Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
bar rayuwar bariki sedai komai ya faru kafin ta farga, haduwarta da Audu, komawarta gida ga kuma aure ubangiji ya fita sanin hikimar yin hakan kuma koma yayane ta godewa Allah daya tsamota daga mummunar rayuwar data fada ba kuma zata butulce masa ba zatayi haquri ta jure duk wani qalubale da zata fuskanta amma tabbas tana tausayawa kanta tana kuma tausayawa Yaran da zata haifa a gaba dan ta bar musu abin gori har jikokinta idan ba'ayi wasa ba. "Meye haka Jamila? Ke Tsare wace irin magana kukeyi haka saboda Allah?" Goggo Fadi ta tsawatar musu, a maimakon maganar ta mutu se ya zama abin cece kuce, wanda a kunji kunji sukaji labarin suka gasgata qus qus ya tashi ko ace qaramar hayaniya kowa na tofa albarkacin bakinsa masu fadar Alkhairi nayi masu tofin ala tsine sunayi wannan ya tilastawa Zubaida da qanwarta Surayya fashewa da kuka sauran yan uwansu kuwa jikinsu yayi laqwas tamkar an watsawa Kaza ruwan zafi. A can Kano a unguwarsu ba kamar yanda ake taammata ba Zubaidan bata samu qalubalen kyara ko hantara ba domin har wanda basu santa ba labarinta suka samu a sanda ta dawo sun karbeta hannu biyu saboda wannan ya taimaka mata gurin sakewa ta fara manta rayuwarta ta baya ta fuskanci gaba. Sun dauka yanda suka manta komai haka sauran Al'umma zasu manta sedai basu san wasu yanzu nema suka samu abin jajantawa da gorantawa. Yanda maganganu suke tashi ya saka dole aka maida Amarya daki tana rusa kuka kamar me domin babu shamaki suke aibatata, tamkar Binta zata taka rawa saboda murna, gumu yayi gumu, masu tsawatarwar basu da yawa dan haka maganar taqi mutuwa har seda. Maza suka shigo ciki, Tsahare uwargidan Yaya Baba data fara tada zancen seda ta karbi Tukuicin saki daya, Jamila matar Aminu data tayata dai ya aikata gida itama amma be furta saki ba, wannan yasa washe gari Asubar fari Audu ya kwashe su suka bar Bechi bayan ya kaftawa Matan Yayyen nasa da sauran Jama'a dake gutsiri tsomar warning, Yan uwanta dai saboda mutuwar jiki basu ko iya rakata dakinta sukace da Direban daya kaisu ya maida su inda ya kwaso su, saga ita se Audu da Binta suka wuce gida. Kwanakin Amarcin Zubaida dai basu zowa Audu a yanda ya tsara su ba dan abinda ya faru a Bechi ba qaramin tabata yayi ba gaba daya ta rasa nutsuwarta balle ta samar masa da tasa. Abin yawa Binta sugar har ta ringa ganin wautarta da tun farko bata hasaso haka ba, data sani Bechi ta tafi tun farko ba Kaduna ba, qila da yanzu gori ya saka Zubaidan neman saki da kanta amma yanzun ma ta samu nayi, ba duka ba zagi amma In sha Allahu da kanta zata tafi dan ba zata barta tasha ruwa a gidan ba. Yanda Angon duk yake a wani sukurkuce ya qara bata damar kafa kanta da nuna masa ita ta Allah ce har a gabansa ta ringa tausar Zubaidan tana gaya mata ta cire komai a ranta ta bar ta mutane. A haka Audu ya gama kwana ukunsa ya komawa Bara'atu kafin yayi kwana biyu ya dawo Qanwar Mahaifiyar Zubaida ta kai mata ziyara. Ita tayi mata maganar data maido da ita hayyacinya, ta gaya mata damuwa ko kuka ba zata mata maganin komai ba qaddararta ce a haka kuma me afkuwa ta afku dan haka ta manta baya ta toshe kunnenta daga jin duk wasu munanan Kalamai ta kuma maida hankali ta gyara gidan Auranta domin a yanzu bata da kowa bata da komai se Mijinta da gidan Auranta, ta dage ta nemi Aljannarta ta kuma tabbatar da cewa tayi tuba na gaske, abubuwan data aikata a baya da suke laifi yanzu lada zata samu akansu dan haka ta dage ta kama Mjinta. Wannan ya zaburar da ita randa Audu ya koma Dakinta Binta bataviya bacci ba saboda lukutin tashin hankalin daya sameta, a garin muguwar dabi'arta ta labe ta jiyo abinda ya kusa zauta mata tunani. Ta yi qoqarin shiga dakin ta dakatar dasu daga abinda sujeyi amma qofar a kulle dole ta wuce dakinta tana kuka wiwi qarin takaici da baqin cikin yanda Audun ya bude baki yana ihu tamkar farin shigan Hauka yanda kasan yau ya fara sanin Mace, washe gari kuwa taga qarshen bariki dan bata tsammatar Audu ya fita sallar Asuba kuma bataga kyallin idonsa ba se yamma lis shima tareda Amarya suka fito suna raha da dariya hannayensu sarqafe da juna yanayin shigarsu ya nuna mata cewar fita zasuyi. "Idan na yarda Allah ya tsine mun albarka" ta fada yana miqewa tsaye harda cire dan kwali tayi damara. Page 19 "Idan na yarda Allah ya tsine mun albarka" ta fada yana miqewa tsaye harda cire dan kwali tayi damara. Duk su biyu suka dakata suka kalleta, fuskar Zubaidan dauke da murmushi harda rausayar da kai tace "Ina wuni Yaya Binta?" "A gidan ubanwa na zama yayarki? Ni zako gwadawa Karuwanci? Koda yake na manta sana'arki ce ai ba a qasa kika tsinta ba" Bintan ta fada murya a sama, "Meye haka ne Binta? Ke baki iya magana a hankali bane dole se kin daga murya kamar meyi da mutanen sama sannan wannan damarar da kikayi ta mecece haka?" Audu ya fada yana kallonta se kuwa ta shiga qara tamke damararta tana cewa "Ba shakka dole ka tambayeni me nakeyi haka wato kaima an dora maka darasi irin nasu na tsofaffin kilaki ko? Saboda tsabagen rashin Adalci tun daren jiya rabona dana sakaka a ido, haka ka kwana kana kurma ihu a gidannan kamar wanda ya samu abinda baze qare ba sannan yau ko kyallin qeyarka ban gani ba se yanzu zaku fito cikin shiri da alama ma waje zakuyi wato ga banza jaka ka ajiye wlh ba zan yarda ba" ta qarasa maganar tana qoqarin fashewa da kukan takaici saboda tuno daren jiya da tayi. Wani murmushi me tafe da qaramar dariya Audun yayi ya kalli Zubaida data sunkuyar dakai, Karuwa da Binta ta kirata ya soki ranta amma tayi shiru tana qoqarin danne damuwarta tareda hana kanta karaya a gaban Bintan, "Ashe dagaske kike da kika ce duk maqota suna jina yanzu yaya zan kalli mutanen waje idan na fita bayan na tafka abin kunya qato dani ace yar yarinyar kamar ke ta sakani ihu a daki? Gaskiya mu koma an fasa fitar nan gara na hada kunyar jiya data yau gaba daya gobe na fita dan bazan fasa ihu ba" Da Binta ta rasa abin fadi se kawai ta fasa kuka me kama da ihu ta juya ta shige daki, Zubaida kuwa dariya ta fashe da ita tana kare fuska saboda kunyar maganar tasa, "Mu koma ciki" ya sake fada yana kama hannunta ta zame tace "Babu ruwana kaje ka rarrashi Yaya Binta kar kasa ta qullaceni" "Ki barta zan lallasheta gobe dan bazanso abinda ze sosa mun rai ba bare harya hanani ware murya dakyau nayi ihun dadi" "Allah ya isa tsakani na dake yar iskar Karuwa, idan ma kuma Asiri kikayi kika shigo gidan nan na rantse da Allah sena karyashi zaki gane dani kike zanje" Binta data fito da Hijabi a jirkice ta fada cikin kuka kafin ta fice daga gidan ko ina zata se Allah, "Ka bita mana kana kallo ta fita" Zubaida ta fada cikin yanayin damuwa, ko a jikin Audu ya juya ciki yana cewa "Duk inda taje ma zata dawo" daga haka ya jata suka koma ciki fitar da suka niyyata aka fasa. Binta kuwa bayan fitarta rasa inda zata nufa tayi, Turai bata nan ta tafi Gumel suna Yayarta ta haihu kaf Kano kuma ita kadai ce qawar da take kaiwa kukanta. Haka nan tasha kwana ta tasamma gidan Lantana wanda tunda ta fara mata aiki shekara uku kenan sau daya ta taba zuwa sanda Salisu Babban dan Lantanar ya rasu se yau data rasa gurin zuwa kawai zuciyarta ta raya mata taje can. Lantana da makwaftanta biyu na tsakar gida sun baza faifan Binta suna caccaka, haka nan kullum aikinsu kenan yanzu labarin kishiyar da aka mata dake neman zauta ta take basu "Ai in gaya miki alqadarinta ya karye, badai ta kori ta Allah ba ai gashi nan an hadota da wadda zataci ubanta ta kowanne fanni, kilaki fa akace yo har a gaya mata iya kissa da kisisina" daya saga cikin matan ta fada, Lantana ta buga cinya ta bude baki zata bada sharhi Binta ta doko sallama suka zabura gaba daya daka kallesu kaga marasa gaskiya "Hajiya, kece?" Lantana ta fada bayab data miqe tana sosa kai kamar me kwarkwata, Bintan ta kallesu irin kallon raini kafin ta nufi wata Farar Kujerar roba dake ajiye a tsakar gidan, "Allah yasa lafiya dai Hajiya keda kanki kika zo gidan nan idan wani abu ne aida se ki aiko a kirani" Lantanar ta sake fada. Cikin muryar qunquni ba tareda ta kalleta ba tace "Lafiya lau, zaman gidan ne ya isheni shine na fito" "Ai to barka, kuma ke kikace na taho da wuri yau ai da yanzu ina can na tayaki hirar to ina wuni?" Cewar Lantana sauran matan da se sannan suka iya magana duk suka gaisheta. "Bari naje Lantana inaga su Shamsiyya sun taso daga Allo yanzu, mace daya ta fada se dayar ma ta miqe tana cewa "Bari na biki ki lallabemun kan nan nawa, Lantana Allah bamu Alkhairi" "Duk tafiya zakuyi? To ku gaida gida nagode" Lantana ta fada ta na miqewa ta taka musu. Binta na zaune tana qarewa tsakar gidan Lantanar kallo yanda kasan wani filin baje koli can kwanukan wanke wanke can kayan yara sun cire sun zubar a qasa harda zannuwanta ga abinci da akaci aka zubar ba'a kwashe ba banda tiqar rake da qutsirarrun Kara gurin murhunta kadai abin kallonne. "Bari na kawo miki ruwa Hajiya" Lantana ta fada Binta ta kalli Randarta ta kalli Lantanar kafin ta zabga tsaki tace "Kika ce mun Mijinki yana aikin Malanta ko? Yana ina? So nake a karyamun duk asirin da waccen tsinanniyar tayiwa Audu a yau nake so ba se gobe ba ta yanda ze mata korar kare ta tafi gidansu komai dare" "Tirqashi" Lantana ta fada a zuciyarta a fili kuwa seta gyara zama tace "To yanzu kin hau saiti kenan Hajiya" "Da ba a saiti nake ba? Karki gayamun magana Lantana saboda kinga nazo gidanki, ki kiramun shi ayimun aikin da yake gabana ba surutun banza nazo muyi ba" "Allah ya baki haquri Hajiya nima ba surutu nake miki ba, amma yanzu dai Malam baya nan ya tafi qauye kuma kwana uku zeyi a can, da ace jiya kikazo da zaki tarar dashi amma da akwai Mijin qawar nan tawa da suka fita yanzu shi yana nan a gida Malam me makarantar Allon nan ta kan kwanar shigowa idan kina so yanzu sena rakaki gurinsa duk abinda Malam zeyi miki shima irinsa yakeyi" Lantana ta fada cikin ladabi. Binta tayi shiru na wani lokaci, zata so ace a yau din nan an karya mata duk wani Asiri da Zubaida tayiwa Audu amma kuma bata son terere, shima Mijin Lantanar data zo gurinsa saboda tasan zatayi komai cikin sirri ne Lantanar ba zata fitar mata da sirri ba wannan da take fada kuwa bata da tabbas a kansa dan haka ta nisa tace "Jibi kikace ze dawo ko?" "In Allah ya yarda Hajiya" "Shikenan, bari naje na dawo" ta fada tana miqewa tsaye, Lantana taso ta jata da wata maganar ta zauna ko Allah zesa taji yanda ake ciki dan daga ganin idanun Bintan da kuma kawo kanta da tayi gurin Mijinta da tayi mata Qaryar yana aikin Malanta tun farkon fara aikinta a gidan tasan banza bata kao zomo Kasuwa kuma duk abinda ya koro Kifi daga ruwa ya fada wuta toh tabbas yafi wutar zafi, zata so taji komenene dan ta samu na yamadidi a unguwa kamar yanda ta saba raba zancen Bintan lungu da saqo a unguwar amma yanzu babu fuska dole ta haqura ta rakata zaure tana jaddada cewar Jibi da Malam ya dawo zata sanar mata. "Ko na biki na tayaki zaman ne Hajiya?" Bata dai sare na ta fada, Binta ta mata Banza tayi gaba. A maimakon ta tafi gida kai tsaye seta bige dabi ta wancan lungun ta bulla wancan seda taji ana kiraye kirayen sallar Magriba kafin ta kama hanyar gidan ranta na quna da tunanin me zataje ta tarar, tana shiga Soro hawaye ya balle mata, wai yau ita Binta ce gidan Audu ya gagareta zama har ta fita tana garari a titi saboda qata Mace? Wlh bata isa ba, taci alwashin seta tozarta Zubaida, yanda ta kori Bara'atu Salin Alin haka itama zata fita ta bar mata gida, Audu da duk abinda ya mallaka nata ne wata mace bata isa tazo ta mata katsalandan a sabgarta ba. A tsakar gida sukaci karo ya fito da Alama masallaci zeje, "Kin dawo? Ga Alhaji can an maidoshi bakya nan yana gurin Yar Dagwas" Audun ya fada mata kafin ta bashi amsa ya rabeta ya fice daga gidan dan har an tayar da sallah. Kamar kububuwa ta doshi dakin Zubaidan babu sallama.bare neman iso ta bankada labule ta fada ciki. "Wane Dan abu ta kazan ne ya baki izinin taba mun yaro? Dana tsarkakakke zaki shafa masa Dattin zina? To bari kiji karki dauka kinga gurin zama a gidan nan, yanda kika shigo da qafa biyu idan bakiyi wasa ba sedai a kwasheki a wilbaro dan sena karairayaki na zubar. Se kinyi nadamar auran mun Miji, sena illataki yanda ko kin koma yawon Karuwancin naki ba zaki samu masu tayawa ba, bani Dana, kuma ki fito ki doramun abincin dare yanzun ba se anjima ma". Zubaida na tsaye da goyon Zakariyya wanda yake ta rigima tunda wata yarinya ta kawo shi daga gidan da Binta take kaishi raino yana ganin Audu ze fita kuma ya saka kuka wannan yasa ta goyashi harya rufe ido da alama daman rigimar bacci ce hargagin uwarsa ya tadashi. Kwanto mata danta tayi ta direshi kan Kujera, Binta ta fizgeshi ya saka kuka saboda yanda taja hannunsa ko tsoron yaji ciwo batayi ba ta fara jansa tana cewa "Kinji abinda nace ai karki bari na maimaita miki" "Bana tsammanin yace miki ya miki bayanin ni wacece a gidan nan, to idan beyi miki ba ni yanzu bari na gaya miki. Yanda kike matar aure da aka auro da sadaki nima haka nake, matsayinmu daya na yar aiki ko me dafa abinci aka kawo miki ba dan haka ke baki da qarfin ikon da zaki sakani na dafa miki abinci a gidan nan kici, idan kinga haka ta faru to Mijina ne ya bani umarni wannan kuwa zanyi saboda shidin shugaba nane, kuma neman Aljanna ya kawoni gidansa bazan tsallake umarninsa ba muddin be sabawa shari'a ba" Zubaidan ta bata amsa kafin ta angizo daurin dankwalinta gaban goshi tace "Karuwa kuma bakiga komai ba daga cikin halinta, ki saka ido ki gani, tsakanin nidake za'aga wadda zaman gidan nan ze gagara" tana gama fada ta wuce cikin daki tana kada jiki tabar Binta tsaye baki a sake, seda ta bugo qofa kafin Bintan ta farga ta fara dura mata Ashar tana cewa idan ta isa ta fito ta gani seta sauke mata rainin da take taqama dashi yau, ta gama hayagagarta taja Zakariyya suka wuce daki tana cigaba da bala'i kamar tsohuwar karya. Zubaida kuwa Alwala ta daura tanayi tana kuka, a duk sanda aka kirata da Karuwa takanci ciwon abin yanda bata taba tsammata ba. A sanda take cikin rayuwar Alfahari take da sunan amma yanzu tana jn muninsa fiye da misali. Yanzu haka za'a ringa alaqanta yayanta da wannan mummunan sunan? Bayan ta idar da sallah bata tashi ba har akayi Isha'i ta dora shafa'i da wutri tayi addu'a kana ta nade abin sallar ta tashi. A gurguje tayi wanka ta shirya, cikin irin dinkunan da Kilallu irin tane a wancam zamanin ta saka riga da siket daya matuqar kamata ta baza qamshi ta ko ina sannan ta kafa dauri a gaban goshi. Audu ya gaya mata kartayi girki ze shigo musu da abinda zasuci dan haka ta dora ruwan shayi baqi ta zuba kayan qamashi sannan ta dauki Kankanar data hada tun yamma tashanye ta koma falo ta zauna bayan ta kunna waqar Aliko makaho tana bi hankali kwance tana gyada kai. "Baki a washe kamar wawa Audu ringa binta da kallo sanda ta karbi ledojin Kaji da kayan Marmarin daya shigo dasu, "Aa kaga yar dagwas, irin wannan Ado haka gaskiya kinci sunan naki na yar dagwas" ya fada yana washe mata haqora. Ta dan bata rai irin na shagwaba dukda tace "Nace maka bana so ka canza mun wani sunan amma banda wannan" har ranta ta tsani sunan a yanzu amma bata so ta nuna masa hakan cikin fushi ko fada, ya zauna yana sake ce mata "Barni kinji, dadi sunan yake mun. Je ki kawo faranti muci Naman nan tun da zafinsa". Ta wuce Madafa tana juya mazaunanta da basufi rabin na Binta ba amma da yake ta iya sarrafasu bala'in dauke masa hankali take idan tana tafiya. A da gani yake ba Macen data kai Binta iya gwalangwaso da kisisina wannan abin ya qara dakusar da Bara'atu a idonsa yaji sam ta dena birgeshi saboda bata ko kamo qafar Bintan ba babu abinda ta iya se wanda ya koya mata amma yanzu daya auro Macen gaske se yaga ashe duk wani sanaben Binta sharar fage ne, wato jiya yaje cloud 9, yaga abinda ya dauka a gurin Hurul'ayni matan Aljanna kadai ze samu yanzu ita kanta Bintan ganinta yake kamar shi dan yanzu ne ya tabbatar ya auri Mace. Yana can lissafin ta dawo, yanda take duqawa ta ajiye kayan ma abin birgewa ne sannan ta kalle shi tayi masa wani farrr da ido se yaji kamar ze suma dan dadi. "Ina na Maman Zakariyya? Kona kirata muci tare?" Ta fada tana bude ledojin. Ya sauka qasa ya zauna yana cewa "Ai tana da Kaji a firinji, kema gobe za'a kawo miki saboda ajiyar Danyan Nama da sauran kayan amfani" ya bata amsa yana daukar kofin data tsiyaya masa baqin shayi a ciki kurba seta shagwabe fuska tace "Haba dai, ya za'ayi muna gida daya ka siyo abu muci mu kadai banda ita da yaronmu? Aa gaskiya bari na dibar mata dan wannan ai ya mana yawa Kaji biyu Manya ina zamu kaisu" taja faranti ta fara dibar Naman, wata qaramar Leda da taji dumi ta bude taga Tsirene a ciki ta aika masa hararar qasa tace "Harda tsirema duk a wane cikin zamu zuba mu kadai?" *MAMAN MARYAM ONLINE BUSSINESS* *Ina kuke Mata Yan kwalisa , Ina nufin isassun Mata ,Wai shin Kuna da labarin shahararren company nan namu na GHT wato good healthtreatments* *Wanda yazo muku da fitattu Kuma* *ingantatattun suppliment ,na dukkan matsalolin ku*❓ *Ina maisan tayi kyau,irin na isassun Mata ya fitar Miki da shef dinki tayi Miki gyara in and out ,nemi royal jelly dinmu na company GHT* *Wanda aka yishi da xuma ,kundai San amfanin Zuma basai na fada miku ba , hajiya ta kixo ki Yi gyara domin ki kerewa sa,a kije taro ko baki da ko sisi kiji Ana rangada Miki hajiya , saboda yanda Zaki Kara kwarjini ,kina walwali acikin mutane , magungunan ght anti agen ne suna maida tsohuwa* *yarinya ,yarinya Kuma ta koma jaririya* *Muna da magunguna iri iri* *NA GYARAN JIKI* *NA GOGE NANKARWA* *NA RAGE QIBA* *NA CIRE TUMBI* *NA QARIN HIPS* *NA GIRMAN BREAST* *NA QARA TSAHON GASHI* *NA QARIN NI'IMA WANDA ZAI SAUKAR MIKI DA NI'IMA YA QARA MIKI DADI DA ZAQI A GURIN OGA* *Muna da hadin bita zai zai ,indai kishiyar ki tana Shan magungunan GHT, tohh lallai sunan ki sorry domin kuwa tazarar dake tsakanin ku kamar tazarar sama ne da kasa* *Muna da Wanda zai matseki ciki da waje Andai na yayin dinki uwargida*, *Sannan company mu na GHTBai tsaya anan ba* *Ya kawo muku maganin dukkan matsalolin ku* *INA MASU HAWAN JINI?* *INA MASU CIWON ZUCIYA?* *INA MASU CIWON QODA?* *INA MASU CIWON HANTA?* *INA MASU SICKLER?* *INA MASU HIV?* *INA MASU CANCER?* *INA MASU NEMAN HAIHUWA?* *Tohh Ku matso GHT taxo muku da magungunan matsalolin ku* *Kuma muna da testimonys da yawa ,na wadanda suka gwada suka da ce* *Munanan a KANO KUNTAU* *Kuma muna tura Kaya ko wanne gari cikin aminci da gaskiya , kuma kayan mu muna badashi ne cikin price Mai rahusa ga kyau ga inganci sannan ga Rahusa* *Kutuntube mu ta wannan number 📞08129249549* *📲07011401314* Ta cika faranti da Kazar da tsire ta lullube da takarda sannan ta bude kayan Marmarin suma ta diba a Leda tana kallonsa tace "Bari na kai mata". Da kai ya amsa mata ta dauka ta fita ya bita da kallo yana tuna lokutan baya a zamanin Amarcin Binta. Kullun ta Allah se sunci Gasashshiyar Kaza da tsire da wani damun fura me shegen dadi da yake siyo musu suci su biyu ko takardar Naman Bara'atu da Yaranta basa gani balle suji qamshi. A sannan ma yakan siyo hardasu amma indai ya fara shiga bangaren Binta dashi to ya zama haramiyarsu daga baya ma ya dena siyowa dasu ta cusa masa ra'ayin ai suna ci a Miya kuma sanda tana Amarya itama an mata dan haka yanzun lokacinta ne taci ita kadai shiyasa yanzun yayi amfani da maganarta ya siyo musu shida Zubaida kadai itace Amarya ai itama tana ci a Miya. Zubaida kuwa a qofar dakin Binta ta tsaya ta rafka sallama, Bintan na zaune ta zabga Tagumi, abin duniya ya isheta taji sallama, bata dauka Zubaidan bace ta amsa harda bada izinin a shiga. Ta shiga tana qara wata qaramar sallamar ganin itace ya saka Binta zabura tana binta da kallo tundaga sama har qasa, dukda kyashi da hassadarta daya cika mata zuciya seda ta yabi kyan da shigarta tayi to ina ga Audu? "Ke bakida hankali koM meya kawoki dakina? Da izinin ubanwa kika shogo?" Ta fada cikin hargowar data zame mata jiki, Zubaidan tayi murmushi tace "Seda nayi sallama fa kika amsa kafin na shigo, kuma ba wani abu ya kawoni ba, kazar Amarci Mijinmu ya sake siyomun shine nace bazanci ni kadai na na raba na kawowa Dana" ta dangwarar mata da Farantin a qasa ta juya tana tafiyar yanga Binta tayi kukan kura ta kai mata cafka, a yanda ta cakumeta Allah ya dubeta kamar jifa sega Audu ya fado dakin badan haka ba ta tabbatar da tace seta ballata ta zuba a wilbaro tabbas abinda tayi niyya kenan. "Baki da hankali Binta meye haka zaki kamata da dambe?" Ya fada yana janye Zubaida da zuciyarta ke buga tsalle daga hannunta. Bata dauka jarabar Matar nan takai haka ba, ita ko doguwar cacar baki ba iyawa tayi ba ina dmga yar bawa hammata iska kuma ace da wannan qansamemiyar basamudiyar ai wata rana murus zata kasheta idan akace suyi dambe. "Dole kace bani da hankali mana wato kai ka aikota tazo tamun cinikinta Abinda aka saba ko? Ni zaka wulaqanta Audu da abinda zaka sakawa ubana kenan bayan duk halaccin da yayi maka a duniya? Karka manta mahaifina shi yayi maka rigar da har ka ringa yawo a gari ka kwaso wannan karuwar, to wlh bazan zauna baqin ciki ya kasheni ba tattarawa zanyi na bar maka gidan ka idan yaso ka auro irinta goma ka ajiye gara na koma gidanmu inda ake sona" tayi bal da farantin kazar da aka kai mata ta shige daki tana kuka wiwiwi, diri diri yayi ya rasa me zeyi, ya bita ne ko kuma su fita su bar mata dakin? "Ka bita mana karfa ta jiwa kanta ciwo kamar watsi take da kaya" Zubaida ta fada jin Binta na zubar da kaya a qasa se ya tafi solo solo ya shiga dakin ita dai Zubaida ta juya ta fice har sannan jikinta be dawo daidai ba daga tsoron shan suburbuda a hannun Binta. Bata san ya suka qare ba dan har bacci ya fara fizgarta kafin ya shigo ransa duk babu dadi ganin haka yasa daman tayi shirin bacci a kwance take tana jiransa se kawai ta gyara kwanciya dakyau tayi baccinta shima ya gama abinda zeyi be nemeta na duk yanda yake cike da zumudin kebewarsu amma ya gagara yin komai, yanda Bintan ta ringa kuka tana fadin zata tafi kawai ta shiga duniya yana wulaqantata ne saboda yaga Dadynta ya goyi bayansa sanda ta koma gida ita kawai gara ta tafi koma inane tunda babu me qaunarta ya shiga

Chapter 18 of 32