murmushi babu abinda yake
Waje ya koma don jira yasamu dakalin kofar gidan
Shiru yayi ya kafe santar tasu da ido yana dorawa daga inda ya tsaya a tunaninshi yana kuma tunano mafarkan dayayi nata a yar kwanciyar nan dayayi
Wanda yafi daga mashi hankali cikinsu shine wanda yayi daga baya bayannan wanda yana cikin yinshi ne kaka ta tadashi
Wai a cikin mafarkin yaga zee zaune da so called cousin din nata suna fira dukda be iya ganin fuskar mutumin ba sosai
Fira suke sosai suna Dariya, kawai sai gashi kamar an jefoshi a wajen
Be nufi kowaba sai saurayin yafara yimashi qarajin ya tashi yabar wajen
Qin tashi mutumin yayi kuma yaqi kallonshi hasalima kamar basu masan dashi ba don firarsu suka cigaba dayi cikin nishadi
Haushi yaji saiya ture mutumin daga kujerar dayake akai ya fadi
Jiyayi zee tayi qara kamar ita ya ture sannan ta tashi tana hayyayako mashi akan meyasa ya ture "man" dinta shikuma ambatar man dinnan yaqara qular dashi sai ya juyo kanta yafara magana cikin hayyayakowa shima, Saidai shi kanshi besan abinda yake cewa ba, kamar ma maganar bata fita don jin maqoshinshi yayi tamau kamar an shaqe amma ahaka yake fizgar magangganun yana gayamata, magangganun ma ko sauti babu
Yana cikin haka yaga ta tureshi gefe taje zata tada wancan wanda ke kasa har lokacin sai ya cafko hannunta ya fizgota ta fado jikinshi beyi wata wata ba ya Hade bakinsu Waje daya
Mutsu mutsun qwacewa tashiga yi amma yaqi bata dama saima farma le66unanta dayayi kamar maye yasamu nama, ahaka yaji ana janshi a baya ana jijjigashi, can yaji muryar kaka na cewa
"kyakyawa ka tashi, kyakyawa na! Kyakyawa! Ka tashi karda ka rasa jam'i"
Sai a lokacin yafara bude idanunshi ahankali har suka bude tarr yaga kaka sunkuye akanshi tana cigaba da tadashi, dan Juyawa yayi saiya fuskanci ashe ma kan katifarshi yake, ashe mafarki yake.
Saida ya tabbatar Yana da tsarkin jiki sannan ya lalla6a ya taso yafito jiki a mace
Jin a dan bubbugi kafadarshi yasashi qara yin firgigit ya dago yadawo daga duniyar tunanin daya sake lulawa
Wani yaro yagani tsaye akanshi bokitin markaden Deen a gefe
"yaya Deen wai ance ga markaden" inji yaron
Miqewa Deen din yayi ya lalubi kudi yaba yaron yace yakai sannan ya dauki markaden yayo gida cikin dan sauri sauri ganin yadda gari yayi fau yayi haske yasan ma kaka nacan tana tunanin lafiya
Illai kuwa yana shiga sukaci karo da kaka datake shirin fitowa jin shirun yayi yawa
Tambayar shi tayi ya akayi ya dade haka yace mata jira ke akwai
Suka dawo ciki tare yaga harta sheqa tukunyar farko ta maida wasu
Murhun qosai yanufa yafara hurawa ita kuma kaka tashiga hada kullun qosan
Cikin dan qanqanin lokaci suka gama kaka tafara tuya izuwa lokacin har yara sunfara Shigowa
Haka dai Deen ya daure yayi attending customers din har suka samu yaqare duka
Lokacin har tara da rabi Hakan yasa kawai yafada bandaki yayi wanka sannan ya fito ya hau shirin school
Har daki kaka ta kawomashi nashi kokon don ya karya
Saida tagama sannan ta miqa mashi magani akan yasha taga haryanzu kamar jikin be warware ba
Kamar zaiyi kuka yake cemata shifa ya warke amma bata kulashi ba Saida yashasu yana kakari yana komai
Sannan ta sallameshi yafito daga gidan lokacin har goma ta wuce yasamu aca6a suka daidaita yahau suka lula
*UMYU*
Koda ya iso school din be nemeta ba don yasan tana class kasancewar yau morning lecture gareta sai kawai yayi wucewarshi inda suka saba zama idan basa library yayi zamanshi can ya dora karatun jakinshi daga inda ya tsaya
Students suke ta fita daga class din.
Ida rubuta abinda take rubutawa tayi sannan ta maida littafin ta rufe ta bude jakkarta ta saka aciki
Itama tashi tayi tabi ayarin masu fita itama tafito
Fiddo wayarta tayi ta duba time taga 11:52am Hakan yasa tasan is either yana library ko wurin da suka saba zama don yau lecture din 1pm gareshi, dama duk sunyi cramming lokacin lectures dinsu aka
Library tafara nufa dukda tasan mawuyacine ace yana can duba da zafin da akeyi a garin don yanzu damuna ta wuce ana zafin gasa dawa
Bata tarar dashi ba wurin kamar yadda tayi hasashe saita juya ta nufi inda suke zama din don tasan tabbas yana can
Daga nesa ta hangoshi zaune bisa benci ya sunkuya qasa amma batasan abinda yakeyi ba
Ida qarasowa tayi, jin motsinta yasa Deen saurin sa kafa ya baje rubutun dayakeyi da dan kara a qasa sannan ya dago yana kallonta, looking so beautiful as ever
Harta qaraso wajenshi be Janye idanunshi akanta ba har Saida ta kyafkyafta mashi yatsu a fuska sannan yadanyi blinking sai kuma ya sauke idanunshi qasa
Zama tayi kan dutsen dake facing dinshi tana cewa
"wannan kallon saikaja inyi tuntu6e"
Bece komai ba kuma be dago ba
"Saida naje library na tarda baka nan, how's my kaka?"
Sai a lokacin ya dago ya kalleta sai kuma ya motsa baki kamar mai ciwon baki yace
"she's fine"
Ganin yanayin dayayi mata magana kamar anyi forcing dinshi yasa bata qara ce mashi komai ba ta zaro wani Littafi ta shiga budewa
"I called jiya baki dagaba" yafada yana kafeta da ido
"yes I was on another call kuma I tried to reach you later amma bata shiga" tafada hankali Kwance batareda ta dago daga bude littafin datake ba
"you're busy with another call, da wa?"
Kafin ta bude baki ta amsa ya tari numfashinta da
*"Your man?"*
Dakatar da bude littafin datake tayi ta dago ta kalleshi and for the first time taga a very serious expression a fuskarshi, tunda take bata ta6a ganinshi in seriousness kamar yau ba, babu alamun wasa ko kadan a fuskarshi
Daga kafadu tayi ta maida hankalinta akan littafin hannunta tace
"yeah, ka canka daidai, I was busy with him"
Jin maganar tata yayi kamar saukar mashi a qahon zuciyarshi, bugun zuciyarshi yashiga gudu sosai
Dukda taji yadda hasken idanunshi ke reflecting a fuskarta bata dago ba saima cigaba da bude littafinta take wanda a zahiri tama wuce inda take son budowa
Hadiye wani yawu mai daci Deen yayi sannan ahankali yace
"Zainab.."
Sosai kiran yashigeta don yayishi ne in a very cool manner
Dagowa tayi ta kalleshi batareda tace komai ba sai zuciyarta dake qara gudu
Kamar bazai ce komai ba sai kuma yaqara tattaro wani yawun ya hadiye sannan yace
"please ina neman wata alfarma wajenki"
Shiru tayi takasa cewa komai saboda yadda zuciyarta ta tsananta bugu jitake kamar data bude bakin zuciyarta zata biyo ta wajen ta fito
Ganin batace komai ba kuma bata bar kallonshi ba yasashi cewa
"please, karki qara... Kulashi" ya qarashe yana kallonta da wani expression mai wuyar ganewa a fuskarshi
Batace komai ba sai kallonshi datake still
"please... Don Allah" yasake fada murya a matuqar sanyaye
Cikin danne abinda ke taso mata a zuciya ta yamutsa fuska
"I don’t get you"
Ajiyar zuciya ya sauke yadan ciji lower lip dinshi yasaki sannan yace
"I mean, your... Cousin, please kibar kulashi"
"why?" tafada tana mashi wani kallo
"because... I think... I don’t like him, please just stay away From him kuma kibar picking call dinshi... Please, do this for me... Please" Sai kuma ya dafe kanshi yana jin yadda zuciyarshi ke zillo
"what? Kasan abinda kake fada kuwa? Kasan matsayin wanda kake magana akai aguna, you just Said it, he's my cousin"
Janye hannunshi daya dafa kanshi dashi yayi yace
"am.. Sorry, nasan family dinki ne but... Just let it remain like that, babu qari babu ragi.
Please kibar kiran shi your man kuma kibar waya dashi like that" yafada shi kanshi yasan he sound so stupid
"me? Meye aciki don nayi waya dashi?"
"ba wayan dashi ne matsalar ba, what you guys are discussing ne"
"me muke discussing?" inji zee tana kallonshi kamar yau tafara ganinshi don sosai yakoma kamar bashi ba yawani burkuce
"I don’t know also amma koma menene it doesn't sound good to me, nasan qila kunyi awa kuna wayar.. And also dare ne, kamata yayi ace barci kike a lokacin"
"kamata yayi ace barci nake a lokacin kuma kai ka kira?"
"na kirane don nayi confirming kinyi barcin ne and also Koda kin daga bewuci mu gaisa ba inyi miki good night muyi hanging call amma shifa? Heaven knows what he's saying to you kuma allah kadai yasan lokacin da kuka gama wayar"
Tunda Deen yafara take kallonshi cikin mammaki deep down kuma farincikine kesata jin kamar ta taka rawa
Ganin wanda kake tunanin kai kadai ke haukanka akanshi na kishinka ba qaramin abu bane mai antaya mutum cikin farinciki, wanda ya tsinci kanshi a wannan yanayin kadai zai iya ganewa
"well ni banga abinda zai dameka ba akan haka"
"but am your friend, dole na damu dake"
"and he's my man, my boyfriend.."
"damn it!" yafada yana qara dafe kai cike da takaici
"wai Deen are you sure you're ok?"
Dagowa yasake yi wannan karon idanunshi sun fara chanza launi
"Nace maki kibar kiranshi your man and you're now calling him your boyfriend"
"wai Deen meke damunka ne? Meye matsalarka dashi"
"I don’t know, I just hate him, can't you get that?!" yafada cikin dan daga murya yana jin kamar yaita ihu don takaici
"you hate him? My boy friend?"
"oh my God! For Heaven's sake kibar kiranshi haka?" yafada jijjiyoyin wuyan shi na tashi
Dukda taji tsoron yanayin shi amma bata fasa cewa
"why? He's my boy friend, he loves me who are you to tell me not to love him back" tafada tana miqewa tsaye tana mashi wani kallo
Shima miqewa tsaye yayi
"No! Qarya ne, wlh ba sonki yake ba, yaudararki zaiyi, he never loved you" yafada yana maida numfashi ahankali
"what?" tafada tana dan ja baya
"yes, he doesn't, I swear, kawai he want to play your heart ne, he want to use and dump your heart, ki yarda dani" yafada yana dan matsota
"Deen, are you sure you're ok?" tafada tana qara jada baya ganin kamar ma ba a hayyacinshi ba yake
"yes.. Yes, yes Zainab, am ok, ki yarda dani, he doesn't love you, baya sonki, nike sonki Zainab, nike sonki..."
Tsit wajen yayi
Dafe kai yayi yana jan numfashi ahankali yayinda zee data qame kamar statue takasa Janye idanunta akanshi
Dagowa yasake yi ya kalleta da idanunshi dasukayi ja
"am... Sorry Zainab, am..." saikuma yaqara dafe kanshi, yakoma wani zararren qarfi da yaji lokaci guda
Sake Dagowa yayi
"Don Allah.. Kiyi hqr, bansani bane, bansan sadda nace haka ba... Amma kuma Gaskiya ce
I.. Love..you, Kiyi hqr amma that's it, the truth
Na dade ina ajiye wannan kalmar a zuciyata, na dade ina juriya wajen ganin na barta iya cikina amma not any more, bazan iya ba kuma. Am sorry.. Am sorry" yafada yana Hade hannayenshi
Ahankali zee da haryanzu idanunta ke kafe akanshi tafara takawa da baya baya
Ganin Hakan yasa yafara Binta shima ahankali
"nasani.. Nasan na wuce iyakata amma don Allah Kiyi hqr, wlh nima bansani ba, bansan sadda nafara sonki ba, please don't leave, please"
Haryanzu batace komai ba kuma bata bar kallonshi ba kuma bata bar tafiya da baya baya ba
"please Zainab, stop moving, say something but please don't leave me, nima nasan I was stupid to think of doing that but I swear nima bansani ba, bansan yadda akayi ba nafara ba, I swear ban saniba" yafada still yana Binta
Juyawa tayi da sauri tafara tafiya da sauri sauri don barin Wurin
Ganin Hakan yasa shima Binta da sauri, Ganin Hakan yasata fara gudu shima yasa gudu yabita Saidai cikin tsautsayi yayi tuntu6e da wani dutse a gabanshi yayi saurin duqawa yana kama kafar
Sake Dagowa yayi yaga takusan shanye kwana Hakan yasa shima yacije ya tashi dukda radadin da qafarshi kemashi yabiyota Saida Koda shima ya shawo kwanar babu ita babu alamunta
Cigaba da tafiya yake yana waige waige, yadai san bata isa takai gate ba don akwai tazara sosai da nan wajen dole ya hangota, dole Saidai idan wani Wurin ta 6oye
"Zainab? Zainab!!" yafada yana dudduba Wurin amma babu ita Hakan yasashi qarawa gaba yana nemanta amma ba ita ba labarin ta, Hakan yasa yadawo yanufi department dinsu yaga ko can tayi
Daga inda take la6e ta hangi shigewarshi kwanar da zata sadashi da department dinshi Hakan yasata fitowa tana share hawayenta ta nufi hanyar gate da sauri sauri tana yi tana waige harta samu tafito daga school din
Wasu adaidaita biyu tagani sunzo wucewa tashiga tsaida na farkon Saida tazo gab taga ashe cike take
Saita koma tana tsaida na biyun
Cikin sa'a babu kowa ciki, fadawa ciki kawai tayi tana cema mai adaidaitan sutafi tana leqen gate din school din
Babu musu mai adaidaitan yaja napep din suka bar wajen
Babu inda be duba ba a department dinsu amma babu ita yasake dawowa inda ta 6oye dazu batanan ya wuce library nan ma haka
"ya sallam!"
Yafada yana zama kan daya daga cikin kujerun library din ya dafe kanshi
"my goodness! Tayaya ma nayi wannan su6ul da bakan" yafada yana rufe fuskarshi da taffukan hannunshi yana furzar da huci
Yes he's in love with zee kuma ya dade da sanin haka Saidai bayada courage din tunkararta da Hakan
Tayaya talaka kamar shi wanda bayan allah da annabinsa beda kowa sai kakarshi zai tunkari mace kamar zee, yarinya yar masu kudi, wanda babanta sannane ne a katsina dama nigeria gabadaya? Tayaya?
Bazai iya tunkararta da hakan ba, gani zatayi yama raina ajinta, gani zatayi don yaga tayi strooping tana abota dashi shine yasa zai wuce makadi da rawa wajen cewa yana sonta
Tabbas yasan zee tafi qarfinshi ata koina, asali, arziqi, class, komai ma
Yanayi ne ma da qaddara yasa suka Hade a school dinnan don yasan tafi qarfin zuwa school din
Tun sadda ya fahimci halin da zuciyarshi ke ciki gameda ita yasa yafara kafa kafa da ita wajen barin Hakan iya zuciyarshi batareda ya barshi ya fito ba
Ya gano Hakan ne tun kwanciyarshi a hospital, yaso yayi denying Hakan amma ita zuciya batasan wannan ba, abinda takeso shi takeso ko kai mai zuciyar kaqi ko kaso
Lokacin da aka sallamesu daga hospital he's very sad
Dik majinyaci farinciki yake a lokacin da aka bashi sallama amma shi akasin haka ne a wajenshi don yasan Hakan na nufin yin nisa da juna, dan ganin ta dayakeyi sau biyu a ranar zai zama tarihi
Hakan yasa lokacin dazasu tafi yakasa tafiya ya tsaya yana kallonta yana jin kamar ya hanata tafiya amma haka ya daure yanaji yana gani ta tafi tabarshi feeling very empty kamar ta tafi mashi da abu mai matuqar muhinmmanci kodayake ta tafi din da abin nashi mai muhinmmanci, zuciya ❤️
Tun daga lokacin yake jin tsananin kewarta da begenta, kullum cikin tunaninta yakeyi da mararin ganinta amma yasan ba hali wataqila shida ganinta sai sunyi resuming
Kwatsam sai gata sati daya da sallamarshi
Lokacin daya shigo ya ganta jiyayi kamar a mafarki don be ta6a kawo Hakan a ranshi ba
Murza idanunshi yashiga yi don tabbatar da ita din ce sai yaji kaka na cewa
"qaraso mana, ita din dai ce"
Qarasowa yayi cikin doqin ganinta Saidai me? Saiya lura ita kamar bata doqin ganinshi don kallo daya tayimashi ta sauke idanunta qasa
Hakan yayi matuqar sanyaya mashi jiki amma ya daure yayi mata magana yana tambayarta yasu mummy
Babu yabo ba fallasa ta amsa mashi saikuma ta tashi wai zata tafi
Beji dadi ba sam don ba Haka yaso ba, so yayi tayi zamanta susha firarsu yayita kallonta yana jin dadi
Ganin dagaske tafiyar zatayi harta miqe yasashi shima tashi ya shiga dakin kaka ya dauko wayar data bashi don maida mata
Koda yafito har takai zaure yayi saurin Binta
Kiranta yayi ta tsaya amma bata juyoba
Tambayar ta yayi tafiya zatayi sai ta juyo tace eh ko yanada matsala da Hakan ne?
Beji dadin amsar ba Amma ya amsa da A'a sannan ya maida mata wayarta, da farko be lura da kallon datake mashi ba sai daga baya lokacin daya miqa mata wayar hannunshi don ta samashi number mummy
Kallon datake mashi lokacin yakuma sanyaya jikinshi sai yaji yakasa yimata dayar maganar wato tasamashi numberta su dinga gaisawa
Ganin taqi barin kallonshi yasashi tambayarta lfy kau? Sai yaga ta kauda kai saikuma tasake juyowa ta amsa da lfy ta amshi wayar tayi yan danne danne ta miqomashi
Qin amsa yayi yana kallonta trying to read her expression amma Abu daya ya iya ganewa, tana fushi
Hakan yasa yakasa qara tambayarta number ta sai ya amshi wayar kawai yana cewa
"Are you sure you're ok?"
Sai gani yayi ta juya tana cewa
"more than you are" ta fice
Binta da kallo yayi yana jin ba dadi, tsawon satin dayayi batareda yasata a idanunta yasa yayi missing dinta sosai yayi tunanin itama Hakan yake a wajen ta yayi tunanin duk lokacinda suka sake ganin juna Dakyar zasu rabu
Fitowa yayi ya tsaya bakin kofar gidansu yana kallonta ta cikin mota dukda baya iya hangota saboda tinted glass din motar, yana ji yana gani aka ja motar aka tafi aka barshi nan
Daga lokacin duk sai jikinshi yayi sanyi, ya kasance kodayaushe cikin tunaninta yake
Bayan kwana biyu da tafiyarta ya matsa ma kaka ta bugama mummy tayi mata godiyar datace zata yimata
Haka yaje yasanyo kati na #200 a lokacin ita kenan ma gareshi duk don yaji lfyar zee in so samu ne ma yaji muryarta
Saidai Koda suka gaisa din kaka ta tambayi zee tace ina take tace mata lfy lau tana dakinta, jiyayi kamar yace ma kaka tace a kai mata amma babu dama haka shima ya amshi wayar suka gaisa sukayi sallama da juna ba don yaso ba
Bayan kwana biyu again yasake tusa kaka gaba akan tasake kira, shima wannan lokacin zee batanan tashiga wanka wai, Hakan ba qaramin sake dagulamashi lissafi yayi ba
A kira na uku ne yaji mummy na gayama kaka zee tayi tafiya zuwa garinsu mummyn, Hakan ba qaramin sake dagulamashi lissafi yayi ba don Hakan ya tabbatar mashi cewa shi da ganinta ko jin muryarta kuma sai sunyi resuming
Haka ya hqr don dole ya cigaba da looking forward na resuming dinsu, kullum cikin qirgar ranakun dasuka rage yake
Ranar daren dazasu koma ko isashen barci beyi ba saboda doqi
Ranar dazasu koma kuma safko ya buga saboda doqi, yaci kwalliyarshi ciki kayanshi na qure daka yatafi Saidai me? Wannan karon ma tarbar dabeyi tunani ba tayi mashi
Yana shiga gate din school din yaganta kuma kallo daya yaimata ya gane itace dukda bayanta yagani, Hakan yasa yafara sauri yana kiran sunanta
Saida yakusan taddota sannan yaga ta tsaya alamun tajishi amma bata juyo ba
Da sauri ya qarasa yana maida numfashin saurin dayayi
Zagayowa yayi gabanta yana kallonta cikin so da shauqin ganinta
"Zainab is this you?" yafada cikin tsananin shauqi da jindadin ganinta
Sai gani yayi ta dago ta kalleshi tayi shiru kamar mai karanta wani abu a face dinshi
"Zainab, are you ok?" yafada ganin yadda ta kafe shi da ido
Still babu amsa kuma batabar kallonshi ba
"Zainab..."
Sai yaga tasa hannu ta toshe duka Kunnuwanta ta runtse idanunta gamm
Ganin Hakan yasashi rudewa, qara kiran sunanta yayi sai yaga tayi saurin Zagayeshi ta wuce Hakan yasashi binta ya sha gabanta
Cikin matsanancin damuwa yasake tambayarta lfy amma saita qara ra6awa zata wuce yasake tareta da sauri yana sake kiran sunanta
Tsawa tayi mashi wanda yajishi har cikin ranshi wanda Hakan Saida yasa yadanja baya
"I said leave me alone, can you get that?!" tafada again a tsawace
Dukda tsoron tsawar dayake Hakan be hana yadan qara matsowa ba yasake kiran sunanta, sai ta dafe kai tajuya takoma ta inda ta fito
Da farko kasa Binta yayi saikuma yabita amma yana zuwa yaga wucewar adaidaita ashe itace a ciki
Sosai jikinshi yayi sanyi yaji kamar yaita kuka, ya dade tsaye a wajen harya gaji yakoma
Koda yakoma ma wuri yasamu kan dakalin wani office ya zauna inda zai dinga hango gate yadda data shigo zai ganta
Amma shiru babu ita babu alamunta har lokacin zuhr yayi dole ya tashi yaje yayi sallah yakuma dawo ya dasa jiranta daga inda ya tsaya Saidai har asr bata dawo ba hakan yasa ya tashi yayi sallah yawuce gida zuciyarshi a matuqar sanyaye
Ranar beyi wani barcin kirki ba saboda damuwa
Washegari ma Hakan take don ranar tun Shigowarta ya ganta kasancewar ranar ma dawuri yaje school din
Yana kallonta har tazo ta wuce sannan shima ya lalla6a yabita har inda tasamu ta zauna
Tsayawa yayi jikin wata bishiya mai facing dinta ya rungume hannayenshi a qirji yana kallonta
Abin mammaki Saida yadan jima ahakan kafin ta farga dashi kuma tana ganinshi ta sake kafeshi da ido irin jiya
Qarasowa yayi gabanta ya tsugunna yafara qoqarin yimata magana tăsake tashi zata tafi
Shan gabanta yayi yana mata magiyar ta gayamashi ko fushi take dashi amma taqi sauraronshi saima tsawar datayi mashi, Ganin Hakan yasashi barinta ta wuce, har tayi nisa ya tsaidata ta hanyar tambayarta ko saboda ya maido mata wayarta take fushi, idan ma don hakane tayi hqr shi bada niyyar ya 6ata mata rai ba yayi Hakan
Bata ko juyo ba tawuce ta barshi nan tsaye
Sai yaji zuciyarshi taqara quntata, sai jiyayi duk murnarshi ta Ayi resuming school yaganta duk ta koma ciki, damuwa ta maye gurbinta
Washegari yazo har yatafi bega 6il6ishinta ba, Hakama Washegari nan ma ko mai kama daita be ganiba Hakan kuma ba qaramin qara tsundumashi kogin tunani da damuwa yayi ba
Ranar juma'a kamar bazai ceba saikuma ya shirya jiki a sanyaye yaje don daya zauna gida yaita tunani gwara yaje can Koda bazai ganta ba atleast zai samu damar tunaninta batareda takurawar kaka ba
Usual inda yasaba zama cikin yan kwanakinnan wato dakalin wannan office din inda ake iya hango gate daga nan ya tsaya ya jingina da bango
Be dade ba kamar a mafarki kawai yaga Shigowar motarta
Be motsa ba hakan zalika be kyafta idonta ba akanta har aka bude mata kofa tafito
Sosai tayi mashi kyau cikin shigar shaddar datayi Hakan yasa ya shawara da kallonta
Kawai sai gani yayi tafara waige waige, sai zuciyarshi tabashi ya 6oye kar ganinshi yasa tasake Juyawa ta koma yau ma
Saidai kafin yayi wani yunkuri harta juyo sun hada ido
Gani yayi ta kafeshi da ido shima sai yakasa Janye nashi akanta yana kallonta zuciyarshi nata zallo kamar zata fito waje
Ga mammakinshi sai yaga ta sakarmashi murmushin da be ta6a ganin wanda ya ta6a yimata kyau irinshi ba
Tashi yayi daga jinginen dayayi yana jin nauyin zuciyarshi na raguwa ahankali
Blinking idanu yayi don ganin ko idanunshi ke gayamashi qarya
Sai yaga dagaske ne, zee daice tsaye tana mashi murmushi
Besan sadda shima yafara murmushi ba harda yar Dariya sannan ya qaraso wajenta da sauri
Murmushi tasake yimashi sannan ta wuce shi ta nufi hanyar library ganin Hakan yasa shima yabita da sauri feeling so happy, baqincikin zuciyarshi na yayewa
To a lokacin ne suka shirya, ranar yayi farincikin daya rabu dayi kuma a ranar bebari damarshi taqara su6uce mashi ba ya amshi number ta kuma ya amshi wayarta data mashi kyautarta
Yaso ya kirata tun ranar amma gudun karya takura mata ko taqara botsare mashi yasa yafasa ya haqura har Washegari, da yaso yabari ya haqura har dare amma yakasa sai ya bugamata a lokacin
Yaji dadin samunta dayayi da kuma dagawar datayi a kira na farko don yadda yasanta da ajinnan yayi tunanin bazata daga ba, kuma ajinta na daya daga cikin abubbuwan dayasa ya kware mata sai kyawawan dabi'unta wanda idan ba saninta kayi ba sosai bazaka ta6a sanin tanada su ba, she's classic but simple, very simple and nice
A ranar badan yaso ba yayi mata ban kwana dawuri ba saidon karya takura mata gashi daman lalla6ata yake yi karta qara yin fushi dashi don yasan shi zaisha wahala don bazai iya yin zuciya ya barta ba don zuciyar bazata bada hadin kai ba, gwara dai ya lalla6a
Ahaka har suka kwashe wadannan lokacin kullum da sonta yake kwana yake tashi don jiyake ma kamar qara huramashi wutar sonta a zuciyarshi
All Chapters
Chapter 1
Chapter 2
Chapter 3
Chapter 4
Chapter 5
Chapter 6
Chapter 7
Chapter 8
Chapter 9
Chapter 10
Chapter 11
Chapter 12
Chapter 13
Chapter 14
Chapter 15
Chapter 16
Chapter 17
Chapter 18
Chapter 19
Chapter 20
Chapter 21
Chapter 22
Chapter 23
Chapter 24
Chapter 25
Chapter 26
Chapter 27
Chapter 28
Chapter 29
Chapter 30
Chapter 31
Chapter 32
Chapter 33
Chapter 34
Chapter 35
Chapter 36
Chapter 37
Chapter 38
Chapter 39
Chapter 40
Chapter 41
Chapter 42
Chapter 43
Chapter 44
Chapter 45
Chapter 46
Chapter 47
Chapter 48
Chapter 49
Chapter 50
Chapter 51
Chapter 52
Chapter 53
Chapter 54
Chapter 55
Chapter 56
Chapter 57
Chapter 58
Chapter 59
Chapter 60
Chapter 61
Chapter 62
Chapter 63
Chapter 64
Chapter 65
Chapter 66
Chapter 67
Chapter 68
Chapter 69
Chapter 70
Chapter 71
Chapter 72
Chapter 73
Chapter 74
Chapter 75
Chapter 76
Chapter 77
Chapter 78
Chapter 79
Chapter 80
Chapter 81
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 30 Chapter of 81