tayi tana murmushi
"zuwa mukayi daukar gimbiyar, mun samu Dakyar an sahale mana muzo" inji saurayin wanda ga dukkan alamu yanada faran2 sosai
Dan hararar shi Feenah tayi tana dan 6ata fuska cikin salo
Murmushi zee tayi tace
"aikau dai yaya, kuma dama kun rabu da shigowa k.t kunga har zuminci sai ayi"
"ashe kin gane, yar daughter mu" injishi yana Dariya
"ya karatu?"
"alhamdullilah yaya, ya aiki"
"gashinan munata fama wlh, wannan abokin nawa fa?" yafada yana kallon Deen dake baya yana sauraronsu
Sai a lokacin Deen ya dago fuskarta dauke da murmushi yayi musu sallama
Atare suka amsa suna maida mashi martanin murmushin
"Yaya Auwal, Aunty Feenah meet my course mate Deen, Deen wannan itace Aunty ta sai yayana"
Fuska dauke da murmushi ya gaidasu calmly sukuma suka amsa suma murmushi a fuskarsu sai kallonshi suke
"ya karatu, fatan za'a qara tighting belt"
"insha allah brother" inji Deen
"to allah ya taimaka, daughter mu zamu wuce" inji Auwal yana dan sunkuyawa ya ciro ledar dayayi mata siyayya ya miqo mata
"gashi Ayi manage"
"kai yaya, harda hidima? Thanks so much" inji zee tana amsa
"Don't mention" yafada yana komawa cikin motar
"to sai munyi waya ko?" inji Feenah tana dan kashe mata ido alamun akwai labari
"to Aunty a gaida kowa da kowa, ace nayi missing dinsu"
"eh, tunda ni yar aikenki ce ba?" tafada itama tana shigewa ta zauna
"pleeease" tafada cikin marairaicewa
"ok amma ba don halinki ba" tafada tana harararta
"eh babu komai" inji zee tana maida mata kofar ta rufe
Tada motar Auwal yayi nan suka shiga daga ma juna hannu harda Deen, Auwal yaja motar suka tafi
Ajiyar zuciya zee ta sauke sannan tajuyo ta kalli Deen
"how was that?"
"nice, they're so nice"
Murmushi kawai tayi suka juya suka koma ciki
Sallah duk suka wuce suka farayi sannan dik suka shiga class kasancewar suna da lecture a lokacin
Saida suka fito sannan suka zauna suka ci kayan da Auwal ya ba zee dukda Deen be wani ci sosai ba
Suna haka akazo daukar zee sukayi sallama ta tafi sannan shima ya fito ya samu abin hawa shima ya tafi
***
*10:15pm*
Kwance zee take kan gado wayarta a hannunta tana danne danne sai murmushi take akai akai da alamun abinda takeyi da ita na bata sugar
"hmm Aunty Feenah, wannan rudewa haka?" ta tura
Can sai message yashigo kamar haka
"wlh zee gayen yayi ๐๐ป wai kinga sadda kuka jero? Yadda kikasan romeo and his juliet๐"
"๐๐ dama kin sansu a kammani ashe?"
"baki da labari ashe ๐คจ"
"banida โน๏ธ"
"to saiki sani tun yau ๐ ashe dai dama da walakin goro a miya ๐ค haba dole ai ki rude ki gigice, taga dan fari kyakyawa ๐"
"kai Aunty, duk kyawunshi ya kaini๐"
"๐ณwa? Ke? ๐คฎ๐คฎ๐คฎ"
"๐ฉ๐ฉ๐ฉ"
"kyaji dashi ๐, Gaskiya maganar Gaskiya kun dace, ya kamata kuyi ku daidaita junanku hakanan, Ca6 you'll make a perfect match, na so naga 'ya'yanku๐ฅฐ"
"kai Aunty ๐๐๐"
"munafuka, anaso ana kaiwa market ๐"
"kai Aunty ๐ซ"
"yanzu dai kuyi ku daidaita junanku musha biki๐๐"
"kai Aunty ๐ nifa yarinya ce haryanzu ๐"
"sannu jaririya ๐ ai naga ko yayeki ba'ayi ba"
"๐๐๐"
"yar rainin sense kawai, ki gaida yaya da daddy, ni zan sauka, barci ๐ฅฑ"
"tun yanzu ๐ณ yau babu wayar ๐๐ปโค๏ธ ne?"
"ungo nan ๐๐ป๐ก"
Dariya zee tayi a zahiri ta turamata
"๐๐ปโโ๏ธ๐๐ปโโ๏ธ๐๐ปโโ"
Sannan ta rufe datarta ta koma ta kwanta rigingine ta jawo pillow ta rungume
Tunawa tayi da dramarsu ta dazu na koyan waqa
Murmushi mai sauti tayi ta murgina tsakiyar gadon ta rungume pillon gamm a jikinta
_*DEEN*_ tafada cikin shauqi da begen mammalakin sunan... โ๏ธ
Ummin fasihu ๐ง๐ปโโ๏ธ?
8/2/21, 9:36 PM - Buhainat๐: *๐๐ปโโ๏ธDEEN ๐๐ปโโ๏ธ?*
*039*
*SIRRIN ZUCIYA โค๏ธ*
Akwana a tashi gashi har su zee sun qulla wata kusan biyu da resuming school
Komai yana tafiya masu daidai kuma sosai suka maida hankalinsu akan karatunsu musanmman ma Deen dake final year
Yana da burika dayawa dayake son cikawa a duniya ciki harda inganta rayuwarsu shi da kaka, most especially ma kaka saboda ita ta tsaya mashi kai da fata wajen karatunshi don kusan dik abinda tasamu nan suke tafiya saboda ta yarda karatu shine gatan mutum kuma ko ba dade ko ba jima zasuci gajiyar shi shiyasa bata wasa da abinda ya shafi karatunshi komai tana iya badawa muddin akan karatunshi ne
Shiyasa shima a nashi bangaren be sanyo wasa ko shiririta a bangaren karatunshi
Yanada burin zama wani abu a duniya ta dalilinshi yadda zai tallafi rayuwar kaka kamar yadda ta tallafi nashi
A 6angaren zee kuwa jiya-i-yau.
Haryanzu tana nan tana dakon soyayyar shi a zuciyarta
Kullum sonshi qara hauhawa yakeyi a zuciyarta kamar yadda kullum shaquwarsu ke qara qarfi
Sosai take azabtuwa da soyayyar shi datayi mata bake bake a zuciya Saidai haryanzu shiru a ta bangaren Deen Saidai akwai signs da symptoms na soyayyarta dayake nunawa amma that wasn't enough, so take ya furta mata, abinda taga bashi da niyyar yi kwata2.
A bangaren Feenah kau biki sai qara gabatowa yake don yanzu bekai wata daya ba, ata kowanne bangare shirye shiryen bikin akeyi musanmman ma bangaren Amaryar kasancewar itace auta shiyasa ata koina ake nuna mata gata.
***
Yau asabar, babu school don haka yini tayi a gida tana hutu
Fitowa tayi daga dakinta dauke da wani dan bowl din tangaran wanda tagama shan fruit salad cikinshi ta fara tako stairs don sauka qasa ta maida
Muryar mummy da daddy taji suna magana da alamu fira sukeyi
Murmushi tayi ta cigaba da saukowa Saidai maganar dataji mummy tayi yasa tafara slowing tafiyarta
"Gaskiya ne, nima dama nayi wannan tunanin, kaga Feenah tun tana makaranta ta tsaida miji, gab da zata gama kuma akasaka rana kaga yanzu duka watanta biyu da gamawa nan da yan satittika asha biki, me yafi wannan? Wlh zaman ba yi bane gwara da angama Ayi auren don shine mutuncin ko wacce 'ya mace dama namiji ma
Kuma idan akace sai an gama karatun sannan za'a samu mijin yaushe za'ayi kenan? Gwara tun yanzu asa sanwar abin bare kai dama ita kenan daya, kowa ya dauko idanu ya zuba maka yaga yadda zakayi
Ni sai inga Hakan shi yafi kawai"
Tsayawa zee tayi takasa qarasowa tana jujjuya maganar mummy cikin son gane inda ta dosa
Daddy taji yana cewa
"nima haka nagani wlh Maimuna, gwara afara tun yanzu. Gashi yaron yanada tarbiyya don nasanshi sosai, muna Yawan hadewa idan naje gidansu ko kuma wasu lokutan idan sunzo tare da baban.
Kuma bayan wannan kinga zumunci zai qara qulluwa, amintarmu da babanshi zai qara qarfi kuma bazanyi fargabar wani abu yasamu diyata ba don ko babu ni a duniya nasan Alhaji Abubakar mai iya riqe amanar iyalaina ne"
Kan zee yaqara kullewa
Tabbas tasan Alhaji Abubakar, babban aminin daddy ne kuma abokin kasuwancinshi.
Sau dayawa shida iyalanshi suna zuwa nan ziyara suma suna zuwa gidanshi Saidai zee bata cika son zuwa ba don yaran gidan mugun yan zafin kai ne, girman kansu yayi over shiyasa basa shiri don kamar yadda suke jinsu su wasu ne haka itama ke jin kanta shiyasa basa shiri sam
"wlh kam, to yanzu yakusan dawowa ne?" inji mummy
"eh, ga yadda muka tattauna dashi Alhaji Abubakar din cewa yayi yagama komai kawai sai yan ide ide, nan da wata daya nasan yadawo, to kinga me ake jira? Aiki dama akwai shi available shi dama yake jira, kinga a lokacin saisu fahimci juna da tashiga level 400 din sai asaka rana tana gamawa sai asha biki, ko yaya kika gani?"
"Gaskiya Hakan yayi Alhaji, kaga zamu sauke dukkan nauyinta akanmu, ga ilimi mun bata kuma mun aurar daita a lokacin daya dace, dama ni na matsu naga anyi Hakan saboda ita 'ya mace ce kuma duk inda hankalin iyayen 'ya mace yake to bazai ta6a kwantawa ba sai sunga sun rabu daita lafiya ta hanyar aurar daita. Allah yasa Hakan shi yafi alhairi kuma allah ya daidaita su kasan diyar taga yar tutsu ce wani sa'in"
Dariya daddy yayi
"ai karki damu, insha allah zaiyi mata 100%, nifa nasan taste din diyata, nasan abinda zataso da abinda bazata so ba kuma am betting you, zaki gani. Da hannu bibbiyu zata amshi tayin bari dai lokacin yayi"
"to allah yasa, ka dai san ba'a shaidar 'ya'yan yanzu, bare wannan diyar taka mai shegen ruwan ido, kana ganin yadda masu neman ta ke zuwa take musu wulaqanci, duk wanda yazo saita nemi makusanshi ta kushe, nayi fadan nayi nasihar a banza"
Dariya daddy yasake yi
"ai jewel din kenan, ita allura ce cikin ruwa, mai rabo ka dauka kuma *Asad* shine mai rabon don dama don shi taqi sauraron kowa, nasan diyata kuma nasan abinda takeso don hakama yasa nasan da Asad zasu dace, kuma zaki gani"
"to allah ya tabbatar da alhairi ai haka akeso" inji mummy cikin farinciki
"hmm kaji su Hajiya Maimuna an kusa zama in-law" inji Alhaji cikin tsokana
Dariya tayi tana juya idanu wanda a wurinta zee ta gado nata
"Ato, kana black stomach ne?"
"A'a, namafi kowa white stomach" yafada shima yana kwaikwayon juya idanun datayi
Dariya duk sukayi mummy na cewa
"to allah dai ya tabbatar mana da alhairi"
"Amin summa amin" inji daddy
Ahankali zee ta juya tafara taka stairs din don komawa batareda tayi motsin dazasu lura daita ba
Bude kofar ta tayi ta shiga sannan ta rufo ta taho ahankali kamar marar lakka ta ajiye bowl din hannunta saman bedside locker ta zauna ahankali gefen gadonta
Shiru tayi tana kallon Kaffafuwanta dake bisa dan carpet din dake gaban gadon kamar anan zataga amsoshin tambayoyin dake tsere a kwalwarta
*kinga a lokacin saisu fahimci juna, da tashiga level 400 sai asaka rana tana gamawa asha biki*
Maganar daddy ce tadawo mata a qwanya
*nasan abinda takeso don hakama yasa nasan da Asad zasu dace*
Wai wa yake magana akai? Waye kuma Asad? Wacece zasu dace dashi?
Hadiye wasu yawu dasuka taru a maqoshinta tayi
Me suke nufi? Tadai san basuda wata 'ya bayan ita kuma taji suna maganar sauke nauyi ta hanyar aurar da 'yar su
_Ni kenan?_
Sai kuma ta girgiza kai
_no this is impossible!_
_it can't be_
Waye wani Asad kuma? Suna ko gishiri babu.
Ca6 dasake wlh, yanzu yanzu ba sai anjima ba zataje tagayawa daddy don karma ya wahalar da d'an mutane wajen zuwa don Hakan bazai ta6a yiwuwa ba don tanada wanda takeso
Zumbur tayi tasake tashi ta nufi kofa
Harta dora hannu akan handle saita kuma dakata
Idan taje me zatace mashi?
"daddy Gaskiya ni banason wannan Asad din, inada wanda nakeso"
Sai yace
"waye?"
Me zatace?
Deen? Deen zata ambata?
Mutumin da har yanzu batasan matsayinta ba a gareshi?
Idan tace Deen din ne yakuma nemi ya ganshi me zatace?
Cewa zatayi ita ke sonshi? Ko cewa zatayi jiranshi take taji matsayinta a wajenshi?
Ahankali ta saki handle din
Tabbas tasan daddy, takuma san idan yayi farinciki to yaga tayi ne
Idan tace mashi bata sonshi bazai gardama mata ba don tasan bazai ta6a yimata dole ba
Amma shi wanda zatayi Hakan akanshi tanada tabbaci akanshi?
Tanada tabbacin yana sonta?
Ahankali takoma da baya2 ta lulubi stool din dressing mirror dinta ta zauna akai
Tasan idan tace bata son wanda suke magana akai zasu nemi sanin wa takeso, idan tace babu bazasu yarda ba musanmman mummy da dama burinta taga tayi aure kuma ga yadda taga ta nuna amincewarta sosai akan wannan maganar da wuya ta barta ta tafi a iska
Idan kuma tace tana da wanda takeso zasu so sanin ko waye, idan ta ambaci Deen zasu so jin ta bakinshi, idan kuma sukaji cewa bema san da maganar ba me kenan?
Hannuwa takai bisa kanta ta cusa yatsunta cikin lallausan gashinta tana maidasu baya sannan tayi interlocking din yatsunta bisa wuya
Anzo wajen!
Anzo ga6ar da take gudu
Lumshe idanuwanta tayi ahankali tana jin baqinciki na mammaye zuciyarta
Har zuwa yaushe? Har zuwa yaushe zata cigaba da jiran shi? Har zuwa yaushe zata cigaba da dakon soyayyarshi? Har zuwa yaushe zata cigaba da wahala
Ranta taji ya 6aci, zuciyarta ta dagule, jitayi kamar taita ihu don takaici.
Dama tasani, wannan slowness din nashi wahala zai bata, dama tasan saita fara zaucewa sannan zai bayyana mata sirrin zuciyarshi.
Haka ta qarashe Wunin ranar rai a matuqar dagule
Baqinciki, 6acin rai, takaici duk sun taru sun tokaremata qirji wanda Hakan yasa taji babu abinda keyimata dadi a duniyar nan
Haka ta qarashe weekend din wannan satin cikin cinkushewar zuciya, sosai takejin haushin Deen har cikin zuciya, jitake kamar ta sameshi taita duka ko zata huce shiyasa Koda yakirata da marece ranar lahadi kamar yadda yasaba sai bata daga ba sai tasa number shi yadda idan ya bugo zaiga line busy
Da daddare ma ta dade batayi barci ba kamar yadda yake a al'adarta indai akwai abu a ranta yakan hanata barcin kirki
Haka taita juyi kafin tasamu dakyar wani barci marar dadi ya dauketa
*WASHEGARI*
Zaune take a library wani qaton textbook a gabanta tana budewa ahankali page by page
A zahiri sai kayi tunanin wani abin kirki takeyi amma maganar Gaskiya ita kanta batasan me take dubawa ba, hankalinta da tunaninta yayi wani wuri daban
Deen ne yashigo library din, waige waige yadan farayi na ganin inda zai ganta sai ya hango ta can qarshen dakin
Murmushi yayi sannan ya nufo inda take cikin tafiyarshi ta nutsuwa
Tunda yashigo ta ganshi amma tayi kamar bata ganshi ba, haushin shi takeji kamar me? Jitake kamar ta tashi taita zazzagamashi abinda ke cin ranta
Tanajin Qarasowarshi amma bata dago ba harya ja kujerar dake facing dinta ya zauna
Sa hannu yayi ya rufe littafin data kafama idanu kamar mai karatun gaske, yana cewa
"hey... Book worm"
Sai a lokacin ta dago ta kalleshi da alamun bazata a fuskarta
"oh! You scared me"
Yar Dariya yayi yace
"ai kece hankalinki na kan Littafi baki jin ko motsin mutane, meye kike karantawa?" yafada yana juyo da littafin gaban shi yadda zai gani
Dan daga kafadu zee tayi tace
"just going through topic da mukayi jiya"
Kada kai yayi yana maida mata littafin shima ya doro nashi littatafan a sama
"good, how's your weekend?"
"Alhamdullilah" ta amsa a gajarce tana sake jawo littafin daya maido mata gabanta tana cigaba da dubawa
"meya samu phone dinki jiya?" yafada shima yana zaro wani littafi a tsakiyar littatafanshi
Zee da maganar nan ma datake yi duk dauriyace don ita tasan me takeji a zuciyarta ta dago ta kalleshi sannan ta daga kafadu
"babu"
"but nayita kira bata Shigowa saima line busy dayaita nunawa"
Qara daga kafadu tayi batareda ta dagoba tace
"qila lokacin waya nake"
"amma fa na dade ina kira tana rubuta Hakan har da daddare ma"
Qara daga kafadu tayi in an I don't care manner tace
"yeah, ina waya ne"
"wow! Da wa? Irin wannan dadewa haka?"
Dagowa tayi tadan yimashi murmushi
"kayi mammaki ne?"
"sosai ma"
Murmushi taqara yimashi tace
"to ka daina"
Shiru yadanyi yana kallonta
"and who is that if I may ask" yafada yana dan bubbude littafin daya ciro
*"my man"*
Cak ya tsaya da bubbude pages din dayake kamar wanda aka tsaida da remote
Saikuma ya dago ahankali ya kalleta yaga ita hankalinta ma na kan textbook din gabanta
"Your man?" yafada yana tsareta da ido
Dagowa tayi itama tana kallonshi and she can swear taga wani abu mai shigen da kishi a idanunshi saikuma taga yayi saurin sauke idanu
Hakan yasata amsawa cikin fara'a
"yes, sorry ban ta6a discussing dinshi da kai ba, he's my cousin, he's very nice insha allah zanyi introducing dinku wa juna watarana"
Tunda tafara maganar ya sake dagowa yana kallonta har takai aya
Wani dry murmushi yayi sannan ya maida kanshi akan littafin gaban shi ya cigaba da budewa
Itama bata qara cewa komai ba ta maida hankalinta kan littafin dake gabanta
Sai wajen ya dauki wani unusual silent da basu saba dashi ba don muddin suna tare babu yadda za'ayi su dauki tsawon lokaci kamar haka batareda sunyi exchanging Koda kalma daya ne
Suna ahaka har lokacin shigar zee class yayi Hakan yasa ta maida littafin ta rufe ta dago ta kalleshi taga idanunshi kafe suke akan littafin gabanshi shima
Tashi tsaye tayi wanda Hakan yasa shima ya dago for the first time bayan maganarsu ta dazu yana kallonta
Maida textbook din tayi a shelve din library din inda ta zaroshi sannan ta dawo ta dauki jakkarta dake kan desk pretending bata lura da kallon dayake binta dashi ba
Rataya jakkar tayi sannan ta kalleshi
"Bari natafi kar na makara Deen, see you" tafada tana dan daga mashi yatsu
Murmushi kawai yayi ya kada mata kai tawuce yabita da kallo harta fice
_*my man*_ kalmar ta ta dazu tadawo mashi a kwanya
Ahankali ya lumshe idanu ya bude yana jan wani nannauyan numfashi
Me Hakan ke nufi? Me take nufi da *her man?*
Koma dai me Hakan yake nufi beyi sounding good to him ba
Haka kawai yaji zuciyarshi ta quntata tayi mashi nauyi ga wani daci daci dayake ji maqoshinshi
Maida littafin gaban shi yayi ya rufe shima ya tashi ya kwashi littafanshi ya rungume ya fice daga library din
Wani quiet wuri yasamu ya zauna don haryanzu akwai kingin lokaci kafin yashiga class
Duk yadda yaso ya maida hankalinshi akan littafin daya kuma zarowa kasawa yayi
Kalmarta kawai take mashi kai kawo a zuciya
*sorry ban ta6a discussing dinshi da kai ba, he's my cousin, he's very nice insha allah zanyi introducing dinku wa juna watarana*
Jiyayi zuciyarshi taqara quntata, yaji ya tsani mutumin tun kafin ma ya ganshi
Haka yaita zama shikadai cikin quncin zuciya har lokacin lecture dinsu yayi ya tashi ya wuce class
Saidai me? A class din ma babu abinda ya fahimta, yadai ga lecturer din nata 6a66atu amma bazai iya riqe kalma daya daya fada ba
Har akayi lecture din aka gama be fahimci komai ba, haka shima ya taso yabiyo ayarin masu fitowa daga class din yafito
Kasancewar anfara kiraye kirayen sallah yasa yawuce masjid din school din don yin sallah
Koda yafito be bi takan inda zasu hadu ba yawuce class ya zauna dukda saura mintuna talatin afara lecture din, haka kawai yaji beson zuwa wajen ta yanzu saboda yadda zuciyarshi kemashi zafi duk in yatuna da kalmarta
Haka ya zauna ya rungume hannayenshi a qirjinshi ya kafe wuri guda da kallo abubbuwa kala2 na kai kawo a qwanyarshi
Ahankali ahankali class din yafara cika har lecturern dazai yimasu darasin shima yashigo
Abin mammaki wannan karon ma babu abinda ya tsinta a abubbuwan da akeyi a class din
Gangar jikinshi ke zaune a class din amma hankalinshi da tunaninshi sunyi nisa, be ankaraba yaga anfara fita daga class din alamun har angama lecture din
Agogon hannunshi ya duba yaga har 4pm saura Hakan yasa shima ya tashi jiki a sanyaye yafito
Koda yazo inda suke zama be ganta ba hakan yasashi wucewa library nan ma babu ita sai ya wuce department dinsu don ganin ko tana can amma canma babu ita don babu ma mutane sosai Wurin Hakan yasashi sanin ta tafiyarta
Sai yaji zuciyarshi taqara quntata, ranshi yaqara dagulewa yaji wani abu ya tokaremashi qirji
Juyowa yayi kawai yanufi hanyar fita school din
Cikin sa'a yana fitowa yaga wata napep ta sauke wadansu sai ya qarasa yayiwa mai napep din magana suka daidaita yashige suka wuce
A bangaren zee kau tun daga reaction dinshi na farko data gani tafara tabbatar da hasashenta
Kamar yadda Deen yayi attending class batareda ya fuskanci komai ba Haka itama tayi
Itama kawai zama tayi a class din amma bata fahimci komai ba, gabadaya hankalinta da tunaninta nakan reaction din Deen na dazu.
Tabbas ta hango wani abu mai shigen kishi a qwayar idanunshi and then sai yarage kuzari, yama qi magana harta taso tabar wajen
Dukda yayi qoqarin 6oye expression din fuskarshi tana iya hango bitterness din fuskar, tabbas maganar ta ta dakeshi don taga alamun Hakan
Cije lip dinta na qasa tayi sosai tana jin yadda zuciyarta ke bugu sosai. Tama rasa tunanin da zatayi.
Koda suka fito lecture din itama masjid ta nufa tayi sallah, tana fitowa kuma ta hangoshi shima ya fito ya nufi hanyar barin wajen, kamar tayimashi magana kuma saita fasa tabi tafiyar dayakeyi a sanyaye da kallo, tabbas muddin ka sanshi sosai kallo daya zakamashi ka gane ba lau
Wani dan murmushi ya su6uce mata tana wani calculating a zuciya sannan ta dan ciji qasan lip dinta itama tafito daga wajen
Koda tafito daga next lecture din nasu bata tsaya jiran shi ba kamar yadda tasaba kawai tashige mota suka fice tana jin wani yaqini a zuciyarta
***
A bangaren Deen haka ya qarasa ranar cikin rashin walwala, ko kaka ma tasan yau ba lau ba
Tambayar duniyar nan tayimashi amma amsar daya ce "babu komai"
Hakan yasa tayi tunanin ko bejin dadi ne shiyasa yake tsoron gayamata saboda shan magani
Hakan yasa taje ta dauko magani tabashi akan yasha
Ga mammakinta sai gani tayi ya amsa babu ko gardama ya watsa a baki ya kora da ruwa ya tamke idanu yana hadiyewa don shima abinda zai sauqaqa mashi abinda yakeji a zuciya yake nema shiyasa beko yimata gardama ba ya amsa yana ganin inhar zai sauqaqa mashi abinda yakeji babu abinda zai sashi yaqi sha
Komawa yayi ya jingina da bangon dakinshi yana maida numfashi
Jiki a sanyaye kaka ke mashi sannu Saidai ko bude idanunshi beyi ba
Ce mashi tayi ya kwanta ya dan rintsa qila kafin ya farka zaiji sauqi
Babu musu ya zame ya kwanta yaqara tamke idanu yana jin yadda zuciyarshi ke tashi kamar zaiyi aman maganin dayasha
Saida yaji fitarta sannan ya bude idanu ahankali ya kalli kofar data rufomashi
Qara maida idanun yayi ya rufe yayi shiru
*my man* muryarta taqara yimashi amsa kuwa a kunnenshi
*he's very nice*
Bude idanun yasakeyi sannan ya miqe zaune ahankali
Wayarshi ya lalubo ya danna power botton takawo haske
Time ya duba yaga 10 saura na dare
Haka kawai sai gani yayi ya shiga contact ya fara scrolling sunayen ciki
Daidai sunanta dayayi saving da *bestie* ya tsaya
Ya dade yana kallon number sannan ahankali kamar mai tsoro ya dannama number kira
_the number you dial is busy with another call, please hold on or try again later_
Abinda yaji baturiyarnan ta m.t.n tafada kenan sannan ta cigaba da ringing
Harta katse bata dagaba Hakan kuma be hana yasake kiraba yanajin zuciyarshi na wani irin zafi kamar a oven
Tambayar dake kai kawo a qwalwarshi itace dawa take wayar? Yayinda zuciyarshi ke hasasomashi qila da so called *man* dinta take wayar
Saida ya jeramata kira uku duk babu wanda ta daga she's busy on another call, qarshe sai tayi sending sms na
_*am busy, please call later*_
Besan ya akayi ba sai gani yayi ya wurgar da wayar ta daki bango ta fado qasa
Be bi takanta ba ya koma ya kwanta kan gadon ya jawo bargo ya rufe jikinshi har kai dukda uban zafin da akeyi
Ya runtse idanunshi Gamm yanajin zuciyarshi na suya kamar a kasko... โ๏ธ
Ummin fasihu ๐ง๐ปโโ๏ธ?
8/2/21, 9:37 PM - Buhainat๐: *๐๐ปโโ๏ธDEEN ๐๐ปโโ๏ธ?*
*040*
*THE CONFESSION๐*
Koda gari ya waye Dakyar kaka ta iya tadashi yafita sallar asuba don dama sai gab da asuban yasamu barcin ya dan daukeshi
Kallo daya zaka yima yanayinshi kayi tunanin beda lfy duba da yadda yaqaro sanyi ya hada da ainahin sanyinshi
Ba'a dade da gama sallar ba yadawo yana jin kamar yayi shigewarshi daki yayi barcinshi amma bazai iya barin kaka da wadannan tulin aikin ba ita kadai
Gaisawa sukayi da kaka kamar yadda suka saba tana Tambayar jikinshi yace mata da sauki ya wuce Domin hura wutar koko
Be wani sha wahala ba takama kasancewar dama ya saba da hurin wutar amma maimakon ya tashi ya dora tukunyar saiya tsaya a tsugunnen dayake ya qurawa jar wutar dakeci ido
Kaka batasan yana yiba har Saida tagama wanke waken data surfa takawomashi don yakai markade sai ta ganshi tsugunne gaban murhun ya qurawa wutar ido kamar mai karantar wani abu jikinta
Magana tayi mashi amma beji ba don yayi nisa sosai Saida ta dan ta6ashi sannan yayi saurin dagowa sai kuma ya kalli wutar yayi saurin tashi yawuce don dauko tukunyar kokon kaka na binshi da kallo
Saida ya dora ruwan sannan ya amshi bokitin waken yafita yo markaden
Kasancewar ya dan makara da zuwa markaden sai ya tararda jira har mijin mai markaden na tsokanarshi wai ko yau ranar barci sukayi
Shidai bayan
All Chapters
Chapter 1
Chapter 2
Chapter 3
Chapter 4
Chapter 5
Chapter 6
Chapter 7
Chapter 8
Chapter 9
Chapter 10
Chapter 11
Chapter 12
Chapter 13
Chapter 14
Chapter 15
Chapter 16
Chapter 17
Chapter 18
Chapter 19
Chapter 20
Chapter 21
Chapter 22
Chapter 23
Chapter 24
Chapter 25
Chapter 26
Chapter 27
Chapter 28
Chapter 29
Chapter 30
Chapter 31
Chapter 32
Chapter 33
Chapter 34
Chapter 35
Chapter 36
Chapter 37
Chapter 38
Chapter 39
Chapter 40
Chapter 41
Chapter 42
Chapter 43
Chapter 44
Chapter 45
Chapter 46
Chapter 47
Chapter 48
Chapter 49
Chapter 50
Chapter 51
Chapter 52
Chapter 53
Chapter 54
Chapter 55
Chapter 56
Chapter 57
Chapter 58
Chapter 59
Chapter 60
Chapter 61
Chapter 62
Chapter 63
Chapter 64
Chapter 65
Chapter 66
Chapter 67
Chapter 68
Chapter 69
Chapter 70
Chapter 71
Chapter 72
Chapter 73
Chapter 74
Chapter 75
Chapter 76
Chapter 77
Chapter 78
Chapter 79
Chapter 80
Chapter 81
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 29 Chapter of 81