakin jiki da fuska data sabayi Ya dade nan tsaye sannan ya juya ya koma ciki a sanyaye Idan ran zee ya kai dubu to duk sun 6aci Tama kasa fasalta abinda takeji a ranta wannan lokacin She's totally and totally dissapointed with him Tayi sati tana kewarshi tana begen ganinshi tana looking forward to ranar haduwarsu cikin zumudi amma sai gashi babu abinda ta kwasa a ranar datake zumudin sai kayan haushi da takaici It hurts idan kadamu da mutum harya kasance koyaya ka motsa saiya fadomaka a rai amma at the end of the day ka gano cewa bakai ke gabanshi ba Koda bala yayi parking bata tsaya ya budemata kofa ba kamar dazu ta bude ya fita tayi gaba Zagayowa bala yayi ya rufe kofar data bari bude cikin ranshi yana gulmarta wai dama idan tafito mota dakanta to ranta a 6ace yake Da sallama ciki2 tashiga falon, babu kowa falon hakan yasa tayi sama direct Kamar tashiga dakin mummy sai kuma tafara bude dakinta ta tilla ledar wayar hannunta saman gadonta sannan ta rufe tawuce kofar mummy tashiga knocking Saida aka bata izinin shiga sannan ta tura kofar tashiga tana kokarin saita fuskarta Mummy daketa lissafe2 ta dago tana kallon zee data shigo dakin Qarasawa zee tayi ta samu wuri ta zauna tana yiwa mummy sannu da aiki "yauwa, harkun dawo?" Kada mata kai tayi tace "eh mummy, tana gaidaki sosai tamace zata kiraki nabata number ki" "masha allah, me jiki fa? Hope ya warware" Wani abu taji ya tsayamata a qasan maqoshi jin anyi maganar Deen "eh da sauqi" ta amsa non-chalantly "to allah ya kyauta gaba dama haka muke fatan ji" Shiru yadan ratsa dakin can zee ta tashi da niyyar tafiya "kunyi waya da daddy?" inji mummy tana dakatar daita "A'a, duk yau bamuyi ba Saidai jiya munyi da daddare" ta amsa "wani abu yafaru ne mummy?" tafada cikin curiosity Murmushi tadanyi tace "ohon muku, ai kunfi kusa, cemin yayi yana kiranki bata shiga wai idan kin dawo ki kirashi" Murmushi tayi tana jin kaso kadan daga cikin 6acin ranta na tafiya "ok zan kirashi yanzu insha allah" Daga haka tayi mata sallama tafita Dakinta tawuce direct Gyallen kanta tafara warwarewa ta cire sannan ta zauna gefen gado tana scrolling din wayar ta Foreign number daddy ta lalubo ta antayamashi kira Bugu biyu ya daga ya dauka yana sallama Shagwa6e

Chapter 21 of 81