Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
a qurarren lokaci basu shiryi tafiyar ba. Ranar Juma'a aka daura Auran, na Yakubu aka fara daurowa da safe a can Rigarsu Balaraba suka dungumo da Amarya da yan uwanta, se bayan sallar Juma'a aka daura na Audu da Bara'atu. Murna kam ba'a cewa komai a gurin Dada da tasha kwalliya cikin kayan da Audu ya dinka mata, haka qannensa Bilki da Aisha sun sha Anko Baballiya kuwa shaddarsa iri daya data angwaye wanda dama Audu ya dinka musu da niyyar suyi fitar bikin Yakubu se gashi abu yazo a daidai. Qarfe tara suna can Majalisa da Abokanai ana ta shaqiyanci sega Baballiya da gudu yake fada musu wai an Kawo Amaryar Yaya Audu. Kowa yayi mamaki dan ko jiya da yaje gurinta seda suka sakeyin maganar tace masa Innarta tace se daga baya zata tare tunda abin yazo babu shiri Babanta kuwa Magriba nayi ya tada ballin se an kaita, an ce masa babu daki yace ta rakuba a na Babarsa da ya san be shirya auran ba yayi haka yan uwa suka rakota ita kam ko a jikinta dan ko cikin Rumbub gidan aka ce ta zauna shiga zatayi tunda dai burinta ya cika ta Auri Audu. A dakin sa aka sauketa da qawayenta da zasu kwana, daren ranar Audu tunanin yanda zeyi kawai yake, da yasan za'ayi haka da ya ququta ko babu dabe itama an tayar mata da daki ko ciki dayane, haka dai gari ya waye, da hantsi yan uwan Balaraba suka gama mata jere tsaf irin na yar gata harda Kumbo nan suka fara shirin tafiya bayan sun qara damqa Amarta a hannun yan uwan Yakubu. Daga bangaren Bara'atu dai babu wanda yazo se qawayenta da suka kwana. A can gidansu ana ta taqaddama tsakanin Babansu da Innarta akan yace ko tabarma baze kai mata ba tunda bata bi abinda yake so ba, ita kuma ta rantse se yayi, da yasan haka ne seya bata lokaci ita da take son auran zatayiwa yarta komai amma yanzu banda kwanuka babu abinda ta tanada dan haka dole ya fito da kayan gado danbaze barwa yarta abin gori ba bayan ba rasa abinda zeyi mata yayi ba gashi tun rana bata daga ba labarin jeran da akeyiwa Balaraba ya fara bazuwa a gari dan itama Babanta Attajirine a rugarsu kuma itace Auta a mata dan haka sun mata bajinta. Hayaniyarsu har dakin Ilu Abokin Audu da suka kwana a gurinsa maqota suke dasu Bara'atun kuma dakinsa jingibe yake da dakin Soron su Bara'atu inda Innar tata da Baba suka shiga wai suna sirri saboda yan biki dake ciki se gashi Audu yaji komai, sulalewa yayi ya tafi cikin garin Kumbotso saboda yafi masa kusa akan yace ze tafi Kano, yasan gurin lokaci lokaci yana zuwa dan har Aboki yake dashi kai tsaye gurinsa ya tafi bayan sun gaisa be bata lokaci ba ya zayyane masa abinda yake tafe dashi na batun kayan daki saboda garinsu Babu Kafinta meyin kayan katako, gadon qarfe kuma a gurinsa shi da yake zaune a birni yake ganin kayan gado da akeyi na Alfarma ya fitar masa yayi. Nura ya kaishi gurin wani Kafinta da ake ji dashi a Kumbotso dan a Kano ya koyo aiki wasu kayan ma daga can yake dakkowa ya kawo. Ya numa masa wani Gado Lamba 1 da Kobud dinsa me biyu ta yan gayu dan harda mudubi a jikin murafenta ga kuma mudubi shima me durowa uku a jiki kayan sunyi kyau gasu Ruwan Hoda irin kalar da Bara'atu take so sedai kudin da aka saka musu a yanayin da yake ciki sun masa yawa ga Katifa da ze siya da pillo, aka tirza aka tisa dakyar dai kaya suka siyu, shima seda Nura yayi masa ciko daga baya zasu warware tunda suna haduwa A Kano, aka loda masa su a A kori kura da dundumemiyar katifa da pillow biyu harda Abin shimfida dana rufa ya kama hanyar gida. Sanda ya dawo yamma tayi rana na gabda faduwa, a waje ya bar masu mota ya shiga ciki nan ya tarar da Dada da yan uwanta da basu wuce ba suna ta kiciniyar kwashe yan kayayyakinta ana shigar dasu dakinsa nasa kuma suna waje da alama dakinta za'a mayar dasu daman ba wani shirgi ne dashi ba Gadon qarfe ne da wata Katifa da yake ta saka ranar canzata tunda ba kullum yake kwana a kai ba se yayi ta mantawa se akwatinsa guda daya. Kunya ta kamashi yanda aka faka kayan a gefe, kenan Dada dakinta zata basu kuma wannan Gadon za'a sakawa Bara'atu "Yawwa ga Audu" Matar Yayan Dada da basu yada zumunchi ba ta fada dan tun safe ake nemansa an rasa shi ga babu waya bare aji inda ya tafi. Dada ta yafa gyale ta yafice shi suka yi soro, Goggo Fadi, Maryo da sauran Maqwafta yan tsogumi da suka baza tabarma, sun gama kallon dakin Balaraba suka fito aka kafa gulmar ana jira aga me za'a sakawa Bara'atu ita kuma, "Koda yake ina dakin ma?" Fadar Goggo Fadi, Maryo ta karkace baki tace "Dukdai qaryar Birnin ta qare, ayita zuwa ana burga a bikin jama'a ga nashi ya tashi ko dakin da za'a ajiye Amarya babu idan da gaske da kudin ai daga tsaida rana yaci a dora ginin Bulon sumunti ma bana qasa ba" suka tafa da matar Hashimu dake kusa da ita. Dada kuwa suna zuwa zaure tace "Ina ka tafi Audu bayan kasan halin da ake ciki babu inda dan uwanka bw zaga a garin nan ba amma ba'a ganka ba Jama'a har ana cewa ka gudu". Dariya ta kwace masa yace "Na gudu kuma Dada naje ina kamar wani mara gaskiya?" "Oho dai duk ba wannan ba, Hasiya tazo ta gaya mun Baban Bara'atu yace bazeyi mata kayan daki ba, da ace mun san da tariyar nan da tuntuni mun fara shiri amma yanzun ma se ayi amfani da abinda Allah ya hore, na bar muku dakina tunda kaga yafi girma ni se na koma na Malam, Babana kuma ya shiga cikinsu Idrisa (Yaran Yaya Baba da suke zama a gidan) kafin muga abinda Allah zeyi, idan an kwana biyu filin can na gefe seka shigo mata dashi ayi bandaki da gurin girki irin na Yayanka kaga shikenan a sannu Allah ze hore duk kuyi muhalli irin wanda kuke buri, wancan gadon naka ma gaskiya Audu ba'a bawa Amarya ba ga Katifa duk Babana yaci qaniyarta idan da sarari ko katifa ce ka siyo da ledar daki a shimfida mata". "mma Dada da baki fita daga dakinki ba wancan dinma ya isa ta lallaba kafin muga abinda Allah zeyi" Audu ya fada, Dada ta juya tana cewa "Kaje dai muga ko katifar da Ledar zasu samu" ya tsayar da ita yana cewa "Shaf na manta da Ledar wlh sedai ko Bilki taje yanzu inda za'a samu, leqa kiga ga kaya nan dai na samu dukda dai nasan basu kai yanda akeyi ba". Dada ta leqa, baki ta saki ganin kaya tuni kuma yara da matan Unguwa da sukazo shiga gidan suka baibaye motar ana kallo dan ba'a taba ganin irinsu a garin ba. "Audu, Kano kaje har ka dawo wannan kaya haka?" Dada ta fada cikin mamaki, Audu yayi murmushi yace "A turo Bilkin ta samo Ledar tunda ita akw fara shimfidawa ko anjima zan miki bayani. Dada ta koma ciki bakinta a washe yaqi rufuwa ta tura masa Bilki. Gidanta ta tafi ta dakko ledar data siya take shirin canza ta dakinta bata rigada ta shimfida ba dama ta bari se an gama hidimar Biki nana da nan aka hadawa Amarya daki ga gado na Alfarma kamar wani gidan zoo haka mata keta leqawa masu gyaran daki na korarsu dan sun hanasu yin aikinsu yanda ya kamata tuni kuma labari yakai wa Innar Bara'atu, ta fashe da kuka tana cewa "Allah na gode maka daka nunawa masu gulma da munafurci qarshensu" tun safen suke qullawa da warewa da yan uwanta akan yanda za'ayi, ta hada dan abinda ya samu, Gadon katako taso tayiwa Bara'atu dan ance Amaryar Yakubu ma shi aka mata amma abinda suka hada baze isa ba kuma wanda za'a tasa ya tafi Kumbotso a yammar shine aiki har sun saddaqar a dauki na qarfen anje shima me siyarwar wai baya nan abin duniya duk ya mata yawa sega wannan labarin farin cikin dukda tasan wata sabuwar gulmar za'a samu ace Miji ne yayi mata ko babu komai sabon salo ne dan babu yarda Miji yaso haka a garin har yayi mata kayan daki. Page Kafin dare dakin Amarya Bara'atu ya dauki haske bakin yan gulma yayi muqus qiri qiri Goggo Fadi ta kasa boye baqin ciki da wannan abu ta ringa yada magana wai Dada tadai tsananta binciken inda Audu yake samunkudi haka ya za'ayi ace daga fita ya dawo da irin kayan nan waya sani ma ko wasu ya bige ya dakko? Ita dai Dada tun tana mamakin lamarinta harta dena, a zamansu idan aka ce mata wata rana Goggo Fadin zata zama yanda take a yanzu qaryatawa zatayi se gashi da ido ta take gani bawai fada mata akayi ba. Innar Bara'atu ta aiko da kwanuka da tayi tanadi aka jere masu reras tun daga qasa har sama. Tana can bagaren Balaraba tun safe Dada tace suje can da qawayenta suyi wanka suka karya nan suka hade da qawayen Balaraba ana ta raha har dare kafin suka fara shirin tarar Angwaye. A bangaren Balaraban tayi wanka tsaf ta shirya cikin daya daga kayan daya dinko mata daga Kano, Balaraba ta bata Humra ta shafa dan ita dai babu shiri aka hankadota, suna zaune Aisha tazo tace au koma can an gama gyara mata daki suka bar Balaraba da nata qawayen can kuwa se santin daki sukeyi qaunar Audu ta sake linkuwa a zuciyarta ko banza ya fitar da ita kunya ya mata abinda tasan ko Baffabta bazeyi mata kamarsa ba. Se qarfe Goma Aka rako angwaye, Yakubu aka fara rakawa tunda shine babba kuna duk Abokanan nasu daya, bayan barkwanci da abinda aka saba akayi siyan baki sukayi musu yar nasiha da tunasarwa akan aure da qalubalen dake ciki dan gaba daya Abokanan da sukayo rakiya su bakwai mutum daya ne mara aure wasu da yayayensu dan haka sun san yanda lamarin yake nan akayi addu'a suka sallami yammata wadanda zasu tafi gidan Fadima Amaryar da su Balaraban suka kawo garin harta hadu da Yakubu. Daga nan aka raka Audu, basu jima ba nan ma akayi addu'a kowa ya watse suka raka Abokanan qofar gida kamin suka koma ciki, Yakubu ya shige bangarensu bayan yayiwa Audu sallama ya sakace qofa, Audu ya tsaya kawai yana tunani, duk yanda yaci burin ranar auransa gashi bata zo masa a yanda yake mafarki ba. Lissafi yake yanzu Yakubu Asirinsu a rufe suna da komai a bangarensu babu wanda ze san me suke ciki amma shifa? Rufin asirin ma bandakin da yake kusa da ace har yanzu da tsohon suke Amfani da tareren yayi yawa. Haka ya shiga daki jiki babu karsashi sosai ya saka a ransa bazeyi komai ba har se randa ya samu yanda yake so dangane da muhalli. Bara'atu ko harta fara gyangyadi akan sabuwar Katifa daman jiya ba wani baccin kirki sukayi ba kuma sun tashi da wurwuri motsinsa ya farkar da ita ta shiga jan mayafi tana boye fuska. Ya bude musu Kazar da suka shigo da ita dakyar ta iya ci saboda Yunwar da takeji taci kadan tasha ruwa tace ta qoshi. Qofa yaji ana kwankwasawa, seda ya tambayi waye yaji muryar Inna Hasiya, ya bude ta miqo masa wani qaton Flask din ruwan zafi wanda ya siyawa Dada a Kano guda biyu saboda lokacin sanyi dukkansu cike da ruwa tana cewa "Da akwai na sirki nan cikin bambu", ta sake miqo masa wani kantamemen baho irin na wankan Jego tana cewa "Allah ya tashe mu lafiya". Kamar wani munafuki haka ya tattara bahon da fulasan gefe ya ajiye ya kalli Bara'atu data takure a gefen gado kamar jinjirar kyanwa yace "Kiyi shiri ki kwanta dare yayi" Da "toh" ta amsa masa ta miqe amma duk ta diririce ta rasa abinyi fahimtar kamar kunya takeji yasa ya fita ya tsaya daga qofar dakin, yana fita ta bude jakar da aka sako mata yan kayanta. Doguwar rigar yadi me laushi ta ciro da qaramin Hijabi. A gurguje ta shirya, ta ninke wanda ta cire kafin ta haye gado ta duqunqune kamar me bacci daidai nan Audu ya shiga dakin. Shirin baccin shima yayi, ya hau kan gadon yanajin wani banbara kwai wai yau shine gado daya da mace. Dukda yanda yayiwa kansa Alqawarin baze tabata ba har se sunyi kebantaccen guri kamar nasu Yakubu amma ya kasa, cikin tattali da tsantsar So ya mayar da ita tasa, a cikin daren ya taimaka mata ta gyara jikinta kamar yar baby haka ta shige bahon ta gasa jikinta tsaf kamar yanda yayarta ta gaya mata kafin tayi wankan Ibadah dukda kunyar idon Audu haka ta shirya shi kuma ya juye ruwan bokiti ya fita dashi ya dawo ya goge gurin tas kafin ya sirka wani ruwan ya dauko fitila ya wuce bayi. Seda yayi wanka shima ya shirya kafin ya kwanta gefen Bara'atu da tuni bacci ya kwasheta, wani irin farin ciki da annushuwa yake ji, daman haka auran yake? Kai dole ashe Abokanan sa su ringa cewa Aure da dadi. Ya tuna Yakubu ma yana can yana kashe Arna qilan yanzu shi kadai kamar sabon kamu ya fashe da dariya a haka bacci ya dauke shi shima cike da nishadin samu Bara'atun tasa a yanda beyi tsammani ba. Kiran sallar farko ya farka dan ya rigada ya zame musu jiki tun suna qanana da an kira sallah Malam ze tayar dasu suyi nafila kafin lokacin Asuba su fita masallaci shiyasa jikinsu ya saba duk gajiya duk bacci basa tsallake wannan lokacin se sun farka. Motsin saukarsa daga gado ya farkar da Bara'atu wadda itama bata da nauyin bacci. Ta kasa kallonsa yayi murmushi yace "Ki kwanta, kiran farko ne". Seta tashi zaune sosai a kunyace tace "Ai bazan iya komawa baccin ba". Audu ya dakko baho ya zuba ruwan zafi ya sirka, ya sake hada wani a buta kafin ya kalleta yace "Toh gashi nan ko zakiyi amfani" yana fadar haka ya dauki wata butar daya cika da ruwa ya fita daga dakin dan bata sarari. Seda ya kalli bangaren Yakubu da suka garqame qofa Asirinsu a rufe babu wanda yasan halin da suke ciki kafin ya wuce Bandaki ya kama ruwa yana cikin daura Alwala aka haskoshi, ya kare fuskarsa tareda kallon inda hasken yake tahowa saga bangaren Goggo Fadi ne, da alama kuma inda yake take nufowa seya dauke kai yaci gaba da Alwalarsa harta iso kansa tana cewa "Har gabana ya fadi wlh na dauka gamo nayi" banza ya mata ya miqe ta sake cewa "Aa, angwayene har aka iya miqewa da farar Asuba? Kaga bayan gudan namune ya fara alamun fadawa shiyasa naji tsoron karna shiga da duhu na rufta kafin a kawo mun agaji ma qila na nutse ina Amaryar, ta tashi ko se an kawo Agaji?" Tsabar takaici harya tsaya ze bata amsar maganarta ta farko amma qarshen yasa ya wuce ba tareda ya ce mata komai ba, wai a kawo agaji ita dai tana tsufa amma se a hankali. Dakin ya koma lokacin Bara'atu ta fita daga ruwan data ji dadinsa sosai ta daura alwala tana tsaye tana tunanin yanda zatayi da ruwan ya shiga dakin. Kamar dazun ya sake juyewa a Bokiti ya dauraye ya fita dashi ya zubar can bakin rariya ya kife bahon qofar Dada tunda ya gama amfaninsa ya koma dakin, seda yayi Nafila kafin aka kira sallah dan haka ya dauki carbinsa ya fita daidai nan Yakubu ya fito daga bangarensa suka rankaya suka tafi masallacin duk su biyun babu me cewa komai suka zama kamar wasu surukai kowanne fuskar sa cike da annuri irin na sababbi Angwaye. Bayan an Idar da sallah Abokanan su suka tare su da tsokana, nan suka zauna har gari yayi haske kafin suka doshi gida seda sukaje soro kuma suka tsaya saboda jiyo muryoyin mata alamar kowa ya tashi har an fara hidimar gida. Audu ya kalli Yakubu kamar tababbu suka fashe da dariya lokaci daya harda duqewa kowanne shiyasan dalilin dariyarsa. Yakubu ya kalli Audu yace "Bazan iya shiga gidan nan ba kunya nakeji" "Ai gara kai daka sha kunu ka wuce ka sakayo qofa shikenan ka gama abinda zakayi a ciki ka fice ni kuwa komai zanyi akan idon mutane" cewar Audu. Shigowar Aminu ta sakasu shiga gidan dole yana ta tsokanarsu shima, a dakin Dada suka yada zango suka gaisheta kamar yanda suka saba, bakinta kamar ze yage saboda farin ciki, yau din wata ranace ta musamman a gurinta burinta ya cika na ganin Yakubu da Audu a matsayin magidanta sauran mata Autanta Baballiya da tasan ba lallai tayi tsahon ran da zataga wannan lokacin ba. Seda gari ya gama wayewa tangarau kafin kowanne ya koma dakinsa. Bara'atu na kishingide ya shiga ta miqe ya kalleta da murmushi yana cewa "Aa yi kwanciyarki Jaruma" Ta rufe fuska da Hijabin jikinta jin abinda yace wai jaruma, to jarumtar me tayi?" Muryar Inna Hasiya dake magana ta sakashi fita ya dawo ya kwashi fulasan jiya ya kai mata ya tambayi Bara'atu Qaramin fulas din Shayi ko Jug ta nuna masa inda suke ya dauka ya fita ya kaiwa Innan daga can ya wuce dakin Shafi'u inda yayi ajiyar kaya. Inna Hasiya tayi sallama Bara'atu ta amsa kafin ta shiga da fara'a Bara'atu ta miqe ta karbi kayan dake hannunta kafin ta duqa har qasa ta gaidata ta amsa tana tambayarta kwanan baqunta ita dai se murmushi take Innan tace mata "Ga ruwan wanka can a kewaye kije kiyo se ki karya sannu ko" ta fada cikin tausasawa. Kan Bara'atu na qasa tace "Toh Inna, amma Kwandon wankana yana bangaren Yaya Balaraba a can na barshi jiya" Cikin jin dadin Yayar da ta kira Balaraba dashi Inna Hasiya ta fita da zummar karbo mata, a hasashe dai Hafastu tayi dacen surukai masu tarbiyya da kuma kunya. Seda ta dauki abin karin su Yakubu wanda Bilki ta ware kafin ta kai musu ta kuma karbowa Bara'atun kayan wankanta. A bandakin ta tarar da Ruwa har bokiti biyu, tayi wanka me kyau ta gasa jikinta dan ruwan da zafinsu kafin ta fito tana sunne kai dan Inna Hasiya da Bilki na tsakar gidan, dab da zata shiga daki Goggo Fadi ta taho tana cewa "Aa Amarsu wanka akayi?" Bara'atu ta durqushe tana gaisheta ta amsa fuska washe da fara'a, Inna Hasiya da fuskarta ta hade bayan fitowar Goggo Fadin tace "Tashi maza kije ki shirya karki bushe". A dakin bayan ta shafa mai ta ciro wata yaluwar Atamfa me ratsin fari dinkin Tazarce riga ta wuce guiwa an tsagata daga gefe gefe se zani ta saka. Ta bude qaramin kwandon da aka zuba mata kayan kwalliyarta. A qyalle ta zazzaga powder ta shafa ta dakko jagira tana niyyar zanawa se kuma ta dakata. Kwalliyar Balaraba ta jiya ta tuna, daga ita har qaqayenta da sukazo daga ruga babu wadda zakaga dambareriyar kwalliya a fuskarta hoda kawai suka saka se kwalli da man lebe kuma sunyi kyau kodan kasancewar su fararene oho? Dukda cewar a ruga suke amma sun fita ita da nata qawayen wayewa ta ta'allaqa hakan da cewar garinsu Wailari yafi nasu kusada Birni har wasu daga cikinsu sukan kai tallar Nono cikin Kano qila a can suke gano kwalliya irin ta matan Birni wanda daman Audu yana kwatanta mata sam baya son wannan Jagira dasu jambakin da suke cike fuska dashi amma ita a ganinta idan ba tayi haka ba ba kwalliya tayi ba. Zuciyarta ta shawarta mata ta gwada simple kwalliya irin ta Balaraban dan haka ta ajiye jagirar, brush ta dauka ta taje girarta da take a cike me kyakykyawan yanayi kamar an zanata fitina take sakata dambara baqin jagira akai ta qarawa fuskarta da bata haske baqi. Bayan ta taje girar ta saka kwalli a dara daran idonta, bazata iya haqura da jambaki ba dan haka ta shafa kadan ta kawo man lebe me kyalli da Audu ya sako mata a kayan fitar biki ta dora akai ita da kanta ta ringa sakin murmushi ganin yanda tayi kyau, fuskarta har qyalli take cike da Annuri irin na Amare. Ta mayar da kayan kwalliyar ta feshe jikinta da turare kafin ta ware dankwari bayan ta gyara zaman ribbon din data tufke jelar Shukun da aka mata. Daurin Maryam Babangida tayi wannan kam gwance ita a gurin kashe dauri, ta ringa juyi a gaban Kwabarta me mudubi daga sama har qasa tana dariyar yarinta dan tayiwa kanta kyau Addu'a take Audu ya shigo ya ganta taji me zece. Motsin qofa yasa ta nutsu ta shiga neman farin gyalen data fitar tareda kayan. Audu ya shigo da sallama hannunsa riqe da Baqar leda babba kana gani kasan gwangwanaye ne a ciki ya kalli Bara'atu fuskarsa ta sake washewa zuciyarsa tacika da alfaharin kasancewar ta mallakinsa ita kuwa se sunne kai take na kunya. Ya kalli kayan karin da aka ajiye musu alamar bata ci ba yace "Kar abincin ya huce kizo kici" a kunyace ta zauna qasa, ya fitar da gwangwanin Madara Peak dana milo se sukarime iyali kwali biyu ya ajiye mata ya juya da ragowar yana cewa "Bari na kaiwa su Yakubu". Kicibus sukayi da Bilki, ta miqo masa Babban farantin silba da aka dora kwanukan samira guda biyu se ledoji farare da aka qullo Madara, Milo da sugar tace "Gashi farfesun Inna tace nata ne ita kadai ta ci ta shanye romon" ta fada cike da shaqiyanci tana kallon Bara'atun, ta dago kuwa ta maka mata harara, idon Audu ne yasa bata bata amsa ba tunda su din qawayene daman sun saba da caccakar juna. Audu ya karbi Farantin ya ajiye ya kwashe kayan shayin cikin ledar wanda yasan cikin manyan gwana gwanan da yake siyowa Dada duk sanda ze zo aka debo yace "Maida su na taho mana da namu mantasu nayi dakin Shafi'i" "Toh Yaya" Bilkin ta karba ta cigaba da tsayuwa dan so take ya fita ta tsokani qawar tata, karantarta yasa yace mata "Muje toh" ba yanda ta iya ta fita amma dai ze fita ya barsu a gidan yau kam Bara'atu ta banu a gurinta dan dalilin daya sakata kwana a gidan kenan ma. Tare suka karya da Bara'atun dukda yanda take ta noqewa bayan sun gama ya miqe yana cewa "Zanje dakin Shafi'i nayi wanka, idan kina buqatar wani abu ki aiko yara su gaya mun" "A dawo lafiya" ta fada tana miqewa itama bayan ta hada kwanukan da sukaci abinci dasu suka fito a tare bayan ta saka takalmi. Gurin da taga an tara wanke wanke ta ajiye na hannunta Audu kuma ya fita daidai nan Balaraba itama ta fito da nasu kwanukan tasha kwalliya kamar dai Bara'atun, suka sakarwa juna murmushi ta ajiye kayan hannunta kafin suka shiga gaisawa. Dakin Dada suka nufa tare suka tarar suma sun gama karyawa kenan Bilki na tattare guri Baballiya na kwance kamar gawar sababi yana tabara ko kunya bayaji waishi Auta. Inna Hasiya ta dana masa duka tana cewa "Dallah tashi ka basu guri su zauna", Dada da bakinta yaqi rufuwa se sannu take musu suka zauna kowacce na sunne kai suka shiga gaishe su. A mutunce suka amsa, tamkar ba surukai ba haka Dadan ta ringa jansu da hira suna amsa mata daddaya cike da kunya Inna Hasiya ta fice tsakar gida se Bilki dake tsokanarsu Dada tana tare musu. "Kuje ki rakasu su gaida Goggonku" Dadan ta fadawa Bilki, ta miqe suka bi bayanta suna fita ta dafa Bara'atu tana cewa "Qawata ya kikaji Auran?" Inna Hasiya ta rafka salati tana cewa "Kin banu Bilki wannan fitsara har ina sirrin Yayan naki kike kiji kome? To bari Audun yazo daidai yake dake". Bilki ta ringa dariya su Bara'atu dai se murmushi da haka suka qarasa dakin Goggo Fadi sun tarar da ita da Aminu wanda tun Asuba daya shigo gidan yana can kome suke tattaunawa se Allah. Cike da girmamawa suka gaidata ta amsa itama basu jima ba suka basu guri, bayan sun fito Bara'atu ta kalli Balaraba tace "Muje kiga dakina nima" suka rankaya Bilki ta wuce gurin Inna Hasiya data kirata. A

Chapter 4 of 32