su dama ake jira, nan take akayi musu caa akan meya faru, ina sukaje
Saida suka zauna sannan Aymaan yafada masu komai daga inda yaje school din da niyyar daukota har hangosu dayayi a parking space din kamar suna hayaniya da mutumin har Qarasowarshi wajen da yadda fadan yakoma kanshi
Sai aka maida akalar Tambayar ga zee akan me ya hadasu
Nan zee ta gayamasu yadda komai yafaru takuma gayamasu haduwarsu da mussadiq din a supermarket lokacin da suka fita da batool siyo jakka Saidai ta 6oyemasu cewa la6el tayimashi ta dinga binshi abaya, kawai cewa tayi tayi 6atan hanya ne sai suka hade dashi shikuma sai yace shi take bibiya
Kowa mammaki ya cika shi da kuma jimami akan abinda yafaru, cikin masu mammakin harda Ahmad da abin yafi kowa kadashi, lallai ba qaramin tsallake rijiya da baya sukayi ba
Mussadiq? Mussadiq al-hassan yasa akamasu kuma ya sakesu da wuri haka?
Nan su Abbu suka yanke shawarar fidda zee daga makarantar saboda tsaro tunda zuwa makarantar na neman zama barazana agareta, kawai gwara a maida ta school dinsu batool tunda ba'ayi nisa a semester din ba qila a kar6eta
Sosai Batool taji dadin Hakan don Hakan na nufin tare zasu dinga zuwa school kenan kuma zasu dinga yini tare
Cikin wadanda sukaji dadin Hakan harda Aymaan don shima abinda ke ranshi kenan kawai sun rigashi furtawa ne kuma yaji dadin da bashi ya furta din ba
A 6angaren zee kau ba taji dadin haka ba sam, Saidai bata nuna ba, that means tabar makarantar annur kenan? Tabar Aysha?
***
Kwance take idanunta akan cieling din dakin tana kallon design dinshi wanda a zahiri bashi take kallo ba tayi nisa ne a tunaninta
"zee nasan bakiji dadin hukuncin dasu ummy suka yanke ba Amma that's the best solution, tunda mutumin nan ya dora ayar tambaya akanki bazai barki ba, zaita bibiyar ki ne har saikin fada tarkonshi so maganin kar ayi kar asoma gwara kibar musu school din"
Ajiyar zuciya zee ta sauke still idanunta akan ceiling din
"ni ba barin school dinne matsala ta ba, rushewar hanyar cikar mission dina yafi damuna, gashi na shaqu da Aysha, zanyi kewarta"
"hakane amma abinda zaki duba anan shine wannan hukuncin is for your own Good, Ahmad yana yawan bani labarin how dangerous that guy is, yana iya yin komai kuma yaci bulus don yanada both matsayi da kudi da connections, ja dashi ba qaramin kasada bane, batun mission dinki kuma allah zai kawo mana mafita ta hanyar da bama zato kawai mu cigaba da addu'a"
Qara sauke Ajiyar zuciya zee tayi tace
"to allah yasa Hakan shiyafi alhairi"
"Amin summa amin" batool ta amsa
Wayar zee ce tayi Ring
Tashi tayi ahankali zaune sannan ta jawo wayar dake kusada ita kan bedside locker
Dan Wara idanu tayi ganin sunan dake yawo a screen din
Ganin Hakan yasa batool cewa
"waye?"
"Aysha" zee ta amsa tana picking call din
"bestie" inji zee cikin fara'a
Wani irin wawan Ajiyar zuciya zee taji Aysha ta sauke sannan cikin murya Kamar zatayi kuka tace
"ummie na"
"na'am sahibatie"
"wayyo ummie na, nayi tunanin bazaki daga kirana ba Tundazu nake son kira amma fargaba ta hanani"
Murmushi zee tayi tace
"inqi dagawa kuma mezai hanani dagawa?"
"komai ma ummie, am sorry, am very very sorry for what happen dazu, da nasan abinda zai faru kenan da ban fara gayyatarshi ba"
Murmushi zee tasake yi
"Don't be, misunderstanding ne kawai"
"wlh bakiji yadda naji ba a lokacin, laifi na ma ne, nasan halin yaya sarai amma banyi tunanin abin zakai Hakan ba da ko sunanki bazan ta6a ambata mashi ba"
"kinga babu komai, kibar damun kanki, komai ya wuce insha allah" inji zee
"nagode qwarai ummie da fahimtarki, fatan dai komai lafiya, ba'ayi muku komai ba ko?"
"babu abinda akayimana, komai lfy lau"
"yayanki fa? Shima is ok ko?"
"kowa lfy lau, na gayamaki babu abinda sukayimana"
"masha allah, naji dadin jin Hakan... Ga ummie ku gaisa"
Wara idanu zee tayi saita kalli batool da itama ta Wara nata idanun don wayar a handsfree take duk tana sauraron su
"Assalamu alaiki habibty" muryar Ummie mai cike da kwarjini ta daki dodon kunnenta
Hadiye wasu yawu tayi sannan cikin nutsuwa itama ta amsa sallamar ta dora da gaisheta, duk maganar dasuke a harshen turanci suke yinta
"lfy lau habibty, ya gida ya mutanen gida"
"alhamdullilah, ummie" inji zee cikin nutsuwa
"masha allah, ina mai baku haquri akan abinda yafaru tsakanin ku da hussain, Gaskiya banji dadi ba kwata2, abin ya 6ata min rai sosai kuma zan dauki mataki akai kuyi hqr kinji"
"haba ummie komai ya wuce insha allah, dama rashin fahimta ce kawai"
"babu wata rashin fahimta, haka yake. Narasa inda yasamo wannan baqar aqidar, shikenan mutum beda yarda kona misqala zarratin? Ai dazu Saida nayi mashi fada sosai nakuma ya sakeku kuma saina dauki mataki akai"
Murmushi zee tayi cikin jin qaunar matar, da wata ce ko ajikinta bare har tayi tunanin kira ta bada haquri
"babu komai ummie, allah yaqara lafiya"
"Amin, ina Ummin naki?"
"tana dakinta"
"kai mata mu gaisa don Allah"
"to ummie, hold on" tafada tana tashi tsaye ta nufi kofa batool ma ta sauko daga gadon ta maramata baya
A daki suka iske Ummu batool tafito daga bayi da alamu ma wanka tayi
Kaimata wayar tayi
Daga gira Ummu batool tayi alamun waye, cikin rada zee tace mata umminsu Aysha ne
Kara wayar Ummu batool tayi a kunne tayi sallama ummie ta amsa ta dayan bangaren
Gaisawa suka farayi cikin mutunci sannan ummie tayi introducing kanta takuma shiga bata hqr akan abinda yafaru
Cikin fara'a Ummu batool ke nuna babu komai ai komai ya wuce insha allah
Sundan jima suna wayar sannan sukayi sallama ummie ta maido ma zee wayarta
Koda ta maida a kunne sai taji muryar Aysha
Nan take gayamata gobe insha allah zatazo
Da farko zee taso hanata zuwa amma saita nace akan saitazo Hakan sukayi sallama bayan tace zee ta turo mata address dinsu
Kallon Ummu batool zee tayi tana Tambayar ta tura mata din
Cewa tayi ta tura mata din tunda zuminci zatazo babu komai taga alamun suna da kirki sosai kuma kamar basuda matsala
Da Hakan ta turama Aysha address din suka koma dakinsu da ita da batool suna cigaba da firar kirkin ummie da Aysha
Sai gashi washegarin kamar yadda tace zatazo tazo din bayan sallar la'asar
Sosai zee tayi murnar ganinta kuma akayimata tarbar mutunci
Sosai suka gaisa da Ummu batool sannan suka wuce daita sama dakinsu zee
Batool tunda taga Aysha taji itama ta kwanta mata a rai lokaci guda don ko ba'afada ba kallo daya zakayi mata kasan tanada nutsuwa sosai
Anan zee tayi introducing din batool agareta suka kuma gaisa cikin mutuntawa sannan zee tafito ta sauko qasa don samarwa qawar tata abin ta6awa.
Lokacin da ta dawo saita tarar firarsu ma sukeyi abunsu saita ajiye masu abin data kawo tana musu bismillah
Tare duk suka sauko qasa kan dan carpet din data shinfida masu suka shiga cin abincin suna fira
"uhmm, abincin nan yayi dadi, daga ji nasan ummie na ta girka" inji Aysha tana lumshe idanunta alamun abincin na kaimata karo
"to ni na dafa, wannan dakike ganinta babu abinda ta iya sai a girka ta shaqe plate taci, duk abincin dazaki shigo gidan nan kici ko agaba ne ni na girka shi" inji batool
Dariya duk sukayi
"kai nidai ban yarda ba, ummie ta tafi kama da wanda ta girka abincin nan"
Dariya suka sakeyi batool tace
"wato har kammani ke akwai kenan na wanda ya girka abinci?"
"qwarai kuwa, da kin kalli abincin kika kalli wanda ya girka sai kiga sunyi matching"
Dariya suka sake sawa
Haka sukaita firarsu har suka gama cin abincin aka kauda abubbuwan dasuka 6ata suka koma kan gado aka shiga fira
"ummie, wlh jiya dake na kwana arai, tsabar yadda nasa abin a raina sai gashi harda su mafarki wai yaya yaqara sawa an kamaki"
Dariya sukayi
"kincika sa abu arai wlh" inji zee tana Dariya
Itama dariyar tayi tace
"wlh, ai haka nake. Gashi dama halin yayan nawa nasani, haka yake bayada yarda kona diss, haka yake tun yana qaramin shi.
Can you believe ko aboki qwara daya baya dashi?
Ummie tace yafara wannan halin ne tun bayan rasuwar dan uwanshi"
Dan Wara idanu zee da batool sukayi cikin hadin baki sukace
"tun rasuwar dan uwanshi?"
Murmushi Aysha tadanyi
"ummie, ban gayamaki mu asalin wayeba, na baki tarihina just briefly batareda na fadamaki wasu abubbuwa ba
Kinsan ko waye yaya na?
Kinsan companies din nurul haqq masu rassa daban daban?"
Batool tayi saurin amsawa
"waye besan nurul haqq ba? Saidai idan ba a dubai yake ba, itama kanta zee datazo jiya jiyan nan tasan wasu wuraren, sis wannan park din damukaje ranan? To shima na nurul haqq ne" tafada tana kallon zee
Zee data dauki hasken abinda batool ke nufi saita Kada kai cikin mammaki tace
"natuna, koba wannan mai girman ba? Mai Hade da zoo"
"shi... Na yayana ne" inji Aysha
Duk Wara idanu sukayi sosai cikin mammaki dukda sunsan komai pretending ne kawai
"yayana ne mammalakin duk wani company na nurul haqq, mussadiq al-hassan"
"ya sallam! Kina nufin ke qanwar mai wadannan wuraren ce?" inji batool cikin kaduwa, yadda take acting din yayi mugun hawa kamar dama yau tafara sani
Murmushi Aysha tayi tace
"eh, duk wadannan wuraren mallakin yaya mussadiq ne, Saidai baya bayyana identity dinshi kamar yadda muma yake hanamu bayyana namu duk don maqiya wai.
Yanada saurin zargi da rashin yarda shiyasa shi kanshi idan ba saninshi kayi ba baka gane babban dan kasuwa ne kuma shi keda wadannan wuraren.
Na ta6a baki labarin cewa twins ne ko?" tafada tana kallon zee dake kallonta Tundazu babu kyaftawa
Kada kai zee tayi saurin yi
"eh kika ce dayan ya rasu ko?"
Kada kai itama Aysha tayi
"eh haka nace amma a zahirin Gaskiya ba mutuwa yayi ba"
Ji zee tayi kamar an kwada mata guduma akai
"b..be mutu ba?" tafada cikin rawar murya itakau batool tama kasa cewa komai sai kallon Ayshar datakeyi
"to ya mutun za'ace amma ba mutuwar allah da annabi ba.. Ina nufin kasheshi akayi"
Wannan karon tashin hankalin zee qarara yafito a fuskarta
"kasheshi akai? Waya kasheshi?"
Da Aysha mai lura ce data lura da yadda zee ta tashi hankalinta fiyeda yadda ya kamata data dora ayar tambaya akan Hakan
"eh, saceshi akayi daga baya aka kasheshi"
"innallilahi waina ilaihi rajiun" zee da batool suka fada atare hankalinsu a tashe
"nima ummie ke bani labari don a lokacin ko haihuwata ba'ayi ba akwai dai qaramin cikina wanda ba'ama san dashi ba.
Mujaheed shine Hassan mussadiq kuma Hussaini, yan biyu ne masu tsananin kama da juna don ummie ma kanta takan kasa banbancesu wani lokacin
Saida suka dan fara girma aka fara samun signs da ake banbancesu dashi
Nafarko shine dimple dinsu.
Mujaheed nada dimple a tsakiyar gemu kamar dai nawa don ance shi na biyo while mussadiq nashi a kumatun haggu yake
Na biyu kuma yanayin qiriniyarsu.
Mussadiq yafi Mujaheed qiriniya nesa ba kusa ba don Saida mussadiq yariga mujaheed fara rarrafe harma tafiya ma
Kamar ummie ke cewa mujaheed yanada sanyi sosai sa6anin mussadiq dake da qiriniya don Mafi yawancin lokuta inda ta ajiye mujaheed nan zatazo ta dauke shi shikau mussadiq daka ajiye shi zai qara gaba yaje yaita 6ana
Haka ma yara basa qwarar mussadiq don shi ba'a sashi kuka Saidai yasa Yayinda shikuma mujaheed babu ruwanshi sai yara suyita bugunshi baya ramawa
Saidai kuma mujaheed yafi mussadiq juriya da haquri don da wuya yayi kuka don cewa tayi ko rashin lafiya yake baya irin rigimar da mussadiq keyi Idan shine bashi da lafiya, Saidai shirunshi da sanyinshi suqara yawa, ko cikin yara yashiga masu qiriniya suna qwararshi baya kuka duk abinda zasuyi mashi idan kaga yayi kuka to abin yakai qurewa
Shiyasa ko a soyayyar dasuke masu ta mujaheed tafi don shi bayan soyayya harda tausayi don yaro mai sanyi dama yafi soyuwa a zuqatan iyaye ko don tausayawa yanayinshi
Abin yafaru ne ranar washegarin wata babbar sallah, lokacin suna saudiya don dama can ne asalinmu daga baya muka dawo nan
Kamar yadda al'adar wannan ahalin take dik washegarin sallah walau babba ko qarama ana haduwa a babban family house dinmu inda anan kowa da kowa na dangi, qwansu da kwarkwatan su saisun hallarta harda wadanda ba garin suke ba
Ana haduwa agidan don taya murnar sallah da sada zuminci
To suma haka suka shirya ranar tunda safe Abbanmu yakai ummie da twins dinta
Lokacin Abbanmu dan kasuwa ne wanda yayi suna sosai a madina a harkar kasuwancinshi kuma a lokacin shima ana iya sashi a sahun masu kudin family dinmu
Kamar yadda ummie ta gayamin tace tunda sukaje gidan Hassan wato mujaheed ya liqemata duk inda yayi yana maqale gashi ranar sanyinshi yaqara yawa fiyeda yadda yake da
Sai tayi tunanin ko bayada lafiya ne dukda jikinshi babu zafi
Saita sa6eshi ta goyashi ta cigaba da aikinta dashi a baya
Haka taita yawo dashi abaya har bayan zuhr don Koda zatayi sallah ma Saidai ta ajiye shi kusada ita yana kallonta har tagama sannan ya rarrafo yadawo kusada ita ya sake lafewa ajikinta
Ganin wannan lauye lauyen nashi yafara yawa yasa tasa aka siyomashi maganin ciwon kai don aganinta qila bejin dadi ne
Tabashi yasha ta maida shi baya ta goya har yayi barci ma
Be farka ba sai wajajen la'asar, tabashi abinci yaci sannan cikin gwarancinshi ya nuna wa ummie zaije wajen mussadiq da tunda suka shigo gidan yake cikin yara suna wasa
Sawa tayi akaishi wajensu din dukda bata cika son yana shiga yaraba saboda qwararshi da akeyi saikuma tayi tunanin ai gwara ya saba qila da haka da haka shima zai iya ramawa idan akayi mashi
Nan ta cigaba da hidimarta cikin dangi anata kai kawo cikin annushuwa da nishadi
Can wajajen bayan la'asar kadan aka fara jin hayaniya a tsakar gidan
Tun suna ji sama sama har abin yafara yawa Hakan yasasu fitowa ciki harda ummie
Abinda ummie tagani yayi matuqar girgizata don Saida jiri yakusan kadata ba don anyi saurin tareta ba
Mussadiq tagani jina jina jikinshi duk ciwo ga kayanshi sunyi futu futu harda yagewa a wasu wuraren
Da gudu suka nufeshi cikin tashin hankali don anason riqeshi amma sai fizge fizge yakeyi
Da gudu ummie ta qarasa gabanshi ta jayoshi ajikinta tana kiran sunanshi cikin kuka
Jin muryar ummie yasa yabar fizge fizgen saiya dago ya kalleta saikuma luuu yafada ajikinta asume.
Kwatanta tashin hankalin da aka shiga a lokacin 6ata baki ne
Nan take aka shiga kiran iyayen maza dasuka fita ta waya cikin qanqanin lokaci saigasu sun duro gidan ciki harda Abbanmu
Lokacin gidan banda koke2 babu abinda akeyi
Cikin gaggawa aka wuce dashi asibiti cikin masu zuwa harda Umminmu
Nan take likitoci suka kar6eshi aka shiga bashi taimakon gaggawa
Saida aka kusan awa sannan akasamu aka shawo kan mussadiq numfashinshi yadawo normal yakuma samu barci sanadiyar allurar barci da akayi mashi
Sai a lokacin likitocin suka fito wajensu ummie da suka kasa tsaye suka kasa zaune nan suka kwantar masu da hankali akan komai ya daidaita yama samu barci
Nan kowanne ya sauke Ajiyar zuciya na jindadin Hakan Saidai ashe zaune bata qareba
Tafiyar su likitocin keda wuya sai ummie da sai a lokacin tasamu zama taqara zabura ta miqe tsaye kamar wanda aka tsikara
Duk sai aka kalleta ana Tambayar lafiya
'mujaheed... Ina mujaheed?'
Nan kowa ya tuna dashi don tashin hankali yasa anma manta dashi
Tofa nan aiki sabo yafara don duk inda aka duba inda akasan za'a ganshi dama inda bazai iya shiga ba Amma babu shi
Babu inda ba'a duba ba a fadin gidan lungu da saqo amma babu mujaheed babu alamunshi
Nanfa hankali ya tashi ba ko kadan ba, tsakanin ummie da Abba aka rasa wanda yafi wani rikicewa
Duk fadin unguwar dama wajenta babu inda ba'a duba ba Amma babu mujaheed
Ummie har qaramin hauka saida tayi suma kau tayishi babu iyaka
Wasa wasa har dare babu mujaheed
Izuwa lokacin an yada cigiya gidajen t.v da radio amma shiru
Daren ranar babu wanda ya runtsa a familynmu, ranar murna ta chanza lokaci guda zuwa ta baqinciki, abu goma da ashirin, ga mussadiq a asibiti ga mujaheed ya 6ata.
Washegari ma dasa neman da akeyi akayi inda aka baza jami'an tsaro sosai wajen nemanshi
Ummie a lokacin bata ganuwa don itama dole qarshe aka bata gado a lokacin ma aka san da cikina.
Wasa wasa kwana daya yakoma biyu yakoma uku amma still babu mujaheed, Izuwa lokacin ummie da Abba sunzama abin tausayi ba kamar ummie don ita abin yafi ta6ata, babu abinda take Tunawa sai maqale mata dayaitayi tun safe, datasanin barinshi fitar datayi yafi cikin kwando Saidai komai muqaddari ne Daga allah, dole allah ya rubuta Hakan zai faru"
Dakatawa tayi ta dago ta kalli su zee da izuwa lokacin fuskarsu sunyi sha6e2 da hawaye sai a lokacin itama taji dumi dumin nata a fuskarta Hakan yasa tasa bayan hannu ta sharesu dukda Hakan ba yana nufin wasu bazasu sake zubowa ba
"A kwana na hudu aka bugo ma Abba waya da number da akayi hiding dinta.
Yana ganinta jikinshi yabashi kiran yashafi mujaheed dinshi
Hannu na rawa ya daga yana jin zuciyarshi kamar zata faso qirji
Kamar yadda yayi tunani Hakan ne don wadanda suka sace mujaheed ne suka bugo suna buqatar kudin fansa inhar suna son a sakomasu dansu.
Da farko Abba qin yarda yayi yace dole saiya ji muryar danshi yakuma tabbatar shine sannan
Aikau sai suka bashi saiga muryar mujaheed radam yana kiran Abba da ummie cikin kuka
Sosai hankalin Abba yayi mugun tashi nan take shima hawaye suka kawo mashi a idanu
Nan take yashiga magiyar don Allah suyi hqr karsu cutar mashi da danshi zai basu duk abinda sukeso
Jin Hakan yasa suka ce zasu sake shi amma sai sun bada kudin fansa
Nan suka yankama Abba kudin dazai bayar na fitar hankali
Abba yaso neman ragi amma firr suka qiya sukace ya za6a ko kudi ko mujaheed
Nan kuma suka jamashi kunne akan karya saki yasako jami'an tsaro aciki don sakosu aciki daidai yake da mutuwar mujaheed, suka kuma ce zasu sake kira don gayamasu inda zasu kai kudin.
Sosai hankalin ahalinmu yasake tashi
Inda duk wanda yaji adadin kudin dasuka nema saiya girgiza
Saidai Abba a shirye yake ya bada dukkan abinda ya mallaka don dawowar danshi Mafi soyuwa a gareshi
A lokacin mussadiq ya dade da farfadowa Saidai wata irin rashin lafiya yake mai zafin gaske ga ciwukkanshi da basu ida warkewa ba kullum cikin kukan ina mujaheed yake abinci ma Dakyar yake ci.
Ummie kuwa tafi kowa zama abin tausayi kodayaushe ciki kuka take duk tabi takoma kamar ba ita ba ga tashin hankali ga ciki.
Wasu daga cikin family dinmu suka bada shawarar sanyo jami'an tsaro acikin case din amma firr Abba yaqi yarda don babu abinda zaisa yayi tempering da rayuwar danshi.
Haka ya hada kudin nan cass family dinsu suma duk sun kawo gudunmawa aka hada kudadden ana jiran suqara bugowa don dole saisun bugo tunda da hidden number suka bugo wancan karon
Sai bayan kwana biyu suka bugo suna Tambayar an hada kudin, baki na rawa Abba ya amsa da eh sai suka fadamashi inda xa'akai
Roqonsu yashigayi cikin magiya kan suqara bashi mujaheed yaji Muryarshi
Babu musu aka bashi
'Abba' mujaheed yafada cikin mugun sanyi
'Abba... Ummie'
Kasa controlling kanshi Abba yayi Saida yayi hawaye
'mujaheed bunnaya, kana lafiya?' yafada cikin rawar murya
'Abba?' mujaheed yasake fada
'kayi hqr zaka dawo kaji? Abba zaizo ya daukeka' inji Abba hawaye na gudu sosai a kumatunshi
'muccadik' mujaheed yaqara fada cikin sanyin murya
'mussadiq nanan lfy, shima zaizo kaji? Kaji dana'
Daga Hakan sai yaji muryar daya daga cikin 6arayin na cewa ya isa haka nan tunda sunyi maganar
Nan yasake gayamasu inda zasu kai kudin da lokacin dazasu kai dakuma qara yimasu gargadi akan karsu sake su sako jami'an tsaro aciki idan ba Haka ba a bakin ran dansu.
Nan aka shirya komai Abba da kanshi yaje bada kudin
Kuma ya ajiyesu inda suka ce sannan yatafi
Saidai shiru shiru basu bugo ba sukace ga inda zasuje su dauki yaron ba
Tun suna jira har hankalinsu yafara tashi da jin yadda shirun yayi yawa
Sai a kwana na biyu da bada kudin sannan aka bugamashi waya, a lokacin saura qiris ya zauce
Nan aka gayamashi inda zaije ya dauki mujaheed cikin wata ash din mota, zasu bar motar a bude dayaje kawai ya bude ya fiddashi ya tafi dashi
Cikin jindadi Abba yayi shirin tafiya, jikinshi har rawa yakeyi don har jiri jiri yakeji na neman dibanshi
Dashi da Hussaininshi suka tafi dauko shi inda akace din
Wuri ne da sai anfara fita daga gari ma, babu gidaje a wajen sai busassun ciyayi don lokacin rani ne
Tun daga nesa suka hango motar ash colour din da akace gefen titi.
Parking Abba yasa Hussaininshi yi tun kafin su qarasa suka fito da sauri suka nufi kofar
Saidai suna kaiwa inda tsakaninsu da motar baya wuce taqi ashirin sukayi mugun ganin da basu ta6a irinshi ba
Motar da akace masu mujaheed na ciki ta tashi da wuta๐ฅ a gaban idanunsu.."โ๏ธ
Ummin fasihu ๐ง๐ปโโ๏ธ?
8/2/21, 9:42 PM - Buhainat๐: *๐๐ปโโ๏ธDEEN ๐๐ปโโ๏ธ?*
*068*
*THE UNVEIL 2*
_๐ni yau ido rufe zanma yi typing saboda kunyar wasu nakeji ๐๐_
Toshe baki zee tayi idanunta awaje tana kallon Aysha da kuka yafara cin qarfinta
"a..agaban idanunsu motar taita ci da wuta... Abbanmu ahakan yaso qarasawa ga motar amma Hussaininshi da tsirarun mutanen da wutar tajawo hankalinsu suka hanashi ta hanyar rirriqeshi.
And..and before his very eyes, beloved son dinshi ya qone qurmus dashi da mot..."
Kasa idawa tayi saboda kukan dayaci qarfinta.
Kamar hadin baki da zee da batool suka rarrafa wajenta suka rungumeta suka hada kai waje guda suna kuka kamar ransu zai fita
Sun dauki tsawon lokaci ahakan anrasa wanda zai rarrashi wani
Can Aysha ta dago da jajjayen idanunta tana kallon su zee da har lokacin kukan sukeyi
"ba acikin hayyacinshi ba aka maido Abbanmu gida, daga nan akayi asibiti dashi.
Itama ummie najin abinda yafaru ta yanke jiki ta fadi, kan kace me jini ya 6allemata
Itama kamar abba sai aka kwasheta sai asibiti.
Kamar hadin baki shima mussadiq jikinshi ya rikice yashiga convulsing, numfashi ma Dakyar yake fizgoshi daga huhunshi.
Iya tashin hankali wannan ahalin sun shigeshi a lokacin.
Nima don Allah yayi zanzo duniyar shiyasa cikin ikon allah aka shawo kan bleeding din da ummie keyi
Lokaci guda happy family dinmu ya tashi daga happy family zuwa akasinshi
Abba tunda ya kwanta gadon asibiti be qara tashi ba
Saida yayi wata daya a kwance sannan watarana yatafi cikin barcinshi.
Yatafi yabi danshi yabar matarshi abar qaunarshi da cikin dake jikinta dakuma danshi da har lokacin beda cikkaken lafiya.
Haka ummie tayi takabarshi, ga ciki ga ciwo don tun lokacin da ta yanke jiki ta fadi lokacin da aka dawomata da labarin mutuwar mujaheed ta hadu da ciwon hawan jini.
Haka tayi takabarshi tagama ta cigaba da zama gidanmu tareda mussadiq da shima izuwa lokacin ya warware sosai Saidai kwata2 ya chanza daga mussadiq din da aka sani.
Mussadiq mai qiriniya mai surutu yakoma so silent.
Yana iya yini batareda ya furta ko kalma daya ba, ga wata rashin yarda da ya bijiro daita lokaci guda.
Baya yarda wani ya ra6eshi ko kadan Duk yadda kau kake dashi.
Ko baqi ummie tayi walau family dinmu ko wasu daban baya yarda yabar jikin ummie duk inda zata yana maqale daita.
Idan baqin zasu shekara suna mashi magana ko kallo bazasu isheshi ba
Idan kuma sukace zasu daukeshi da tsiya sai ya fasa ihu kamar wanda ake yankawa Hakan yasa duk masu qulafucin daukarshi suka haqura Saidai gani daga nesa wato ajikin ummie
Da farko ummie tayi tunanin yarinta ne kuma qila harda abinda yagani ranar da abin yafaru tunda tana kyautata zaton kome yafaru a ranar mussadiq yagani tunda da alamu ma kamar shi kuftowa yayi Saidai a lokacin ko an tambayeshi bazai iya bada amsa ba don qarami ne sosai magana ma bata gama nuna a bakinshi ba
Hakan yasa take yimashi addu'o'i sosai da rubutun sha duk na dangana wanda zai kuma taimaka mashi wajen manta abinda ya faru din
Saidai abin yafara bata tsoro ne
All Chapters
Chapter 1
Chapter 2
Chapter 3
Chapter 4
Chapter 5
Chapter 6
Chapter 7
Chapter 8
Chapter 9
Chapter 10
Chapter 11
Chapter 12
Chapter 13
Chapter 14
Chapter 15
Chapter 16
Chapter 17
Chapter 18
Chapter 19
Chapter 20
Chapter 21
Chapter 22
Chapter 23
Chapter 24
Chapter 25
Chapter 26
Chapter 27
Chapter 28
Chapter 29
Chapter 30
Chapter 31
Chapter 32
Chapter 33
Chapter 34
Chapter 35
Chapter 36
Chapter 37
Chapter 38
Chapter 39
Chapter 40
Chapter 41
Chapter 42
Chapter 43
Chapter 44
Chapter 45
Chapter 46
Chapter 47
Chapter 48
Chapter 49
Chapter 50
Chapter 51
Chapter 52
Chapter 53
Chapter 54
Chapter 55
Chapter 56
Chapter 57
Chapter 58
Chapter 59
Chapter 60
Chapter 61
Chapter 62
Chapter 63
Chapter 64
Chapter 65
Chapter 66
Chapter 67
Chapter 68
Chapter 69
Chapter 70
Chapter 71
Chapter 72
Chapter 73
Chapter 74
Chapter 75
Chapter 76
Chapter 77
Chapter 78
Chapter 79
Chapter 80
Chapter 81
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 55 Chapter of 81