Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
yasan yadda zaiyi. ahaka suka cigaba da tattaunawar har zuwa wani lokaci anan ummie tashiga tambayar ina zee nan akace tana sama, sai ummy tasa su batool suje sutaho daita halan batasan da zuwansu bane. tunda aka ambaci sunan zee Deen yaqara rasa yar nutsuwarshi bugun zuciyarshi ce ta sauya yayinda wani feeling mai tsuma jiki ya mamayeshi sauke kanshi yayi qasa ya cigaba da sauraron firar dasu ummie keyi sama sama yayinda duk hankalinshi da nutsuwarshi suka tattara sukayi hanyar dayaga su batool sukayi, dukda ba kallon wajen yake ba amma gabadaya hankalinshi na wajen. ahankali bugun zuciyarshi tafara sauyawa tana yin doubling ahankali yashiga murza taffukan hannunshi together kamar mai son yin maganin sanyin nan sosai tsigar jikinshi ke tashi yanajin kamar ya dago amma yakasa dagowar ahakan ya tsinkayi muryar da kunnuwanshi suka jima suna bege da marari, muryar da sai yanzu yasan iya adadin kewar dayaimata "Ummie" yaji tafada cikin zazzaqar muryar da har yanzu beji mai irinta ba cigaba dazuwa mashi muryar tayi cikin gaisawar dasuke da ummie kasa riqe kanshi yayi daga qin dagowa ahankali yafara dago oily eyes din nashi kamar wanda ake controlling da remote daidai nan itama ta kallo wajen kamar tasani caraff oily eyes dinshi ya sarqe da nata large pure white eyes din...✍? *ga post din dare😆 nasan wasu harsun fidda rai🙁* Ummin Fasihu🧚🏻‍♀? 8/2/21, 9:44 PM - Buhainat😝: *🙍🏻‍♂️DEEN🙍🏻‍♂?* *088* Qirjinsu yabada damm lokacin da idanun nasu suka gauraya dajuna ko seconds biyu batayi ba tana kallonshi ta janye idanunta ta maidasu akan ummie dake mata magana murmushi tayi tadan sunkuyar dakai Jin yadda ummie keta mata godiya itama cikin murmushi zee kecewa babu komai ai allah shine abin godiya kasa janye idanu Deen yayi akan zee, gani yake kamar mafarkan daya sabayine kamar ba dagaske ita yake gani ba komai nata nanan her geogous smile, her melodious voice, her breathtaking beauty sanye take cikin wata doguwar hijab harqasa milk colour, fuskarta babu makeup sosai amma she looks so cute ahankali yakejin yadda zuciyarshi ke melting in emotions ga yadda zuciyarshi ke bugu sosai linkin yadda takeyi ada A bangaren Mussadiq ma ita yake kallo dan murmushi na forming agefen bakinshi wanda duk kwakwarka baka iya gane yanayi saishi dakeyin abinshi yadda zee ta basar ta hanyar avoiding qara kallon gefensu yabashi dariya, irin wannan dabi'un nata na Jin kai da class yasa tunfarko tafara burgeshi ahankali yayi gyaran murya sannan yace "hyy good afternoon" ko bata juyo ba ta gane mai muryar kuma tasan daita yake amma saitayi kamar bata saniba don saima kallon Aysha tayi cikin murmushi tana mata magana "yaya namiki magana ummie" inji Aysha tana nuna Mussadiq da qarfi tayi maganar so kowa yaji hakan yasa zee juyawa ta kalli saitin data nuna maimakon idanunta sufada akan Mussadiq din saisuka sake sauka Acikin na Deen da haryanzu ita yake kallo saurin sake janye idanun tayi tana jin yadda zuciyarta taqara bugawa da qarfi "hmm hyy" tafada ahankali batareda taqara kallon gefensu ba "thanks so much for your effort, words can't express our gratitude to you, jazakillah biljannah" inji Mussadiq yana kallonta "amin, thanks too" ta amsa batareda tasake kallon gefensu ba saikuma ta tashi tsaye kamar wadda ke kan allura ta riqo hannun Aysha "let's go upstairs" tafada tana janta "gulma zakuje yi ko?" inji ummy cikin tsokana dariya Kawai sukayi suka tashi su ukun sukayi hanyar sama suka haye. ta qasan ido Deen yabisu da kallo harsuka haye saman wani sad feeling yaji ya mamaye zuciyarshi ahankali ya lumshe idanunshi ya bude yana jin wani daci daci a maqoshinshi sama sama ya cigaba da sauraron firar su ummie jiyake kamar yatashi yafita ko yadanji sauqin Abinda yakeji a zuciyarshi idan yashaqi iskar waje kamar Mussadiq yasan meke ranshi sai ji Deen yayi yana excusing kansu akan cewa zasu dan fita waje jin sun amince yasa Deen saurin miqewa kamar dama akan qaya yake sauran ma suka miqe suka fice wajen atare wajen qarafunan da aka qawata entrance din yanufa yana dafawa yayi inhaling iskar dake kad'awa mai sanyi sannan yafesar qarasowa Mussadiq da habeeb dake bayanshi sukayi suma shiru wajen ya dauka yayinda Deen yakafe harabar wajen da kallo da idanunshi dasuka sauya launi abun da matuqar ciwo ace kuna under roof daya da wadda kake matuqar so da bege amma ko kalma daya takasa shiga tsakaninku ga yadda yaga tanayi ma kamar batama ganeshi ba don ko kallon kirki batayi mashi ba, she looks so okay and calm kamar ma ganinshin be tunamata da komai ba kodai dagasken tayi aure ta manta dashi? tayiwu nan din gidansu mijinta ne, tayiwu Abbu da ummy iyayen mijinta ne, then waye mijin? daidai nan sukaji anyi horn abakin gate atare duk suka kalli saitin gate din daidai lokacin da shima maigadi yaruga don zuwa budewa cigaba da kallon wajen sukayi har aka bude gate din wata ash colour mota ta danno kai tashigo ciki direct parking space tanufa tayi parking kauda kai Mussadiq yayi yana dan ta6e baki don ko ba'a fada ba yasan ko waye bude kofar akayi a bangaren driver aka fito sannan aka maida aka rufe da kallo Deen yabi aymaan daya zagayo ta dayan side din motar ya bude backseat ya fiddo briefcase dinshi maida kofar yayi yarufe ya kulle motar sannan yajuyo hannunshi daya riqeda briefcase dayan kuma rataye da farar lapcoat dinshi hada idanu sukayi da Deen dake kallonshi har lokacin Dan dakatawa aymaan yayi da tafiyar don beyi expecting ganinsu ba saikuma ya cigaba da tahowa yana janye idanunshi daga na Deen Deen dai cigaba da kallonshi yayi har ya qaraso, babu irin tunanin dabaizo mashi ba arai akan aymaan ganin ya kusan qarasowa yasashi dan janye idanu shima yana dan lumshesu yana Jin yadda zuciyarshi kemashi wani irin zafi da sallama aymaan ya qaraso wajen yana Dan kallonsu atare duk suka amsa suna dagowa suna kallonshi banda Mussadiq daya juyar dakai ma dukda shima ya amsa sallamar "likita bokan turai" inji habeeb cikin washe baki murmushi aymaan yayi yace "kune agidan namu?" "eh wlh barka da dawowa" inji habeeb yana Bashi hannu musabaha sukayi aymaan na amsawa da barka dai shima Deen danne zuciyarshi yayi yadanyi forming murmushi yabashi hannu "welcome" yafada ahankali "welcome too" aymaan yafada sunayin musabahan "why are you here?" inji aymaan batareda yako kalli gefen Mussadiq ba bare su gaisa "yanzu muka fito ai" inji Deen kafin susake magana sukaji muryoyin su ummy zasu fito duk atare suka juya daidai lokacin dasu ummie suka fito harda su zee suna fira cikin wasa da dariya "A'a Dr, andawo?" inji ummie don ta shaidashi murmushi yasaki sannan yadan matso yana gaidata cikin girmamawa amsawa tayi cikin kulawa tana tambayarshi ya aiki da alhamdulillah ya amsa yana tambayarta ya qarfin jiki amsa mashi tayi da da sauqi sosai ko bega alama ba cikin dariya yace eh yaga alamu ma ba alama bama kadai duk dariya sukayi banda Deen da Mussadiq da abin bewani basu dariya ba shidai Deen sai kallon aymaan yake akaikaice yakasa janye idanu akanshi Kasancewar idanunshi na akanshi yasa yaga lokacin da aymaan ya dagawa zee gira daya itakuma tayi murmushi shyly tana kauda kai shima murmushin yayi yana binta da wani kallo sauke idanunshi Deen daga kansu yana jin zuciyarshi na yin jingim, jiyake kamar an doramashi qaton dutse akai itadai Aysha bata ma yarda suka hada idanu da aymaan ba don sai kauda kai takeyi tunda talura da yadda yake wani shasha mata qamshi yana hade haden rai idan yaganta ta yanke shawarar fita sabgarshi itama sallama ummie tashiga yimasu bayan ta amshi address dinsu Ahmad akan suma zataje hargida tayimasu godiya, dama kuma already sunyi exchanging number akan zasu dinga kiran juna akai akai akan maganar Kaka har wajen motarsu suka rakasu Inda anan ummie tasa su Mussadiq suka fiffidomasu kayan dasuka zomasu dasu dafarko sunso qin amsa suna cewa yayi yawa gashi dama sun hado su aymaan da tilin kaya jiya nacewar da ummie tayi yasa akan dole suka amsa suna masu godiya sosai Nan sukayi sallama cikin aminci da fara'a kamar wadanda suka dade dasanin juna itadai zee tuni takoma ciki don tunda suka tsaya jayayya akan kaya ta silale ta fece suna nan har motar tasu ta tashi maigadi yabude masu gate suka fice da taimakon su aymaan suka kwashi kayan dasu ummie suka kawo suma suka koma ciki *** cigaba da kai kawo yake waya kare a kunnenshi, kallo daya zakamashi kasan cewa yana cikin damuwa sosai don sosai hakan ya bayyana a fuskarshi haryanzu amsa daya ake bashi, lambobin dayake kira kwata2 basa shiga Ajiyar zuciya ya sauke yana sauke wayar daga kunnenshi sannan yajuyo ya kalleta tana nan Inda take buga uban tagumi, idanunta harsun gaji da zubar da hawaye "innalillahi waina ilaihi rajiun.. meke faruwa ne haka? wlh haryanzu babu wayar kodaya acikinsu datake shiga" inji Alhaji Bashir cikin tsantsar damuwa "innalillahi waina ilaihi rajiun, allahuma arjini fi musibati, wannan wane irin abu ne? kuma harda number abokin naka dayaje wajenshi din bata shiga?" inji mami dake zaune kusada Kaka cikin damuwa "wlh harda ita, I don't know what's going on. dukkansu nambobinsu bata shiga" inji Alhaji cikin damuwa qara fashewa da kuka Kaka tayi cikin dakussashiyar muryarta wadda tagaji da kuka "dama saida raina yabani, saida naji banason tafiyar nan saida naji ajikina tafiyar nan ba alhairi bace, yanzu gashi ta tabbata innalillahi waina ilaihi rajiun, yanzu ina zansakaina ni ma'u? ya zanyi da rayuwata? wlh bazan iya rayuwa babu kyakyawana akusadani ba, wlh mutuwa zanyi" saikuma tafashe da matsanancin kuka Lailah dake kusada ita da damqe hannunta itama tana hawaye tun shekaran jiya wancan suke cikin tashin hankali kwata2 number Deen dana habeeb sunbar shiga gashi shekaran jiya yakamata sudawo amma haryanzu shiru babu su babu alamunsu ga numbersu bata shiga jawo Kaka mami tayi ajikinta tashiga bata baki tana kwantar mata da hankali amma yadda kasan qara zugata takeyi "banida kowa saishi, shima beda kowa saini. tunda ya bude idanu duniya ni kadai yasani nashi, bayan ni besan kowa ba bayada hayaniya, babu ruwanshi da kowa meyasa ake bibiyarshi da sharri? dama ni ban yarda da wannan abokin nashi dayace zaima aiki ba, aiki ace harsai kabar qasarka kaje Inda bakasan uban kowa ba? ai daji ba alhairi bane gashi beda lafiya, akasi kadan za'a samu ciwonshi na namonia (pneumonia) yatashi kuma idan yatashi dakyar yake sha kamar bazaiyi rai ba haka yakeyi abu goma da ashirin duk suntaru sun hau kanshi ya akeson yayi da rayuwarshi? yanzu haka muggai ne azzalumai sunsa yafito yazo qasarsu Inda babu yadda zaiyi dasu, yanzu yazanyi idan wani abu yasamu Kamal? yazanyi da rayuwata?" duk cikin kuka sosai take wannan xancen, tsabar kukan datasha muryarta ma bata fita sosai don tun shekaran jiya take abu guda ko abinci bata iyaci saboda tashin hankali "kiyi hqr Kaka insha allah babu Abinda zai faru dasu, ki kyautata masu zato na tabbata wani akasi akasamu qila amma insha allah zasu dawo cikin qoshin lafiya Kuma karki manta baban yaron abokinane, tsohon abokinane damukayi primary da secondary dashi daga baya kuma aka rarrabu insha allah mundin yana taredashi babu Abinda zai faru dashi na cutarwa" inji Alhaji cikin son kwantar mata da hankali "tsohon abokinka? tsohon aboki fa kace, waya san meya zama bayan rabuwarku? Kawai daga kunyi firamari da sakandiri atare shikenan saika yarda dashi kusani tura jikana wajenshi? wayasan meya zama bayan rabuwarku? ai muggayen mutane.sai daga baya suke zama mugaye bawai la'akari za'ayi da yarintarsu ba" "yanzu dai insha allah daga nan zuwa gobe xan tabbatar nasamo mana information.ko yaya ne akansu, don allah ki.kwantar da hankalinki Kaka, jifa yadda kika koma ko abinci fa bakya ci sai aikin kuka. Balarabe yanzu babu Abinda yafi buqata wanda yafi addu'a, ki kwantar da hankalinki Kaka" inji Alhajin cikin rarrashi "kiyi hqr Kaka mu cigaba da kyautata musu zato.insha allah zasu dawo garemu cikin qoshin lafiya, mu cigaba dayimasu addu'a insha allah zasu dawo garemu cikin aminci" inji mami haka dai suka taru sunata rarrashin Kaka da kwantar mata da hankali Lailah kau na gefe itama damuwa ce rubuce koina a fuskarta, bata jin tana iya jurewa idan wani abu yasamu Balaraben ta, fatanta allah ya kareshi aduk Inda yake ya maido masu shi lafiya. *** Washegari su ummie sukaje gidansu Ahmad Inda su shigar dare ma sukayi musu don saida suka ma kirasu saboda dama sun amshi contact dinsu awajen su abbu sosai su iyayen Ahmad sukaji dadin zuwan nasu Inda anan sukayiwa juna tarbar mutunci godiya sosai ummie tashiga yimusu suma tana samasu albarka musanmman ma Ahmad sosai suma suka nuna babu komai ai d'a nakowa ne suna kuma tayasu murnar sake saduwa Ahmad kau fita dasu Deen yayi waje Inda suka samu wani tent sukayi zamansu suna fira abin mammaki saigashi tasu tayi saurin zuwa daya da Mussadiq don nan da nan suka jiki da juna kan kace me sunyi nisa a firarsu wanda mostly ta Abinda yashafi aikinsu ne wato Business shidai Deen becika sakamasu baki ba don mostly besan akan me suke magana akai ba daga baya ma tashi yayi ya koma gefe ya tsaya yana bin harabar gidan da kallo yana feeling daddadan iskan dare dake kadawa gabadaya daga jiya zuwa yau duk ya chanza yakoma kamar bashi ba sosai damuwa ta bayyana a tattare dashi dukda iya bakin qoqarin dayakeyi na 6oyewa yakasa mantawa da image din Zainab, zuciyarshi taqi bashi sukuni dukda yana tunanin da aure akanta kuma auren wannan likitan yasan indai har tanada auren what he's doing was wrong don it's very wrong kadinga tunanin matar wani saidai yarasa dalilin dayasa yakasa tankwara zuciyarshi akan haka don with every passing minute tunaninta qara addabarshi yake soyyayarta kuma qara qaruwa takeyi hakan yasa duk yabi ya susuce yarasa Abinda kemashi dadi ahakan har lokacin tafiyarsu tayi suka kamo hanyar gida a hanya ummie taita tambayarshi meke damunshi don duk yadda yake qoqarin 6oye damuwarshi musanmman ma agabanta saida tagane yana cikin damuwa murmushi Kawai yakeyi yace babu komai yagaji ne Kawai haka ummie ta kyaleshi ba don ta yarda gajiyar bace saidai bata takura mashi ba suna isa gida ta kadasu part dinsu wai suje su kwanta tunda duk agajiye suke musanmman ma Deen din koda suka shiga part din nasu duk shirin barci sukayi kowa yanemi lafiyar gado ya kwanta bayan sun.kashe wuta Deen dai dama ba barci yakeji ba don haka kwance yake Kawai staring to dark space ya dade sosai ahakan don dare yayi ma sosai don koina yayi tsit, kamar.daga sama yaji muryar Mussadiq nacewa "she's not married" shiru ya ratsa dakin nawani lokacin kafin wutar bedside lamp yakawo sanadiyar kunnawa da Deen yayi "bakayi barci ba?" inji Deen yana kallon side din Mussadiq Kasancewar kowa dama da bed dinshi sai alokacin Mussadiq yajuyo daga juyamashi bayan dayayi "kaima ai bakayi ba" yabashi amsa "me kace yanzu?" inji Deen "nace batayi aure ba" Mussadiq yabashi amsa shiru Deen yayi yakura mashi ido for sometimes sannan yace "tayaya akayi kasani?" "Ahmad ya gayamin, she's not married amma she will be soon idan kayi sake" yafada yana gyara kwanciyarshi shiru Deen yasakeyi na wani lokaci dagaske batada aure? kenan he still has another chance? amma meyasa yace zatayi soon idan yayi sake? "meyasa kace hakan?" inji Deen "saboda akwai masu harinta" Mussadiq yabashi amsa "masu harinta? su waye?" inji Deen yana kallonshi beson ko dauke ido akanshi "kai yanzu baka gane wannan annoying likitan sonta yake ba?" "ni dafarko nayi tunanin shine mijin nata ai" kya6e baki Mussadiq yayi "Zaidai zama idan kayi sake, sonta yake na dade dasanin hakan kuma he can do anything to win her heart don haka kanada babban aiki agabanka" shiru Deen yayi yana tunani yes it's possible ace aymaan son zee yake, bazai manta da kallon dayayi mata ba rannan, the look is something else, gashi the guy is perfect atakoina, ga kyau ga ilimi ga gayu he can easily win any girl's heart saiya tsinci kanshi da comparing kanshi dashi da me da me yafishi? shima aymaan din dame dame yafishi saidai beyi nisa a comparison dinba zuciyarshi ta tuna mashi da matsayinshi awajen zee yanzu zee yanzu ba kallon wancan Deen din nata take mashi ba, yasan kallon mayaudari take mashi, maqaryaci maci amana tunawa yayi da yadda tanuna halin ko in kula dashi ranar nan yitayi ma kamar batasan da wanzuwarshi ba awajen wataqila ma ta tsaneshi ko ganinshi batason yi, gashi shikanshi kunyarta yakeyi, tayaya ma zai iya sake tunkararta? me zaice mata? dawane ido zai kalleta "kayi shiru" inji Mussadiq jin shirun yayi yawa "Mussadiq banajin inada wata dama kuma, banajin zee zata sake saurarata bare tasake bani wata dama, tunkararta da niyyar sake samun yardarta is just a lost battle, bazanci nasara ba" Dan dagowa Mussadiq yayi yana kallon Deen a mammakince "wait.. wai kana nufin harka sare kafinma ka gwada sa'arka?" girgiza kai Deen yayi "meye amfanin gwada sa'ar da kasan baxakayi nasara ba? nasan zee bazata ta6a qara yarda dani ba, nasan yanzu haka ma ta tsaneni" shiru Mussadiq yayi yana kallonshi har lokacin da unknown expression a fuskarshi can yadan saki murmushi yakoma ya kwanta yana cewa "good... kace yanzu nadawo cikin game din kenan" kallonshi Deen yayi "kamar yaya kadawo game?" murmushi Mussadiq yayi "dama ina cikin game din ai, bayyanarka dakuma jin cewa kaima kana ciki yaso sani janyewa amma yanzu no need, am still in" kallonshi Deen yake cikin rashin fahimta can yace "meaning?" juyowa Mussadiq yayi yadda zasu fuskanci juna sosai yace "meaning ina sonta and zan cigaba da trying wajen winning heart dinta" wara manyan oily eyes dinshi Deen yayi "what?"...✍? Ummin Fasihu🧚🏻‍♀? 8/2/21, 9:45 PM - Buhainat😝: *🙍🏻‍♂️DEEN🙍🏻‍♂?* *089* Dan murmushi Mussadiq yayi ganin irin kallon da Deen kemashi "yes, you know what? Abinda bakasaniba shine a rayuwar nan idan bakayi kau ban wuri akeyi, idan kai kana iya wasa da opportunity dinka wasu irina baxasu iya bada even the slighest chance wajen su6ucewar damarsu ba, what you don't know is kafin zuwanka nafara developing feelings akanta, banace inamata mahaukacin so ba irin wanda bazan iya rabuwa daita ba ko idan narasata zan shiga wani hali, I just like her, attitude dinta na burgeni sosai and idan so samune zanso mallakarta amma zuwanka dakuma jin labarinku yasani jin cewa babu wanda ya cancanceta sama dakai and na yanke shawarar barmaka ita amma tunda you can't do it ina tunanin gwara nadawo cikin game din don bazan iya haqura wannan Dr din yasameta ba just like that" yana kaiwa nan yajuya ya gyara kwanciyarshi yarufe entire jikinshi da bargo kasa dauke idanu Deen yayi akanshi still cigaba yayi da kallonshi yanajin yadda zuciyarshi tayi wani irin jingim wait, is Mussadiq serious? this is crazy! kenan yana nufin yana iya soyayya da wadda yakeso? saiya tsinci kanshi da kishin Mussadiq fiyeda aymaan sai jiyayi yana iya haqura da zee yabarwa aymaan amma badai Mussadiq ba maimakon firar dasukayi yasashi jin sauqin Abinda yake damunshi sai abin yaqara worsen daren ranar be runtsa ba yadda yaga rana haka yaga dare. Washegari Deen yatashi yarasa Abinda kemashi dadi aduniyar nan da zancensu da Mussadiq ya kwana kuma haryanzu zancen yaqi sakinshi shidai gani yake kamar wasa yakeyi, ai da kunya ma yaso wadda yakeso saidai kuma bega alamun da wasa Mussadiq yake ba, what if dagaske yake? ga mammakinshi sai yaji yafi kishin Kasancewar zee da Mussadiq bisa ga aymaan ina? bazai yiwuba, bazai ta6a barin hakan ya yiwuba. Mussadiq kau hankali kwance yake hidindimun gabanshi yana lura da Deen amma yayi kamar besan yana yiba yayinda deep down yake mashi dariya lallai mutum ga kishi ga tsoro, zai koyamashi hankali ne ahaka akayi kwana biyu cikin kwanaki biyun nan Deen ba qaramin shiga damuwa yayi ba he so much crave to see Zainab don wani lokacin saiyaji kamar yayi tsuntsuwa yaganshi agabanta yaga fuskarta koda na second daya ne sosai kewanta da begenta ke nuqurqusarshi agefe guda kuma haryanzu hankalinshi yaqi kwanciya adalilin maganar dasukayi da Mussadiq cikin kwanaki biyun nan babu wanda yasake tada ma Dan uwanshi maganar amma Deen yakasa sukuni don harwani sanyama Mussadiq ido yayi yana studying movement dinshi A bangare guda kuma kewar Kaka ke addabarshi, he missed her so very much, yanaso yaji muryarta koda sau dayane amma ya haqura yaqi kiranta ko bude wayarshi don gani yake it's not yet time. sosai shaquwa da sabo yashiga tsakanin Deen da sabon family dinshi don kowa jidashi yakeyi most especially ummie don ko motsi yayi saita tambayi akwai damuwa? yadda ummie take nuna tsantsar damuwarta da qaunarta akanshi yasa yake iya qoqarinshi wajen 6oyemata halin dayake ciki na damuwa Aysha ma sosai jininsu ya hadu da Deen don sunfi shiri ma dashi busaga Mussadiq she's very fond of him don muddin tana nan to kodayaushe suna tare tana mashi fira kokuma kagansu tana koya mashi larabci shima he's very fond with her don kusan dabi'unsu daya daita habeeb kau anzama dan gida, shi yana waya da mutanenshi na 9ja dukda baya yawan barin wayar akunne gudun kiran Alhaji Bashir shi sosai qasar tayimashi don kusan kodayaushe saiyasa Mussadiq ya hadashi da driver ya dan yawata dashi yaga gari ko kadan qasar bata isheshi ba bare yaji yagaji da zamanta, he's living happily Acikin familyn Deen din. fitowa Deen yayi yana dan strolling yana qarewa gidan kallo haryanzu mammakin irin girman gidan yake don yadda kasan unguwa guda ce tsari da kyawun gidan baya misaltuwa don shi tunda yake beta6a gani ko yataka gida mai irin kyawunshi ba ahankali yake tafiya hannayenshi zube a aljihu sosai Deen yaqara chanzawa cikin yan kwanakinnan, yaqara wani irin kyau da fresh ga kwarjininshi daya sake fitowa sosai. habeeb bayanan as usual, yafita yawon zaga gari dinshi shikuma Mussadiq yana garden yana wasu yan ayyuka a laptop, Aysha kuma tana school. gajiya dayayi dazama shikadai yasashi fitowa shima don yadan sha iska yana tafe ma'aikatan gidan na gaidashi yana amsamasu da dan murmushi harya qaraso garden din garden din ya hadu ga trimmed grass carpet tun daga farkon garden din har qarshe ga wani dan swimming pool daga can kusurwar garden din mai kyan gaske ga shufke shufken kayan itatuwa daya qara qawata garden din yakuma bada shades ga garden din wani iska mai sanyin dadi ke kadawa a garden din, garden din is very quiet sai dan kukan tsuntsaye da akeji akai akai ahankali yanufi Inda Mussadiq yake zaune ya duqufa akan aikin gabanshi Mussadiq besan da shigowarshi ba garden din ba saida yaji motsi akusada shi dagowa yayi daidai lokacin da Deen kejan kujerar dake facing dinshi ya zauna murmushi Mussadiq yayi mashi shima ya maida mashi martani "sannu workaholic" qara murmusawa Mussadiq yayi yace "yauwa ai kaima ka kusan zama hakan, lokacin kadan yarage yanzu haka chanza komai nakeyi yadda zai dawo da sunanmu mu biyu" kalloshi Deen yayi "ban gane ba" "yes, lokaci yayi da zamuyi running komai mu biyu" inji Mussadiq wani kallo Deen yayi mashi "cemaka akayi na iya business? karma kasoma don banada ra'ayin business kwata2" "hmm ai aikin gama ya gama mallam, nufinka ni,zan cigaba da running komai bayan gaka? impossible" "look seriously nifa banida ra'ayin business sam, is better ka cigaba da running abinka yadda kafara don ni bama shi na karanta ba" "me ka karanta?" "engineering" "wow! still ba'a makara ba ai sai ka karanci business din ai shima" "A'a bana ra'ayinshi kwata2 ne, koda xanyi wani abu to engineering zan cigaba dayi" "wane irin engineering ka karanta?" "constructional engineering amma yanzu mechanical engineering nakeso nasake karanta nayi zurfi akai" "why?" "saboda nadan fara aikin mechanic ne kwanakin baya and I love it, zanso na cigaba" "yaushe kayi aikin mechanic?" "bayan rabuwarmu da zee" shiru Mussadiq yayi saikuma yadan kada kai "not bad but still komai saiya koma da sunanmu mu biyu afterall dukiyar ai batawa bace ni kadai tamuce all, aikina Kawai juyamana ita" "nidai A'a, continue the way it is please, karka chanza komai" Dan ta6e baki Kawai Mussadiq yayi ya cigaba da Abinda yakeyi besake tanka mashi ba shiru yadan ratsa wajen "kenan ka iya gyaran motoci?" Mussadiq yayi breaking silent din murmushi Deen yayi "ko kanada wadda za'a gyara maka ne?" murmushi shima Mussadiq yayi "yanzu kam babu amma za'a samu soon, amma you're talented kuma kace da kana carpentry?" kada kai Kawai Deen yayi bece komai ba "wow! ga carpentry ga mechanic ga singing, duk kai kadai?" murmushi Kawai Deen yayi "wane kafiso ciki?" shiru Deen yadanyi can yace "gaskiya mechanic" "why?" "hakanan Kawai aikin gives me joy" Dan shiru Mussadiq yayi cikin tunani sai yace "what of ka koma school ka karanci mechanical engineering din kaga saika bude wani forum kafara displaying dinshi, waya sani ko nan gaba kama dinka qirqirar motocin dakanka?" dan wara idanu Deen yayi "really?" "yes, wannan aikin is very talented something, kaga tunda.kace it gives you joy allah kadai yasan Abinda zaka iya creating if you put it to work" "wow Ka kawo shawara, Kawai haka za'ayi" inji Deen cikin jindadi "but waqarka fa?" "nifa inayin waqa don nishadi ne, banma ta6a tunanin zanci abinci daita ba" dariya Mussadiq yayi "ikon allah kenan ai, amma twinnie kanada basirori wlh, idan babu wannan akwai wannan idan babu wannan akwai wannan duk Inda tafadi shaa nikau daga business sai business, dull me" murmushi Deen yayi yace "business din ma,ai aikin qwalwa ce da basira, babu aikin datafi chaza qwalwa da kai kamar business, you're talented too" murmushi Kawai Mussadiq yayi ya cigaba da danne dannenshi "ya kamata nafara zazzagawa dakai companies.dinmu" inji Mussadiq hankalinshi akan screen din laptop din dan ta6e baki Deen yayi don wannan bashi ne damuwarshi ba asali ma Abinda yakawoshi wajenshi daban shiru wajen yadauka nawani lokaci kafin Deen yace "kaje wajenta?" tsaida Abinda yakeyi Mussadiq yayi for a moment sannan

Chapter 71 of 81