gota sanda Munira ta hada musu yan abinda zasu buqata Binta ta coccogala suka fita daga gidan Audu saboda tsoron abinda ze iya biyo bayan zamansu Alhalin yace su tafi. Gidan Turai suka nufa dan babu halin Tafiya Kaduna a wannan lokacin, suka hadu suka ringa jimamin al'amarin.
"An auna arziqi dabe furta ya sake ki ba ai, lokaci kawai zaki bashi ya danyi fushinsa ya sakko komai ze daidaita" Turai ta fada.
Binta dake kwance magashiyyan Zazzabi na nuqurqusarta a haka ma wai taje Chemis an bata maganin rage radadi dana zazzabin shine taji dama dama.
"Yanzu ta mutuma amma tsinanniyar matar nan ba zata barni na zauna lafiya da Mijina ba Allah ya isa tsakanina da Bara'atu" ta fada tana sakin kuka. Munirah tace
"Yanzu ashe ba zaki saduda ba Yaya Binta? Wannan abun be isa ya zame miki ishara ba?"
"Zanci uwarki idan kika sake saka mun baki a magana" ta fadawa Muniran daga nan tayi shiru tana jinsu da Turai suna maganganu akan matakin daya kamata su dauka, ita dai Allah ya gani tayi nadama kuma tana fatan itama Bintan ta ganr gaskiya tun lokaci be qure mata ba sannan da sun je gida dole ta warwarewa Iyayensu komai daya faru saboda ayiwa tufkar hanci, muddin Binta bata rabu da wannan matar da alamu suka nuna ita take sake dorata a hanyar banza ba ba zata taba komawa ga Allah ba. Washr gari suka tattara suka wuce Kaduna, Binta bata tsammaci abinda ta gani bayan da Munirah ta fasa kwai ba, gigicewar da Salima da Sakina sukayi ba kadan bace Ummu ko fadi take
"Kun gani ko? Kunga abinda nake jiye muku ko? Yanzu wa gari ya waya? Gashi nan ta mutu ta bar muku duniyar kuji da dakon haqqinta".
Alhaji Zakariyya wanda yake fama da ciwon bugawar zuciya kusan shekara hudu kenan da ciwon ya ta'azzara masa abu kadan yake tayar masa dashi wannan tashin hankali daya riskeshi na abinda Yaran nasa suka aikata ya sake motsa masa ciwon sosai, ita kanta Maman Seda Hawan jininta ya tashi, Allah ya sani daga ita har Mijinta babu me muguwar zuciya da baqin rai irin wanda Yaransu suka gwada. Rashin lafiyar Alhajin tasa basu bi takan Binta ba qoqarin yanda zasu cetoshi kawai sukeyi a sannan.
AUDU
Tattara yaran yayi ya maidasu Bechi bayan da Binta ta bar gidan harda Zakariyya da bata tafi dashi ba, rayuwa ta masa quncin da be taba zaton ze tsince kansa a makamancinsa ba, komai ya sukurkuce masa, duk ya gigice ya fita a hayyacinsa shi kadai yake rayuwa a gidan abinci sedai ya siya ko yaje gidajen Abokanansa yaci. Be bi takan Binta ba balle yasan me take ciki dukda har yanzun be yanke hukunce dangane da cigaban zama da ita ba ko akasin haka cikin wannan yanayi ya share watanni biyu, Yakubu yazo Kano ya tarar dashi gashi nan shi ba me hankali ba shi ba zararre ba, dukda cewar yana da fushinsa a zuciya amma akace Jini ba wasa ba ya tausayawa Audun.
Shi ya ringa tausarsa ya nuna masa cewar kuskure dai ya rigada ya aikata a rayuwarsa yanzu abinda ya rage masa shine ya gyara sannan rabuwa sa Binta ba shine mafita ba a yanzu tunda dai ya fahimci wacece ita ya kuma san tuggu da makircin da take shirya masa a gida seya hankalta ya kuma san me yakeyi, sannan ya bashi shawara da ya hade kan gidansa, yaje ya maido da Zubaida ta raini Yayanta a gidan ubansu yasan kuma ita zata iya riqe Marayun Bara'atu ta hada da nata saboda zancen yace ze maidasu Bechi ma be taso ba ya kuma jaddada masa ya tashi ya koma makaranta ya nemi ilili na boko dana Muhammadiyya saboda Ilimi shine gishirin rayuwaz daga shi har Bintan Jahilci shine jigon abinda yake qara ingizasu ga shirmen da suke aikatawa a rayuwarsu.
Karo na farko da Yakubun ya dangantashi da Jahilci kuma ya amsa beji Haushi ba ya kuma tabbatar masa da ze bazama neman Ilimi ze kuma gyara mu'amalarsa, zancen Zubaida kuwa daman ya dade yana saqa hakan a zuciyarsa tun ma kafin Bara'atu ta sake fita daga gidansa dan haka ya roqr Yakubun dayayi masa Jagora suje dan yana kunyar Idon Mahaifinta ya sani be kyautawa Tsohon ba. Yakubu beqi ba suka shirya sukaje, ko a fuska Malam Hassan be nuna musu komai ba ya ringa Maraba dasu ga Yan Biyu sunyi girma sosai sunyi wayo idan ka gansu zaka dauka sun shekara uku ko sama kamanninsu daya sak sedai banbancin halayya inji Malam Hassan ya nuna Hussaini yana cewa
"Kaga wannan kaiya biyo sak, rigima a cikin Hussaini harda ta bayarwa sadaka shi kuwa takwarana yanda kasan wannan dan uwan naka salihin bawa babu ruwansa haka Tagwai din zeyita cin zalinsa yayi shiru na zakaji bakinsa ba". Audu ya sunkuyar da kai dan ji yayi kamar zaginsa Malam Hassan yake a fakaice Yakubu kuma yayi murmushi yana cewa
"Dama hakane ai duk tagwaye se an samu wannan banbancin dabi'ar daya me sanyi daya me zafi"
"Wannan gaskiya ne dan nima nawa Hussainin Allah ya jaddada rahma a gareshi haka muka sha fama tun quruciya har zuwa girma shekarun mu Arba'in da biyar Allah yayi masa rasuwa sedai shi be bar baya ba yaya hudu ya haifa duk kuma sun rigashi mutuwa" Inji Malam Hassan.
"Allah ya jaddada rahma a gareshi" Audu da Yakubu suka hada baki gurin fadi. Shiru sukayi nadan lokaci kafin Yakubu ya numfashi ya amayarwa da Malam Hassan abinda yake tafe dasu.
"Wai, ashe baka sani ba? Ai yau kwana Ashirin da tara kenan da Zubaida ta daura aure kwana goma sha biyu kuma da tarewarta, nan qasan mu babu nisa take Yaron Aminina Malam Bala ta Aura wannan da kuka taba gaisawa a nan har nake ce maka Daga qasar waje ya dawo yayo karatun Likitanci" Malam Hassan ya fada yana duban Audu Audun kuma ya kalli Yakubu kamar dashi ake maganar,
"Tooo ai babu labari Baba, da yake muma din an samu Rashi ne uwargidansa ce ta rasu a Makka sunje aikin Hajji ba'a dawo da ita ba wannan ya tayar masa da hankali har yasa ya dauki lokaci haka be leqo Yaran ba. Ashe kuma haka ubangiji ya qaddaro babu rabon komawarsu da itaz to masha Allahu munyi murna Allah ya sa hakan shine mafi Alkhairi a rayuwarsu baki daya" inji Yakubu.
*MAMAN MARYAM ONLINE BUSSINESS*
*Ina kuke Mata Yan kwalisa , Ina nufin isassun Mata ,Wai shin Kuna da labarin shahararren company nan namu na GHT wato good healthtreatments*
*Wanda yazo muku da fitattu Kuma* *ingantatattun suppliment ,na dukkan matsalolin ku*❓
*Ina maisan tayi kyau,irin na isassun Mata ya fitar Miki da shef dinki tayi Miki gyara in and out ,nemi royal jelly dinmu na company GHT*
*Wanda aka yishi da xuma ,kundai San amfanin Zuma basai na fada miku ba , hajiya ta kixo ki Yi gyara domin ki kerewa sa,a kije taro ko baki da ko sisi kiji Ana rangada Miki hajiya , saboda yanda Zaki Kara kwarjini ,kina walwali acikin mutane , magungunan ght anti agen ne suna maida tsohuwa* *yarinya ,yarinya Kuma ta koma jaririya*
*Muna da magunguna iri iri*
*NA GYARAN JIKI*
*NA GOGE NANKARWA*
*NA RAGE QIBA*
*NA CIRE TUMBI*
*NA QARIN HIPS*
*NA GIRMAN BREAST*
*NA QARA TSAHON GASHI*
*NA QARIN NI'IMA WANDA ZAI SAUKAR MIKI DA NI'IMA YA QARA MIKI DADI DA ZAQI A GURIN OGA*
*Muna da hadin bita zai zai ,indai kishiyar ki tana Shan magungunan GHT, tohh lallai sunan ki sorry domin kuwa tazarar dake tsakanin ku kamar tazarar sama ne da kasa*
*Muna da Wanda zai matseki ciki da waje Andai na yayin dinki uwargida*,
*Sannan company mu na GHTBai tsaya anan ba*
*Ya kawo muku maganin dukkan matsalolin ku*
*INA MASU HAWAN JINI?*
*INA MASU CIWON ZUCIYA?*
*INA MASU CIWON QODA?*
*INA MASU CIWON HANTA?*
*INA MASU SICKLER?*
*INA MASU HIV?*
*INA MASU CANCER?*
*INA MASU NEMAN HAIHUWA?*
*Tohh Ku matso GHT taxo muku da magungunan matsalolin ku*
*Kuma muna da testimonys da yawa ,na wadanda suka gwada suka da ce*
*Munanan a KANO KUNTAU*
*Kuma muna tura Kaya ko wanne gari cikin aminci da gaskiya , kuma kayan mu muna badashi ne cikin price Mai rahusa ga kyau ga inganci sannan ga Rahusa*
*Kutuntube mu ta wannan number 📞08129249549*
*📲07011401314*
Haka suka tattara suka tashi guiwoyi a sage, har sun shiga Mota Audu ya kalleshi yace
"Mu koma mu tafi da yaran"
"Idan ka dakko su ina zaka kaisu? Ko kuwa kai zaka haqura da fita nema ka zauna rainon Yara? Koda zaka karbe su ba yanzu ba ka fara bari ka nutsu kasan alqiblar daka kama sannan se kayi batun dakko Yara, yanzu dai gashi yayanka shida Audu Aure uku, ina fatan ya zama na qarshe saboda Aure Aure bashi da dadi, sau da yawa yana kawo rarrabuwar kawuna Ahali musamman a gida irin naka da Shugaban gidan be zama tsayayye ba, kaje ka zauna kayi shawara ka yankewa kanka hukuncin abinda ya kamata kayi a yanzu, kaga dai Bara'atu ta tafi inda babu dawowa, Zubaida Tayi Aure nasan kuma sedai wata qaddara ta ubangiji ce zata fiddota daga gidan auranta Binta kadai ta rage maka uwar Yaya da kake da damar cigaba da zama da ita dan haka ka maidota ta riqe Yayanta kana iya nemo wata Macen daka yarda da tarbiyyarta da zata mayewa wadannan Iyayen da basu tare dasu domin na tabbatar Bintan dana sani bazata riqa maka Yaro ko guda daya tsakani da Allah ba.
BAYAN WATANNI UKU
Watanni uku suka shude wata biyar kenan tun bayan rasuwar Bara'atu da kuma barin Binta gidan Audu, be waiwayeta ba be kuma je Kadunan ba kamar yanda Suma Iyayenta basu nemi da yaje ba. Mahaifinta yace duk hukuncin da Audun ya yanke akanta dai dai ne kuma shi baze shiga cikin maganar su balle Alfarmarsa tasa ya yanke hukuncin da bashi yaso a zuciyarsa ba. Wannan zama ya quntata Binta matuqa da gaske, babu walwala ko Yancin da take dashi a baya ta zama kamar wata mujiya kowa kyararta yakeyi tsakanin Iyayen abinda yake qara rura wutar Bala'i a zuciyarta kenan ta sake cin Alwashi kala kala akan komawarta gidan Audu.
Wulaqancin daya mata baze tafi a banza ba wlh seya gane kurensa.
A bangaren Audu kuwa bayan dogon tunani da shawarwari daga yan uwa da Abokanan Arziqi ya yanke shawarar sake Aure, duk wanda ya masa maganar Binta fa se yace yana sane lokaci ze nuna abinda ya kamata yayi da ita da yawa sun dauka ya saketa ne ma ganin an tasarma rabin shekara babu labarinta a gidab. Wannan karon mata biyu ya rakito a lokaci daya, Hadiza data kasance Bazawara auranta biyu na farko Mijin ya rasu sena biyun kuma rabuwa sukayi tana da yarinya daya dashi yar Ƙofar dawanau ce amma tana yawan zuwa Goron dutse gidan Yayarta a nan suka hadu da Audun kamar da wasa yayiwa Mijin Yayarta magana wanda suke gaisuwar mutunci dashi babu bata lokaci ya shige masa gaba magana taje gaban Manya.
Ta biyun kuma Aisha, yace ga Sarkin Ƙaraye Maimartaba Alhaji Ahmadu Isah na biyu. Ita din Ƙanwace ga Abokin kasuwancin sa Najibullahi Amadu wanda suka hadu sanadin Noman Rani da Audu yakeyi a gonakinsa da suke Kusalla wani Ƙauye dake ƙarqashin Ƙaramar hukumar ta Ƙaraye Gonakin Audun sunyi iyaka dana Najibullahin wannan tasa suke haɗuwa idan sunje zagayen Gona daga haka kuma zumumci ya Ƙullu harta kai Audun yana zuwa gidan Najibu duk sanda ya shiga qaraye a nan kuma yaga Aisha kamar da wasa yacewa Najibun tayi masa dukda yarinya ce ƙarama shekarunta basu haura sha hudu ba tana cikin ta sha biyar sannan ganinta yana tuna masa da Bara'atu lokacin daya aureta banbancin ita Aisha tana da dan girman Jiki kadan tafi Bara'atu cika ido a lokacin da take da shekarunta.
Najibu ya tabbatar masa in har da gaske yake shi ze shige masa gaba akan maganar wannan tasa daya yanke shawarar Ƙarin Auran ya tuntubeshi, babu bata lokaci kuma ya gabatar dashi ga Maimartaba. Shaidar daya samu daga Najibu da sauran Mutanen garin da suke masa aiki tasa har Sarki ya Aminta dashi ya kuma ce yaje ya nemi yardar Aisha dan shi bayayiwa Yaransa Auran dole.
Aisha tasan Audu dukda Ƙarqarinsu gaisuwa duk sanda yaje gidan Yayan nata, tana bala'in girmamashi dan ganin babban mutum take masa kwatsam sega maganar Aure tana qoqarin shiga tsakaninsu, ita din yarinya ce me matuqar sanyin hali da biyya ga Manyanta wannan dalili ya saka sanda Yayanta ya sameta da maganar Abokinsa ya ganta yana sonta ya tambayeta ko tana da wani da take so tace masa Aa, shikenan magana ta Ƙullu har anje Tambaya.
Yakubu ne ya Tilasta masa cewar dole yaje gidansu Binta, babu yanda za'ayi yaci gaba da jingineta gaban iyayenta tsayin lokaci dan sun masa shiru bayana nufin basu son yarsu bane kawaici kawai sukayi masa kuma da son itama su koya mata darasi ta ganr kuskuren abinda ta aikata dan gaka baze saura sabon aure ba tareda Binta ta san Matsayarta ba. Dole ya shirya zuwa Kaduna, yanda Alhaji Zakariyya ya ringa bashi haƙuri yasa duk yaji wani iri, kamar ze durqusa masa yake roqonsa da yayi haƙuri akan abinda Ƴaƴansa suka aikata masa a madadinsu yana nema musu afuwa, ya Ƙara da cewa
"Bana so ka dubeni cikin yanke hukuncin makomarku kaida Mamana, karka cutar da kanka, idan har kana ganin bazaka iya cigaba da zama da ita ba ina goyon bayanka daka sauwaƙe mata domin tayi abinda ta cancanci hakan, amma idan kana ganin zaka iya yafe mata kayi mata uzuri to, ina da yaqinin abinda ya faru a baya baze maimaita kansa ba domin iyakar Fada, Nasiha da Tunatarwar daya kamata muyi mata a matsayin mu na Iyayenta munyi muma kuma fatan taji".
Se yaga kamar a fakaice Alhajin roƙonsa yakeyi akan ya mayar da Bintan, kuma bai kamatu ace mutum da yayi masa tarin Alkhairi a rayuwa kamar Akhaji Zakariyya ace shi ya gagara maida masa ba, darajar tasa shi Amincewa yayi bikon Binta, ya kuma sanarwa da Alhaji zancen auran da ze daura da Mata biyu sati biyu masu zuwa Alhajin yayi masa murna da fatan Alkhairi haka ma Mama sannan ya kira Binta a gabansa ya shaida mata muddin ta koma ta sake aikata wani abu da ze tunzura Audun ya sake aikota gida to daga can ta nemi gurin zuwa badai gidansa ba, ya sake ja mata kunne sosai kanta na Ƴasa tana kukan munafunci tamkar taji abinda yake faɗi kuma zatayi amfani dashi.
Kwanan sa biyu da zuwa suka juyo tare, zaman dai babu yabo babu fallasa sabgoginsa yake yana ta shirye sgiryen bikinsa. Ta tarar da an sake Ƙalƙale gidan, banda dakinta da yake a kulle hatta da samansa an bare Asalin Tarazo da yake gurin an maida Na zamani kayansa ya sakko dasu dakin da Abdullahi yake ciki nan ya kafa Gadonsa yake kwana yanzun, tsakar gidan ma am Canza Tarazo, kitchen dinsu na waje an gyarashi sosai kamar dai na cikin dakunan su se aka yanki filin tsakar gidan aka sakeyin wani Kitchen din na Langa langa, babu fus bare ta tambayeshi wannan sabon shirin na menene haka a haka taci kwanaki goma da dawowa wanda kuma ya rage saura kwana biyu a daurawa Audu Aure ranar taga ana shigowa da sababbin kayan gado da Kujeru aka haura sama dasu.
Daya dawo da daddare ta dauka ranar zasu koma saman tunda an saka kaya harda katifa amma setaga ya bude sabon dakinsa ya shige abinsa se washe gari yake shaida mata gobe Daurin auransa, amma Amarya daya ce zata tare a goben dayar se wani satin.
Kamar sabuwar galahanga haka ta bude baki tana kallonsa jin wannan magana, wai Amarya daya, ita dayar se wani satin,
"Amaren har su nawane?" Ta jefa masa tambayar, ya wani kalleta sheqeqe kafin yace
"Su biyu ne kafin Allah ya kawo cikon ta hudun"
"A nan gidan zaka zubamu mu ukun?" Ta sake tambayarsa wannan karon kallonta kawai yayi be amsa mata ba ya juya ya fita.
Kuka ta fashe dashi, kishiya har biyu rana daya ita Binta ita za'ayiwa wannan tozarcin? Duk Bara'atu ce ta janyo mata wlhba zata saɓu ba dole ta nemi mafita. Har ta saɓi mayafinta zata fita ta tuno cikin sababbin sharuɗɗan daya gindaya mata harda fita babu izini, ta mayar dan yanzu neman yarda takeyi dole tayi biyayya akan duk abinda aka gindaya mata. Kuka wiwi ta ringayi, Turai take so taje ta gani su shawarta babu halin fita, tayi data sanin ƙin nemo Lantana tunda ta dawo da yanzu ita zata tasa kawai ta aiketa gidan Turan tunda ita ba zata iya zuwa ba. Yanzu haka zata zauna a kawo mata Kishiyar babu ko wanda ze tayata zama ya danne mata Ƙirji?
Washe gari kuwa kamar yanda yace tun farar Safiya yasha wanka ya bar gidan, fitarsa babu jimawa sega mota cike da Yan Bechi, su Bilki da wasu daga cikin faccalolinta. Tsohon falon Bara'atu suka baza tabarma suka aje kayayyakinsu. Gaisuwa kadai sukayi da Bintan suka hau haramar dora abincin dan sunzo da cefanensu rankatakaf kafin su shigo Audun ya fada musu inda zasu tsaya su karba danyan abinci kadai suka diba a store dinta suka hau girki.
Binta na daki kamar tsohuwar mayya ita da gidanta amma bata iya fitowa su kuwa hidima suke suna raha suna dariya, suka sauke abinci suka ware na Yan Daurin Aure idan dawo da kuma na karbar Amarya sukaci nasu kafin suka hau wanka da shiryawa.
Afujajan kamar an jehota Lantana ta diro gidan, taje sau babu Adadi sanda Binta bata nan seda Audu yace ze saka a kulleta idan ta sake zuwar masa gida neman wata Binta kafin ya samu salama ta dena zuwa. Binta na kwance ta dirar mata kamar jifa tana haki harta bata tsoro,
"Hajiya, ashe har bayan mutum ya mutu ma yana iya cigaba da kitsa tuggu da munafunci?" Lantanar ta tambayeta, Binta tana gyara zama ta galla mata harara tana cewa
"Wane kalar hauka da dabbanci yake damunki Lantana zaki faɗo mun daki haka se kace Asiri? Yaushe na fara sakar miki fuska da zakiyi mun wannan sakarcin?"
"Hajiya ki ƙyale wannan maganar tukunna muyi wadda ta kawoni, kinsan wacece Amaryar da Alhaji ya auro miki kuwa?" Lantana ta bagarar da maganar Bintan, itama jin an soso mata inda yake mata Ƙaiƙayi yasa ta zabura tana tambayar wacece.
"Ƙanwar Sadiya ce Aminiyar Kishyarki Marigayiya Bara'atu, nidai nace ko a mafarki take zywarwa Sadiyar suka Ƙulla wannan Munafuncin? Ko kuwa daman tun Marigayiyar na raye ita Sadiyar tayi niyyar cin Amanarta ta aurawa Alhaji Ƙanwarta?"
"Allah mungode maka daka bamu lafiyar jiki data Ƙwaƙwalwa" Bilki datavshiga tambayar Binta ta bada abinda za'a saka mata abinci ta tsinci zancen nasu me kama dana zararru.
"Ban shiga sabgarku ba Bilki karki kuskura kishiga tawa" Binta ta gargadeta, se da tayi irin dariyar nan me cusa takaicin kafin tace
"Allah ya huci zuciyar Hajiya Binta uwargidan Dan Uwana Audu, daman kwano nazo ki bada a saka miki abinci, idan kuma kin Ƙoshi shikenan"
"Ku kuke yunqar Abinci nida kika ganni kinsan daga gidan wadata na fito abinci ya ishemu shiyasa har muka cida Dan uwan naki Butulu dayaci ya Ƙoshi yake gwada mana halin nas ana butulci, ita kuma annamimiyar da tana Ƙasa a kwance ma ba zata barni na huta ba wlh zamu gamu, Addu'a zan durfafiyi ubangiji ya shiga tsakanina da ita" Binta ta zaburoqa Bilki, seta juya tana dariya tace
"Tabbas jahilci yafi hauka ciwo, amma naji dadi da kikace zaki durfafi Addu'a, Allah ya dubeki ya kawo miki sauqi cikin lalular da take damunki Binta" daga nan ta fice Binta ta yunqura zata bita taji ba'asi wai tace mata Jahila kuma mahaukaciya Lantana ta tareta.
"Hajiya keda akuyarki tayi kura dan Allah ki nutsu ki Ƙyalesu yanzu matan unguwar nan zasu fara shigowa dan Sadiya babu wanda bata gayyata ba daman surutunki ya gama cika unguwa wasu ma cewa suke Asiri kikayiwa Bara'atu dukda ta fita daga gidan nan seda kika aikata lahira da yawa kinga ba fuskar da zasu shigo miki suka samu ba yanzu ko dalilin bikin nan kowa zata shigo kinayin abu a tafi dake a baki sharri se iya wanda kikaji wlh" da wannan ta tausheta suka zauna jigum jigum babu jimawa kuwa mata suka fara tururuwa a cikin gidan.
Ana sallame sallar isha'i aka kawo Amarya gida ya sake cika danƙam da mata, Lantana ce ta fita ta gano mata ina za'a saka Amaryar dan tana ta lissafa inda ze ajiye dayar tubda dai gidansu dakin mata biyu ne ko kuwa can ze gwamutsu kowa ta dauki daki daya su haɗa falo bata san musu ba.
Lantana tazo mata da labarin daya sake gigitata, wai sama aka dora Amarya, dama tana ta jiyo dudubniyar mutane ta dauka zazzabi da ciwon kan daya rufetane yasa take jiye jiye ashe da gaske ne, lallai wato da Gaske Audu ya tashi ci mata mutunchi a wannan karon.
Page 30
Se gurin sha biyu na dare suka samu sauqin Jamar da suka cika gidan maqil kamar wani sabon yinin biki akeyi,Binta na daki ita da Lantana da yau ta samu guri ga qugunta gana Binta akan Kujera tana bata shawarwari ita dai Binta jinta kawai take badanta fahimta ba, yanayin da take ciki yau din baze misaltu ba, Tashin hankali Kishiya biyu a rana daya. Bata iya runtsawa ba har gidan yayi shiru alamar kowa ya watse, maganganun habaici tasha su a waqe sedai wai yau ita Binta ta gagara yin gaba da gaba da mutanen da sukazo har gidanta suka takaleta da bala'i, yanda yan uwan Hadizan suka zo, dukda basu shigar mata ba waqe waqensu kadai ya sanar mata a shirye suke jira suke ta tanka musu su qaddamar mata dan haka ta kama kanta tana lissafin abinda zatawa Amaruar da zarar an watse domin ta rantse ba'ayi Macen da zata sha gabanta a gurin Audu ba, dole ta fita ta bar mata gida tun gabanin dayar da yake iqirari ta shigo.
Tana zaune tana gyangyadi Audu ya shigo, tayi firgigit ta miqe, Lantana dai tuni ta kwanta tana janna Rago taji Laushin Katifa ita ko tuna tana da Miji da yaya batayi ba ta baje a dakin Bintan.
"Bakuyi bacci ba ashe? Daman wasu kaya nazo dauka se gobe idan Allah ya kaimu zan shigo gidan" ya fada daga inda yake tsaye kafin kuma tace wani abu ya juya abinsa ya fice.
Washe gari ma haka gidan ya tashi da hayaniyar Ƙawayen Hadiza da suka kwana a gidan kamar wanda suka rako budurwa, tana jinsu suna cigaba da Habaice habaicen da suka fara jiya, gidanbe zama nasu ba se bayan la'asar zuwa sannan Yan Bechi sun tafi Ƙawayen Hadizan ma duk sun tafi gida ya rage Binta da Amaryarta dake can sama abinta. Audu be shigo ba se bayan sallar Isha'i, Niƙi Niƙi da ledoji yana daga labulenta ƙamshin gasassun Kaji dana Tsire suka ziyarci hancinta dan ita din ba daga nan ba gurin iya tantance ƙamshi. A tsaitsaye suka gaisa yace mata seda safe ya fita, data rasa abinyi se kawai ta dora hannaye a kai ta rushe da kuka.
Washe gari bayan data gama lallashinkanta ta kuma tsara yanda zata ci uban Amarya domin ance ba'a bori da sanyin jiki, Ƙarfe tara tayi wanla tsaf ta sheƙa kwalliya irin wadda ta manta rabon da tayita, ta kashe ɗauri ta fesa Turaren da Mama ta bata sanda zasu taho, fuskarta fes amma da za'a tona ƙasan ranta yafi gawayi duhu. Ta fito saɓe da Naziru, tana fitowa tayi kyakykyawan gani, Amarya Hadiza cikin nata salon gayun ta fito daga tsohon kitchen ɗinsu na tsakar gida hannunta dauke da Fulas na ruwan zafi da kuma na Abinci.
Cikin taku me kama da rausaya ta kama matakalar bene ta haye abinta kamar bata lura da tsayuwar Bintan ba. Binta ta bita da idanu tana jin tamkar ta shaƙota amma ta cije, seda ta daidaici Hadizan ta isa saman har yaci ace ta zauna kafin ta yunƙura zata bi bayanta sallamar Lantana ta sake dakatar da ita.
"Yawwa, riqemun shi" ta fada tana miƙa mata Naziru ya lafe amma haka ta yakiceshi ta bawa Lantana ya kuwa tsanyara kuka amma bata dakata ba ta haye saman tana fadin
"Shegen Yaro me dafar tsiya".
Seda ta saisaita kanta ta gwada takun da zata shiga dashi kafin ta tura
All Chapters
Chapter 1
Chapter 2
Chapter 3
Chapter 4
Chapter 5
Chapter 6
Chapter 7
Chapter 8
Chapter 9
Chapter 10
Chapter 11
Chapter 12
Chapter 13
Chapter 14
Chapter 15
Chapter 16
Chapter 17
Chapter 18
Chapter 19
Chapter 20
Chapter 21
Chapter 22
Chapter 23
Chapter 24
Chapter 25
Chapter 26
Chapter 27
Chapter 28
Chapter 29
Chapter 30
Chapter 31
Chapter 32
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 29 Chapter of 32